Yadda Mutum Zai Kasance Mai Wadatar Zuci

0
426

1) Wadatuwa da abin da Allah ya ba ka.

2) Karanta rayuwar magabata na ƙwarai da gudun duniyar su, da wadatar zucinsu da koyi da su.

3) Gudanar da rayuwa matsakaiciya, ba ƙwauro babu kuma almubazzaranci.

4) Yawaita addu’a, Allah ya azurta ka da wadatar zuci kamar yadda Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yake cewa; “Ya Allah ina roƙon ka shiriya, da taƙawa da kamewa da wadatar zuci”

5) Yin cikakken imani cewa kowa a duniyar nan arzikinsa yake ci, tuni Allah ya gama raba arziki, babu yadda za a yi wani ya ci rabon wani.

6) Tursasa zuciya a kan yarda rabon ta da arzkin da Allah ya ba wa mutum da nisantar kwaɗayi, da sa ido a kan abin hannun mutane.

7) ƙarfafa imani da Allah da amincewa da shi

8) Kullum ka rinƙa duban na ƙasa da kai, ka da ka rinƙa duban na sama da kai.

9) Yarda da cewa Allah ta’ala ya ƙaddara lallai sai wani ya fi wani wadata. Tilas ka ga wasu sun fi ka, amma kuma ka fi wasu; wasu kuma kun yi daidai, haka Allah yai tsarinsa, to ina dalilin damuwa?

10) Ka yawaita tunanin mutuwa da ziyartar maƙabarta, sai ka ji duk abin duniya ma ba ya ɗaɗa ka da ƙasa, domin ƙarshe dai ko me aka samu mutum zai tafi ya bar shi.

11) Yawaita karanta Alƙur’ani da la’akari da ayoyin da suke magana a kan arziki da talauci da kuma haƙiƙanin ita kanta duniyar.

12) Ka sani cewa girma da mutunci yana cikin wadatar zuci, shi kuwa kwaɗayi da talaucin zuci, ba ya haifar da komai sai ƙasƙanci da wulaƙanci.

Domin karanta cikakken bayani a kan Hikimomi Akan Wadatar Zuci danna nan.

Domin karanta cikakken bayani a kan Harsashin Gina Al’umma (Iyaye) danna nan.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Jerin Littafan Hadisai Arba’in (40) Littafi Na Biyu; Akan (Falalar Wadatar Zuci, Neman Halal Godiya Ga Allah Da Illolin Bara Da Roƙo); wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

labarin da ya wuceDabarun Zaman Lafiya Da Mutane
Labarin na GabaƘa’idoji Da Laduban Neman Halal