Tag: Ibada

  • Kaffarar Azumin Ramadan

    Kaffarar Azumin Ramadan

    Game da kaffara kuwa; ya gabata cikin hadisin Abu Hurairah (Radiyallahu Anhu); inda wani mutum ya sadu da iyalinsa da tsakar rana a watan azumin Ramadan; kuma aka ce akwai ramuwar kaffara a kan sa, wato ‘yanta wuyaye, idan bai samu dama ba; to azumin watanni biyu a jere; idan kuma ba zai iya ba; to ya ciyar da miskinai sittin.

    An ce, kaffarar jima’i a kan zaɓi ake yi ba a tartibi (jere) ba; sai dai waɗanda suka rawaito tartibin sun fi yawa. Saboda haka ruwayarsu ta fi rinjaye saboda sun fi yawa, kuma suna da ƙarin masaniya (ilimi) sama da ragowar; inda suka yi ittifaƙi kan cewa azumin wanda ya yi jima’i ya warware; wanda hakan ba ta samu ba cikin ragowar ruwayar, kuma wanda ya sani hujja ne a kan wanda bai sani ba; kuma daga cikin abin da ke rinjayar da tartwikiibin cewa ya fi taka tsantsan kuma riƙo da shi ya isar; idan mun ce zaɓi ne ko ba zaƙi ba, saɓanin idan muka riƙi ragowar hadisan.

    Haka kuma wanda kaffara ta hau kansa, kuma ya kasa ‘yanta wuyaye ko yin azumi ko ciyarwa; to za ta sauƙa daga kansa, saboda ba a kallafa abu sai har idan za a iya. Allah Maɗaukakin Sarki ya ce:

    “Allah ba ya kallafawa rai abu face wanda za ta iya”. (Baqara: 286).

    Kuma ga dalilin aikin Ma’aiki (Sallallahu Alaihi Wasalam); wato inda Ya ɗauke kaffara kan mutumin nan yayin da ya gaya masa wahalar da yake ciki, har ma ya ba shi dabino akan ya je ya ciyar da iyalansa.

    Sannan kaffara ba ta hawa kan macen da mijinta ya neme ta; saboda Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) an ba shi labarin abin da ya faru tsakanin wannan mutumi da matarsa, amma bai wajabta mata kaffara ba, sai guda ɗaya (wato ramuwar azumin). Allahu a’alam.

    Domin karanta cikakken bayani akan Ramuwar Azumin Ramadan danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Raya Daren Lailatul ƙadari danna nan.

    Wannan bayanin anciro shine daga Littafin Guziri Ga Mai Azumin Ramadana (Bisa Koyarwar Alƙur’ani Da Sunnah); wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi; Don karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Ƙa’idoji Da Laduban Neman Halal

    Ƙa’idoji Da Laduban Neman Halal

    Abu ne sananne ga kowa cewa addinin Musulunci bai bar komai ba, sai da ya yi tanadin yadda yake so a fahimce shi, ko a aikata shi. Neman halal ko kasuwanci da sana’a ginshiƙi ne a rayuwar mutum, saboda haka ba a bar mutum ya yi yadda ya ga dama ba, a kasuwanci ko harkokin sana’arsa.

    Da farko an gina tunani da aƙidar ɗan kasuwa musulmi a kan waɗannan dirkoki:

    1) Dukiya Ta Allah ce:- Wato mutum ya sani ya kuma yarda cewa, duk dukiyar da take cikin duniyar nan, da ita kanta duniyar, mallakin Allah ce shi kaɗai. Amma ya bai wa ɗan Adam damar amfani da ita a bisa dokokin da ya tsara masa na shari’a. Wato duk abin da kake da shi kamar aro ko ajiya aka ba ka, amma an yarda ka ɗan taɓa daidai da tsarin da aka yi maka (Shari’a)

    2) Neman Falalar Allah: Duk sana’ar da kake ka dinga yin ta da fatan samun falala daga Allah a cikin ta, wato ka yarda Allah shi kaɗai ne mai bayarwa, kuma shi ne mai hanawa.

    3) Dogaro Ga Allah: Kada ka dogara da wayonka, iyawarka ko jarinka ko iyayen gidanka, kawai ka dogara ga Allah shi kaɗai shi ne mai azurtawa, kuma shi ne mai karɓe arziki yadda yake so, wanda ya so, a lokacin da ya so, kai dai ka yi ƙoƙari da dogara gare shi, sai ya taimake ka, ya yi maka fiye da yadda kake zato.

    4) Imani da Hisabi:- Musulmi ya yi imani da cewa ranar lahira za a yi masa hisabi kan duk abin da yadda ya yi amfani da shi, ta hanyar halal ne, ko ta hanyar haram? wannan imani zai hana musulmi hauma-hauma da ya-ki-halal da kuma ya-ki-haram a kasuwanci, zai kuma hana shi almubazzaranci da zalunci da saɓa wa Allah ta’ala da dukiyarsa.

    5) Neman Kuɗi ba ya hana bin Allah:- A kowane hali musulmi yake komai girman hada-hadarsa, kada ya mance da dokakin Allah da ambatonsa da kula da ibada, musamman sallah. A Musulunci, babu wani aiki ko sana’a da za a ce ba ruwan Allah da shi, ko kuma a ce ai in ba ai ƙarya, ba za a samu komai ba a kan waɗannan harkoki, ya wajaba dukkan musulmi ya gina harkar neman abincinsa. Allah ya sa mu dace. Amin.

    Bayan haka, ga wasu ƙa’idojin neman halal a Musulunci a taƙaice:

    1) A kauce wa Riba a kowanne Hali:-Allah ta’ala ya haramta riba da duk wata mu’amala da take da alaƙa da riba. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Allah ya la’anci mai cin riba, da mai ciyar da ita, da mai rubuta ta, da masu shaida a kanta; ya ce duk matsayin su ɗaya” Muslim ne ya ruwaito shi.

    2) An haramta Algus da Ha’inci da yaudara: Duk wani nau’i na ha’inci da yaudara, zamba da cin amana haramun ne a kasuwanci. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Wanda ya yi mana algus ba ya daga cikinmu”. (Muslim ne ya ruwaito shi).

    Hanyoyin ha’inci da algus suna da yawa kaɗan daga cikin su sune:

    1) Sayar da kaya marasa inganci da waɗanda lokacin amfaninsu ya ƙare (expiring date).

    2) Tauye mudu da ma’auni da rage nagartar abin sanyarwa (quality).

    3) Sanya tsofaffin kaya a cikin sabbin kwalaye da ledoji da gyara su,su zama kamar sababbi, a yi musu kuɗin sababbi.

    4) Sayar da duk wani abu da yake cutarwa ga lafiya da rayuwar ɗan Adam da dabbobi da tsirrai.

    5) Bayannan ƙarya da zugwigwita kayan sayarwa don kawai a jawo hankalin mai saye, musamman magunguna.

    6) Ha’inci a wajen gini, ta hanyar rage sumunti, ko rodi, a yi ginin da nan da nan zai tsatstsage ko ma ya ruguje.
    (2) Kaucewa duk wani aiki na haram ko wani abu da aka haramta amfani da shi a kasuwanci.

    Iri-iren waɗannan harkoki suna da yawa, kaɗan daga cikinsu su ne:

    1) Haramta saye da sayar da giya da dukkanin kayan maye.

    2) Saye da sayar da fina-finan batsa da mujalla da hotuna da duk wani abu da yake yaɗa ɓarna da ta’addanci.

    3) Keɓantar ta sakatariya wannan haramun ne, haka ma duk kasancewar ta sakatariya wannan haramun ne, haka ma duk wani aiki ko sana’ar da sai mace ta bayyana jikin ta sannan za ta yi ta.

    4) Sana’ar raye-raye da kaɗe-kaɗe da wasannin kwaikwayo da duk masu hannu a ciki irin su mai ba da umarni, mai ɗaukar hoto, mai kwalliya, mai ƙir- ƙirar labari, mai bada kuƙi , mai tsara waƙa, mai rerawa da sauran su.

    Na san wasu za su ga wannan hukuncin kamar ya yi zafi, to tambaya a nan gare su ita ce, shin a Musulunci wasan kwaikwayo (film) yana daga cikin uzurin ko dalili da suke halatta bayyana tsiraici yin ƙarya? Shin yana halatta keɓantar mace da wanda ba muharraminta ba? Shin wasan kwaikwayo zai iya halatta ɗimbin ayyukan saɓo, sabo da keta alfarmar shari’a da kyawawan ɗabi’o’i, har ma a ce wai sana’a ce ta faɗakarwa da ilmantarwa?

    Ni dai a iya ɗan karatuna, wanda bai kai ko rabin cikin cokali ba, da kuma gurguwar fahimtata, ban ga inda film zai iya halatta haramun ba. Sai dai an ce fahimta fuska?

    5) Saye da sayarwa da dillancin kayan sata da na ƙwace, duk wannan haramun ne. Haramun ne saye da sayar da duk wani abu da yake cutarwa ga hankali da lafiyar mutane da zaman lafiyarsu.

    Duk wata sana’a ko harka da ta ƙunshi zamba, yaudara, ha’inci, algus da rashin tabbas (garari) kan abin saye ko kuɗin wannan ma haramun ne.

    Waɗannan kaɗan ne daga ƙa’idodin kasuwanci a Musulunci, sai mu kula ko ma samu albarkar nemanmu.

    Su kuwa laduban kasuwanci, wato ɗabi’u da halaye da ya kamata duk wani ɗan kasuwa ko mai sana’a ko ma’aikaci ya siffantu da su, su ne:

    1. Kyakkyawar niyya ya kasance niyyarsa da burinsa a wannan harka da yake yi mai kyau ce.

    2. Fita a kan lokacin zuwa kasuwa ko gurin sana’a ko aiki. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya roƙi Allah ya sa albarka a harkar masu zuwa a kan lokaci, ban da masu makara.

    3. Ambaton Allah lokacin shiga kasuwa sai ka ce: la ilaha illallahu wahdahu la sharika lahu lahul mulku wa lahul hamdu yuhyi wa yumitum wa huwa ala kulli sha’in ƙadir.

    4. Yiwa mutane sallama da amsa sallamar su a wurin sana’a ko kasuwa.

    5. Sauƙi da rangwame yayin saye da sayarwa da biyan bashi, ko karɓar bashi da yin sassauci ko afuwa ga wanda yake cikin ƙunci.

    6. Gaskiya da amana, babu abin da yake bunƙasa kasuwanci da kowacce harka sama da gaskiya da riƙon amana.

    7. Sifantuwa da kyawawan halaye kamar haƙuri, kyauta, kunya, godiya da sauransu.

    8. Cika mudu da ma’auni da bin ƙa’idojin aiki sau da ƙafa da inganta sana’a da kyautata ta.

    9. Yawaita ba da sadaka da fitar da zakka idan dukiya ta kai kuma lokaci ya yi.

    10. Cika alƙawari, ban da ƙarya, ban da yaudara.

    11. Ka guji yawan rantsuwa ko da a kan gaskiya ne ballantana a kan ƙarya.

    12. Kada ka ba da cin hanci, kuma kada ka karɓa.

    13. Ka guji duk wata mu’amala ta cuta da haram.

    14. Ka kula da sallah da sauran dokokin Musulunci.

    15. Ka guji saɓa wa Allah a gurin nema, kamar zina da luwaɗi shaye-shaye da sauransu.

    16. Ka kasance mai tsafta a jikinka da gurin sana’arka da abin sayarwarka ka ƙawata shi.

    17. Ka kasance mai sakin fuska da magana mai daɗi ga duk wanda hulɗa ta haɗa ka da shi.

    18. Ka kai zuciyarka nesa ka danne zuciyarka, ka guji saurin fushi da hasala.

    19. Ka dogara ga Allah shi kaɗai, ka yi ta godiya a gare shi, ka yi ta roƙon sa, ka yi ta ambaton sa.

    20. Ka mayar da hankalinka a kan sana’arka duk abin da bai shafe ka ba, ka rabu da shi.

    Duk ɗan kasuwa ko ma’aikaci ko mai sana’ar da ya kula da waɗannan ƙa’idoji da ladabai, haƙiƙa Allah ta’ala zai sanya masa albarka a cikin nemansa.

    Allah ta’ala ya taimaka mana. Amin.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Illolin Karɓe-Karɓe Da Barace-Barace danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ma’anar Roƙo Take danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Jerin Littafan Hadisai Arba’in (40) Littafi Na Biyu; A kan (Falalar Wadatar Zuci, Neman Halal Godiya Ga Allah Da Illolin Bara Da Roƙo); wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Yadda Mutum Zai Kasance Mai Wadatar Zuci

    Yadda Mutum Zai Kasance Mai Wadatar Zuci

    1) Wadatuwa da abin da Allah ya ba ka.

    2) Karanta rayuwar magabata na ƙwarai da gudun duniyar su, da wadatar zucinsu da koyi da su.

    3) Gudanar da rayuwa matsakaiciya, ba ƙwauro babu kuma almubazzaranci.

    4) Yawaita addu’a, Allah ya azurta ka da wadatar zuci kamar yadda Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yake cewa; “Ya Allah ina roƙon ka shiriya, da taƙawa da kamewa da wadatar zuci”

    5) Yin cikakken imani cewa kowa a duniyar nan arzikinsa yake ci, tuni Allah ya gama raba arziki, babu yadda za a yi wani ya ci rabon wani.

    6) Tursasa zuciya a kan yarda rabon ta da arzkin da Allah ya ba wa mutum da nisantar kwaɗayi, da sa ido a kan abin hannun mutane.

    7) ƙarfafa imani da Allah da amincewa da shi

    8) Kullum ka rinƙa duban na ƙasa da kai, ka da ka rinƙa duban na sama da kai.

    9) Yarda da cewa Allah ta’ala ya ƙaddara lallai sai wani ya fi wani wadata. Tilas ka ga wasu sun fi ka, amma kuma ka fi wasu; wasu kuma kun yi daidai, haka Allah yai tsarinsa, to ina dalilin damuwa?

    10) Ka yawaita tunanin mutuwa da ziyartar maƙabarta, sai ka ji duk abin duniya ma ba ya ɗaɗa ka da ƙasa, domin ƙarshe dai ko me aka samu mutum zai tafi ya bar shi.

    11) Yawaita karanta Alƙur’ani da la’akari da ayoyin da suke magana a kan arziki da talauci da kuma haƙiƙanin ita kanta duniyar.

    12) Ka sani cewa girma da mutunci yana cikin wadatar zuci, shi kuwa kwaɗayi da talaucin zuci, ba ya haifar da komai sai ƙasƙanci da wulaƙanci.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Hikimomi Akan Wadatar Zuci danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Harsashin Gina Al’umma (Iyaye) danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Jerin Littafan Hadisai Arba’in (40) Littafi Na Biyu; Akan (Falalar Wadatar Zuci, Neman Halal Godiya Ga Allah Da Illolin Bara Da Roƙo); wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Hikimomi A Kan Wadatar Zuci

    Hikimomi A Kan Wadatar Zuci

    1) Guntun gatarinka, ya fi sari ka ba ni.

    2) Rabon kwaɗo ba ya hawa sama.

    3) Adon wadata kyauta, adon talaka wadatar zuci.

    4) Abubuwa biyu ba sa zama guri ɗaya, wadatar zuci da hassada, abubuwa biyu ba sa rabuwa, kwaɗayi da hassada.

    5) Mai neman ɗaukaka ya bi Allah, mai neman wadata ya kasance mai wadatar zuci.

    6) Wadatar zuci ita ce tsantsar ‘yanci, kwaɗayi shi ne tsantsar bauta.

    7) Mai matalauciyar zuciya ba zai taɓa wadatuwa ba har abada.

    8) Dutsen da yake hannunka, da shi kake jifa.

    9) Ƙwai a baka, ya fi kaza a akurki.

    10) Duk wanda bai gamsu da kaɗan ba, ba zai gamsu da mai yawa ba.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ƙa’idoji Da Ladaban Neman Halal danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Kyautata Tarbiyyar ‘Ya’ya danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Jerin Littafan Hadisai Arba’in (40) Littafi Na Biyu; Akan (Falalar Wadatar Zuci, Neman Halal Godiya Ga Allah Da Illolin Bara Da Roƙo); wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Sadaƙa Tana Kawar Da Musiba

    Sadaƙa Tana Kawar Da Musiba

    An karɓo daga Mu’awiyya Ibn Haidah (Radiyallahu anhu) ya ce; Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalam) ya ce:

    “Haƙiƙa yin saƙaka a asirce tana gussar da fushin Ubangiji, Kuma haƙiƙa ayyukan alhairi suna kawar da mummanar faɗuwa”(Musibu da Asarori) Ɗabarani 951; Sahihul Jami’il Sagir (3759).

    Domin karanta cikakken bayani a kan Mu Yi Alhairi, Mu Guji Rowa danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) Yake Shan Ruwa. danna nan

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Azumin Kwanaki Goma Na Farkon Watan Zul-Hijja

    Azumin Kwanaki Goma Na Farkon Watan Zul-Hijja

    Watan Zul-Hajji wata ne mai tarin falala da ɗimbin daraja, cike yake da alhairai masu yawa.

    Kuma a cikinsa ake yin aikin hajji, kwanaki goma na farkonsa, kwanaki ne masu daraja, saboda haka ake son yin azumi a cikinsu.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Azumin Kwanaki Goma Na Farkon Watan Zul-Hijja danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Azumin Watan Muharram danna nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Falalar Azumin Kwanaki Goma Na Farkon Watan Zul-Hijja

    Falalar Azumin Kwanaki Goma Na Farkon Watan Zul-Hijja

    An karɓo daga Ibn Abbas (Radiyallahu anhu) “Babu waɗansu kwanaki da Allah ya fi son aikin alhairi a cikinsu irin waɗannnan kwanaki goma; sai suka ce:

    “Ya Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) har jihadi? Sai ya ce,”Har jihadi, sai dai mutumin da ya fita da ransa da dukiyarsa; sannan bai dawo da komai ba”. (Bukhari, Muslim).

    Ma’anar wannan hadisi shi ne; Mujahidin wanda ya yi shahada shi ne kaɗai ya fi wanda ya yi ayyukan alhairi a waɗannan kwanaki goma lada.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Azumin Ranar Arfa danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Azumin Ranar Arfa danna nan.

    Don karanta cikakken bayani a kan Azumin Kwanaki Goma Na Farkon Watan Zul-Hijja danna nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Falalar Azumin Ranar Arfa

    Falalar Azumin Ranar Arfa

    Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) ya ce:

    “Azumin ranar Arfa ina nema da ga Allah ya kankare zunuban shekarar da ta gabata da shekarar da ta zo bayanta”. (Muslim 1162).

    Domin karanta cikakken bayani a kan Azumin Kwana Uku A Kowanne Wata danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Azumin Ranar Arfa danna nan

    Don karanta cikakken bayani a kan Laccocin Ramadan Na Mumbarin Jawabi Daga Malamai danna nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Azumin Kwana Uku A Kowanne Wata

    Azumin Kwana Uku A Kowanne Wata

    Ana son a kowane wata mutum ya yi azumin kwana uku, kuma an fi so su kasance fararen kwanaki,, wato ranakun 13, 14, da 15 na kowane wata.

    Falalar Azumin Kwanaki Uku A Kowanne Wata

    Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) ya ce; da Abdullahi Ibn Amr “Ka yi azumin kwana uku a kowanne wata; saboda aikin lada ɗaya daidai yake da goma, sai ya kasance kamar mai yin azumi kullum”. (Bukhari 1976, Muslim 1159).

    Domin karanta cikakken bayani a kan Azumin Litinin Da Alhamis da kuma Falalarsa danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) Ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Azumin Litinin Da Alhamis

    Azumin Litinin Da Alhamis

    Kamar yadda ake son azumin ranakun Alhamis da Litinin.

    Falalarsa.

    An karɓo daga A’isha (Radiyallahu anha) ta ce: “Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) ya kasance yana yin azumin ranakun Litinin da Alhamis” (Tirmizi 7451 Nasa’i 2/86).

    Kuma Usama Ibn Zaid ya tambayi Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) kan azumin litinin da Alhamis da yake yi, sai ya ce: “Waɗannan ranaku ne biyu da ake bujirar da ayyuka ga Ubangijin Taliƙai a cikinsu, in an so a bujirar da aikina ina azumi”(Nisa’I 2357, Ahmad 5/201).

    Domin karanta cikakken bayani akan Azumin Annabi Dawud (Alaihis salam) da Falalarsa danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Azumin Kwanaki Shida A Watan Shawwal (Sitta Shawwal) danna nan.

    Don karanta cikakken bayani a kan Falalar Azumin Watan Muharram danna nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.