Addu’o’i Domin Neman Tsari Daga Azzalumai

0
567

Addu’o’in Tsari Daga Azzalumai; An karɓo daga Abdullahi ɗan Mas’ud (Radiyallahu Anhu) ya ce; Idan ɗayanku yana jin tsoron wani azzalumin shugaba sai ya ce:

Allahumma rabbussamawatis sab’i, wa rabbul arshil azim, kun li jaran min wa atba’ihi min halƙika minal jinni wal insi an yafruɗa alayya ahadun minhum au an yaɗga, azza jaruka wa jalla sana’uka wa la’ilaha illan anta”.

Asbahani ne ya ruwaito shi daga Ibn Mas’ud danganta maganar ba ga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) (Mauƙuf).

An karɓo daga Abdullahi Ibn Abbas (Radiyallahu Anhu) ya ce; “Idan ka je wurin wani shugaba mai kwarjini wanda kake jin tsoron zai afka maka sai ka ce:

Allah Akbar Allah a’azzu min khalƙihi jami’an, Allahu a’azzu mimma akhafu wa ahzaru, a uzu billahillazi laa ilaaha illaa huwa almumsikus samawati an yaƙa’a na alal ardi illa bi iznihi min sharri abdika wa junudihi wa atba’ihi wa ashya’ihi minal jinni wal insi. Allahumma kun li jaaran min sharrihim jalla sana’uka wa azza jaruka wa tabarakas muka, wa laa ilaahha gairuka”(sau uku).

Ibn Abi Shaiba ne ya ruwaito shi, daga Ibn Mas’ud.

Ƙarin Bayani

Wannan hadisi sahihi ne mauƙufan wato zuwa ga Ibn Mas’ud, amma bai inganta ba zuwa ga Annabi. Haka kuma addu’a ta biyu ta inganta daga Ibn Abbas (Radiyallahu Anhu).
Addu’o’i ne kyawawa da mutum zai iya yi duk lokacin da ya ji tsoron zaluncin wani azzalumin shugaba. A wurin da babu komai sai a faɗi sunan shugaban.

Fassara

Fassarar addu’a ta farko:

Ya Allah Ubangijin sammai bakwai, Ubangijin Al’arshi; mai girma ka kare ni daga sharrin wane ɗan wane da dukkan mabiyansa daga halittunka aljanu da mutane; kada ka ba wa ɗaya daga cikinsu dama ya afka min ko ya yi min ta’addanci; kariyarka ta buwaya, yabonka ya girmama. Babu wanda ya cancanta a bautawa sai kai.

Ita kuwa addu’a ta biyu ga fassararta:

Allah shi ne mafi girma, Allah shi ne mafi buwaya daga halittunsa gaba ɗaya. Allah shi ne mafi buwaya daga abin da nake tsoro da fargaba. Ina neman tsari da Allah wanda babu wanda ya cancanta a bauta wa sai shi; wanda yake riƙe da sammai kada su faɗo kan ƙasa sai da izininsa. Ka kare ni daga sharrin bawanka wane da jami’an tsaronsa da mabiyansa da ma magoya bayansa mutane da aljanu.
Ya Allah ka kasance mai kariya a gare ni daga sharrinsu, yabonka ya girmama, wanda ka baiwa kariya ya buwaya, sunanka ya yi albarka babu wanda ya cancanta a bautawa sai kai.

Domin karanta cikakken bayani akan Sahabban Da Suka Fi Kowa Rawaito Hadisai danna nan.

Domin karanta cikakken bayani akan Hadisi Na Ɗaya A Kan Haramcin Goyon Bayan Azzaluman Shugabanni danna nan.

labarin da ya wuceFalalar Adalci, Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu
Labarin na GabaYadda Ake Dawo Da Abin Da Aka Goge A Kan Komfiyuta