Category: Amsoshi

Amsoshin tambayoyin da aka yi

  • Abubuwa Goma Da Mai Azumi Ya Kamata Ya Sani

    Abubuwa Goma Da Mai Azumi Ya Kamata Ya Sani

    ZAFAFA GOMA: ABUBUWA 10 DA MUSULMI YA KAMATA YA SANI SANNAN YA KIYAYE A LOKACIN AZUMIN WATAN RAMADANA.

    GABATARWA:
    Alhamdulillahi Rabbil ‘Alamin. Tsira da amincin Allah (SWT) su tabbata ga Manzon Allah صلى الله عليه وسلم, iyalansa da sahabbansa baki ɗaya. Muna yi wa Allah (SWT) godiya da Ya raya mu har muka sake gamuwa da watan Ramadan, watan rahama, gafara da tsira daga wutar Jahannama.

    Ibadar azumin ramadana ibada ce wacce ta samo asali da umarni daga Allah (SWT) kuma ibada ce wacce aka umarci al’ummomin baya da ita. Dalilin haka shi ne faɗin Allah (SWT) “ya ku waɗanda suka yi imani an farlanta muku azumi kamar yadda aka farlanta ma waɗanda suka gabace ku domin ku yi taƙawa”. Duba bakara: 2:183.

    Haka kuma Allah (SWT) yana cewa “watan ramadana shi ne wanda aka saukar da alkur’ani a cikinsa domin zama shiriya ga mutane……”Duba bakara: 2:185. Haka zalika, An ruwaito manzon Allah (SWT) yana cewa: “ haƙiƙa watan Ramadana ya zo muku. Wata ne mai albarka. Allah yana lulluɓeku (da rahamar sa) a lokacin sa.

    Yana saukar da jin ƙan sa, yana kankare zunubai kuma yana karɓar addu’o’i. Allah yana kallon tsere da kuke yi ta ɓangaren kyawawan ayyukan ku sannan ya sanar da mala’iku cikin girmama ku. Saboda haka ku nuwa Allah nagartar ku. Tabbas matsiyaci shi ne wanda ya kasa samun rahamar Allah a lokacin Ramadan ”Duba “ Majma’uz-zaw’id 3:142

    Haka kuma Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yace “duk wanda ya azumci Ramadana yana mai imani da kwaɗayin samun lada, za a gafarta masa dukkan zunuban sa da suka
    gabata….”.Duba Bukhari 2014 da muslim 759-760. A wani hadisin ƙudusi Allah (SWT) yana cewa “ dukkanin aiki (mai kyau) na ɗan-adam da ya yi yana da lada goma kwatankwacinsa har zuwa ɗari bakwai amma banda azumi.

    Haƙiƙa azumi nawa ne kuma ni zany ni sakayyarsa. Shi mai azumi ya bar cinsa da shansa, da sha’awarsa saboda umarni na” manzon Allah ya cigaba da cewa “ mai azumi yana da farin ciki har guda biyu. Farin ciki lokacin da yake buɗa baki da kuma farin ciki lokacin da zai haɗu da ubangijinsa” ….Duba Bukhari 1904 da muslim 161-1151

    A cikin wannan taƙaitacciyar tunatarwa, na ambaci abubuwa goma da Musulmi ya kamata ya kiyaye domin azuminsa ya zama karɓaɓɓe mai cike da falala. Allah (SWT) ya ba mu ikon amfana da wannan tunatarwa da kuma ikon aiki da waɗanan abubuwa (ZAFAFA GOMA) domin rabauta da dacewa.

    NA FARKO: NIYYA

    Azumi ibada ce, kuma ibada ba ta inganta sai da niyya tun daga dare kafin a tashi
    da azumi. Wajibi ne mutum ya ƙulla niyyar azumi da zarar an ga wata tun kafin ya
    kwanta bacci ko kuma kafin fitowar alfijir.

    Hujja: Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya ce:“Duk wanda bai yi niyyar azumi da dare ba, babu azumi a gare shi.” (Abu Dawud, Tirmizi)

    NA BIYU: ƊAUKAR AZUMI DA GANIN WATA

    Azumin Ramadana yana farawa ne da ganin wata ko kuma cikar wata (sha‟aban zuwa 30) kuma yana ƙarewa da ganin wata (na shawwal).

    Hujja: Annabi صلى الله عليه وسلم ya ce:“Ku yi azumi idan kun ga wata, ku buɗa azumi idan kun gan shi. ”(Bukhari da Muslim)

    NA UKU: TSAYAWA DA SALLOLIN FARILLA

    Ko da mutum yana azumi, idan ya raina sallah, ya jefa kansa cikin haɗari. Allah (SWT) yana cewa “ ku kiyaye sallolin ku musammam sallar (tsakiya) La‟asar….. Duba bakara 2:238

    Hujja: Annabi صلى الله عليه وسلم ya ce:“Abu na farko da za a tambayi bawa a ranar Alƙiyama shi ne sallah….” (Tirmizi)

    NA HUƊU: YAWAITA KARATUN AL-KUR’ANI

    Ramadan wata ne na Al-Kur‟ani, don haka ake ƙwaɗaitar da musulmi da ya dage
    wajen yawaita tilawa da sauraron alkurani ba dare ba rana. Karatun alkurani shi ne
    zikiri mafi girma kuma a watan ramadana aka saukar da shi.

    Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya kasance duk watan ramadana mala‟ika Jibril yana zuwa sau biyu wajen sa domin tilawar alkurani tare da shi kuma an ruwaito sahabbai da magabata sun kasance suna duƙufa ba dare ba rana wajen raya dukkan kwanaki da karatun alkurani. Ana so mutum ya shagaltu sosai da karatun alkurani kuma ya zama shine mafi yawan ibadar sa acikin ramadana.

    Hujja: Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya ce:“Ku karanta Al-Kur‟ani, domin lallai shi zai zo ranar Alƙiyama yana yi wa masu shi ceto.” (Muslim)

    NA BIYAR: YAWAN ZIKIRI

    Zikiri yana rayar da zuciya kuma yana ɗaga darajar bawa.
    Hujja: Annabi صلى الله عليه وسلم ya ce:“Kalmomi biyu ne masu sauƙi a harshe, masu nauyi a sikeli, masu soyuwa ga Rahama…” (Bukhari da Muslim)

    NA SHIDA: YAWAITA SALATI GA ANNABI صلى الله عليه وسلم.

    Salati hanya ce ta samun rahamar Allah. Don haka yawaita salati ga manzon Allah
    صلى الله عليه وسلم a kowane lokaci ibada ce mai albarka da ɗimbin lada musammam kuma a lokacin azumi.

    Hujja: Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya ce:“Duk wanda ya yi mini salati sau ɗaya, Allah zai yi masa sau goma.” (Muslim)

    NA BAKWAI: YAWAITA ADDU’A, MUSAMMAN A SAHUR DA BUƊA BAKI

    Mai azumi yana da matsayi na musamman wajen Allah. Lokacin da bawa ke azumi
    lokaci ne na addu’a gaba ɗaya amma kuma akwai keɓaɓɓun gurare da aka ayyana cewa
    ana so a yawaita addua kamar lokacin buɗa baki da lokacin sahur da sauransu.
    Hujja: Annabi صلى الله عليه وسلم ya ce:“Mai azumi yana da addu‟a wadda ba a mayar masa da ita ba a lokacin buɗa bakinsa.” (Tirmizi)

    NA TAKWAS: SALLAR TARAWIHI DA TSAYUWAR DARE

    Wannan wata dama ce ta gafara da gyaran rayuwa.
    Hujja: Annabi صلى الله عليه وسلم ya ce: “idan mutum ya tsaya domin sallar dare (tarawih ko ƙiyamul laili) tare da liman har aka ƙare sallar, Allah zai rubuta masa lada kamar wanda ya raya daren gaba ɗaya da sallah.” (Abu dawud 1375)

    NA TARA: SADAKA DA CIYAR DA MAI AZUMI

    Ramadan wata ne na tausayi da taimakon juna.
    Hujja: Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya ce: “Duk wanda ya ciyar da mai azumi, zai samu irin ladan azuminsa.” (Tirmizi)

    NA GOMA: I’ITIKAFI, ZAKATUL FITR DA UMARA GA MAI HALI

    Goman ƙarshe lokaci ne na ƙara kusanci da Allah da dagewa sosai domin ƙara yawaita ibadu musammam a kwanakin da ake sa ran dacewa da lailatul kadari watau daren 21, 23, 25, 27 da kuma 29. I’itikafi ibada ce mai tarin lada da samun kusanci da Allah (SWT) kuma ana shiga I’itikafi ne a goman ƙarshe a Ramadan.

    Haka, zakkar fidda kai (zakatul fitr) ibace wacce aka shar’anta ta a kan dukkan musulmi namiji ko mace, babba ko yaro ko ɗan jariri kowa ana fitar masa da zakkar
    fidda kai.
    Hujja: An rawaito cewa Annabi صلى الله عليه وسلم yana yin I’itikafi a goman ƙarshe na Ramadan.(Bukhari). Haka kuma ya wajabta Zakatul Fitr (zakkar fidda kai) domin tsarkake azumi, kuma ya ce: “Umara a Ramadan tana da ladan Hajji.” (Bukhari da Muslim).

    ‘Ƴan uwa masu girma haƙiƙa duk wanda ya kiyaye waɗannan abubuwa goma, ya yi azuminsa da ikhlasi, to da yardar Allah zai samu cikakkiyar falalar Ramadan wanda Allah kaɗai ne ya barwa kansa sanin irin tanadin ladan da zai ba shi. Allah Ya karɓi ibadunmu, Ya gafarta mana zunubanmu, Ya sa mu dace da Lailatul Qadr.
    Ameen.

    Husain M. Inuwa.
    usainiskima@gmail.com
    09042152353

    Danna nan don karanta Shan Azumi Ga Matafiya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Waɗanne Abubuwa Ne Ke Lalata Azumi A Ɓoye?

    Waɗanne Abubuwa Ne Ke Lalata Azumi A Ɓoye?

    Amsa: Abubuwan dake lalata azumi a ɓoye su ne:

    Akwai yi da wani da shaidar zur da gulma da ƙin yin sallah sai lokacinta ya wuce, babu wani dalili na shari’ah, ƙin yin sallah kwata-kwata.

    Hujja: “Wanda duk bai bar zancen zur ba, da aikata zur, da yiwa mutane mummunar fassara; Allah baya buƙatar yabar abincinsa da abin shansa”.

    Marawaici Abu Huraira, littafi Sahihul Bukhari da Sahihu Muslim.

    Domin karanta cikakken bayani akan Shin Rashin Yin Sallah A Cikin Jama’a Na Lalata Azumi? danna nan

    Domin karanta cikakken bayani akan Dalilan Wajabcin Azumin Ramadana danna nan.

  • Matsayin Tsibbu Da ‘Yan Tsibbu A Wurin Shehu Usman Bn Fodiyo

    Matsayin Tsibbu Da ‘Yan Tsibbu A Wurin Shehu Usman Bn Fodiyo

    Jagoran jaddada Musulunci a ƙasar Hausa, Shehu Usman Ɗanfodiyo a cikin rubuce-rubucensa da yawa, ya yi gargaɗi; ya tsoratar, ya kuma yanke hukunci ga ayyukan tsibbu na duba da hisabi da sihiri da siddabaru da layu.

    Don ƙarin haske, za a iya duba littafan Shehu irin su Nurul-albab da Wasiƙatul Ikhwani da Sirajul Ikhwani; da Bayanil Bidi’i da Tabsiratul Mubtadi da kuma Tamyizil Ahlis Sunnu. A inda ya tabbatar da fitar su daga tafarkin tsira, zuwa ga tafarkin ɓata, tare da wajabcin yaƙar su.

    Koda yake a ɓangare guda, akwai gunaguni da wasu ke yi game da rabuce-rubucen da wasu mataimakan Shehu suka yi, wanda ke marawa tsibbu baya.

    Rubuce-rubucen sun haɗa da: Ƙirar Ahibba’i da Muhawwanatil Ikhwani ila Mubashshiratil Miswani da Kitabul Hisabi wal Asrari; da kuma Ma’awanatil Ahibba’i Fil Ilmil Adibb’i waɗanda Muhammad Bello da Muhammad Tukur; da Abdullahi da kuma Muhammad Buhari suka rubuta.

    Amsa a nan ita ce, koda an danganta musu irin waɗannan ra’ayoyi, to lallai za a ga suna nuna irin maganin da ya halatta a yi da tsantsar Alƙur’ani da Hadisan Annabi (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ne. Kamar kuma yadda za a iya gani cikin babukan littafan Bukhari da Muslim da sauran Sittu sihah.

    Ma’ana waɗanda ba a jirkita ayoyin Alƙur’ani ba, kuma ba a amsa umarnin aljanu da shaiɗanu ba. Don ƙarin gamsuwa sai a nemi waɗancan littafai don a nazarce su.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ƙalubale Ga Makarantun Tsangaya danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Wasu Birane Da Garuruwa Da Makarantu Da KumaTsangayu A Arewacin Najeriya danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Shin Mene Ne Tsafi Ko Sihiri?

    Shin Mene Ne Tsafi Ko Sihiri?

    Sihiri shi ne ƙulla yarjejeniya tsakanin matsafi da aljani, bisa sharaɗin matsafin zai aikata wasu ayyukan saɓo. Sannan aljanin ya taimaka masa ta hanyar yi masa biyayya cikin umarninsa.

    A duk lokacin da aikin saɓo ya fi muni da nesata daga Ubangiji Maɗaukaki, to kuwa aikin da aka sa aljanin ya fi saurin ci. Daga nan ne ake kiran irin waɗannan ‘yan tsibbu Malam Gobe-da-nisa.

    Amma idan matsafi ya taƙaita amsa umarnin shaiɗanin ko aljanin, to ba zai yi masa biyayya ba.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Aiki Kamar Yankan Wuƙa danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan SHUGABANCI A WURIN HAUSAWA danna nan.

    Wan nan baya nin anciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya, Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su wanda Dr.Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Su Wane ne Mu?

    Mu halitta ce ta jinsin mutane, kuma muna daga cikin waɗanda Allah bai halicce su domin komai ba, sai domin su bauta masa kawai, saboda haka Ya ba mu hankali don mu yi ilmi, da shi ne za mu san daidai, kuma mu san abin da ba daidai ba. Mu san gaskiya daga ƙarya, mu gane bambanci shiriya da ɓata. Da haka za mu yin aiki nagari mu kuma nesanci miyagun ayyuka.

    Mutum cikakke shi ne wanda ya yi imani da Allah da Manzonsa, kuma ba ya rabuwa da yin managarcin aiki, idan aka samu saɓani, ya yi tuntuɓe, ya aikata kuskure, sai ya yi sauri ya tuba ya koma ga Allah, sabo da shi mai imani ne da Allah, kuma mai yin koyi da Manzon Allah (S.A.W).
    Wannan ita ce siffa ta cikikken mutum, a mahangar Musulunci. Ba kawai kasancewar sa mai ɗauke da kai da ƙafa da iya magana, da dariya ba, ya zama dole sai ya haɗa waɗannan siffofi sannan zai amsa sunansa Ɗan’Adam. Daga nan ne idan an yi tambaya: “Su wane mu” Za mu cancanci bayar da amsar: “Mu mutane ne.”
    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Ɗan’Adam kamar yadda Allah Yaee Son sa. wanda M. Aminu Isma’il Sagagi ya wallafa domin karanta cikekken littafin nan DANNA KOREN RUBUTUNNAN

  • SHAN RUBUTU DA NUFIN SAMUN MIJIN AURE

    SHAN RUBUTU DA NUFIN SAMUN MIJIN AURE

    Tambaya

    Assalamu Alaikum warahmatullah. Malam don Allah ina neman fatawa ce.

    Wata ce take neman miji kasancewar duk masu zuwar mata ba da gaske suke yi ba, to shi ne ta nemi taimako wurin malamin zaure, yake ba ta tana shan rubutu da niyyar Allah ya sa ta dace. Toh malam abin tambaya a nan shi ne, shin mece ce makomar abin da ta aikata, shin Malam ta yi shirka ne ko kuwa ta yi ba daidai ba? nagode.

    Amsa

    Da farko game da shan rubutu, muddin ayar QUR’ANI ce tsantsa, babu wasu zane zanen hatimi, to ya halatta,  IBN TAIMIYYA ya tabbatar a MAJMU’UL FATAWA, haka ma WAHEED ABDUSSALAM BAALY ya tabbatar da hakan a SARIMUL BATTAR,
    Amma in akasin haka ne haramun ne, don yakan zama shirka ce da surkulle,
    Fadin cewa Malamin zaure ne na gargajiya, to galibi irin na shirkan suke yi, don haka ki tuba tsakaninki da Allah da alkawarin ba za ki sake zuwa wurin su ba, don kare addininki da mutuncinki.
    Don samun biyan bukatunki sai ki zage da addu’a da kiyamul laili da azumi da istigfari, kuma kina iya lazimtar wannan adu’ar domin ita  Annabi Musa ya yi, ya sami aikin yi da matar aure a ranar, ga adu’ar👉🏼
    رب إني لما أنزلت إلي من خير فقير
    Allah ya yafe mana kuma ya ba ki miji nagari,
    ALLAHU A’ALAM.

    Amsawa Sheikh Abubakar BN Mustafa Biu
    05/10/2019

    Daga : ZAUREN ISLAMIC SUNNAH