Tag: addu;a

  • Falalar Ayoyi Goma Na Farko Ko Ƙarshen Suratul Kahfi

    Falalar Ayoyi Goma Na Farko Ko Ƙarshen Suratul Kahfi

    An karɓo daga Abu Darda’i (Radiyallahu Anhu)

    Haƙiƙa Annabin Allah (Sallallahu alaihi wasalam) ya ce: “Wanda ya haddace ayoyi goma na farkon Suratul Kahafi, Za a kare shi daga Dujal” (Muslim 809) A wata ruwayar ayoyin goma na Ƙarshen suratul kahfi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Falalar Suratul Tabarakallazi Biyadihil Mulku Ta Ke danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Raka’o’in Ɗawafi danna nan.

    Don karanta cikakken bayani a kan Kalmomi Guda Biyar Masu Amfani A Duniya Da Lahira danna nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Falalar Biyawa Wani Hajji Ko Umra

    Falalar Biyawa Wani Hajji Ko Umra

    Haƙiƙa duk wanda ya kasancce sanadin aikata alhairi, za a ba shi lada dai-dai da ladan wanda ya aikata wannan aikin ba tare da an rage komai daga ladansa ba..

    A kan haka, wanda ya biyawa wani kuɗin aikin hajji ko Umra; za a ba shi lada da za a baiwa wanda ya yi aikata aikin hajji ko umra. Saboda haka, magabata suka kasance suna ɗaukar nayin waɗanda ba su taɓa yin aikin hajji ko umra ba.

    Misalin Waɗannan magabata akwai Muslim Ibn Yasar da Abdullahi Ibnul Mubarak; waɗanda suka kasance suna aikin hajji duk shekara, kuma suna tafiya da mutane da suke ɗaukar nauyinsu!.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Falalar Karatun Al-Ƙur’ani Ya Ke danna nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Addu’ar Buɗe Sallah 2

    Addu’ar Buɗe Sallah 2

    Addu’ar buɗe salla (watau bayan anyi kabbarar harama) 2

    سُبحانَكَ اللَّهُمَّ وَبِحَمْدِكَ وَتَبارَكَ اسْمُكَ وَتَعَالَى جَدُّكَ وَلا إِلهَ غَيْرُكَ.

    Subhanakal-lahumma wabihamdika watabarakas-muka wata’ala jadduka wala ilaha ghayruk.

    Tsarki ya tabbata gareKa, Ya Allah, tare da yabo gareka; Albarkatun sunanka sun yawaita; mulkinka da girmanka sun ɗaukaka; babu abin bautawa da gaskiya sai kai.

    Danna nan don karanta Addu’ar Buɗe Sallah

    Edita@rumasau-kallamu

  • Addu’ar Gama Alwala

    Addu’ar Gama Alwala

    Addu’ar da mutum zai yi bayan ya gama Alwala

    اَشْهَدُ اَنْ لا إِلَهَ إِلَّا اللهُ وَحْدَهُ لَا شَرِيكَ لَهُ وَأَشْهَدُ أَنَّ مُحَمَّدًا عَبْدُهُ وَرَسُولُه

    اللّهُمَّ اجْعَلْنِي مِنَ التَّوَّابِينَ وَاجْعَلْنِي مِنَ الْمُتَطَهِّرِينَ

    Ash hadu alla ilaha illallah, wahdahu la sharikalah, wa ash hadu anna muhammadan ‘abduhu wa rasuluh. Allahummaj ‘alni minat tawwabina waj ‘alni minal muta tahhirin.

    Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah. Shi Kaɗai, kuma ba shi da abokin tarayya, kuma ina shaidawa cewa Annabi Muhammadu bawansa ne kuma manzonsa ne.

    Ya Allah! Ka sanya ni a cikin masu yawan tuba, kuma ka sanya ni a cikin masu tsarkake ka.

    Danna nan don karanta Adu’ar Buɗe Sallah

    Edita@rumasau-kallamu

  • Addu’ar Buɗe Sallah

    Addu’ar Buɗe Sallah

    Addu’ar Buɗe Sallah (wato Bayan An yi Kabbarar Harama)

    اللَّهُمْ بَاعِدْ بَينِي وَبَيْنَ خَطاياي كما باعَدْتَ بَيْنَ المَشْرِقِ وَالمَغْرِبُ ، أَللَّهُمْ نَقْنِي مِنْ خَطاياي كما يُنقى الثوبُ الأَبْيَضُ مِنَ الدنس ، اللهُمَّ اغْسِلْنِي مِنْ خَطَايَايَ بالثلج والماءِ وَالبَرَد

    Allahumma ba’id baynee wabayna khatayaya kama ba’adta baynal-mashriki walmaghrib, allahumma nakkinee min khatayaya kama yunakkath-thawbul-abyadu minad-danas, allahummagh-silnee min khatayaya biththalji walma’i walbarad.

    Ya Allah! Ka nisanta tsakanina da laifuffukana kamar yadda Ka nisanta tsakanin gabas da yamma; Ya Allah! Ka tsarkake ni daga laifuffukana kamar yadda ake tsarkake farar tufa daga dauɗa, Ya Allah! Ka wanke ni daga laifuffukana da ƙanƙara da ruwa da raɓa.

    Domin karanta Addu’ar Daren Lailatul ƙadri danna nan 

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Addu’ar Daren Lailatul Kadri

    Addu’ar Daren Lailatul Kadri

    Nana Aisha (R.A) tace, Ya Manzon Allah (S.A.W) shin kana ganin idan na gane wane dare ne na Lailatul kadri, me zan ce a cikinsa? sai yace ki ce:

    “اللَّهُمَّ إِنَّكَ عَفُوٌّ تُحِبُّ الْعَفْوَ فَاعْفُ عَنِّي”

    “Allahumma innaka afuwwun tuhibbul afwa fa’afu anni”

    MA’ANA: “Ya Allah kai mai afuwa ne kuma kana son afuwa, to ina roƙon ka yi mini afuwa” (Tirmidhi da Ibn Majah)

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Falalar Suratul Fatiha

    Falalar Suratul Fatiha

    An karɓo daga Abu Sa’id Ibnul Mu’alla (Radiyallahu anhu) yace; Na kasance ina salla a masallaci sai Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya kira ni.

    Sai ban amsa ba, sannan sai ne je wajensa na ce salla neke yi. Sai ya ce; “Shin Allah bai ce: ” Ku amsawa Allah da Manzonsa ba idan suka kira ku? Sai ya ce; zan sanar da kai surar da ta fi kowace sura girma a cikin Alƙur’ani kafin ka fita daga masallaci”.

    “Sai ya riƙe hannuna, da muka kusa fita sai na ce; “Ka ce za ka sanar da ni surar da tafi kowace sura girma a cikin Alƙur’ani, sai ya ce; “Ita ce Alhamdu lillahhi rabbil alamin; Ita ce (Mai ayoyin) bakwai da maimaitawa kuma ita ce Alƙur’ani, mai girma da aka ba ni” (Bukahri: 4202).

    Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Suratul Baƙara danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Ziyarar Mara Lafiya danna nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Addu’ar Da Ake Ma Wanda Ya Sanya Sabuwar Tufa

    Addu’ar Da Ake Ma Wanda Ya Sanya Sabuwar Tufa

    “Tublii wa yukhliful laahu ta’ala”.

    {Allah ya sa ka mayar da ita tsumma, kuma Allah Maɗaukaki ya mayar maka da wata (tufar}.

    “Ilbis jadiidan wa ish hamiidan wa mut shahidan”.

    {Allah ya sa} ka sanya sabo, kuma ka rayu kana abin yabo; kuma ka mutu kana shahidi (wanda aka kashe a tafarkin Allah).

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Addu’ar Shiga Da Fita Daga Banɗaki danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Za Ka Mayar Da Gidanka Masarautarka danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunna; wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Addu’ar Fita Daga Masallaci

    Addu’ar Fita Daga Masallaci

    “Bismil-laahi was-salaatu was-salaamu alaa Rasuulil-laahi (Sallallahu Alaihi Wasallam), Allaahumma inni as’aluka min fadhlika, Allaahumma’asimnii minas-shaiɗaanir rajiimi”.

    {Da sunan Allah, tsira da aminci su tabbata ga Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam). Ya Allah! Ina roƙonka daga falalarka. Ya Allah! Ka kare ni daga shaiɗan tsinanne}.

    Domin karanta cikakken bayani akan Addu’o’in Kiran Sallah danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Addu’a Idan Mutum Ya Yi Fushi danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunna wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Addu’ar Tashi Daga Majalisi

    Addu’ar Tashi Daga Majalisi

    Addu’ar Tashi Daga Majalisi (Domin Neman Yafewa Ga Abin Da Ya Gudana A Cikin Majalisin).

    A’isha, Allah ya yarda da ita, ta ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam), bai taɓa zama a wani majalisi ba, ko ya karanta Alƙur’ani, ko ya yi wata sallah face ya cika da waɗannan kalmomi:

    “Subhaanakal laahumma wa bi hamdika ashhadu an laa ilaaha illaa anta astagfiruka wa atuubu ilaika”.

    {Tsarki ya tabbata gare ka, ya Allah, da yabo gare ka. Ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai kai; ina neman gafararka, kuma ina tuba zuwa gare ka}.

    Sai A’isha ta ce:- “Ya Manzon Allah! Na lura cewa ba ka taɓa zama a wani majalisi ba, ka yi karatun Alƙur’ani, ko ka yi sallah face ka faɗi waɗannan kalmomi. Sai ya ce: “Ƙwarai. Duk wanda ya faɗi wani alheri sai waɗannan kalmomi su zama kamar hatimi ne ga alherin da ya aikata, wanda kuma ya faɗi sharri, sai su zama kaffara ne gare shi”.

    Domin karanta cikakken bayani akan Addu’a A Lokacin Da Mutum Zai Haw Abin Hawa danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Ladubban Addu’a A Musulunci danna nan.

    Edita; RMK