Tag: Ibada

  • Shin Idan Naga Watan Ramadan, Zan Yi Shiru Nena Ɗauki Azumin Ni Kaɗai, Ko Yaya Zanyi?

    Shin Idan Naga Watan Ramadan, Zan Yi Shiru Nena Ɗauki Azumin Ni Kaɗai, Ko Yaya Zanyi?

    Amsa: Idan mutum yaga watan azumin Ramadan, zai sanar da hukumar dake da alhakin sanar da al’umma, domin ɗaukar azumin.

    Hujja: “Bilal faɗa wa mutane su tashi da azumi gobe….”

    Marawaici Ibn Abbas. littafi Ibnu Kuzaima, Ibnu Hibban, Nassa’i.

    Domin karanta cikakken bayani akan Menene Sahur? danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Dake Cikin Yin Sahur danna nan.

    Danna link ɗinnan; https://chat.whatsapp.com/JtD82AjZZmo3AtSTaKP05r domin shiga WhatsApp group namu na Ramadan.

  • Wane Ne Azumin Ramadan Ya Wajaba Akansa?

    Wane Ne Azumin Ramadan Ya Wajaba Akansa?

    Amsa: Wanda azumin Ramadan ya wajaba akansa, shine wanda gashin mara ya fito masa, mace ko namiji.

    Hujja: “Shari’ar Musulunci bata aiki akan mutum uku, su ne: Ƙaramin yaro har sai ya balaga….”

    Marawaicin Aliyu ibn Abi Ɗaalib, Ummuna A’isha, littafi Musnadu Ahamada.

    Domin karanta cikakken bayani akan Mutum Nawa Ne Ake Buƙatar Suga Wata Kafin A Ɗauki Azumi? danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Waɗanne Abubuwa Ne Na Fili Dake Karya Azumi? danna nan.

    Danna link ɗinnan; https://chat.whatsapp.com/JtD82AjZZmo3AtSTaKP05r domin shiga WhatsApp group namu na Ramadan.

  • Da Me Zan Dogara Wajen Ɗaukar Azumin Ramadan; Shin Sai Naga Watan Ramadan Da Idanuna Ƙuru-Ƙuru?

    Da Me Zan Dogara Wajen Ɗaukar Azumin Ramadan; Shin Sai Naga Watan Ramadan Da Idanuna Ƙuru-Ƙuru?

    Amsa: Mutum zai dogara ne da abin da shari’ar Musulunci ta umarce shi yayi; shi ne ya ɗauki azumi da zarar hukuma ta sanar daɗaukar azumin, ko kuma  ajiyeshi.

    Hujja: “Ku ɗauki azumin Ramadan da zarar kunga jaririn wata,ku ajiye azumi da zarar kunga jaririn watan Shawwal”

    Marawaiji Ibn Umar, littafin Bukhari & Muslim.

    Domin karanta cikakken bayani akan Wane ne azumin Ramadan ya wajaba akansa? danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Niyyar Ɗaukan Azumi danna nan.

    Danna link ɗinnan; https://chat.whatsapp.com/JtD82AjZZmo3AtSTaKP05r domin shiga WhatsApp group namu na Ramadan.

  • Jan Hankali Game Da Sallar Asuba

    Jan Hankali Game Da Sallar Asuba

    Sallar Asuba itace mafi Alheri fiye da barci, mu rage barci don mu ribanta da goben mu.

    Barci amsawar zuciya ne; ita kuwa sallah amsawar kiran Ubangiji ne.

    Barci mutuwa ne; ita kuwa sallah rayuwa ce.

    Shi barci hutu ne na gangar jiki; sallah kuwa hutu ne na ruhi.

    Shi baci, da mumini da kafiri duk suna yinsa ita kuwa sallah mumini ne kaɗai yake yinta.

    Masu tashi lokacin futowar Alfijir sun rabauta, fuskarsu kuma ta haskaka; goshinsu kuma yayi haske da ƙyalli, lokacin su kuma yayi Albarka. Idan kana cikinsu toh ka godewa ALLAH daya fifita ka, idan kuwa baka cikinsu toh ka roƙi ALLAH Ya saka ka cikin su.

    Amma menene yafi Alfijir kyau?

    Farillarsa (Sallar Asuba) zata saka ka acikin kulawar Ubangiji

    Sunnarsa (Rak’ataanil fajr) ta fi Duniya da abinda ke cikinta (Hadeeth)

    Ita Sallah Asuba da Mala’iku masu dutyn dare; da Mala’iku masu dutyn safe duka suna Halartar ta. Ya kai ɗan’uwa, ya ke yar’uwa, kisani fa kaima kasani duk wanda ya rayu akan wani toh akansa zai mutu, wanda ya mutu kan wani aiki kuma akansa za’a tashe shi.

    Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Raka’atil Fajr danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Nafilolin Sallah danna nan.

  • Halayen Da Ya Kamata Mai Azumi Ya Siffantu Da Su

    Halayen Da Ya Kamata Mai Azumi Ya Siffantu Da Su

    Halayen mai Azumi – Akwai waɗansu muhimman halaye da ya kamata mai azumi ya siffanta da su; a gan su da gaske a tattare da shi. Cikin halayen akwai:

    1. Haƙuri, wato mai azumi ya siffantu da haƙuri wanda shi zai zama jagaba a cikin lamuransa; ya hana shi bin son zuciya da saɓa wa Allah. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce “Idan ɗayan ku yana azumi, kada ya yi maganganun fasiƙanci. Idan wani ya zage shi, ya ce Ni mai azumi ne” (Sahihul Bukhari 1894, Sahih Muslim 1151).

    2. Riƙon amana, yana da kyau mai azumi ya zama mai riƙon amana; domin tana daga cikin abar da za ta taimaka masa wajen kiyaye azuminsa.

    3. Rahama, ana son mai azumi ya siffantu da rahama, da sakin hannu da karamci, da kuma yalwar zuciya. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Duk wanda ya ciyar da mai azumi, yana da kwatankwacin ladan wanda ya ciyar ba tare da an rage ladan wanda aka ciyar ɗin ba” (Sunan al-Tirmizi 647, Sunan Ibn Majah 17).

    4. Nasiha, yana da kyau mai azumi ya kasance mai yin nasiha da kuma umarni da kyakkyawa da hani ga mummuna.

    5. Sulhu, mai azumi yana da kyau ya kasance mai yin sulhu da sasanta mutane; musamman la’akari da cewa ƙiyayya da gaba na kawo tsaiko wajen karɓar ibada da addu’a.

    6. Kame harshe, ya kamata mai azumi ya kame harshensa daga maganganu na shirme da shashanci, sannan ya nesanci giba, zagin mutane da yi musu ƙage ko sharri da ƙarya ko musu marar dalili; musamman abin da ya shafi siyasa ko wasan ƙwallo ko wanin waɗannan.

    An karbo hadisi daga Abu Huraira (Radiyallahu Anhu) cewa; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Wanda duk bai bar faɗin magana ta zur da aiki da ita ba; to Allah ba shi da buƙatar ya bar cinsa da shansa”. (Bukhari 4/99).

    Haka nan wani hadisin dai daga Abu Huraira (Radiyallahu Anhu) dake cewa; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Ba azumi ba ne barin ci da sha, shi azumi shi ne na yasasshen zance da batsa; ko da wani ya zage ka, ko ya yi maka wauta, to ka ce; “Ni mai azumi ne”. (Ibn Khuzaima 1996). Ibnu Majah ya fitar da hadisi mai ɗauke da razani ga mai yin maganganun banza a yayin da yake azumi, ya ce; “Sau da yawa wani mai azumin ladansa shi ne yunwa da ƙishirwa”.

    7. Rintse ido da kame farji, yana da kyau mai azumi ya rintse idanuwansa daga kallon haramun; ya kuma kare farjinsa daga dukkanin haramtattun abubuwa. A nan muna jan hankalin waɗanda ke ganin kallon fina-finai ko tashoshi na gusar musu da yunwa; haƙiƙa wannan kuskure ne babba da kuma munana zato ga Allah, da kuma keta iyakokin Sa. Su ma masu sanya fina-finai a tashoshi wajibi su ji tsoron Allah; su sani ribar rayuwa da albarkar abin da suke so shi ne ginawa bisa tafarkin Musulunci.

    8. Iklasi, ya kamata mai azumi ya ƙudurce cewa lalle yana yin wannan azumin ne saboda Allah; kuma domin neman yardar Allah, ba domin mutane su yabe shi ba. A nan, ana jan hankalin yan’uwa masu yin sadaka ko ciyar da masu azumi da masu tafsirin Alkur’ani; da limamai masu rera tilawa, da masu zuwa Umarah, da sauran aiyuka nagari; wajibi su sanya iklasi kada shaiɗan ya lalata musu ayyukansu.

    9. Bin sunnar Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam); wajibi ne mai azumi ya nesanci bidi’o’i, ya tsaya kan sunna ka’in da na’in; domin kyakkyawan aiki yana cikin koyi da Fiyayyen Halitta (Sallallahu Alaihi Wasalam).

    10. Tarbiyya, wajibi ne mai azumi ya tsaya wajen ƙoƙarin tarbiyyantar da kansa da ‘ya’yansa; ko ‘yan’uwansa ko waɗanda yake da iko a kansu. Kuma iyaye su ɗauki wannan wata a matsayin lokacin roƙarwa ‘ya’yansu shiriya.

    Domin karanta cikakken bayani akan Mafifitan Aiyukan Mai Azumi danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Azumin Tasu’a Da Ashura danna nan

    Wannan bayanin anciro shine daga Littafin Guziri Ga Mai Azumin Ramadana (Bisa Koyarwar Alƙur’ani Da Sunnah); wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Niyyar Ɗaukan Azumi

    Niyyar Ɗaukan Azumi

    Ana ɗaukar niyyar azumi ne kafin fitowar alfijir; saboda hadisin da Nana Hafsat (R.A) ta rawaito daga Manzon Allah (S.A.W) cewa: “Wanda bai ɗauki niyyar azumi da dare ba (kafin fitowar alfijir) ba shi da azumi”.

    (Sheikh Nasiruddeen Albani ya yi tahƙiƙinsa a cikin Sahih Jami’ al-Saghir, 6536).

    Sannan a yayin niyya, ba a ƙulla ta da lafazin cewa, na yi niyyar yin azumi, a’a ana ƙulla ta ne a zuci, da zimmar gobe zan tashi da azumi idan Allah ya kai mu rai da lafiya.

    Domin karanta cikakken bayani akan Mafifitan Ayyukan Mai Azumi danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Shin Rashin Yin Sallah A Cikin Jama’a Na Lalata Azumi? danna nan.

    Wannan bayanin anciro shine daga Littafin Guziri Ga Mai Azumin Watan Ramadan (Bisa Koyarwar Alƙur’ani Da Sunnah); wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Mafifitan Ayyukan Mai Azumi

    Mafifitan Ayyukan Mai Azumi

    Ayyukan Mai Azumi – Akwai ayyuka mafifita da ya kamata mai azumi ya kusance su; daga ciki akwai:

    1. Karatun Alƙur’ani Mai Girma, wato mai azumi ya lazimci karatun Alƙur’ani da kuma fahimtar saƙon da yake cikinsa, amma idan ba za a iya karatun ba, to babu laifi a lazimci majalasin karatun, wato wajen da ake karantawa tare da fassara Alƙur’ani.

    Nana A’isha, Abu Huraira da Ibn Abbas (Radiyallahu Anhuma), sun faɗa cikin hadisin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) cewa, “Mala’ika Jibrilu ya kasance yana karanta wa Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) Alƙur’ani a kowane dare na watan Ramadana, sau ɗaya a kowacce shekara, sai ya karanta masa sau biyu a shekarar da zai yi wafati”. (Sahihul Bukhari 4997 – 4998, Sahihu Muslim 2450).

    Wannan hadisi ya nuna cewa karatun Alƙur’ani shi ne mafificin aikin ibada ga mai yin azumi a watan Ramadana, don haka, sai a himmatu da karatunsa.

    2. Kyauta, ana son mai azumi ya yawaita kyauta ta hanyar ciyar da jama’a da kuma sakin hannu gare su, da taimakon gajiyayyu da makusanta. An karɓo hadisi daga Abdullahi Ibn Abbas (Radiyallahu Anhu) cewa, Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya fi kowa kyauta, kuma ya fi yawaita kyautarSa a cikin watan Ramadan, musamman a lokacin da yake ganawa da Mala’ika Jibrilu. (Bukhari 4997).

    Haka nan Ibn Abbas (Radiyallahu Anhu) ya ce, “Alherin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya fi sakakkiyar iska”. (Bukhari 1902).

    3. Sallar Nafila, ana so mai azumi ya yawaita nafila, musamman Ƙiyamul Laili (wato sallar dare); saboda kwaɗaitarwar da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya yi cikin hadisin Abu Huraira (Radiyallahu Anhu) cewa, “Duk wanda ya tsaya yin sallar Ƙiyamul Laili, yana mai imani da neman lada, za a gafarta masa zunubansa da suka gabata”. (Bukhari 2009).

    Haka nan cikin hadisin Abu Dharrin Alghiffariy (Radiyallahu Anhu) ya ce; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce, “Wanda ya yi sallar asham tare da liman, har ya idar, za a rubuta masa ladan ƙiyamul laili”. (Sunan Tirmizi 646, Ibnu Majah 1327).

    4. Yawaita zikiri, ana son mai azumi ya yawaita yin zikiri da salatin Fiyayyen Halitta (Sallallahu Alaihi Wasalam); domin akwai gwaggwaɓan lada ga yin zikiri da salatin Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam).

    5. Ciyar da mai azumi abin buɗa-baki, yana daga cikin mafificiyar ibada ciyar da masu azumi abin buɗa-baki. Hadisi ya tabbata daga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) cewa; “Duk wanda ya ciyar da mai azumi abin da zai yi buɗa-baki, yana da kwatankwacin ladan mai azumin, ba tare da an rage ladan wanda ya ciyar ba”. (Sunan Tirmizi 647, Ibnu Majah 1746).

    A nan, muna jan hankalin masu hali a kan su taimaka wa mabuƙata, musamman makusantansu. Domin za ka iske mutumin da yake da hali a unguwa; amma kaso mafi yawa suna rasa abin da za su yi buɗa-baki, a wani lokacin kuma, masu ƙoƙarin yin sadakar ma, za ka iske suna yi ne cikin rashin kyautatawa, face kaɗan. Yana da kyau masu hali da shugabanni su gane, taimakawa a irin wannan lokaci; cikin iklasi da neman yardar Allah, wallahi rabautuwarsu ce. Amma ina tausayi da rahama, kai ka ci mai kyau, amma maƙwabtanka suna fama da yunwa!

    Yana da kyau ku ciyar daga mafi kyawun dukiyarku; kuma cikin abu mai kyau; tare da sakin zuciya da jin dadi da walwala.

    6. Umarah, yin Umarah cikin watan Ramadana na daga cikin mafifitan ayyuka; don haka, mutumin da yake da iko sai ya ɗauki azama. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce, “Yin Umarah a cikin watan Ramadan daidai yake da aikin Hajji”. A wata ruwayar kuma Ya ce, “Wanda ya yi Umarah a watan Ramadan; tamkar ya yi aikin Hajji ne tare da Ni”. (Sahihul Bukhari 863).

    A nan ma, muna ƙara jan hankali, musamman ga waɗanda sun yi Umara; amma suna ta ƙara maimaitawa, alhali maƙwabtansu na fama da yunwa, da baƙin talauci. Ku sani, duk da wannan falala ta Umara ta nafila; duk da wannan lada, ciyarwa ita ta fi sama da Umarar da za ka tafi, alhali ga maƙwabtanka; ko danginka na fama da yunwa, da wahala ta rashin abin da za su ci, idan za su yi sahur; ko za su ci, idan za su yi buɗa-baki.

    Kuskure ne alhazan ke yi, sun je, ba sau ɗaya ba; ba sau biyu ba, su ƙara niƙar gari su tafi, alhali ga mabuƙata nan a kewaye da su.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Abubuwan Da Suke Ɓata Azumi danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Azumin Watan Muharram danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Guziri Ga Mai Azumin Ramadana (Bisa Koyarwar Alƙur’ani Da Sunnah); wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi; Don karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Idan Nayi Haɓo Da Azumi A Bakina, Yaya Azumina Zai Kasance?

    Idan Nayi Haɓo Da Azumi A Bakina, Yaya Azumina Zai Kasance?

    Idan Nayi Haɓo Da Azumi A Bakina Kafina Sha Ruwa, Yaya Azumina Zai Kasance?

    Amsa: Duk wanda haɓo ya same shi, kuma da azumi abakinsa, babu komai, azuminsa na nan daram.

    Hujja: (Daarul Ifata’i Almisiriya). (Alajnatu da’ima lilbuhusul ilmiya wal ifta’i 10/264).

    Domin karanta cikakken bayani akan Ina Alwala, Na Haɗiye Ruwa Garin Kurkure Baki, Yaya Lafiyar Azumina? danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Idan Na Ɗanɗana Miya, Na Tofar Ban Haɗiye Ba, Ya Batun Azumina? danna nan.

  • Idan Na Ɗanɗana Miya, Na Tofar Ban Haɗiye Ba, Ya Batun Azumina?

    Idan Na Ɗanɗana Miya, Na Tofar Ban Haɗiye Ba, Ya Batun Azumina?

    Idan na ɗanɗana miya domin naji fitowar gishiri, amma na tofar ban haɗiye ba, yaya batun azumina?

    Amsa: Idan mutum ya ɗanɗana miya, gishiri, suga, zuma, zobo, juicy, azuminsa na nan matsawar bai haɗiye ba.

    Hujja: “Wanda yaci ko ya sha, bisa mantuwa, azuminsa yana nan”.

    Marawaici Abu Huraira, littafi Sahihul Bukhari Sahihu Muslim.

    Domin karanta cikakken bayani akan Idan Na Shaƙi Mantaleta, Rob Ko Na Saka Aleɓe, Ya Makomar Azumina? danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Watan Ramadana 1 danna nan.

  • Ina Alwala, Na Haɗiye Ruwa Garin Kurkure Baki, Yaya Lafiyar Azumina?

    Ina Alwala, Na Haɗiye Ruwa Garin Kurkure Baki, Yaya Lafiyar Azumina?

    Amsa: Mutumba zai rama azumi ba, idan ya haɗiye ruwa lokacin kurkurar baki, bada ganganci ba; a cikin alwala ko ba acikin alwala ba.

    Hujja: “Allah ya yafewa al’ummata abubuwa guda uku, kuskure da mantuwa da kuma abinda aka tilasta su a kai”.

    Marawaici Ibn Abbas, Sunan Ibn Maajah, Sahihu Ibnu Hibban, Mu’ujamu Ɗabara’ni.”Ba ku da laifin abinda kuka yi bisa kuskure, sai abinda zuciyarku tayi da gangan”. Suratul Ahzab aya 5.

    Domin karanta cikakken bayani akan Idan Na Ɗanɗana Miya, Na Tofar Ban Haɗiye Ba, Ya Batun Azumina? danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Azumin Ranar Arfa danna nan.