Ladubban Addu’a A Musulunci

0
1618

WAƊANDA ALLAH KE GAGGAUTA AMSA ADDU’ARSU

1. Addu’ar Annabawan Allah.
2. Addu’ar mala’ikun Allah
3. Addu’ar wanda aka zalunta.
4. Addu’ar mai Ƙarfin imani da tsoron Allah.
5. Addu’ar da mai biyayya ga iyayensa.
6. Addu’ar mai Azumi.
7. Addu’ar shugaba adali.
8. Addu’ar iyaye (nagartattu) ga ‘ya’yansu.
9. Addu’a ga ɗan uwa avbayan idonsa.
10. Addu’ar mai jihadi.
11. Addu’ar mai hajji ko umrah.
12. Addu’ar mai dauwama cikin zikirin Allah.
13. Addu’a ga mai karatun AlQur’ani.
14. Addu’ar matafiyi (tafiya ta halal).
15. Addu’ar mai taka tsantsan wajen haram;abincinsa,abin shansa,tufafinsa da mazauninsa.

ABUBUWAN DA SUKE KAWO JINKIRIN AMSA ADDU’A

1. Shirka ƙarama da babba.
2. Ta’amuli da haram ci, sha ko tufafi.
3. Nauyin zunubai da ƙeƙashewar zuciya.
4. Barin umarni da kyakkyawa da hani ga mummuna.
5. Tafseel (Dalla-dalla) a cikin addu’a
6. Wasa da wargi a cikin addu’a.
7. Addu’a da zuciya gafalalliya mai shagala.
8. Rashin ladabi a gaban Allah Jalla Wa’ala.
9. Ta’allaƙa addu’a ga mashi’ah (In ka so)
10. Gaggawa a cikin addu’a.
11. Al-Istihsaar( Shi ne mutum ya bar addu’a saboda gajiya da kosawa)
12. Rokon abin da hukuncin Allah ya gama da shi.
13.Saja’i a cikin addu’a (shi ne mutum ya tilasta wa kansa daidaita harafin ƙarshen jumlolin addu’a )
14. Bidi’o’i a cikin addu’a.
15. Roƙon wani abu da ya shafi saɓon Allah ko yanke zumunta.

Duba:
1. TAS’HIHUD DU’A na Dr.BAKR
2 ARRIYADUN NAZIRAH na Shk.Abdur Rahman Nasir Sa’adiy

Domin karanta nasbar Manzo allah danna nan

labarin da ya wuceWaɗanda Allah Ke Gaggauta Karɓar Addu’ar Su
Labarin na GabaWace Ce Ta Karɓi Haihuwar Annabi Muhammad(S.A.W)?