Wajibcin Karatun Fatiha A Cikin Sallah

0
536

Karatun fatiha ga kowanne mai yin sallah wajibi ne; babu sallah ga wanda bai karanta Fatiha ba, sai dai banda mutum 1, wato sabon musulunta da bai iya karanta komai cikin Alqur’ani ba; zai yi sallah a haka, koda bai iya Fatiha ba.

Amma sai a ba shi sunan Allah da zai yi masa kirari da shi, da kalmomin neman gafara da rahama da shiriya; wanda zai nemi Allah ya yi masa amadadin karatun Fatiha kafin ya koyi yadda ake karanta ta.

Haka kuma, karanta Fatiha ɗin a tsaye wajibi ne, sai dai idan mutum yana da larura, misali; mara lafiya da ba zai iya sallah a tsaye ba, sai a zaune; ko mai buƙata ta musamman da ba shi da ƙafafun da zai tsaya.

Yana da kyau ga mai yin sallah shi kaɗai ko limanci idan ya zo aya ta ƙarshen Fatiha ya ce; “Aamiin”. Wato Allah ka amsa mana.

Haka kuma, mamu dake bin limami sallah, su ma su ce, “Aamiin”, idan mutum ya dace wajen faɗar kalmar Aamiin, tare da mala’iku, Allah zai masa gafara.

Domin karanta cikakken bayani akan Zaɓi Ga Maamu Wajan Karatun Fatiha A Cikin Sallah danna nan.

labarin da ya wuceMuhimmancin Aure a Ƙasar Hausa
Labarin na GabaYadda Za Ki Kula Da Fatarki
Lawan Bello
Abu muzaffar Malami ne masanin ilimin zamani da na addini bisa tsaren Ƙur'ani da tafarkin manzon Allah sallallahu alaihi wa sallam, mai hangen nisa a addini da kuma alummma, shugaban Abu Muzaffar foundation.