Addu’ar Tashi Daga Majalisi

0
21

Addu’ar Tashi Daga Majalisi (Domin Neman Yafewa Ga Abin Da Ya Gudana A Cikin Majalisin).

A’isha, Allah ya yarda da ita, ta ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam), bai taɓa zama a wani majalisi ba, ko ya karanta Alƙur’ani, ko ya yi wata sallah face ya cika da waɗannan kalmomi:

“Subhaanakal laahumma wa bi hamdika ashhadu an laa ilaaha illaa anta astagfiruka wa atuubu ilaika”.

{Tsarki ya tabbata gare ka, ya Allah, da yabo gare ka. Ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai kai; ina neman gafararka, kuma ina tuba zuwa gare ka}.

Sai A’isha ta ce:- “Ya Manzon Allah! Na lura cewa ba ka taɓa zama a wani majalisi ba, ka yi karatun Alƙur’ani, ko ka yi sallah face ka faɗi waɗannan kalmomi. Sai ya ce: “Ƙwarai. Duk wanda ya faɗi wani alheri sai waɗannan kalmomi su zama kamar hatimi ne ga alherin da ya aikata, wanda kuma ya faɗi sharri, sai su zama kaffara ne gare shi”.

Domin karanta cikakken bayani akan Addu’a A Lokacin Da Mutum Zai Haw Abin Hawa danna nan.

Domin karanta cikakken bayani akan Ladubban Addu’a A Musulunci danna nan.

Edita; RMK

labarin da ya wuceAddu’a Idan Mutum Zai Yi Tafiya
Labarin na GabaYadda Ake Addu’ar Ziyarar Maƙabarta
wikiHausa
wikiHausa kundin ilimi (insakulofidiya) ce da ke ilimantar da jama'a yara da manya da maza da mata wajen samun ilimi a saukake, cikin harshen Hausa.