Tag: sallah

  • Falalar Salla A Masallacin Haramin Makka Da Madina

    Falalar Salla A Masallacin Haramin Makka Da Madina

    An karɓo daga Abu Hurairah (Radiyallahu anhu) ya ce: Haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalam) yace; “Salla a masallaci na ta fi salla a wani masallaci sau dubu ban da masallaci mai alfarma”(Bukhari 1190 Muslim 1394).

    An karɓo daga Abdullahi Ibn Zubair (Radiyallahu anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalam) yace: “Salla a masallaci na tafi salla dubu a sauran masallatai ban da masallacin harami, kuma salla a masallacin harami tafi salla dubu ɗari a wannan masallacin” (Ahmad, Ibn Khuzaimaha, Suhihul Jami’I 3841).

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Falalar Zama A Madina Ya Ke danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Sallar Idi danna nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Yadda Falalar Zikiri Bayan Sallar Asuba Har Zuwa Ɓullowar Rana Ya Ke

    Yadda Falalar Zikiri Bayan Sallar Asuba Har Zuwa Ɓullowar Rana Ya Ke

    An karɓo daga Anas ɗan Malik (Radiyallahu Anhu) yace; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) yace; “Wanda ya yi sallar asuba a cikin jam’i, sannan ya zauna yana ambaton Allah har rana ta ɓullo; sannan ya yi salla raka’a biyu za a ba shi lada hajji da umra cikakku, cikakku, cikakku (Tirmizi 586).

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Falalar La Ilaha Ilallahu Ta Ke danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Ƙulhuwallahu Ahad danna nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Sallar Idi

    Sallar Idi

    Idin musulmi guda biyu ne, idin buɗa baki (karamar sallah), bayan watan Ramadan, da idin layya (Babbar sallah) bayan ranar Arfah. Allah Maɗaukakin Sarki ya canza mana da su daga idikan jahiliyya da ma duk wani idi ƙirƙirarre.

    An karɓo daga Anas ɗan Malik (Allah ya yarda da shi)ya ce, Mutanen jahiliyya suna da kwana biyu a shekara da suke wasa a cikinsu, yayin da Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم ) ya zo Madinah, sai ya ce, “Kuna da kwana biyu da kuke wasa a cikinsu, kuma haƙiƙa Allah ya sauya musu da waɗanda suka fi su alheri, idin buɗa baki, da idin layya” (Nisa’i ne ya rawaito shi).

    Ba ya halatta a yi tarayya da kafirai a cikin idinsu, saboda idi shi ne babbar alamar kowane addini ta fili, da tsarinsa. Allah Maɗaukakin Sarki ya ce, “Kada ka bi son zuciyarsu wajen barin abin da ya zo maka na gaskiya, kowanne daga cikinku mun sanya masa shari’arsa da tsarinsa” (Suratul Ma’ida aya ta 48).

    Idi a musulunci ya haɗa wasu ibadu da bayyana farin ciki da cin abubuwa daɗaɗa na halal, saboda haka waɗannan kwanaki suka zama kwanakin farin ciki da na jin daɗi, da ci da sha. Ba ya halatta a haɗa idi da abin da ya saɓawa koyarwar musulunci. Misali kamar cakuɗuwar maza da mata, ko tozarta lokutan salloli, ko shan abin da aka haramta, ko wasa da abin da Allah ya haramta, ko jin abin da Allah ya haramta, ko wanin haka daga cikin abubuwan haramun.

    Hukuncin Sallar Idi Biyu

    Sallar idi nafila ce, kuma abar kwaɗayi ne a kan kowane musulmi ya himmatu wajen zuwa idi, saboda ana samun lada mai tarin yawa sosai gami da gafarar Allah (S.W.A). Sannan kuma Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) ya yi umarni da maza da mata su fita zuwa sallar idi, sannan kuma a sadar da zumunta gami da rarraba abinci da abin sha ga mabuƙata.

    Yadda Ake Sallar Idi Biyu

    Sallar idi raka’a biyu ce, ba a kiran sallah, ba a yin iƙama, ana bayyana karatu a cikinsu, ga yadda ake yin su :

    1. Raka’ar farko zai yi kabbara bakwai, bayan ya yi kabbarar harama, sai ya yi addu’ar buɗe sallah, kafin ya fara karatu. Amma a mazahabar Imamu Malik bin Anas, an ware wasu surori, wanda ake buƙata ya karanta a raka’a ta farko kamar Suratul A’ala, ko Suratul Ƙamar.

    2. Idan ya kammala raka’a ta farko, to a raka’a ta biyu, da zarar ya miƙe tsaye, zai yi kabbarta sau biyar ne, sai ya karanta Fatiha da wata surar. Ita ma a raka’a ta biyu a mazahabar Imamu Malik bin Anas an ware wasu surori da ake buƙatar a karanta su; Suratul Ghashiyati ko Suratul Kahfi, ko Suratul Shamsi da sauransu.

    Saboda haka, idan mutum ya duba da kyau, zai ga an yi kabbarori guda goma sha uku, duk da kabbarar harama. Sannan ita sallar idi, ba a yi mata nafila, saboda ita ma nafila ce. Haka kuma sallar idi sai an gama ta tsaf, sannan liman zai ta shi ya yi huɗuba, wanda sauraron huɗuban liman, Allah yana cewa da Mala’iku “Ku shaida dukkanin wanda ya tsaye a wannan wajen, na gafarta masa dukkanin zunubansa”.

    Wurin Da Ake Sallar Idi Biyu

    A sunna dai, shi ne a yi sallar idi a filin sallah, ba a cikin  masallaci ba, wato ita sallar idi ba a so a yi ta a inda yake da rufi, a fili fayau ake buƙatar a yi ta, amma idan  akwai buƙatar haka, wato ruwan sama ya cike inda za a yi sallar, ko kuma ruwan sama ya hana a yi sallar, ko sanyi ya tsananta, ko dai wani abu wanda shari’a ta amince da shi, sai ayi ta kawai a cikin masallacin Juma’a.

    Abubuwan Da Ake So A Idi

    1. Maza su yi ado da kyawawan kayansu, mata kuwa su fita sallah ba tare da ado da turare ba.

    2. Mutane su fito masallaci da wuri.

    3. Canza hanyar tafiya, wato idan mutum ya bi ta wata hanya a lokacin da zai tafi masallaci, to idan zai dawo sai ya canza wata hanyar.

    4. Yawaita kabbara tun daga gida har zuwa masallacin.

    5. Cin dabino kafin a yi sallar idi ƙarama, da kuma cin dabino bayan an yi sallar idi babba (dabino guda uku ko biyar ko bakwai).

    6. An so a jinkirta sallar idi ƙarama, don musulmi ya samu damar bayar da zakkar fidda kai, ga waɗanda ba su gama bayarwa ba.

    Hukunce-hukuncen Idi

    1. An karhanta sallar nafila kafin sallar idi da bayanta, sai dai in a masallaci za a yi ta, to sai a yi gaisuwar masallaci idan an shiga.

    2. Sunna ne idan sallar idi ta wuce, ko wani ɓangarenta ya kubce wa mutum, ya rama ta kamar yadda take, ya sallace ta raka’a biyu da kabbarorinta, haka ma abin da ya rasa daga cikinta ya rama shi kamar yadda take.

    3. Allah Maɗaukakin Sarki ya shara’antawa bayinSa, a ƙarshen Ramadan su yi masa kabbara, Allah ya ce, “Don ku cika adadin kwanakin (azumi), kuma don ku yi wa Allah kabbara a kan abin da ya shiryar da ku”. (Suratul Baƙara yaya 185). Ma’anar ku yi wa Allah kabbara shi ne, ku girmama shi a cikin zukatanku da harsunanku.

    Lafazin kabbarar shi ne : “Allahu Akbarul Lahu Akbar, La’ilaha Illal Lahu, Wal Lahu Akbar, Allahu Akbar, Walillahil Hamdu”.

    4. Sunna ne maza su ɗaga muryarsu da mata kuwa za su ɓoye ta (ƙasa-ƙasa), a lokacin da suke yi waɗancan kabbarorin.

    5. Za a dinga yin waɗancan kabbarorin ne tun daga lokacin da aka ce an ga watan Shauwal (gama azumi) har zuwa lokacin da liman zai shigo masallaci, don yin sallar idi ƙarama, amma kuma idan a sallar idi babba ne, to mutum zai wuce da yin waɗancan kabbarorin ne har zuwa rana ta ukun bayan sallar idi, saboda ana so mutum ya yi waɗancan kabbarorin a gurbin kowace sallah ta ranar idi babba, wanda zai fara tun daga sallar azahar ɗin ranar har zuwa asubahin rana ta uku ga sallah, wanda idan mutum ya lissafa da kyau, zai ga an samu salloli goma sha biyar ke nan.

    Abin Da Ya Kamata Musulmi Ya Yi Ranar Idi

    1. Samun sallar asubar ranar Idi.

    2. Wankan zuwa Idi.

    3. Ba da zakkar fidda-kai ga mabuƙata.

    4. Cin abinci kafin tafiya masallaci (ga ƙaramar sallah, babba kuma sai an dawo).

    5. Sanya tufafi masu kyau.

    6. Takawa zuwa masallaci.

    7. Zikiri yayin tafiya.

    8. Ba a sallar nafila a filin idi.

    9. Sauraron huɗuba bayan sallar idi.

    10. Gaisawa da juna bayan sallah.

    11. Sauya hanyar tafiya wajen dawowa.

    12. Yara da mata da tsoffi duka na zuwa idi.

    13. Mata masu haila za su iya zuwa sallah, amma za su tsaya a gefen guda na masallaci.

    14. Ana son musulmi su yi wa junansu murnar idi.

    15. Ana son bayyana farin ciki da idi, da yi wa`yan uwa da masoya da makusanta murna.

    16. Idi wata dama ce da ya wajaba a ribace ta, don sada zumuncin da aka yanke, da sulhuntawa a tsakanin masu husuma.

    17. Ba shara’anta ziyarar maƙabarta ba a ranar idi, don hakan ya saɓawa farin cikin da annushuwa cikin idi.

    18. An shara’anta yalwatawa iyali da tufafi da abinci da kayan cin daɗi, waɗanda Allah ya halatta, a ranar idi, saboda idi kwanaki ne na farin ciki da annushuwa.

    Domin karanta Addu’ar Daren Lailatul Ƙadri danna nan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’ar Tafiya Zuwa Masallaci

    Yadda Ake Addu’ar Tafiya Zuwa Masallaci

    “Allahumma ja’al ,fii ƙalbii nuuran, wafii lisaanii nuuran, wafii sam’ii nuuran, wafii basarii nuuran, wamin fauƙii nuuran, wamin tahtii nuuran, wa’an yamiinii nuuran, wa’an shamaali nuura, wamin amaamii nuuran, wamin kalfii nuuran, waj’al fii nafsii nuuran, wa a’azim lii nuuran, wa azzim lii nuuran, waj’al lii nuuran, waj’alnii nuuran, Allahumma A’aɗinii nuuran, waj’al fii asabii nuuran, wafii lahmii nuuran, wafii basharii nuuran, Allaahumma ja’al lii nuuran fii ƙabarii, wa nuuran fii izaamii, wa zidnii nuuran, wa zidnii nuurann fii izaamii, wa zidnii nuuran, wa zidnii nuuran, wa hab lii nuuran”.

    {Ya Allah ka sanya haske a cikin zuciya ta, da haske a kan harshena, da haske a ji na; da haske a gani na, da haske a ɓirɓishi na, da haske a ƙarƙashi na, da haske a baya na; ka sanya haske a cikin rai na, ka girmama haske gare ni, ka sanya ni (na zama) haske; ka sanya haske a cikin jijiyoyi na, da haske a cikin nama na, da haske a cikin jini na; da haske a cikin gashi na, da haske a cikin fata ta. Ya Allah ka sanya mini haske a cikin ƙabari na, da haske a cikin ƙasusuwa na; ka ƙara mini haske, ka ƙara mini haske, ka ƙara mini haske, ka ba ni haske a kan haske}.

    Domin karanta cikakken bayani akan Addu’ar Shiga Masallaci danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Addu’ar Ismullahil A’azim danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunna; wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Addu’ar Shiga Masallaci

    Addu’ar Shiga Masallaci

    “A’uzu bil-laahi aziimi, wabi wajhihil kariimi, wa sulɗaanihil ƙadiimi, minas-shaiɗaanir rajiimi. Bismil-laahi, was-salaatu was-salaamu alaa Rasuulil-laahi, Allaahummaftahlii abwaaba rahmatika”.

    {Ina neman tsarin Allah Mai girma, da na Fuskarsa mai Alfarma, da na Mulkinsa daɗaɗɗe, daga shaiɗan tsinanne. Da sunan Allah, tsira da aminci su tabbata ga Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam). Ya Allah! Ka buɗe mini ƙofofin rahamarka}.

    Domin karanta cikakken bayani akan Addu’ar Fita Daga Masallaci danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Nafilolin Sallah danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunna; wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Addu’o’in Kiran Sallah

    Addu’o’in Kiran Sallah

    Wanda ya ji kiran sallah zai faɗi dukkan abin da ladanin yake faɗi, sai dai idan ya ce:

    “Hayya alas-salaati (da) Hayya alal falaahi”.

    {Ku taho ga sallah; ku taho ga babban rabo}.

    A maimakon haka sai shi ya ce:

    “Laa haula walaa ƙuwwata illaa bil-laahi.

    {Babu dabara, babu ƙarfi sai da Allah}.

    Bayan ladanin ya yi kalmar shahada, sai shi kuma (mai sauraron) ya ce:

    “wa’ana Ashhadu an laa ilaaha illallaahu wahdahu laa shariika lahuu wa’anna Muhammadan abduhu warasuuluhu, radhiitu bil-laahi Rabban, wabi Muhammadin Rasuulan wabil Islaami diinan”.

    Bayan ya gama amsa kiran sallar, sai ya yi salati ga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam). Sannan kuma sai ya ce:

    “Allaahumma Rabba haazihid da’awatit tammati was-salaatil ƙaa’imati ati Muhammadan wasiilata wal fadhilata wab’as’hu maƙaaman mahmuudal lazii wa’adtahu innaka laa tukhliful mii’adi”.

    {Ya Allah! Ubangijin wannan kira kammalalle, da wannan sallar da za a tsayar da ita, ka ba wa Muhammadu (Sallallahu Alaihi Wasallam) wasila (matsayin kusanci a Aljanna), da Matsyin fifiko, kuma ka tashe shi a matsayin abin godewa, wannan wanda ka yi masa Alƙawarinsa. Lalle kai ba ka saɓa Alƙawari}.

    Sannan ya yi wa kansa addu’a a tsakanin kiran sallah da tayar da iƙama, domin addu’a a wannan lokaci ba a ƙin karɓar ta.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Addu’a A Yayin Sujjada danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Abin Da Ya Kamata Mai Yin Sallah Ya Yi Bayan Ya Tafi Sujudah danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunna; wanda Sheikh Sa’id Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Addu’a A Yayin Sujjada

    Addu’a A Yayin Sujjada

    “Subhaana Rabbiyal a’alaa”.

    {Tsarki ya tabbata ga Ubangijina mafi ɗaukaka}. Sau uku (3).

    “Subhaanakal laahumma rabbanaa wa bihamdika Allaahummagfir lii”.

    {Tsarki ya tabbata gare ka, ya Allah! Ya Ubangijinmu! Tare da godiya gare ka. Ya Allah! Ka gafarta mini }.

    “Subbuhun ƙuddusuun Rabbul Mala’ikati war ruuhi”.

    {(Ubangiji) abin tsarkakewa, mai kuɓuta daga dukkan abin da bai kamace shi ba, Ubangijin Mala’iku da Jabrilu}.

    “Allaahumma laka sajadtu wa bika aamantu, walaka aslamtu sajada wajhii lillazii khalahu wa sauwarahu wa shaƙƙa sam’ahu wa basarahu tabaarakal laahu ahsanul khaaliƙiina”.

    {Ya Allah! Gare ka na yi sujada, kuma da kai na yi imani, kuma gare ka na miƙa wuya. Fuskata ta yi sujada ga wanda ya halicce ta. Kuma ya yi mata sutura, kuma ya tsaga ji da gani a gare ta. Allah mafi gwanintar masu halitta, ya girma, kuma alherinsa ya yawaita}.

    “Subhaana zil jabaruuti, wal malakuuti, wal kibriyaa’i, wal azamati”.

    {Tsarki ya tabbata ga (Allah) Mai dole, da mulki, da ƙasaitar ɗaukaka da girma}.

    “Allaahummagfil lii zanbii kullahu, diƙƙahu wa jillahu, wa auwalahu wa akhirahu wa alaaniyatahu wa sirrahu”.

    {Ya Allah! Ka gafarta min zunubaina dukkanninsu, ƙanananansu da manyansu, na farkonsu da na ƙarshensu, bayyanannunsu da ɓoyayyunsu}.

    “Allaahumma inni a’uzu bi ridhaaka min sakhaɗika, wabi mu’aafaatika min uƙuubatika wa a’uzu bika minka, laa uhsii sanaa’an alaika anta kamaa asnaita alaa nafsika”.

    {Ya Allah! Ina neman tsari da yardarka daga fushinka, da kuma rangwamanka daga uƙubarka, kuma ina neman tsari da kai daga gare ka. Ban isa na tuƙe ga yabo mai cancanta gare ka ba; kai dai kamar yadda ka yabi kanka ne}.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Tahiyya danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Yin Ruku’u danna nan.

    Wannan bayanin anciro shi ne daga littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunna; wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Yadda Ake Tahiyya

    Yadda Ake Tahiyya

    Attahiyyaatu lil-laahi was salawaatu waɗɗayyibaatu, assalaamu alaika ayyuhan nabiiyu wa rahmatul-laahi wabarakaatuhu, assalaamu alaina wa alaa idadil-laahis saalihiina. Ashhadu an laa ilaaha illallaahu, wa Ashhadu anna Muhammadan abduhu warasuulahu”.

    {Dukkan nau’in ban girma ya tabbata ga Allah, da kuma salloli da kyawawan kalmomi. Aminci ya tabbata gare ka ya Annabi. Da rahamar Allah da albarkatunsa. Aminci ya tabbata gare mu, da kuma ga bayin Allah salihai. Ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma ina shaidawa cewa Annabi Muhammadu (Sallallahu Alaihi Wasalam) bawansa ne kuma Manzonsa ne}.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Salati Ga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) Bayan Tahiyya danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Sallar Kisfewar Rana Da Wata (Zazzaɓin Rana Da Wata) danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunna; wanda Sheikh Sa;id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Ɗagowa Daga Ruku’u

    Ɗagowa Daga Ruku’u

    Ɗagowa Daga Ruku’u: Bayan kowacce gaɓa ta koma mazauninta; ya tsaya daram kar ya mayar da hannuwansa kan ƙirjinsa, wato; (Qabdu) su ne kaɗai zai bar su a sake kamar yadda mafi yawan malamai suka ce.

    Sannan sai ya yi kabbara, ya tafi sujuda; zai tafi sujuda ne da hannuwansa a wajan wasu malamai; ko da gwuiwar kafafunsa, a wajan wasu malamai ana so ya saɓawa yadda raƙumi ke faɗuwa idan zai kwanta.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Tafiya Sujudah danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Yin Sallar Istihara danna nan.

  • Yadda Ake Yin Tasbihi A Ruku’u

    Yadda Ake Yin Tasbihi A Ruku’u

    Tasbihi A Ruku’u: Mutum zai yi tasbihi a lokacin da ya yi ruku’u kamar haka; “Subahaana Rabbiyal Azim wabi hamdihi” sau uku ko kasa da uku.

    Ba zai ɗago daga ruku’u ba, har sai kowace gaɓa da ya malƙwasa ta ta koma mazaunin ta shi ne gwargwadon yadda tsayin ruku’un nasa zai zama.

    Haka kuma idan yana ɗagowa daga ruku’u zai ce “Sami Allahu liman hamidah” da zaran ya tsaya daram kuma sai ya ce,

    “Rabbana lakal hamdu ko walakal hamdu”.

    Zai tsaya gwargwadon yadda kowacce gaɓa za ta koma mazauninta kafin ya tafi sujudah.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ɗagowa Daga Ruku’u danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Sallar Alwala Da Falalarta danna nan.