Category: Addu’o’i

Mun samar da wannan ɓangaren ne, domin samar da Addu’o’i na addinin musulunci a harshen Hausa kuma a sauƙaƙe. Za ku iya kai wa gare su ta hanyar amfani da kwamfutoci ko wayoyin hannu cikin sauƙi.

WikiHausa ta kowa ce. Kowa zai iya taimakawa da ilimi ko gyara.

Bugu da ƙari, kowa na iya amfani da wannan kafa domin koyo ko koyarwa.

  • Yadda Ake Addu’ar Nema Wa ‘Ya’ya Tsari

    Yadda Ake Addu’ar Nema Wa ‘Ya’ya Tsari

    Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya kasance yana nema wa Hasan da Husain tsari da wannan addu’ar:

    أُﻋ ِ ﯿﺬﱠِﺑِﻜَﻠِﻤَﺎتِﷲﻟﺘﱠﺎﻣﱠﺔﻣِﻦ ْﻛُﻞ ﺷَﯿْﻄَﺎن ٍﱢﱠو َھَﺎﻣﱠﺔٍ ِو َ ﻣِﻦ ْﻛُﻞ ﻋَﯿْﻦ ٍ ﻻَﻣﱠﺔٍ ُ

    Uʿīzu bikalimātillāhi t-tāmmati, min kulli shayṭānin wa hāmmah, wa min kulli ʿaynin lām.

    Ina neman muku tsari da Kalmomin Allah Cikakku daga dukkan Shaidan da wata dabba mai dafi, da kuma dukkan wani mai kambun baka, mai cutarwa.

    Danna nan don karanta Yadda Ake Addu’ar Barka Ga Wanda Aka Yi Wa Haihuwa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’ar Barka Ga Wanda Aka Yi Wa Haihuwa

    Yadda Ake Addu’ar Barka Ga Wanda Aka Yi Wa Haihuwa

    و َ ﺷَﻜَﺮ ْ ت َ ﻟَﻚ َ ،اﻟْﻤَﻮ ْ ھُﻮبِ ﻓِﻲﻟَﻚ َ ﷲَُ ﺑَﺎر َ ك َ.ﺑِﺮ َ هُ و َ رُزِﻗْﺖ َ ،أَﺷُﺪﱠهُ و َ ﺑَﻠَﻎَ ،اﻟْﻮ َ اھِﺐ َ

    Washakarat laka,al-mawhubi fīka,laka Allahu bāraka,bihī wa ruziqta,ashuddahu wa balagha, al-wāhibu.

    Allah ya yi albarka ga abin da aka azurta ka da shi, kuma Ya sa ka godewa Wanda ya ba ka
    (shi), kuma Ya sa shi ya rayu har zuwa ga matukar karfinsa, kuma a azurta ka da biyayyarsa.

    Karanta Yadda Ake Addu’ar Gamuwa Da Abokan Gaba Ko Wani Mai Iko 

    Edita@rumasau-kallamu

  • Lailatul Ƙadri

    Lailatul Ƙadri

    Wasu kwanaki ne masu ɗimbin falala, waɗanda suka fi watanni dubu, sannan kuma ba a samunsu, sai a cikin watan Ramadan, a kwanaki goman ƙarshensa.

    حدثنى زياد عن مالك عن يزيد بن عبدالله بن الهاد عن محمد بن إبراهيم إبن الحارث التيمى عن أبى سلمة  بن عبدالرحمن عن أبى سعيد الخدرى أنه قال :كان رسول الله صلى الله عليه وسلم يعتكف العشرالوسط من رمضان فاعتكف عاما , حتى إذا كان ليلة إحدى وعشرين وهى اليلة التى يخرج فيها من صبحها من اعتكافه قال : من اعتكف معي فليعتكف العشر الأوخر, وقد رأيت هذه اليلة أنسيتها , وقد رأيتنى أسجد من صبحها فى ماء وطين فالتمسوهافى العشر الأخر والتمسوهافى كل وتر ,قال أبو سعيد فأمطرت السماء تلك اليلة وكان المسجدعلى عريش فوكف المسجد قال أبو سعيد :فأبصرت عيناي رسول الله صلى الله عليه وسلم إنصرف و على جبهته وأنفه أثر الماء والطين , من صبح ليلة إحدى وعشرين .

    An ruwaito daga Ziyadi daga Malik daga Yazidu bin Abdulllah bin Hadi daga Muhammad bin Ibrahim bin Haris Al-tamimi daga Abu-Salma bin Abdullahman daga Abu-Sa’idul Kudri, haƙiƙa shi ne yace, Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) ya kasance yana Ittakafi a goman tsakiyar watan Ramadan, sai ya yi Ittikafi a wannan shekarar, har sai da ya kasance daren ashirin da ɗaya (ta same shi a cikin masallaci) ita ce da ya fita safiyarta, wanda zai yi Ittikafi a cikinta yace “Duk wanda zai yi Ittikafi tare da ni, to a daren goma ƙarshen (Ramadan), haƙiƙa ya ga a cikin wannan daren, sannan sai ya manta da ita, haƙiƙa na ganni ina sujjada a cikin safiyarta, akwai ruwa da taɓo, sannan (sai annabi yace) ku neme ta a cikin kwanaki goman ƙarshen (Ramadan ), sannan (ya ƙara cewa) ku neme ta a cikin kowace rana (na ranar).

    Saboda haka wannan hadisin ya yi magana a kan abubuwa guda biyu Ittikafi da lailatul ƙadri, Ibin Abdulbari yace wannan hadisi shi ne ya inganta a wannan babi, saboda annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) ya kasance yana Ittakafi a kwanakin goman tsakiyar watan Ramadan.

    Haka kuma  imamu Hafiz Ibin Hajar yace, shi ne da yi wa wawin damma da kuma sin sakina (ɗauri ko mara wasali), sannan kuma Ibin Abdulbarri yace wannan ruwarta (ta Manzon Allah) yana Ittikafi  har sai da ya kasance a daran ashirin da ɗaya, ita ce daran da ya fice a cikin ta da safiyarta, domin yin Ittikafi’’.

    Wannan ruwayar tana ɗaya daga cikin ruwayar Yahaya da Abubakar da shafi`i, amma a cikin ruwayar kala biyu ce da ta  Ibin wahabi da Ibin Ƙasim, waɗanda suka fitar da ita (annabi yana Ittikafi), amma kuma basu ambaci safiyar ba.

    Amma kuma shi Ibin Hazim ya faɗa misalin wannan ruwayar, inda yake cewa a cikin huɗubar daran ashirin da ɗaya,  annabi ya shiga Ittikafi, ita ce daran ashirin da biyu, saboda abin da aka faɗa a ƙarshen wannan hadisi.

    Sai ya buɗe idonsa, sai ga  annabi (Sallallahu alaihi wasalla) a gefensa a ranar, sannan kuma sai ga alamar ruwa da taɓo a cikin safiyar daren ashirin da ɗaya.

    Abin nufi a nan shi ne, mutum ya shiga Ittikafi kafin daren ashirin da ɗaya (lailatul ƙadri), sannan sai ya manta da ita, sai yace “annabi ya ga mala’ika da haske da idansa”, sannan kuma ya gani  a farkon wannan daran ya ga kaza da kaza a cikin daren, ya ga masallaci, mai girma kuma ga haske, sannan kuma a saman masallaci, ruwa yana zuba, saboda haka alamomin da ake iya gane daren lailati ƙadri ne.

    Misali kamar su gushewar rana, zubar ruwan sama, washewar sararin samaniya, gari ya yi tsit, rashin jin sautin karnuka ko dabbobi, da sauransu. Sannan kuma ana iya samu daren lailatul ƙadri a ranar daren ashirin da ɗaya ko da uku ko da biyar ko da bakwai, ko da tara waɗannan su ne ranakun da ake iya samun lailatul ƙadri.

    Amma Abi-Sa’id yace, sama ta kece da ruwa a wannan daren, sannan masallacin ya kasance tamkar ginshiƙi, sai masallacin ya tsaya, sannan kuma  Abi-Sa’id yace sai annabi (Sallallahu alaihi wasalla) ya buɗe idanunsa, sai ya juya sai ga goshinsa da hancinsa akwai alamar ruwa da tabo a daren Asubahin da ya shiga na watan Ramadan.

    An ruwato daga Ziyadu daga Malik daga Abudullah bin Dinari daga Abdullah bin Umar (yace) haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalla) yace’’ ku binciki (ku kirdado) daren lailatul ƙadri a cikin bakwai ɗin ƙarshe.

    Abun nufi a nan shi ne a kwanaki ashirin da bakwai ɗin ƙarshen.

    حدثنى زياد عن مالك عن هشام بن عروة عن أبيه : أن   رسول الله صلى الله وسلم قال “تحروا ليلة القدر فى العشر الأخرين من رمضان.

    An ruwaito daga Ziyaddu daga Malik daga Hishamu ‘’ku binciki daran Lailatul ƙadri a cikin (kwanaki) ashirin ɗin ƙarshen watan Ramadan.

    حدثنى زياد عن مالك عن أبى النضر مولى عمر بن عبيدالله : أن عدالله إبن أنيس الجهني قال لرسول الله صلى الله عليه وسلم : يا رسول الله , إنى رجل شاسع الدارفمرنى ليلة أنزل لها , فقال رسول الله صلى الله عليه وسلم ” أنزل ليلة ثلاث وعشرين من رمضان ”

    An ruwaito daga Ziyadu daga Malik daga Abi-nadhir mai yi wa Umar bin Ubaidullah hidima (yace), haƙiƙa Abdullah bin Unaisu Aljuhaniyyu yace da Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalla), ya manzon Allah ni mutum ne mai rushe-shshen gida, ka umarce ni da daren da aka saukar da ita (Lailatul ƙadri), sai Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalla) yace da shi “An saukar da daran (Lailatul ƙadri), ashirin da uku a cikin watan Ramadan”.

    Amma Ibin Abdulbarri yace wannan ruwayar yankakkiya ce, saboda Abi-nadhir bai riski Abdullah bin Unaisu ba, sannan kuma bai gan shi ba, amma haƙiƙa Imam Muslim ya sadar da wannan hadisin ta hanyar Dhahaku bin Usman daga Abidi daga Busra bin Sa’id daga Abdullah bin Unaisu da lafazin Hadisin Abi-Sa’id daga Daud ya sadar da shi ta hanyar Ibin Ishak daga Muhammad bin Ibrahim Attamimu daga Umrata bin Abdullah bin Unaisu daga mahaifansa kamar yadda wannan hadisin na Muwaɗɗa Malik ya nuna haka.

    An ruwaito daga Ziyadu daga Malik daga Humidu Aɗɗawilu daga Anas bin Malik, tabbas ne yace, Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalla) ya fita tare da mu a cikin watan Ramadan, sai yace ‘’ni na ga mutane biyu suna jayayya, sai suka ɗaga ta,(sai yace da su) ku neme ta a cikin (ashirin da) tara ko bakwai ko biyar’’.

    حدثنى زياد عن مالك أنه بلغه : أن سعيد بن المسيب كان يقول : من شهد العشاء من ليلة القدر , فقد أخذ بحظه منها.

    An ruwaito daga Ziyadu daga Malik (yace) haƙiƙa shin labari ya same shi lalle Sa’id bin Musayyibin ya kasance yana cewa, duk wanda ya shaida (ya yi sallah) Isha’i a cikin Lailatul ƙadri (Ai a cikin ranakun da ake sa ran ganinsu), haƙiƙa ya riski daren lailatul ƙadri.

    Haka kuma Ibin Abdulbarri yace, wannan ba zai iya kasancewa ba, sai kawai ra’ayi ne, sannan ba zai riƙi komai ba, sai  dai neman dacewar Allah (Subhanahu wata’ala) a cikin wannan ranar.

    Saboda haka malamai sun ƙarawa junarsu sani a kan daren Lailatul ƙadri, saɓanin mai yawa, daga cikin su akwai maganar baban malamin nan Al-araki, saboda ita (Lailatul ƙadari) ba ta yi dai-dai da sauran shekaru ba ko ranaku.

    Ma’ana ganin wannan daran sau ɗaya ya taɓa faruwa azamanin Manzon Allaah (Sallallahu alaihi wasalla), sannan kuma an faɗa awata maganar, wannan daran yana kewayawa ne a kowace shekara, a wata faɗar kuma an ce Lailatul ƙadri tana cikin rabin watan Sha’aba, sannan kuma wasu sun ce, A’a an keɓance ta ne a cikin watan Ramadan.

    Sannan za a iya samunta a cikin kowanne dare (Ramadan), Bugu da ƙari kuma Sheikh Sabkiyu ya yarinjar da shi, amma malam Sarkhisu ya faɗa a cikin sharhin ‘’ Hidayatu’’. Maganar Abi-Hanifa yace zamu samu ta (daren Lailatul ƙadri) an ciro ta ne a cikin dukkanin Ramadan, haka nan ma abokinsa ya faɗi haka sauransu.

    Haka ma an ruwaito daga Ibin Abi-Asim daga Anas yace, babu wanda ya sani daga cikin mu (ranar ganin Lailatul ƙadri), sai wani malami daga cikinsu yace, A a, Lailatul ƙadri, tana cikin rabin watan Ramadan, sai kuma wani mutum yace, A a tana cikin daren goman sha shida ne, na Ramadan.

    Sai kuma wani yace, A a tana cikin daren goman sha bakwai, sannan sai wani yace, A a tana cikin daren goma sha takwas, sai kuma wani ya ƙara cewa, A a tana cikin daren goma sha tara ne, sai kuma wani ya sake cewa, Aba tana cikin daren ashirin ga watan Ramadan.

    Haka kuma sai wani yace, A’a ita Lailatul ƙadri abar so ce, sannan kuma tana cikin goman tsakiyar watan ramadan, sai kuma wani yace A’a ita kuma abin so ce, sannan tana cikin goman ƙarshe.

    Sai kuma wani yace, A a, Lailatul ƙadri tana cikin daren ashirin da biyu na watan Ramadan har zuwa daren talatin ga watan Ramadan, sannan kuma wasu suka ce Lailatul ƙadri, tana ci kin goman tsakiyar watan Ramadan, wasu kuma suka ce tana cikin goman ƙarshen.

    Amma a cikin mazahabar Imam shafi’i jamhurum Sahabbai (mutanan mu) suka ce. haƙiƙa ita Lailatul ƙadri tana goman ƙarshe watan Ramadan, sannan kuma abar so ce a kan mu, sai dai ita abar ayyanawa ce a kan wannan al-amari, sannan kuma wannan daren na Lailatul ƙadri ba za ta gushe ba, har zuwa ranar lahira, kowanne ranaku goman ƙarshe (na wata) abar ɗaukakawa ce.

    Daga ƙarshe kuma, mazahabar imam shafi’i sun rinjayar da daren ashirin da ɗaya shi ne daren Lailatul ƙadri, sannan kuma dukkanin mazahaban nan guda huɗu sun yi bayani a kan kwanakin sa ran ganin Lailatul ƙadri.

    A takaice, alamomin daren lailatul ƙadri suna da yawa, amma dai idan ana cikin tsananin zafi ko sanyi, to a ranar daren za a samu sauƙi, idan kuma garin akwai duhu, to za a samu haske a garin da sauransu.

    Danna nan don karanta Azumin Watan Ramadan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Zikiri Kafin (Gabanin) Da Bayan An Gama Alwala

    Zikiri Kafin (Gabanin) Da Bayan An Gama Alwala

    Zikiri Kafin (Gabanin) Alwala

    “Bismillaahi”.

    {Da sunan Allah}.

    Zikiri Bayan An Gama Alwala

    “Ashhadu an laa ilaha illallahu wah dahu laa sharika lahu wa Ashhadu anna Muhammadu abduhu wa rasuluhu”.

    {Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kaɗai, babu abokin tarayya a gare shi, kuma ina shaidawa cewa Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) bawansa ne kuma manzonsa ne}.

    “Allahumma ja’alnii minat-tauwaabina waj’alnii minal mutaɗahhiriina”.

    {Ya Allah! Ka sanya ni a cikin masu yawan tuba, kuma ka sanya ni a cikin masu tsarkaka}.

    “Subhanakal-laahumma wabi hamdika Ashhadu an laa ilaaha illaa anta wa astagfiruka wa atubu ilaika”.

    {Tsarki ya tabbata gare ka ya Allah tare da yabo gare ka. Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai kai, ina neman gafararka kuma ina tuba gareka}.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Zikiri Yayin Fita Daga Gida danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Ayyukan Gida Domin Taimako Juna danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunna; wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Yadda Ake Addu’ar Gamuwa Da Abokan Gaba Ko Wani Mai Iko 

    Yadda Ake Addu’ar Gamuwa Da Abokan Gaba Ko Wani Mai Iko 

    اللهُمَّ إِنَّا نَجْعَلُكَ فِي نُحُورِهِمْ وَنَعُوذُ بِكَ مِنْ شُرُورِهِمْ
    Allahumma ina naj’aluka fee nuhurihim wana’uzu bika min shururihim

    Ya Allah! Mu Muna sanya Ka a gabansu, kuma Muna neman tsarinka sharracensu.

    اللّهُمَّ أَنتَ عَضُدِي ، وَأَنْتَ نَصِيرِي، بِكَ أَحُولُ وَبكَ أَصُولُ وَبكَ أُقَاتِلُ

    Allahumma anta adudee, wa’anta naseeri, bika ahulu abika asulu wabika ukatilu

    Ya Allah! Kai ne Mai ƙarfafa ni, kuma Kai ne Mataimakina. Da ƙarfinka ne nake yin dabarun yaƙi, kuma da ƙarfinka ne nake kai hari, kuma da ƙarfinka ne nake yin yaƙi.

    حَمَّنَا اللهُ وَنِعْمَ الْوَكِيلُ
    Hammanal lahu wani’’imal wakeelu

    Allah ne Mai isar mana, kuma madalla da Shi abin dogaro.

    Karanta Abin Da Mutum Zai Yi Idan Ya Yi Mafarki Mara Kyau

    Edita@rumasau-kallamu

  • Abin Da Mutum Zai Yi Idan Ya Yi Mafarki Mara Kyau

    Abin Da Mutum Zai Yi Idan Ya Yi Mafarki Mara Kyau

    Wanda ya yi mafarki mara kyau ko ya ga abu mummuna a mafarki, to sai ya yi waɗannan abubuwan:

    -Ya yi tofi ta gefen hagunsa sau uku.

    -Ya nemi tsarin Allah daga Shaiɗan da kuma sharrin abin da ya gani, sau uku.

    -Kada ya gaya wa kowa wannan mafarkin.

    -Ya juya daga kwuiɓin da ya kasance yana kwance a kansa.

    -Idan ya so, ya iya tashi ya yi salla

    Karanta Addu;ar Sanya Sababbin Tufafi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Addu’ar Sanya Sababbin Tufafi

    Addu’ar Sanya Sababbin Tufafi

     

    اللّهُمَّ لَكَ الْحَمْدُ أَنتَ كَسَوْتَنِيهِ، أَسْأَلُكَ خَيْرَهُوَخَيْرَ مَا صُنِعَ لَهُ وَأَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّهِ وَشَرِّ مَا صُنِعَ لَهُ

    Allahumma lakal hamdu anta kasautanihi ,as’aluka khairahu wa khaira ma suni’a lahu, wa a’uzu bika min sharrihi wa sharri ma suni’a lahu

    Ya Allah! Dukkan yabo ya tabbata gare Ka, Kai ne Ka tufatar da ni shi (wannan tufar). Ina roƙonka alherinsa da alherin abin da aka yi shi dominsa, kuma ina neman tsarinka daga sharrinsa da sharrin abin da aka yi shi dominsa.

    Karanta Yadda Ake Adduar Razana A Cikin Barci

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’ar Razana A Cikin Barci

    Yadda Ake Addu’ar Razana A Cikin Barci

    Addu’ar wanda ya razana a cikin barci, da wanda ya kasa barci

    أَعُوْذُ بِكَلِمَاتِ اللهِ التّامَّاتِ مِنْ غَضَبِهِ وَعِقَابِهِ ، وَشَرِّ عِبَادِهِ ، وَمِنْ هَمَزَاتِ الشَّيَاطِينِ وَأَنْ يَحْضُرُون

    A’uzu bikalimaatil lahit tammati min gadabihi wa’iƙabihi, wa sharri ibadihi,wa min hamazaatish shayaɗeen wa’ayyahdurun

    Ina neman tsari da Kalmomin Allah cikakku daga fushinsa, da uƙubarsa, da sharrin bayinsa da kuma zungure-zunguren shaiɗanu, da su halarto ni (a cikin al’amurana).

    Karanta Yadda Ake Addu’ar Cire Tufafi

    Edita @rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’ar Cire Tufafi

    Yadda Ake Addu’ar Cire Tufafi

    بِسْمِ الله.

    Bismillah

    Da sunan Allah.

    Addu’ar Sanya Tufa

    .الْحَمْدُ لِلّهِ الذِي كَسَانِي هَذَا الثَّوْبَوَرَزَقَنِيهِ مِنْ غَيْر حَوْل مِني وَلاَ قُوَّةٍ
    Alhamdulillahil lazi kasani hazas sauba warzuƙnihi min gairi haulin minna wala ƙuwwa

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, wanda ya tufatar da ni wannan tufa, kuma ya arzurta ni da ita, ba tare da wata dabara daga gare ni ba ko wani ƙarfi.

    Addu’ar Wanda Ya Ji Tsoron Zaluncin Wani Mai Iko

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’ar Tafiyar Da Ƙuncin Zuciya

    Yadda Ake Addu’ar Tafiyar Da Ƙuncin Zuciya

    لاَ إِلَهَ إلا اللهُ الْعَظِيمُ الْحَلِيمُ، لاَ إِلَهَ إلا الله رَبِّ الْعَرْشِ الْعَظِيمُ، لاَ إِلَهَ إِلَّا اللهُ رَبُّ السَّمَوَاتِ وَرَبُّ الأَرْضِ وَرَبُّ الْعَرْشِ الْكَرِيمُ .

    La’ilaha illallahul azeemul haleem, la’ilaha illallahu rabbil arshil azeem, la’ilaha ilallahu rabbus samawati warabbul ardi wa rabbul arshil kareem.

    Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Mai girma (wanda babu abin da yake girmama a gare Shi), Mai haƙuri (Mai jinkirin azaba tare da cikakken ikon aiwatar da ita). Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ubangijin Alarshi, Mai girma. Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ubangijin sammai, Ubangijin ƙasa, Ubangijin Al’arshi, Mai yawan baiwa.

    اللّهُمَّ رَحْمَتَكَ أَرْجُو فَلا تَكِلْنِي إِلَى نَفْسِيطَرْفَةَ عَيْنٍ وَأَصْلِحْ لي شأني كلهلا إله إلاأَنتَ.

    Allahumma rahmataka arju fala takilni ila nafsee ɗarfata aini wa’aslih lee sha’ani kullah, la’ilaha illa anta.

    Ya Allah! Rahamarka nake kauna, don haka Kar Ka kyale ni da kaina ko da kiftawar ido ne, kuma Ka kyautata mini sha’anina dukkansa; babu abin bautawa da gaskiya sai Kai.

    لاَ إِلَهَ إلا أنتَ سُبْحَانَكَ إِنِّي كُنْتُ مِنَ الظالمين

    La’ilaha illa’anta subhanaka inni kuntu minaz zalimeen

    Babu abin bautawa da gaskiya sai Kai. Tsarki ya tabbata gare Ka, lalle ni na kasance daga cikin azzalumai.

    الله الله رَبِّى لاَ أُشْركُ بِهِ شَيْئاً
    Allah Allah rabbi la ushrika bihi shai’an

    Allah! Allah ne Ubangijina, ba na yin tarayya da Shi da wani abu a cikin bauta.

    Karanta Yadda Ake Addu’a A Kan Abokan Gaba

    Edita@rumasau-kallamu