Tag: Ramadan

  • Waɗanne Abubuwa Ne Ke Lalata Azumi A Ɓoye?

    Waɗanne Abubuwa Ne Ke Lalata Azumi A Ɓoye?

    Amsa: Abubuwan dake lalata azumi a ɓoye su ne:

    Akwai yi da wani da shaidar zur da gulma da ƙin yin sallah sai lokacinta ya wuce, babu wani dalili na shari’ah, ƙin yin sallah kwata-kwata.

    Hujja: “Wanda duk bai bar zancen zur ba, da aikata zur, da yiwa mutane mummunar fassara; Allah baya buƙatar yabar abincinsa da abin shansa”.

    Marawaici Abu Huraira, littafi Sahihul Bukhari da Sahihu Muslim.

    Domin karanta cikakken bayani akan Shin Rashin Yin Sallah A Cikin Jama’a Na Lalata Azumi? danna nan

    Domin karanta cikakken bayani akan Dalilan Wajabcin Azumin Ramadana danna nan.

  • Waɗanne Abubuwa Ne Na Fili Da Ke Karya Azumi?

    Waɗanne Abubuwa Ne Na Fili Da Ke Karya Azumi?

    Amsa: Abubuwan fili da suke karya azumi su ne:

    Cin abinci ta hanyar tauna ko haɗiya.

    Shan ruwa ko wani abin sha mai kama da ruwa.

    Kwanciyar aure ga masu aure.

    Fitar da maniyi ga wanda ba shi da aure ta hanyar kallace-kallace a fili ko mujalla ko wayoyin hannu ko talabijin.

    Sauraran labaran batsa, ko na motsa sha’awa kai tsaye daga wani ko ta hanyoyin sadarwa da gangan.

    Hujja: “Wanda yaci, ko ya sha, ko ya kusanci iyalinsa, ya karya azuminsa”.

    Marawaici: Abu Huraira, littafi Sahihul Bukhari da Sahihu Muslim, Sunan Abu Dawud, Sunan Turmuzi, Sunan Nassa’i Sunan Ibn Maajah.

    Domin karanta cikakken bayani akan Waɗanne Abubuwa Ne Ke Lalata Azumi A Ɓoye? danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Azumin Watan Ramadana 2 danna nan.

  • Falalar Azumin Watan Ramadana 2

    Falalar Azumin Watan Ramadana 2

    Azumin watan Ramadana na da falala mai yawa, daga cikin falalar akwai:

    1. Azumi garkuwa ne. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam); ya umarci wanda sha’awar aure ta yi tsanani gare shi da ya yi azumi, sai ya sanya azumin garkuwa ne ga sha’awar; domin cewa shi azumi yana kange gaɓoɓi daga sha’awa.

    2. Azumi sababin shiga Aljanna ne, sannan kuma yana nesantar da bawa daga wuta; kamar yadda ya zo cikin hadisin Abu Umamata (Radiyallahu Anhu) ya ce; “Ya Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) shiryar da ni kan aikin da zai kai ni ga shiga Aljanna”. Sai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasalam ya ce; “Na hore ka da yin azumi, ba shi da tamka”. (Imam Ahmad 5/255-258. Ibnu Hibban 929).

    Haka zalika, ya zo cikin hadisin da Imam Bazzar ya fitar cikin littafinsa cewa; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce da Huzaifah; “Ya Huzaifa, duk wanda ya cika da azumin yini ɗaya mai nufin yardar Allah, Allah zai shigar da shi Aljannah”.
    Game da nesantar da bawa daga wuta kuwa, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Babu wani bawa da zai yi azumi na kwana ɗaya domin neman yardar Allah, face Allah ya nesantar da fuskarsa daga wuta tsawon shekaru saba’in”. (Bukhari, 6/35. Muslim, 1153).

    A hadisin da Tirmizi ya fitar, cewa ya yi, “Duk wanda ya yi azumin kwana ɗaya domin neman yardar Allah; Allah zai sanya tazara tsakaninsa da wuta kamar tazarar sama zuwa ƙasa”.

    A wani hadisin kuma ya ce; “Azumi garkuwa ne da bawa zai kare kansa daga wuta”. (Imam Ahmad 3/241).

    3. Ana sakanya wa mai azumi da lada ba tare da ƙididdiga ba.

    4. Mai azumi yana da farin ciki biyu. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ambata cikin wani hadisi cewa; “……. Kuma mai azumi yana da farin ciki biyu: idan ya yi buɗa-baki yana da farin ciki; haka idan ya haɗu da Ubangijinsa zai yi farin ciki da azuminsa”. (Bukhari 1805, Muslim 163).

    5. Warin bakin mai azumi ya fi turaren almiski ƙamshi a wajen Allah. Kamar yadda hadisi ya tabbata daga Abu Huraira (Radiyallahu Anhu) cewa, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Dukkan aikin ɗan Adam a gare shi ne, ban da azumi, domin nawa ne, kuma ni zan sakanya masa, azumi garkuwa ne.

    Idan ya kasance ranar azumin ɗayanku, to kada ya yi batsa, kada ya yi jahilci (shirme); idan wani ya zage shi ko ya neme shi da faɗa, to ya ce masa “Ni azumi nake yi”. Na rantse da wanda ran Muhammad ke hannunsa; warin bakin mai azumi ya fi turaren almiski ƙamshi a wajen Allah.

    Kuma mai azumi yana da farin ciki biyu; idan ya yi buɗa-baki yana da farin ciki; haka idan ya haɗu da Ubangijinsa zai yi farin ciki da azuminsa”. (Bukhari 1805, Muslim 163).

    6. Azumi da Alkur’ani suna ceton ma’abocinsu, kamar yadda ya zo cikin hadisi cewa; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce, “Azumi da Alkur’ani za su ceci bawa ranar ƙiyama, azumi zai ce; Ya Ubangiji, na hana shi abinci da sha’awarsa, ka ba ni cetonsa…………….”.

    7. Azumi yana kankare zunubai, Bukhari da Muslim sun fitar da hadisi daga Huzaifata Bin Yaman (Radiyallahu Anhu) cewa; Umar Bin Khaɗɗab (Radiyallahu Anhu) ya ce; “Wane ne wanda ya kiyaye hadisin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) wanda ya yi magana a kan fitina? Sai Huzaifa ya ce; “Ni ne. Na ji Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) yana cewa; “Fitinar da mutum zai samu a cikin iyalansa, da dukiyarsa, da makwancinsa, sallah da azumi da sadaka suna kankare su”.

    8. Ƙofar Rayyan ta masu azumi ce, kamar yadda ya zo a hadisin Sahal Ibn Sa’ad (Radiyallahu Anhu) cewa; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Tabbas a cikin Aljanna akwai wata ƙofa, ana ƙiranta Rayyan, masu azumi ne za su shige ta ranar ƙiyama; babu wanda zai shige ta sai su, kuma idan suka shige ta za a rufe ta, babu wanda zai ƙara shiga. Kuma duk wanda ya shiga zai sha ruwa; kuma duk wanda ya sha ruwan, ba zai ƙara jin ƙishirwa ba har abada”. (Bukhari 4/95, Muslim 1/52).

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Watan Ramadana 1 danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Azumin Watan Muharram danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Guziri Ga Mai Azumin Ramadana (Bisa Koyarwar Alƙur’ani Da Sunna); wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Falalar Watan Ramadana 1

    Falalar Watan Ramadana 1

    Falalar Watan Ramadana – Hadisi ya tabbata daga Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) cewa, “Wanda ya azumci watan Ramadan, yana mai imani da neman lada, za a gafarta masa zunubansa da suka shuɗe”.

    Haka nan, a wani hadisi, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Idan watan Ramadan ya shigo, ana buɗe ƙofofin rahama da ƙofofin Aljanna, kuma ana rufe ƙofofin Jahannama; kuma ana ɗaure shaiɗanu”. Haka kuma an rawaito daga Anas Ibn Malik Radiyallahu Anhu cewa; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Lalle wannan wata na Ramadana, haƙiƙa ya halarto muku, a cikinsa akwai wani dare wanda ya fi watanni dubu alheri. Duk wanda aka haramta masa (samun alherin dake cikinsa); haƙiƙa an haramta masa alheri dukkansa. Kuma babu wanda ake haramta wa alherinsa sai wanda ba shi da rabo”. (Sunan Ibn Majah 1644).

    A dunƙule, za mu iya lissafo wasu cikin manyan falalolin watan Ramadan kamar haka:

    1. A cikinsa Allah ya saukar da Alkur’ani daga Lauhul Mahfuz, zuwa saman duniya.

    2. Wata ne da ake ɗaure shaiɗanu, ayyukan sharri suna ƙaranci a ban-ƙasa. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasalam ya ce; “Idan watan Ramadan ya zo, sai a buɗe ƙofofin Aljanna, sannan a rufe ƙofofin wuta, kuma a kulle shaiɗanu”. (Bukhari 4/97, Muslim 2/757).

    Dukkan wannan yana kammaluwa daga lokacin da daren farko na wata mai albarka ya shigo, saboda faɗin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam)cewa; “Idan daren farko na Ramadana ya kasance, sai a kulle shaiɗanu da kangararrun aljanu, a rufe ƙofofin wuta, babu wadda za a bari daga cikinta, a buɗe ƙofofin Aljanna ba za a bar ko ɗaya a rufe ba. Sai wani mai kira hhya yi kira; “Ya mai neman alheri matso kusa, Ya mai neman sharri yi nesa!

    Kuma Allah yana da wasu ‘yantattu daga wuta, wannan kuwa yana faruwa a kowanne dare”. (Tirmizi 682, Ibnu Majah 1642).

    3. A cikinsa ne ake samun dare mafi daraja, wato Daren Lailatul Ƙadri. Anas Ibn Malik (Radiyallahu Anhu) ya ce, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce, “Lalle wannan wata na Ramadana, haƙiƙa ya halarto muku, a cikinsa akwai wani dare wanda ya fi watanni dubu alheri. Duk wanda aka haramta masa (samun alherin dake cikinsa), haƙiƙa an haramta masa alheri dukkansa. Kuma babu wanda ake haramta wa alherinsa, sai wanda ba shi da rabo”. (Sunan Ibn Majah 1644).

    4. Amsar addu’a da kuma ‘yanta bayi daga wuta a kowanne dare cikin watan Ramadana.

    5. Gafarta zunubai, kamar yadda ya zo cikin hadisin da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) cewa, ya hau minbari sai ya ce, “Amin! Amin! Amin!”. Sai aka tambaye shi, sai ya ce, “Haƙiiƙa Jibrilu (Alaihis Salam) ya zo ya ce mini: “Duk wanda ya riski watan Ramadan bai yi abin da za a gafarta masa ba, har aka shigar da shi wuta, to Allah ya nisantar da shi daga rahamarsa,”. Ka ce “Amin”. Sai na ce, “Amin”….(Imam Ahmad 2/246).

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Azumin Watan Ramadana 2 danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Gaggauta Buɗa Baki danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Guziri Ga Mai Azumin Ramadana (Bisa Koyarwar Alƙur’ani Da Sunnah) wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Sharuɗan Wajabcin Azumin Watan Ramadan

    Sharuɗan Wajabcin Azumin Watan Ramadan

    Azumin watan Ramadan yana sauka a kan wasu, sakamakon waɗansu dalilai da Shari’a ta aminta da su; shi ya sa wajen ci gaba da ayar da ta gabata, malamai suka bayyana ire-iren waɗannan mutane, tare da dalilan. Ci gaba da bayani, sai Allah ya ce; “Waɗansu kwanaki ne ababan ƙidayawa.

    To wanda ya kasance mara lafiya a cikinku, ko a kan wata tafiya; to (idan ya sha ruwa) sai ya rama a waɗansu kwanakin na daban, har ma waɗanda za su iya yin azumin; su ba da fansa ta ciyar da abinci ga miskini guda ɗaya, to dukkan wanda ya ƙara (a kan abincin miskini), to wannan ya ƙara wa kansa alheri.

    Amma ku riƙa yin azumin shi ne ya fi alheri a gare ku, in har kun kasance kuna sani”. Watan Ramadan shi ne wanda aka saukar da Alqur’ani a cikinsa, shiriya ce ga mutane, kuma ayoyi bayyanannu na shiriya, kuma mai rarrabewa tsakanin ƙarya da gaskiya. Don haka dukkan wanda ya halarci watan cikin ku, to ya azumce shi. Kuma wanda ya kasance marar lafiya, ko a kan tafiya, (to idan ya sha ruwa) sai ya rama a waɗansu kwanaki na daban.

    Allah yana nufin sauƙi a gare ku, kuma ba ya nufin tsanani a gare ku. Don haka ku cika adadin (kwanakin Ramadan); kuma domin ku girmama Allah bisa ga shiryar da ku da ya yi, kuma ku zamo masu godiya gare shi. Kuma idan bayina suka tambaye ka game da ni, to ni kusa nake (da su); ina amsa kiran mai kira, da zarar ya kiraye ni. To su nemi amsawata, kuma su yi imani da ni, domin su shiryu.

    An halatta muku saduwa da matayenku a daren watan Azumi, su sutura ce gare ku, ku ma suturu ce a gare su. Allah ya san ku kun kasance kuna ha’intar kawunanku, sai ya dawo da ku, kuma ya yi muku afuwa. To a yanzu ɗin ku sadu da su (da daddare), kuma ku nemi abin da Allah ya rubuta muku; kuma ku ci, kuma ku sha har farin zare ya bayyana daga baƙin zare na alfijir; sannan ku cika azumi zuwa dare, kuma kar ku sadu da su alhali kuna i’itikafi a masallaci.

    Waɗannan iyakoki ne na Allah, kada ku kusance su! Kamar haka ne, Allah yake bayyana ayoyinsa ga mutane; don su zamo masu taƙawa” (Bakara: 184 – 187).

    Waɗannan ayoyi a dunƙule sun yi bayanin waɗanda shari’a ta dauƙe musu azumin watan Ramadan; sakamakon wasu dalilai da karɓaɓɓu ne a Shari’a da sharaɗin bayan waraka daga waɗannan al’amura; sawa’un rashin lafiyar da za ta hana yin azumin ne, ko mace mai shayarwa ko juna (kamar yadda wasu malamai irin su Ibn Taimiyya da almajiransa; Auza’i, Hasanul Basri da Ibrahimul Nakha’i suka tafi a kan su ma marasa lafiya ne), ko matafiya ne; to za su rama waɗannan azumi da suka sha bayan kwanakin azumin, ma’ana bayan Ramadan.

    Sannan a cikin su, akwai bayanin waɗanda za su ciyar da miskinai abinci, sakamakon rashin lafiya; ko tsufa da mai ciki ko shayarwa bisa fatawar Abdullahi Ibn Umar, Abdullahi Ibn Abbas da Ishaq Ibn Rahawaihi; kamar yadda Sheikh Nasiruddeen Albani ya fitar a cikin littafinsa Irwa’ Alghalil 4/18 – 24).

    Shahid dai, waɗannan ayoyi ƙunshe suke da cikakkun bayanai game da wajabcin azumin Ramadana; da kuma nuni a kan waɗanda azumin ya wajaba a kansu, misali dukkanin musulmi, baligi, mai hankali; kuma wanda yake da ikon yi, mazaunin gida. Sannan an bayyana matakan da aka bi wajen shar’anta shi, da kuma waɗanda azumin ya zama wajibi a kansu. Domin neman cikakken bayani, sai a tuntuɓi malamai a majalisunsu domin jin yadda abin yake.
    A gefe guda kuma, akwai waɗanda azumin Ramadana ya sauka a kan su, ma’ana, su azumin Ramadana bai wajaba a kan su ba.

    Cikin irin waɗannan akwai:

    i. Kafiri.

    ii. Yaro, amma za a iya umartar sa da yin azumin domin ya saba.

    iii. Mahaukaci, wannan kuwa koda balagagge ne, domin ba ya cikin hankalinsa. Kuma Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasalam ya ce, “An ɗauke alƙalami a kan mutum uku: mai barci har sai ya farka, yaro har sai ya balaga, da mahaukaci har sai ya warke”. (Sahihul Jami’ al-Saghir (3513).

    iv. Tsoho, amma zai bayar da mudun-nabi guda biyu, ko ya ciyar da miskini dafaffen abinci a madadin kowacce rana.

    v. Marar lafiya, sai dai akwai ramuwa a kansa bayan ya warke, wannan kuwa ko da bayan shekara nawa ne. Amma cutar da ƙwararrun likitoci suka tabbatar ba za a warke ba, sai dai kawai a ciyar a madadin kowacce rana.

    vi. Matafiyi, zai yi ramako bayan Ramadana.

    vii. Mai jinin haila ko jinin biƙi, amma ita ma akwai ramuwa a kanta.

    viii. Mace mai ciki ko shayarwa, ita ma za ta iya ajiye azumi idan tana tsoron cutuwarta ko cutuwar abin dake cikinta, ko abin da take shayarwa idan ta ci gaba da azumin.

    An rawaito hadisi daga Anas Ibn Malik Al-Ka’abi (Radiyallahu Anhu) cewa, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce, “Haƙiƙa Allah ya ɗauke wa matafiyi rabin sallah, kuma ya ɗauke azumi ga matafiyi da mai ciki da mai shayarwa”. (Sunan Ibn Majah, (1667).

    A nan malamai suka yi bayanin cewa, idan matuƙar dai matafiyi da mara lafiya za su rama azumi, to babu abin da zai sa a ce mai ciki ba za ta rama ba.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tsayuwar Watan Ramadan danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Dake Cikin Yin Sahur danna nan.

    Wannan bayanin anciro shi ne daga Littafin Guziri Ga Mai Azumin Ramadana (Bisa Koyarwar Alƙur’ani Sa Sunnah); wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Sallar Asham Da Raka’o’inta

    Sallar Asham Da Raka’o’inta

    Sallar Asham ita ce nafilfili da ake yi a bayan sallar Isha’i a cikin watan Ramadan, wato da zarar labarin ganin wata ya bayyana, domin wannan dare na Ramadan ne. Sannan yin ta cikin jam’i, sunna ce.

    Hadisi ya tabbata daga Nana A’isha (Radiyallahu Anha) cewa; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya fita a wata rana da tsakar dare, sai ya yi sallah a Masallaci, sai wasu cikin sahabbai suka bi shi. Da gari ya waye sai mutane suka ba wa junansu labari, da dare ya yi sai yawan mutane ya ƙaru, sai ya yi sallah su ma suka bi Shi.

    Da gari ya waye sai mutane suka ƙara bai wa junansu labari, sai Masallaci ya cika a dare na uku, sai Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya fito ya yi sallah. A dare na huɗu mutane suka taru har Masallaci ya gaza ɗaukarsu; sai Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ƙi fitowa har zuwa sallar Asubahi.

    Yayin da ya idar da sallar Asubahin, sai ya juyo ya fuskanci mutane, Ya ce; “Lalle halinku bai ɓuya gare Ni ba; sai dai Ni na ji tsoron kada a wajabta muku ita ku zo ku gaza”. (Bukhari 3/220, Muslim 761).

    Bayan wafatin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) shari’a ta gama cika, tsoron da ake ji ya kau; sai Sayyadina Umar Bin Khaɗɗab (Radiyallahu Anhu) ya raya wannan Sunnah; kamar yadda Abdulrahman Bn Al-ƙariy ya faɗa cewa; “Na fita tare da Umar Bn Khaɗɗab a wani dare cikin Ramadan zuwa masallaci, sai ga mutane a warwatse, wani yana sallah shi kaɗai; wani yana sallah da yan mutane kaɗan.

    Sai Umar ya ce: “Ni ina ganin da a ce na haɗe mutane bayan karatu ɗaya da ya fi kamata”.

    Sai ya yi ƙoƙarin haɗe su a bayan Ubayyu Ibn Ka’ab (Radiyallahu Anhu). Sannan muka fita tare da shi a wani daren, mutane suna sallah a bayan limaminsu, sai Umar ya ce; “Madalla da wannan sabon abu…”

    Game da adadin raka’o’inta kuwa, ya zo cikin hadisin Nana A’isha (Radiyallahu Anha) cewa; “Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasalam ba ya wuce raka’a goma sha ɗaya a Ramadan ko waninsa”. (Bukhari: 1147). Sannan ta bayyana yadda kyawun wannan sallah take; da kuma yadda yake jimawa a tsaye, wanda har ƙafafuwanSa ke kumbura saboda tsayuwa.

    Hadisi daga Jabir Bn Abdullahi (Radiyallahu Anhu) cewa; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) yayin da ya raya daren Ramadan da mutane; ya yi sallah raka’a takwas sannan ya yi wutiri. (Ibn Hibban 920).

    Domin karanta cikakken bayani akan Ma’anar Azumi A Musulunci danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Kaffarar Azumin Ramadan danna nan.

    Wannan bayanin anciro shine daga Littafin Guziri Ga Mai Azumin Ramadana (Bisa Koyarwar Alƙur’ani Da Sunnah); wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Zakkar Fid-Da-Kai

    Zakkar Fid-Da-Kai

    Zakkar fid-da-kai sunnah ce daga cikin sunnonin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam), domin ya fitar kuma sahabban Sa masu albarka ma sun fitar. Shari’a ta shar’anta wannan zakka domin tsarkake masu azumi daga yasasshen zance da batsa; kuma ciyarwa ga miskinai inda za ta wadatar da su a ranar sallah ta farin ciki.

    Hadisi daga Abdullahi Bn Umar (Radiyallahu Anhu) ya ce; “Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam)ya farlanta zakkar fid-da-kai ta bayan Ramadan kan mutane” (Bukhari 3/291, Muslim 984). Haka zalika hadisin Abdullahi Ibn Abbas (Radiyallahu Anhu), wanda Abu Dawud da Nasa’i suka fitar ya nuna hakan.

    Hadisi ya tabbata daga Abu Sa’id Alkhudri (Radiyallahu Anhu) ya ce; “Mun kasance muna bayar da ita a zamanin Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) sa’i ɗaya daga abinci; ko sa’i ɗaya daga dabino, ko sa’i ɗaya daga alkama, ko sa’i ɗaya daga zabibi (busasshen inibi). A wata ruwayar “Sa’i ɗaya daga cikwi”. (Bukhari 1508, Muslim 985).

    Ana fitar wa yaro, babba, mace, namiji da kuma bawa da ‘yantacce; saboda hadisin Abdullahi Bn Umar (Radiyallahu Anhu) da ya ce; “Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya yi umarni a fitar wa yaro, babba, bawa da ‘yantaccen daga waɗanda kuke ɗaukar nauyinsu”.

    (Darukuɗniy 2/141, Baihaƙiy 4/161).

    Sannan ana bayar da ita ce kafin tafiya sallar idi, ba ya halarta a jinkirta ta har zuwa lokacin sallah; koda kwana ɗaya ko biyu kafin ranar sallah; ya halatta a fitar saboda abin da ya zo daga aikin Abdullahi Bn Umar (Radiyallahu Anhu).

    Ya zo cikin hadisin Abdullahi Bn Abbas (Radiyallahu Anhu) cewa; “….. wanda duk ya bayar da ita kafin sallah, to ya yi ta karɓaɓɓiya; wanda kuma ya bayar bayan an yi sallah, to sadaka ce daga cikin sadakoki”.

    Domin karanta cikakken bayani akan Azumin Kwanaki Shida A Watan Shawwal (Sitta Shawwal) danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Azumin Kwanaki Goma Na Farkon Watan Zul-Hijja danna nan.

    Wannan bayanin anciro shine daga Littafin Guziri Ga Mai Azumin Ramadana (Bisa Koyarwar Alƙur’ani Da Sunnah); wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Cikakken Bayani A Kan Sahur

    Cikakken Bayani A Kan Sahur

    Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya kwaɗaitar da yin sahur; har Ya ambata cikin falalar sahur a hadisin Anas Ibn Malik Radiyallahu Anhu cewa, “Ku yi sahur, domin haƙiƙa akwai albarka a cikin yin sahur” (Sahihul Bukhari 1923).

    An karɓo hadisi daga Salman (Radiyallahu Anhu) cewa, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; “Albarka na cikin abu uku: jama’a, abincin rashi da kuma abincin sahur”. (Ɗabrani cikin Mu’ujamul Kabir 6127).

    Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ambaci sahur da kumullo mai albarka; kamar yadda yake cikin hadisin Al’irbadh Bn Sariyata, da Abud-Darda’a (Radiyallahu Anhu) cewa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Ku taho mu yi kumullo mai albarka, yana nufin sahur”.

    Haka nan hadisi ya tabbata daga Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) cewa; “Sahur abinci ne mai albarka. Don haka kada ku bar shi, ko da ruwa ne ɗayanku ya kurɓa. Haƙiƙa Allah da mala’ikunsa na yin salati ga masu yin sahur”. (Sahih Targhib wal Tarhib 1066).

    Sannan Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya bambanta azuminmu da na ma’abota littafi (Yahudu da Nasara); da sahur, kamar yadda ya ce, “Bambancin da ke tsakanin azuminmu da na ma’abota littafi; shi ne yin sahur”. (Sahih Muslim 1096).

    Game da lokacin da ake yin sahur ko bari kuwa, akwai hadisai da suka zo a kai. An karɓo hadisi daga Anas Ibn Malik (Radiyallahu Anhu), daga Zaid Ibn Thabit (Radiyallahu Anhu) ya ce; “Mun yi sahur tare da Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) sannan sai ya tashi zuwa sallah. Sai na cewa Anas, “Yaya tsawon da ke tsakanin kiran sallah da yin sahur ɗin yake? Sai ya ce; “Gwargwadon karanta ayoyi hamsin”. (Bukhari 1921, Muslim 1097).

    Wani hadisi daga Sahl Ibn Sa’ad ya ce; “Na kasance ina yin sahur cikin iyalina; bayan wannan sai na yi gaggawa domin samun sujada (sallah) tare da Manzon Allah(Sallallahu Alaihi Wasalam)”. (Bukhari 1920).
    Wannan hadisi ya nuna ana yin sahur ne dab da ketowar alfijir.

    Amma yayin da mutum ke yin sahur, sai alfijir ya keto, to zai ƙarasa cin abincinsa ne; dogaro da hadisin Abu Huraira (Radiyallahu Anhu)cewa, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Idan ɗayanku ya ji kiran sallah alhali ƙwarya tana hannunsa, kada ya ajiye ta, har sai ya biya buƙatarsa”. (Abu Dawud 2060).

    Amma a nan mutum ya yi hattara kada ya mayar da wannan ita ce ɗabi’arsa; wato jinkirtawar da zai fita daga lokaci.

    Wani abin lura game da alfijir, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya nuna iri biyu ne cikin hadisin da aka karɓo daga Ibn Abbas, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; “Alfijir iri biyu ne, na farko ba ya haramta abinci; kuma ba ya halatta sallah, na biyu kuwa yana haramta abinci, yana halatta sallah”.

    A wannan gaɓar, wajibi a ja hankalin ladanai waɗanda ke kiran sallah, wato lokacin da ake daina yin sahuur; domin ba sa kula da fitowar alfijir. Misali, a kalandar Jihar Yobe; alfijir zai hudo a farkon azumi da misalin ƙarfe 4:37 a bana; yayin da a ƙarshen azumi zai kai ƙarfe 4:40. To amma za ka ga ladanai ba sa kiran sallar daina sahur (assalatu), sai misalin ƙarfe 4:55; wasu ma sai ƙarfe 5:00, alhali da yawa daga cikin mutane sun dogara ne da kiran assalatu wajen daina cin abinci.

    Haƙiƙa ladanai su sani, yin hakan kuskure ne da kuma ɗaukan haƙƙin al’umma; don haka su ji tsoron Allah, da sannu za su tsaya a gabansa, kuma za a tambaye su kan dukkan abin da suka aikata.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Buɗa-baki danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ɗabi’ar Lokaci, Saurin Wucewa danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Guziri Ga Mai Azumin Ramadana (Bisa Koyarwar Alƙur’ani Da Sunnah); wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Falalar Yin Umara A Watan Ramadan

    Falalar Yin Umara A Watan Ramadan

    An karɓo daga Abdullahi Ibn Abbas (Radiyallahu anhu) ya ce; “Yin umara a watan Ramadan dai-dai da ladan aikin hajji ne; ko kuma dai-dai da ladan aikin hajji tare da ni yake”. (Bukhari 1764, Muslim !69).

    Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Shan Ruwan ZamZam danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Sallar Roƙon Ruwa danna nan.

    Wannan bayani anciro shine daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Azumin Kwanaki Goma Na Farkon Watan Zul-Hijja

    Azumin Kwanaki Goma Na Farkon Watan Zul-Hijja

    Watan Zul-Hajji wata ne mai tarin falala da ɗimbin daraja, cike yake da alhairai masu yawa.

    Kuma a cikinsa ake yin aikin hajji, kwanaki goma na farkonsa, kwanaki ne masu daraja, saboda haka ake son yin azumi a cikinsu.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Azumin Kwanaki Goma Na Farkon Watan Zul-Hijja danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Azumin Watan Muharram danna nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.