Tag: addu;a

  • Yadda Ake Addu’ar Nema Wa ‘Ya’ya Tsari

    Yadda Ake Addu’ar Nema Wa ‘Ya’ya Tsari

    Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya kasance yana nema wa Hasan da Husain tsari da wannan addu’ar:

    أُﻋ ِ ﯿﺬﱠِﺑِﻜَﻠِﻤَﺎتِﷲﻟﺘﱠﺎﻣﱠﺔﻣِﻦ ْﻛُﻞ ﺷَﯿْﻄَﺎن ٍﱢﱠو َھَﺎﻣﱠﺔٍ ِو َ ﻣِﻦ ْﻛُﻞ ﻋَﯿْﻦ ٍ ﻻَﻣﱠﺔٍ ُ

    Uʿīzu bikalimātillāhi t-tāmmati, min kulli shayṭānin wa hāmmah, wa min kulli ʿaynin lām.

    Ina neman muku tsari da Kalmomin Allah Cikakku daga dukkan Shaidan da wata dabba mai dafi, da kuma dukkan wani mai kambun baka, mai cutarwa.

    Danna nan don karanta Yadda Ake Addu’ar Barka Ga Wanda Aka Yi Wa Haihuwa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’ar Barka Ga Wanda Aka Yi Wa Haihuwa

    Yadda Ake Addu’ar Barka Ga Wanda Aka Yi Wa Haihuwa

    و َ ﺷَﻜَﺮ ْ ت َ ﻟَﻚ َ ،اﻟْﻤَﻮ ْ ھُﻮبِ ﻓِﻲﻟَﻚ َ ﷲَُ ﺑَﺎر َ ك َ.ﺑِﺮ َ هُ و َ رُزِﻗْﺖ َ ،أَﺷُﺪﱠهُ و َ ﺑَﻠَﻎَ ،اﻟْﻮ َ اھِﺐ َ

    Washakarat laka,al-mawhubi fīka,laka Allahu bāraka,bihī wa ruziqta,ashuddahu wa balagha, al-wāhibu.

    Allah ya yi albarka ga abin da aka azurta ka da shi, kuma Ya sa ka godewa Wanda ya ba ka
    (shi), kuma Ya sa shi ya rayu har zuwa ga matukar karfinsa, kuma a azurta ka da biyayyarsa.

    Karanta Yadda Ake Addu’ar Gamuwa Da Abokan Gaba Ko Wani Mai Iko 

    Edita@rumasau-kallamu

  • Falalar Salla A Masallacin Haramin Makka Da Madina

    Falalar Salla A Masallacin Haramin Makka Da Madina

    An karɓo daga Abu Hurairah (Radiyallahu anhu) ya ce: Haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalam) yace; “Salla a masallaci na ta fi salla a wani masallaci sau dubu ban da masallaci mai alfarma”(Bukhari 1190 Muslim 1394).

    An karɓo daga Abdullahi Ibn Zubair (Radiyallahu anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalam) yace: “Salla a masallaci na tafi salla dubu a sauran masallatai ban da masallacin harami, kuma salla a masallacin harami tafi salla dubu ɗari a wannan masallacin” (Ahmad, Ibn Khuzaimaha, Suhihul Jami’I 3841).

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Falalar Zama A Madina Ya Ke danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Sallar Idi danna nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Yadda Ake Addu’ar Gamuwa Da Abokan Gaba Ko Wani Mai Iko 

    Yadda Ake Addu’ar Gamuwa Da Abokan Gaba Ko Wani Mai Iko 

    اللهُمَّ إِنَّا نَجْعَلُكَ فِي نُحُورِهِمْ وَنَعُوذُ بِكَ مِنْ شُرُورِهِمْ
    Allahumma ina naj’aluka fee nuhurihim wana’uzu bika min shururihim

    Ya Allah! Mu Muna sanya Ka a gabansu, kuma Muna neman tsarinka sharracensu.

    اللّهُمَّ أَنتَ عَضُدِي ، وَأَنْتَ نَصِيرِي، بِكَ أَحُولُ وَبكَ أَصُولُ وَبكَ أُقَاتِلُ

    Allahumma anta adudee, wa’anta naseeri, bika ahulu abika asulu wabika ukatilu

    Ya Allah! Kai ne Mai ƙarfafa ni, kuma Kai ne Mataimakina. Da ƙarfinka ne nake yin dabarun yaƙi, kuma da ƙarfinka ne nake kai hari, kuma da ƙarfinka ne nake yin yaƙi.

    حَمَّنَا اللهُ وَنِعْمَ الْوَكِيلُ
    Hammanal lahu wani’’imal wakeelu

    Allah ne Mai isar mana, kuma madalla da Shi abin dogaro.

    Karanta Abin Da Mutum Zai Yi Idan Ya Yi Mafarki Mara Kyau

    Edita@rumasau-kallamu

  • Abin Da Mutum Zai Yi Idan Ya Yi Mafarki Mara Kyau

    Abin Da Mutum Zai Yi Idan Ya Yi Mafarki Mara Kyau

    Wanda ya yi mafarki mara kyau ko ya ga abu mummuna a mafarki, to sai ya yi waɗannan abubuwan:

    -Ya yi tofi ta gefen hagunsa sau uku.

    -Ya nemi tsarin Allah daga Shaiɗan da kuma sharrin abin da ya gani, sau uku.

    -Kada ya gaya wa kowa wannan mafarkin.

    -Ya juya daga kwuiɓin da ya kasance yana kwance a kansa.

    -Idan ya so, ya iya tashi ya yi salla

    Karanta Addu;ar Sanya Sababbin Tufafi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Addu’ar Sanya Sababbin Tufafi

    Addu’ar Sanya Sababbin Tufafi

     

    اللّهُمَّ لَكَ الْحَمْدُ أَنتَ كَسَوْتَنِيهِ، أَسْأَلُكَ خَيْرَهُوَخَيْرَ مَا صُنِعَ لَهُ وَأَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّهِ وَشَرِّ مَا صُنِعَ لَهُ

    Allahumma lakal hamdu anta kasautanihi ,as’aluka khairahu wa khaira ma suni’a lahu, wa a’uzu bika min sharrihi wa sharri ma suni’a lahu

    Ya Allah! Dukkan yabo ya tabbata gare Ka, Kai ne Ka tufatar da ni shi (wannan tufar). Ina roƙonka alherinsa da alherin abin da aka yi shi dominsa, kuma ina neman tsarinka daga sharrinsa da sharrin abin da aka yi shi dominsa.

    Karanta Yadda Ake Adduar Razana A Cikin Barci

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’ar Razana A Cikin Barci

    Yadda Ake Addu’ar Razana A Cikin Barci

    Addu’ar wanda ya razana a cikin barci, da wanda ya kasa barci

    أَعُوْذُ بِكَلِمَاتِ اللهِ التّامَّاتِ مِنْ غَضَبِهِ وَعِقَابِهِ ، وَشَرِّ عِبَادِهِ ، وَمِنْ هَمَزَاتِ الشَّيَاطِينِ وَأَنْ يَحْضُرُون

    A’uzu bikalimaatil lahit tammati min gadabihi wa’iƙabihi, wa sharri ibadihi,wa min hamazaatish shayaɗeen wa’ayyahdurun

    Ina neman tsari da Kalmomin Allah cikakku daga fushinsa, da uƙubarsa, da sharrin bayinsa da kuma zungure-zunguren shaiɗanu, da su halarto ni (a cikin al’amurana).

    Karanta Yadda Ake Addu’ar Cire Tufafi

    Edita @rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’ar Cire Tufafi

    Yadda Ake Addu’ar Cire Tufafi

    بِسْمِ الله.

    Bismillah

    Da sunan Allah.

    Addu’ar Sanya Tufa

    .الْحَمْدُ لِلّهِ الذِي كَسَانِي هَذَا الثَّوْبَوَرَزَقَنِيهِ مِنْ غَيْر حَوْل مِني وَلاَ قُوَّةٍ
    Alhamdulillahil lazi kasani hazas sauba warzuƙnihi min gairi haulin minna wala ƙuwwa

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, wanda ya tufatar da ni wannan tufa, kuma ya arzurta ni da ita, ba tare da wata dabara daga gare ni ba ko wani ƙarfi.

    Addu’ar Wanda Ya Ji Tsoron Zaluncin Wani Mai Iko

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’ar Tafiyar Da Ƙuncin Zuciya

    Yadda Ake Addu’ar Tafiyar Da Ƙuncin Zuciya

    لاَ إِلَهَ إلا اللهُ الْعَظِيمُ الْحَلِيمُ، لاَ إِلَهَ إلا الله رَبِّ الْعَرْشِ الْعَظِيمُ، لاَ إِلَهَ إِلَّا اللهُ رَبُّ السَّمَوَاتِ وَرَبُّ الأَرْضِ وَرَبُّ الْعَرْشِ الْكَرِيمُ .

    La’ilaha illallahul azeemul haleem, la’ilaha illallahu rabbil arshil azeem, la’ilaha ilallahu rabbus samawati warabbul ardi wa rabbul arshil kareem.

    Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Mai girma (wanda babu abin da yake girmama a gare Shi), Mai haƙuri (Mai jinkirin azaba tare da cikakken ikon aiwatar da ita). Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ubangijin Alarshi, Mai girma. Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ubangijin sammai, Ubangijin ƙasa, Ubangijin Al’arshi, Mai yawan baiwa.

    اللّهُمَّ رَحْمَتَكَ أَرْجُو فَلا تَكِلْنِي إِلَى نَفْسِيطَرْفَةَ عَيْنٍ وَأَصْلِحْ لي شأني كلهلا إله إلاأَنتَ.

    Allahumma rahmataka arju fala takilni ila nafsee ɗarfata aini wa’aslih lee sha’ani kullah, la’ilaha illa anta.

    Ya Allah! Rahamarka nake kauna, don haka Kar Ka kyale ni da kaina ko da kiftawar ido ne, kuma Ka kyautata mini sha’anina dukkansa; babu abin bautawa da gaskiya sai Kai.

    لاَ إِلَهَ إلا أنتَ سُبْحَانَكَ إِنِّي كُنْتُ مِنَ الظالمين

    La’ilaha illa’anta subhanaka inni kuntu minaz zalimeen

    Babu abin bautawa da gaskiya sai Kai. Tsarki ya tabbata gare Ka, lalle ni na kasance daga cikin azzalumai.

    الله الله رَبِّى لاَ أُشْركُ بِهِ شَيْئاً
    Allah Allah rabbi la ushrika bihi shai’an

    Allah! Allah ne Ubangijina, ba na yin tarayya da Shi da wani abu a cikin bauta.

    Karanta Yadda Ake Addu’a A Kan Abokan Gaba

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’a A Kan Abokan Gaba

    Yadda Ake Addu’a A Kan Abokan Gaba

    اللَّهُمَّ مُنْزِلَ الْكِتابِ ، سَرِيعَ الْحِسابِ ، اهْزِمِ الأَحْزَابَ ، اللّهُمَّ اهْزِمُهُمْ وَزَلْزِلْهُمْ .

    Allahumma munzilal khitabi, sari’al hisabi, ihzimil ahzaaba, allahumma ihzimuhum wazalzilhum.

    Ya Allah! Mai saukar da Littafi, Mai gaggawan sakamakoKa karya kungiyoyin abokan gaba. Ka karya su, Ka girgiza su.

    Karanta Addu’ar Wanda Ya Ji Tsoron Zaluncin Wani Mai Iko

    Edita@rumasau-kallamu