Tag: Ramadan

  • Abubuwa Goma Da Mai Azumi Ya Kamata Ya Sani

    Abubuwa Goma Da Mai Azumi Ya Kamata Ya Sani

    ZAFAFA GOMA: ABUBUWA 10 DA MUSULMI YA KAMATA YA SANI SANNAN YA KIYAYE A LOKACIN AZUMIN WATAN RAMADANA.

    GABATARWA:
    Alhamdulillahi Rabbil ‘Alamin. Tsira da amincin Allah (SWT) su tabbata ga Manzon Allah صلى الله عليه وسلم, iyalansa da sahabbansa baki ɗaya. Muna yi wa Allah (SWT) godiya da Ya raya mu har muka sake gamuwa da watan Ramadan, watan rahama, gafara da tsira daga wutar Jahannama.

    Ibadar azumin ramadana ibada ce wacce ta samo asali da umarni daga Allah (SWT) kuma ibada ce wacce aka umarci al’ummomin baya da ita. Dalilin haka shi ne faɗin Allah (SWT) “ya ku waɗanda suka yi imani an farlanta muku azumi kamar yadda aka farlanta ma waɗanda suka gabace ku domin ku yi taƙawa”. Duba bakara: 2:183.

    Haka kuma Allah (SWT) yana cewa “watan ramadana shi ne wanda aka saukar da alkur’ani a cikinsa domin zama shiriya ga mutane……”Duba bakara: 2:185. Haka zalika, An ruwaito manzon Allah (SWT) yana cewa: “ haƙiƙa watan Ramadana ya zo muku. Wata ne mai albarka. Allah yana lulluɓeku (da rahamar sa) a lokacin sa.

    Yana saukar da jin ƙan sa, yana kankare zunubai kuma yana karɓar addu’o’i. Allah yana kallon tsere da kuke yi ta ɓangaren kyawawan ayyukan ku sannan ya sanar da mala’iku cikin girmama ku. Saboda haka ku nuwa Allah nagartar ku. Tabbas matsiyaci shi ne wanda ya kasa samun rahamar Allah a lokacin Ramadan ”Duba “ Majma’uz-zaw’id 3:142

    Haka kuma Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yace “duk wanda ya azumci Ramadana yana mai imani da kwaɗayin samun lada, za a gafarta masa dukkan zunuban sa da suka
    gabata….”.Duba Bukhari 2014 da muslim 759-760. A wani hadisin ƙudusi Allah (SWT) yana cewa “ dukkanin aiki (mai kyau) na ɗan-adam da ya yi yana da lada goma kwatankwacinsa har zuwa ɗari bakwai amma banda azumi.

    Haƙiƙa azumi nawa ne kuma ni zany ni sakayyarsa. Shi mai azumi ya bar cinsa da shansa, da sha’awarsa saboda umarni na” manzon Allah ya cigaba da cewa “ mai azumi yana da farin ciki har guda biyu. Farin ciki lokacin da yake buɗa baki da kuma farin ciki lokacin da zai haɗu da ubangijinsa” ….Duba Bukhari 1904 da muslim 161-1151

    A cikin wannan taƙaitacciyar tunatarwa, na ambaci abubuwa goma da Musulmi ya kamata ya kiyaye domin azuminsa ya zama karɓaɓɓe mai cike da falala. Allah (SWT) ya ba mu ikon amfana da wannan tunatarwa da kuma ikon aiki da waɗanan abubuwa (ZAFAFA GOMA) domin rabauta da dacewa.

    NA FARKO: NIYYA

    Azumi ibada ce, kuma ibada ba ta inganta sai da niyya tun daga dare kafin a tashi
    da azumi. Wajibi ne mutum ya ƙulla niyyar azumi da zarar an ga wata tun kafin ya
    kwanta bacci ko kuma kafin fitowar alfijir.

    Hujja: Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya ce:“Duk wanda bai yi niyyar azumi da dare ba, babu azumi a gare shi.” (Abu Dawud, Tirmizi)

    NA BIYU: ƊAUKAR AZUMI DA GANIN WATA

    Azumin Ramadana yana farawa ne da ganin wata ko kuma cikar wata (sha‟aban zuwa 30) kuma yana ƙarewa da ganin wata (na shawwal).

    Hujja: Annabi صلى الله عليه وسلم ya ce:“Ku yi azumi idan kun ga wata, ku buɗa azumi idan kun gan shi. ”(Bukhari da Muslim)

    NA UKU: TSAYAWA DA SALLOLIN FARILLA

    Ko da mutum yana azumi, idan ya raina sallah, ya jefa kansa cikin haɗari. Allah (SWT) yana cewa “ ku kiyaye sallolin ku musammam sallar (tsakiya) La‟asar….. Duba bakara 2:238

    Hujja: Annabi صلى الله عليه وسلم ya ce:“Abu na farko da za a tambayi bawa a ranar Alƙiyama shi ne sallah….” (Tirmizi)

    NA HUƊU: YAWAITA KARATUN AL-KUR’ANI

    Ramadan wata ne na Al-Kur‟ani, don haka ake ƙwaɗaitar da musulmi da ya dage
    wajen yawaita tilawa da sauraron alkurani ba dare ba rana. Karatun alkurani shi ne
    zikiri mafi girma kuma a watan ramadana aka saukar da shi.

    Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya kasance duk watan ramadana mala‟ika Jibril yana zuwa sau biyu wajen sa domin tilawar alkurani tare da shi kuma an ruwaito sahabbai da magabata sun kasance suna duƙufa ba dare ba rana wajen raya dukkan kwanaki da karatun alkurani. Ana so mutum ya shagaltu sosai da karatun alkurani kuma ya zama shine mafi yawan ibadar sa acikin ramadana.

    Hujja: Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya ce:“Ku karanta Al-Kur‟ani, domin lallai shi zai zo ranar Alƙiyama yana yi wa masu shi ceto.” (Muslim)

    NA BIYAR: YAWAN ZIKIRI

    Zikiri yana rayar da zuciya kuma yana ɗaga darajar bawa.
    Hujja: Annabi صلى الله عليه وسلم ya ce:“Kalmomi biyu ne masu sauƙi a harshe, masu nauyi a sikeli, masu soyuwa ga Rahama…” (Bukhari da Muslim)

    NA SHIDA: YAWAITA SALATI GA ANNABI صلى الله عليه وسلم.

    Salati hanya ce ta samun rahamar Allah. Don haka yawaita salati ga manzon Allah
    صلى الله عليه وسلم a kowane lokaci ibada ce mai albarka da ɗimbin lada musammam kuma a lokacin azumi.

    Hujja: Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya ce:“Duk wanda ya yi mini salati sau ɗaya, Allah zai yi masa sau goma.” (Muslim)

    NA BAKWAI: YAWAITA ADDU’A, MUSAMMAN A SAHUR DA BUƊA BAKI

    Mai azumi yana da matsayi na musamman wajen Allah. Lokacin da bawa ke azumi
    lokaci ne na addu’a gaba ɗaya amma kuma akwai keɓaɓɓun gurare da aka ayyana cewa
    ana so a yawaita addua kamar lokacin buɗa baki da lokacin sahur da sauransu.
    Hujja: Annabi صلى الله عليه وسلم ya ce:“Mai azumi yana da addu‟a wadda ba a mayar masa da ita ba a lokacin buɗa bakinsa.” (Tirmizi)

    NA TAKWAS: SALLAR TARAWIHI DA TSAYUWAR DARE

    Wannan wata dama ce ta gafara da gyaran rayuwa.
    Hujja: Annabi صلى الله عليه وسلم ya ce: “idan mutum ya tsaya domin sallar dare (tarawih ko ƙiyamul laili) tare da liman har aka ƙare sallar, Allah zai rubuta masa lada kamar wanda ya raya daren gaba ɗaya da sallah.” (Abu dawud 1375)

    NA TARA: SADAKA DA CIYAR DA MAI AZUMI

    Ramadan wata ne na tausayi da taimakon juna.
    Hujja: Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya ce: “Duk wanda ya ciyar da mai azumi, zai samu irin ladan azuminsa.” (Tirmizi)

    NA GOMA: I’ITIKAFI, ZAKATUL FITR DA UMARA GA MAI HALI

    Goman ƙarshe lokaci ne na ƙara kusanci da Allah da dagewa sosai domin ƙara yawaita ibadu musammam a kwanakin da ake sa ran dacewa da lailatul kadari watau daren 21, 23, 25, 27 da kuma 29. I’itikafi ibada ce mai tarin lada da samun kusanci da Allah (SWT) kuma ana shiga I’itikafi ne a goman ƙarshe a Ramadan.

    Haka, zakkar fidda kai (zakatul fitr) ibace wacce aka shar’anta ta a kan dukkan musulmi namiji ko mace, babba ko yaro ko ɗan jariri kowa ana fitar masa da zakkar
    fidda kai.
    Hujja: An rawaito cewa Annabi صلى الله عليه وسلم yana yin I’itikafi a goman ƙarshe na Ramadan.(Bukhari). Haka kuma ya wajabta Zakatul Fitr (zakkar fidda kai) domin tsarkake azumi, kuma ya ce: “Umara a Ramadan tana da ladan Hajji.” (Bukhari da Muslim).

    ‘Ƴan uwa masu girma haƙiƙa duk wanda ya kiyaye waɗannan abubuwa goma, ya yi azuminsa da ikhlasi, to da yardar Allah zai samu cikakkiyar falalar Ramadan wanda Allah kaɗai ne ya barwa kansa sanin irin tanadin ladan da zai ba shi. Allah Ya karɓi ibadunmu, Ya gafarta mana zunubanmu, Ya sa mu dace da Lailatul Qadr.
    Ameen.

    Husain M. Inuwa.
    usainiskima@gmail.com
    09042152353

    Danna nan don karanta Shan Azumi Ga Matafiya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Azumin Watan Ramadan 2

    Azumin Watan Ramadan 2

    Idan kuma mutum ya kusa haɗiye abinci ko abin shan, sannan kuma sai ya ji ana kiran sallah, idan lokaci ne, ma`ana shi ne wanda ya fara kiran sallah a lokacin ko kuma mutumin yana da saurin yin kiran sallah, saboda shi mutumin ya tashi da wuri ya yi sahur ɗinsa, to mutum zai iya yin sauri ya haɗiye wancan lomar ko abincin ko abin shan.

    Saboda haka yana da matuƙar mahimmanci ko amfani ga mai azumi haɗi da mai kiran sallah su san lokacin da alfijir yake fitowa ko alamar fitowar alfijir a kowace rana, saboda wasu ladanan suna kiran sallar asubah ko kiran sallah na biyu kafin alfijir ya fito, wasu kuma ladanan suna kiran sallah ne bayan alfijir ya fito da jimawa, wasu kuma masu yin azumi da su suke yin la`akari.

    Haka kuma ya kamata ladanai da masu yin azumi mu san hukunce-hukuncen na yin azumi haɗi da yadda alfijir yake fitowa da yadda rana take faɗuwa, saboda a nan ma ana samun wasu matsaloli da yawa ga wasu ladanan, saboda suna kiran sallah magariba kafin rana ta gama faɗuwa ko lokacin kiran sallah magariba ya yi, su kuma wasu mutane da su ke la`akari da zarar sun ji kiran sallah sai su ɗauki abin shan su ko abin cin su, sai su kama ci ko sha ba tare da yin la`akari da duba lokacin shan ruwa ba.

    Saboda haka yana da matuƙar mahimmanci ga mai yin azumi, idan zai sha ruwa ya tabbatar lokacin shan ruwan ya yi, saboda da mutum ya yi gagggawar shan ruwa, kuma bai tabbatar lokacin shan ruwan ya yi ba, to gara ya jinkirta shan ruwa bayan an yi sallah, sai mutum ya sha ruwan, saboda idan ya sha ruwa kafin lokacinn shan ruwan ya yi, to ba shi da azumin wannan ranar, haka kuma idan mutum da gangan ko alfahari ko taƙama ya sha ruwan, to ya karya azuminsa, sannan kuma akwai kaffaran azimi a kansa guda sittin a jere haɗi da guda ɗayan can da ya karya.

    Saboda waɗannan misalan ya kamata ‘yan uwana musulmai mu tashi tsaye wajen ilimi addini da na zamani, saboda malam mai ” ahlari ” yace “bai kamata ba ga wani mutum ya aikata wani abu a cikin addinin musulunci, har sai ya san hukuncinsa ko abin da Allah (da manzom Allah) yace a kan abin da zai aikata a cikinsa”.

    Haka kuma wannan ƙa`idar take a cikin addinin musukunci, babu wani abu da wani mutum ya isa ya aikata har sai ya san hukuncinsa a addinin musulunci, saboda haka yana da matuƙar mahimmanci ga ladanai su koyi yadda ya kamata su dinga kiran sallah, saboda kaucewa wasu kura-kurai na kiran sallah.

    Bugu da ƙari kuma, idan mutum ya yi mafarki suna ganawa da rana da wani mutum (mace ko namiji), sannan kuma a cikin watan azumin Ramadan, yaya azuminsa yake ?, amsa, azuminsa yana nan matuƙar a wannan yanayin hakan ta faru.

    Amma kuma idan mutum tunanin wani abu ne ko kuma ya kalli wasu abubuwa ne, sai ya fitar da wani abu daga gabansa mai kauri-kauri, sannan kuma fari-fari kamar ruwan kwakwamba ko ƙurji, to hukuncinsa shi ne, hukuncin wanda ya karya azumi da gangan, zai rama azumi guda sittin a jere na kaffara, sai kuma guda ɗaya wanda ya karya.

    Danna nan don karanta Guzirin Ramada Daga Rayuwar Sahabbai Da Magabata Na Gari

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Azumin Watan Ramadan

    Azumin Watan Ramadan

    Azumin watan Ramadan, wajibi ne a kan kowane musulmi, kuma wanda yake baligi, sannan kuma mai hankali, saboda mara hankali zai iya aikata duk abin da ya ga dama kuma a lokacin da ya so, ba tare da yin la`akari da halaccin ko haramcin abin da yake aikatawa ba, saboda babu hankali a tare da shi a lokacin da yake aikata haka.

    Haka kuma azumi yana zama ko tabbata ne, saboda cikar watan sha`aban (kwanaki ashirin da tara ko talatin) ko kuma saboda ganin jinjirin watan Ramadan da yamma, kafin ko bayan sallar magariba ta hanyar gani da ido ko samun labarin ganinsa (wata) a  wata jihar ko  garin ko unguwa, ta hanyar wasu mutane amintattu kuma masu halaye masu kyau haɗi da mu`amala mai kyau a tsakaninsu da mutane.

    Saboda haka da zarar mutane sun ga wata ko sun samu labarin ganin wata daga wajen irin waɗancan mutane, to azumi ya zama wajibi a kan mutum sai ya yi ko ya ɗauka, haka kuma za a aikata ko lura a lokacin ajiye azumi, ta hanyar ganin sabon tsayuwar watan shauwal ko ta hanyar cikar watan Ramadan kwana lokacin talatin(30).

    Bugu da ƙari kuma, ana iya ɗaukar niyyar azumin watan Ramadan ne, bayan ko a lokacin da mutum ya samu labarin ganin wata ko ya gani da idonsa kafin fitowar alfijir, saboda tabbatar tsayuwar watan Ramadan.

    Sannan kuma idan mutum ya ɗauki abincisa zai ci, to kafin ya fara cin abincin, dole ne sai ya tabbatar ya wanke hannunsa ko cokalin da zai ci abinci da shi haɗi da bakinsa, sannan kuma sai ya ƙulla niyyar yin azumin watan Ramadan guda ashirin da tara ko takatin.

    Misali, idan mutum ya ɗauki abincinsa ya ajiye a gabansa, kafin ya fara cin abincin, sai ya yi Bismillah,  sannan yace “Allahumma Inni nawaitus siyamu Ramadan tis`a wa ashiruna au salasuna” ko kuma mutum yace “Nawaitus siyamu Ramadan tis`a wa ashiruna au salasuna” .

    Ma`ana ya Allah na yi niyyar yin azumin watan Ramadan guda ashirin da tara ko guda talatin.

    Saboda haka idan mutum ba zai iya faɗar wancan kalma ba da larabci, to zai iya faɗar kalmar da harshen Hausa ko Fulatanci, Barbanci, Yarabanci ko harshen da yake iya magana da shi, hakan ya halatta, Misali “Na yi niyyar yin azumin watan Ramadan guda ashirin da tara ko guda talatin”,. amma kuma an fi so mutum ya faɗa da larabci.

    Bugu ƙari kuma, idan mutum ya yi niyyar yin azumin watan Ramadan tun a daren da aka ga wata, ma`ana tun niyyar da ya yi na azumin sa na farko,to wannan ya isar masa a cikin dukkanin azuminsa na wannan watan, saboda babu wani sharaɗi a kan mai yin azumi na sake yin niyya a cikin kowane azumi ko rana, matuƙar azumin na sa a jere zai yi, amma kuma idan ba a jere zai yi su ba, saboda wata matsala, to dole ne a kansa  sai ya sake yin niyyar azumin a duk lokacin da zai yi(azumi).

    Sannan kuma  yana daga cikin sunnah yin azumi gaggauta shan ruwa da jinkirta yin sahur, ma`ana da zarar mutum ya ji an kira sallar magariba, sai ya yi saurin shan ruwa (da dabino ko “yayan itatuwa ko ruwa) kafin mutum ya yi sallar magariba, saboda haka ne ma yake da matuƙar kyau ko ake buƙatar a samu kamar mintuna  huɗu ko biyar a tsakanin kiran sallah da yin sallah.

    saboda mutane su samu damar aikata wancan sunnah ta azumi kafin suyi sallah, amma kuma ba dole ba ne sai mutum ya aikata haka, amma kuma aikata haka yana da matuƙar kyau sosai, soboda sunnah ce ta annabi Muhammmad (Sallallahu alaihi wasallam).

    Sai kuma jinkirta yin sahur, ma`ana kada mutum ya tashi cikin dare ya yi sahur, ma`ana kamar misalin ƙarfe biyu na dare ko kafin a kira sallah na farko, amma kuma idan mutum ya aikata haka azuminsa ya yi, sai dai bai aikata sunnah ba.

    Haka kuma mutum ya nisanci cin abinci ko abin sha a lokacin da alfijir yake fitowa ko a lokacin da ake kiran sallah na biyu, saboda ana buƙatar a samu kamar mintuna goma  ko mintuna goma sha biyar(15) a tsakanin kiran sallah da gama yin sahur, amma idan mutum ya sa abinci a cikin bakinsa, sai kuma ya ji ana kiran sallah na biyu ko asubah, to sai ya yi sauri ya fitar da abin da yake bakinsa, saannan kuma ya kuskure bakinsa sai ya ci gaba da yin azuminsa.

    Danna nan don karanta Yaƙe-yaƙen Annabi SAW A Watan Ramadan

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Halayen Da Ya Kamata Mai Azumi Ya Siffantu Da Su

    Halayen Da Ya Kamata Mai Azumi Ya Siffantu Da Su

    Akwai waɗansu muhimman halaye da ya kamata mai azumi ya siffanta da su, a gan su da gaske a tattare da shi. Cikin halayen akwai:

    i. Haƙuri, wato mai azumi ya siffantu da haƙuri wanda shi zai zama jagaba a cikin lamuransa, ya hana shi bin son zuciya da saɓa wa Allah. Manzon Allah (S.A.W) ya ce “Idan ɗayan ku yana azumi, kada ya yi maganganun fasiƙanci. Idan wani ya zage shi, ya ce Ni mai azumi ne” (Sahihul Bukhari 1894, Sahih Muslim 1151).

    ii. Riƙon amana, yana da kyau mai ya zama mai riƙon amana, domin tana daga cikin abar da za ta taimaka masa wajen kiyaye azuminsa.

    iii. Rahama, ana son mai ya siffantu da rahama, da sakin hannu da karamci, da kuma yalwar zuciya. Manzon Allah (S.A.W) ya ce “Duk wanda ya ciyar da mai azumi, yana da kwatankwacin ladan wanda ya ciyar ba tare da an rage ladan wanda aka ciyar ɗin ba” (Sunan al-Tirmizi 647, Sunan Ibn Majah 17).

    iv. Nasiha, yana da kyau mai azumi ya kasance mai yin nasiha da kuma umarni da kyakkyawa da hani ga mummuna.

    v. Sulhu, mai azumi yana da kyau ya kasance mai yin sulhu da sasanta mutane, musamman la’akari da cewa ƙiyayya da gaba na kawo tsaiko wajen karɓar ibada da addu’a.

    vi. Kame harshe, ya kamata mai azumi ya kame harshensa daga maganganu na shirme da shashanci, sannan ya nesanci giba, zagin mutane da yi musu ƙage ko sharri da ƙarya ko musu marar dalili, musamman abin da ya shafi siyasa ko wasan ƙwallo ko wanin waɗannan.

    An karbo hadisi daga Abu Huraira (R.A) cewa, Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Wanda duk bai bar faɗin magana ta zur da aiki da ita ba, to Allah ba shi da buƙatar ya bar cinsa da shansa”. (Bukhari 4/99).

    Haka nan wani hadisin dai daga Abu Huraira (R.A) dake cewa: Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Ba azumi ba ne barin ci da sha, shi azumi shi ne na yasasshen zance da batsa, ko da wani ya zage ka, ko ya yi maka wauta, to ka ce: “Ni mai azumi ne”. (Ibn Khuzaima 1996). Ibnu Majah ya fitar da hadisi mai ɗauke da razani ga mai yin maganganun banza a yayin da yake azumi, ya ce: “Sau da yawa wani mai azumin ladansa shi ne yunwa da ƙishirwa”.

    vii. Rintse ido da kame farji, yana da kyau mai ya rintse idanuwansa daga kallon haramun, ya kuma kare farjinsa daga dukkanin haramtattun abubuwa. A nan muna jan hankalin waɗanda ke ganin kallon fina-finai ko tashoshi na gusar musu da yunwa, haƙiƙa wannan kuskure ne babba da kuma munana zato ga Allah, da kuma keta iyakokinSa.

    Su ma masu sanya fina-finai a tashoshi wajibi su ji tsoron Allah, sani ribar rayuwa da albarkar abin da suke so shi ne ginawa bisa tafarkin Musulunci.

    viii. Iklasi, ya kamata mai Azumi ya ƙudurce cewa lalle yana yin wannan azumin ne saboda Allah, kuma domin neman yardar Allah, ba domin mutane su yabe shi ba. A nan, ana jan hankalin yan’uwa masu yin sadaka ko ciyar da masu Azumi da masu tafsirin Alku’ani, da limamai masu rera tilawa, da masu zuwa Umarah, da sauran aiyuka nagari, wajibi su sanya iklasi kada shaiɗan ya lalata musu ayyukansu.

    ix. Bin sunnar Manzon Allah (S.A.W), wajibi ne mai azumi ya nesanci bidi’o’i, ya tsaya kan sunna ka’in da na’in, domin kyakkyawan aiki yana cikin koyi da Fiyayyen Halitta (S.A.W).

    x. Tarbiyya, wajibi ne mai azumi ya tsaya wajen ƙoƙarin tarbiyyantar da kansa da ‘ya’yansa ko ‘yan’uwansa ko waɗanda yake da iko a kansu. Kuma iyaye su ɗauki wannan wata a matsayin lokacin roƙarwa ‘ya’yansu shiriya.

    Domin Karanta Abubuwan da Suke bata Azumi danna nan

  • Tambayoyin Ramadan (117) Tare Da Amshoshin Su

    Tambayoyin Ramadan (117) Tare Da Amshoshin Su

    1. Da me zan dogara wajen ɗaukar azumin Ramadan, shin sai na ga watan Ramadan da idanuna ƙuru-ƙuru?

    Amsa: Mutum zai dogara ne da abin da shari’ar Musulunci ta umarce shi ya yi, shi ne ya ɗauki azumi da zarar hukuma ta sanar da ɗaukar azumin, ko kuma ajiye shi.

    Hujja: “Ku ɗauki azumin Ramadan da zarar kun ga jaririn wata, ku ajiye azumi da zarar kun ga jaririn watan Shawwal” Marawaiji Ibn Umar, littafin Bukhari & Muslim.

    2. Wane ne azumin Ramadan ya wajaba a kansa?

    Amsa: Wanda azumin Ramadan ya wajaba a kansa, shi ne wanda gashin mara ya fito masa, mace ko namiji.

    Hujja: “Shari’ar Musulunci ba ta aiki a kan mutum uku, su ne: Ƙaramin yaro har sai ya balaga” Marawaicin Aliyu ibn Abi Ɗaalib, Ummuna A’isha, littafi Musnadu Ahamada.

    3. Mutum nawa ne ake buƙatar su ga wata kafin a ɗauki azumi?

    Amsa: Mutum ɗaya idan ya ga watan azumi, ya wadartar ga mutanen wannan ƙasar, da mutum ɗayan nan ke ciki kowa ya ɗauki azumi.

    Hujja: “Wani Balaraben ƙauye ya ce, “Ya ga jaririn watan Ramadan”, sai Manzo ya ce, “Ka shaida babu abin bauta da cancanta sai Allah, ka shaida Allah ne ya aiko ni?” Sai Balaraben ya ce, “Na shaida”. Sai aka umarci Bilal ya faɗa wa mutane, su tashi da azumi gobe”. Marawaici Ibn Abbas, littafi Ahamad, Turmuzi, Nassa’i Ibnu Maajah, Abu Dawud.

    4. Akwai wata alama dake tattare da jaririn watan Ramadan?

    Amsa: Babu wata alama da mutum zai gani, sai dai kawai zai ga jaririn watan Ramadan ne kamar yadda ake ganin sabon kowane wata idan ya kama.

    Hujja: “Mutane sun ga jaririn wata, sai na ba wa Shugaban halitta labarin cewa, ni ma na gan shi” Marawaici ibn Umar, littafi alAbu Dawud, Haakim, Ibn Hibban.

    5. Shin idan na ga watan Ramadan, zan yi shiru ne na ɗauki azumin ni kaɗai, ko yaya zan yi?

    Amsa: Idan mutum ya ga watan azumin Ramadan, zai sanar da hukumar dake da alhakin sanar da al’umma, domin ɗaukar azumin.

    Hujja: “Bilal faɗa wa mutane su tashi da azumi gobe…….. ” Marawaici Ibn Abbas. littafi Ibnu Kuzaima, Ibnu Hibban, Nassa’i.

    6. Mene ne sahur?

    Amsa: Sahur shi ne abincin da wanda zai tashi da azumi yake ci, kafin fitowar alfijir.

    Hujja: “Ku yi sahur, domin a cikin sahur akwai albarka” Marawaici Anas Ibn Malik, littafi Bukhari Sahihul Muslim.

    7. Shin dole ne sai mutum ya ci abinci sosai sannan za a ce ya yi sahur?

    Amsa: Ko da ruwa mutum ya kurɓa, ko ya ci dabino, shi ake kira sahur, ba sai lalle ya ci abinci ba.

    Hujja: Ko da ruwa ne mutum ya kurɓa, ya yi sahur, mala’iku na addu’a ga masu yin sahur”. Marawaici, Abu Sa’idul Ƙuduri, littafi Musnadu Ahamad, Sahihu Ibnu Hibban, Haisami, Attargib Wattarhib.

    8. Idan na farka a makare lokacin sahur, ina fara cin abincin sahur, sai alfijir ya fito, yaya zan yi?.

    Amsa: Mutum zai cinye abin da ya saka a bakinsa lokacin sahur, ko da alfijir ya fito, haka kuma, idan ruwa ne zai shanye wanda yake cikin kofin, ko da alfijir ya fito.

    Hujja: “Idan ɗayanku yana cin abinci, sai ya ji kiran sallah, ya ƙarasa cin abincinsa”. Marawaici: Abu Huraira, littafi Musnadu Ahamad sunan, Abu Dawud, Ibn Hazmin, Ibnul Kayyim.

    9. Ta yaya zan gane lokacin da zan dakatar da sahur, idan zan ɗauki azumi?

    Amsa: Mutum zai dakatar da yin sahur, ta hanyar kiyaye lokutan fitowar alfijir da ake rubutawa na kowacce rana a kalanda, ko kafofin sadarwa kamar gidajen radiyo da talabijin da wayoyin hannu.

    Hujja: “Ku ci, ku sha lokacin sahur, har sai hasken alfijir ya fito muku a fili”. Suratul Baƙara aya 187.

    10. Zan iya amfani da kiran assalatu wajen dakatar da sahur?

    Amsa: Mutum zai iya yin hakan, amma abin da ya fi shi ne, ya yi amfani da lokaci, maimaikon kiran assalatu, saboda wasu na saka assalatu a farkon kira, wasu kuma a ƙarshen kira, shi ma ladanin da lokacin yake amfani.

    Hujja: “Bilal ne zai fara kiran sallar farko, ku ci, ku sha, har sai Ibnu Ummul Maktum ya yi kiran sallah ta biyu”. Makaho ne ba ya kira, har sai an ce masa alfijir ya fito. . marawaici: Ibn Umar, littafi Sahihul Bukhari da Sahihu muslim.

    11. Shin idan na kwanta barci, sai na wayi gari janaba ta same ni, ta hanyar mafarki ko kwanciyar aure, zan iya ɗaukar azumi, ko sai na yi wanka?

    Amsa: Mutum zai ɗauki azumi da janaba a jikinsa, wannan ba ya taɓa azuminsa.

    Hujja: “Shugaban halitta yana wayar gari da janaba, sannan ya yi wanka” marawaici Ummuna A’isha da Ummus Salama, littafi: Sahihul Bukhari, Sunan Nassa’i, Tamhid ibn Abdulbarri.

    12. Daga wane lokaci zuwa lokaci ne zan kasance da azumi a bakina?

    Amsa: Mutum zai ɗauki azumi tun kafin hudowar alfijir, har ya zuwa faɗuwar rana.

    Hujja: “Har sai hasken alfijir ya fito, ya bayyana, sannan ku kame daga ci da sha da mu’amalar auratayya, har ya zuwa faɗuwar rana”. Suratul Baqara, aya 187.

    13. Waɗanne abubuwa ne na fili dake karya azumi?

    Amsa: Abubuwan fili da suke karya azumi su ne: cin abinci ta hanyar tauna ko haɗiya, shan ruwa ko wani abin sha mai kama da ruwa, kwanciyar aure ga masu aure, fitar da maniyi ga wanda ba shi da aure ta hanyar kallace-kallace a fili ko mujalla ko wayoyin hannu ko talabijin, sauraran labaran batsa, ko na motsa sha’awa kai tsaye daga wani ko ta hanyoyin sadarwa da gangan.

    Hujja: “Wanda ya ci, ko ya sha, ko ya kusanci iyalinsa, ya karya azuminsa”. Marawaici: Abu Huraira, littafi Sahihul Bukhari da Sahihu Muslim, sunan Abu Dawud, Sunan Turmuzi, Sunan Nassa’i Sunan Ibn Maajah.

    14. Waɗanne abubuwa ne ke lalata azumi a ɓoye?

    Amsa: Abubuwan dake lalata azumi a ɓoye su ne: Akwai yi da wani da shaidar zur da gulma da ƙin yin sallah sai lokacinta ya wuce, babu wani dalili na shari’ah, ƙin yin sallah kwata-kwata.

    Hujja: “Wanda duk bai bar zancen zur ba, da aikata zur, da yi wa mutane mummunar fassara, Allah ba ya buƙatar ya bar abincinsa da abin shansa”. Marawaici Abu Huraira, littafi Sahihul Bukhari da Sahihu Muslim.

    15. Shin rashin yin sallah a cikin jama’a na lalata azumi?

    Amsa: rashin yin sallar jam’i ba ya lalata azumi, matsawar mutum yana yin sallar a kan lokaci, kawai dai yana tabka asarar lada mai yawa.

    Hujja: “Sallar mutum a cikin jama’a, ta fi sallarsa shi ɗaya a kasuwa ko gida da lada ashirin da biyar ko lada ashirin da bakwai”. Marawaici Abu Huraira, Ibn Umar, littafi Sahihul Bukhari.

    16. Idan ina alwala, sai na zo kurkure baki, sai na haɗiye ruwa garin kurkure baki, yaya lafiyar azumina?.

    Amsa: Mutum ba zai rama azumi ba, idan ya haɗiye ruwa lokacin kurkurar baki, ba da ganganci ba, a cikin alwala ko ba a cikin alwala ba.

    Hujja: “Allah ya yafe wa al’ummata abubuwa guda uku, kuskure da mantuwa da kuma abin da aka tilasta su a kai”. Marawaici Ibn Abbas, Sunan Ibn Maajah, Sahihu Ibnu Hibban, Mu’ujamu Ɗabara’ni.”Ba ku da laifin abin da kuka yi bisa kuskure, sai abin da zuciyarku ta yi da gangan”. Suratul Ahzab aya 5.

    17. Idan ina magana da safe bayan na ɗauki azumi, sai na haɗiye sauro ko kuma na haɗiyi ƙuda da rana yaya azumina yake?

    Amsa: Idan mutum ya haɗiyi sauro, ko ƙuda ko wani kwaro, ko wani abu kamar zare, ko gashi, azuminsa na nan daram, babu komai.

    Hujja: Mardaawi cikin littafin Ijma’a, Ibn Muflih cikin littafin Furu’u, Jasas cikin tafsirin da Zaila’i cikin littafin Haka’iki).”

    18. Idan na ɗanɗana miya domin na ji fitowar gishiri, amma na tofar ban haɗiye ba , yaya batun azumina?.

    Amsa: Idan mutum ya ɗanɗana miya, gishiri,suga,zuma,zobo, juicy, azuminsa na nan matsawar bai haɗiye ba.

    Hujja: “Wanda ya ci ko ya sha, bisa mantuwa, azuminsa yana nan”. Marawaici Abu Huraira, littafi Sahihul Bukhari Sahihu Muslim.

    19. Idan na shaƙi Mantaleta ko Rob ko na saka a leɓe, shin yaya makomar azumina?.

    Amsa: Idan mutum ya shaƙi Mantaleta ko Rob, ko kuma ya shafa a lebe, babu komai; azuminsa na nan daram.

    Hujja: (Littafin fatawa lamba 55455, littafin fatawa lamba 107799),

    20. Idan na shaƙi hayaƙin turaren wuta ko turaren ƙamshi na ruwa, ko na sakawa a ɗaki, yaya azumina?

    Amsa: Idan mutum ya shaƙi hayaƙin turaren wuta, ko turaren ƙamshi na ruwa, babu komai, azuminsa na nan daram.

    Hujja: (littafin Fatawa 55455, littafin Farawa 107799).

    21. Shin zan iya shaƙar maganin shaƙa na masu asma idan na ɗauki azumi sakamakon ciwon asma?

    Amsa: Idan mutum yana fama da ciwon asma, ya hallata ya shaƙi maganin na masu asma, a lokacin da yake azumi.

    Hujja: Fatawa Shaikh Usaimin.

    22. Idan na yi haɓo da azumi a bakina kafin a sha ruwa, yaya azumina zai kasance?

    Amsa: Duk wanda haɓo ya same shi, kuma da azumi a bakinsa, babu komai, azuminsa na nan daram.

    Hujja: ( Daarul Ifata’i Almisiriya). (alajnatu da’ima lilbuhusul ilmiya wal ifta’i 10/264).

    23. Idan na saka kwalli a idona, kuma sai na yi kaki, sai na ga wannan kwallin da na saka a idona a cikin wannan kakin, yaya azumina?

    Amsa: Idan mutum ya yi kaki, sai ya ga kwallin idon da ya saka a cikin kakin da ya yi, babu komai, azuminsa na nan daram.

    Hujja: (sahifatu ittihaadul kahira) “Sayyidina Anas Ibn Malik yana saka kwalli idan yana azumi” Marawaici Abu Dawud, littafi Sunan Abu Dawud, malaman dake ganin halaccin saka kwalli, Ibrahimun Nak’i,aamash.

    24. Idan na yi amai da azumi a bakina, shin yaya azumina?

    Amsa: Idan mutum ya yi amai, amma bai haɗiye wani ɓangare na aman da ya yi ba, babu komai, azuminsa na nan daram.

    Hujja: “Wanda duk ya yi amai, babu komai na ramuwa avkan shi” Marawaici Abu Huraira, littafi Sahihu Ibnu Hibban, Darulkuduni, Haakim, Daarami.

    25. Idan na tara yawu a bakina, sai na haɗiye, yaya azumina?

    Amsa: Idan mutum ya haɗiye yawu, ko wani kaki, azuminsa na nan daram.

    Hujja: (Allamatul dasuqi alma’liky,ibnu habib, littafi Hashiyatu Dasuqi 525/1.

    26. Idan gumina ya shiga bakina, na haɗiye yaya azumina?

    Amsa: idan mutum ya haɗiyi guminsa da azumi a bakinsa, babu komai, azuminsa yana nan daram.

    Hujja: (Almazid fil fatawa 164965).

    27. Idan na ɗauki yaro jariri, sai ya yi min tumbuɗi a cikin hanci, yaya azumina?

    Amsa: Idan mutum ya ɗauki jariri, sai ya yi masa tumbuɗi a cikin hancinsa, azumin shi yana nan daram.

    Hujja: (Almazid fil Fatawa 123962).

    28. Idan navyi amai, kuma bai gama fita ba; akwai ragowa a maƙogwarona, sai na haɗiye, ba tare da ya fito kan harshena ba, shin yaya matsayin azumina?

    Amsa: Duk mutumin da ya yi amai, sai ya mayar da ragowar dake maƙogwaronsa kafin ya fito kan harshensa, ya ci gaba da azuminsa, babu komai.

    Hujja: (Faawar Ibn Abbas da Ibn Mas’ud) littafi Yusuful Qardawi.

    29. Idan na saka jan baki a leɓena, sai harshena ya taɓa, har na haɗiye, tare da yawun bakina, shin yaya azumi na?

    Amsa: Duk matar da ta haɗiye jan baki, sakamakon taɓawa da harshenta yake yi, har ta haɗiyi yawu da shi, azuminta yana nan, babu komai.

    Hujja: (Ibnu Najim) littafi Albaharu Ra’iqu, Fatawa 181305. Mazhab Hanafiya.

    30. Idan mutum yana wanka, sai ruwan sabulu ya shiga hancinsa, azuminsa yana nan?

    Amsa: Idan ruwan sabulun wanka ya shiga hancin mai azumi, babu komai, azuminsa yana nan.

    Hujja: (Alfatawa 261682).

    31. Idan mutum ya saka maganin ciwon Ido, sai ya ji maganin har maƙogwaro, yaya azuminsa.

    Amsa: Duk mutumin da ya saka maganin ciwon Ido, kuma ya ji shi har maƙogwaro, babu komai, azuminsa na nan.

    Hujja: (Mazhabu Hanafiya, Ibnu Taimayyah).

    32. Idan haƙorina yana min ciwo, zan iya barbaɗa magani ko ɗigawa a kan haƙorin, alhali kuma na ɗauki azumi?

    Amsa: Babu laifi idan mai azumi yana fama da ciwon haƙori wanda bai hana shi ɗaukar azumi ba, ya ɗiga magani, ko ya barbaɗa magani a kan haƙorin.

    Hujja: (Alfatawa 6338).

    33. Mutum ne yake da larurar haƙori, wanda jini yake fita daga haƙorinsa, wani lokacin idan ya tofar da yawu, yana ganin jini, kuma ga shi yana azumi, shin idan ya haɗiyi yawu da wannan jinin, azuminsa ya karye?

    Amsa: Babu abin da ya karya masa azumi a nan, kawai dai ya dinga ƙoƙarin zubar da yawun, saboda kar ya haɗiyi ƙwayoyin cuta, ya kuma nemi magani.

    Hujja: (Fatawa Almisiriya).

    34. Idan ƙuraje suka fito min a kan harshena, idan na goga tumaturi suna warkewa, shin zan iya hakan ko da ina azumi?

    Amsa: Mai azumin da ƙuraje suka fito masa Akan harshe, ya hallata ya goga tumaturi, amma kar ya haɗiye yawun bakinsa na lokacin, sai dai ya tofar.

    Hujja: (Alfatawa 6338)

    35. Wani lokacin idan na tofar daga baya kuma na kan ji ɗanɗanonsa idan na haɗiyi yawu, shin ya azumina?

    Amsa: Duk abin da mai azumi ya ɗanɗana shi a kan harshe, ya tofar daga baya, kuma ya haɗiyi yawu, sai ya ji ɗanɗanon abin, a dalilin rashin kurkure baki, azuminsa yana nan daram.

    Hujja: (6338).

    36. Shin ya hallata na wanke baki da man wanke baki idan ina azumi?

    Amsa: Ya halatta mai azumi ya wanke bakinsa da kowane irin sinadarin wanke baki, babu komai.

    Hujja: ( Daarul Ifata’i).

    37. Shin zan iya zuwa a yi min allura da azumi a bakina?

    Amsa: Yin allura ga mai azumi ya halatta, sai idan likita ne ya ce, ya ajiye azumin, to, wajibi ne ya ajiye, amma ita allurar ba ta karya azumi, ko da mutm ya ji wani abu mai kama da ɗanɗanonta a maƙogwaronsa.

    Hujja: (Alfatawa 143225).

    38. Idan mutum yana da cutar (ulcer), zai iya yin gwajin bututun zurawa a ciki, wanda ake zura shi ta baki?

    Amsa: Matsawar likita ya ce ya yi, ba tare da ya ajiye azumi ba, to, ya halatta, saboda shi yin gwajin, ba ya karya azumi.

    Hujja: (Mazhabu Hanafiya, Almu’utamarul Islami fi Dauratih Al’ashirah).

    39. Shin zan iya azumin tazarce?

    Amsa: A’a. Bai hallata mutum ya yi azumin da babu buɗa-baki ba, wato azumin tazarce kenan.

    Hujja: “Mun ga kana yin azumin tazarce,to, wane a cikinku irina? Ni Allah yana ciyar da ni, ya shayar da ni” Marawaici: Abu Huraira, littafi Sahihul Bukhari da Sahihu Muslim.

    40. Shin zan iya bada gudunwamar jini kuma da azumi a bakina?

    Amsa: Bayar da gudunwamar jini ba ya karya azumi, sai idan likita ne ya ce, mai bada gudunwamar ya ajiye azumin nasa.

    Hujja: (Lajnatul Fatawa bi Majmu’il Buhusul Islamiya).

    41. Shin mai azumi zai iya ajiye azuminsa saboda (minor surgery) ƙaramar tiyata wadda ake wa mutum idonsa biyu?

    Amsa: ya hallata idan likita sahihi ya ce da shi, sai ya ajiye azuminsa.

    Hujja: (Daarul Ifata’i Almisiriya).

    42. Shin idan mutum yana da buƙatar ƙarin jini, kuma yana azumi, hakan zai taɓa azuminsa?

    Amsa: Idan likita ya ce ana iya ƙara masa, ba tare da ajiye azumi ba, to, ya halatta, saboda shi ƙarin jinin ba ya karya azumi, sai idan likita ne ya ce ya ajiye azuminsa.

    Hujja: (Lajnatul Fatawa bi Majmu’il Buhusul Islamiyya).

    43. Idan mutum yana fama da rashin lafiya, yaya zai yi da azumi?

    Amsa: Ya hallata mutum ya ajiye azumi saboda rashin lafiya da yake fama da ita, amma kuma rashin lafiya ta kasu gida 3, akwai ta ɗan lokaci, akwai dogowar jinya da take da magani, akwai dogowar jinya wacce ba a kai da gano maganinta ba, ko kuma babu maganin wannan jiyyar a ƙasar da majinyacin yake zaune, saboda dalilai masu yawa, misali ƙarancin ci gaban wannan ƙasa.

    Hujja: “Waɗanda suke fama da rashin lafiya ko suke kan hanyar tafiya, su rama bayan sallah”. Suratul Baqara aya 184.

    44. Idan jinya ce ta ɗan lokaci fa, zan ajiye azumin?

    Amsa: Za ka ci ba shi, sannan kanrama idan ka warke bayan sallah.

    Hujja: “Waɗanda suke fama da rashin lafiya ko suke kan hanyar tafiya, ya rama bayan sallah”. Suratul Baqara aya 184.

    45. Idan jinya ce doguwa fa, zan ajiye azumi ne sai na rama?

    Amsa: Idan dogowar jinya ce, wacce take ɗaukar shekaru ba ta warke ba, ciyarwa zai yi.

    Hujja: “Ga waɗanda za su iya azumin, amma da ƙyar, sai su ciyar da abinci ga miskinai”. Suratul Baqara aya 184.

    46. Idan jinya ce wacce ba ta da magani, ko kuma ba a gano maganinta ba, shin zan iya ciyarwa?.

    Hujja: “Ga waɗanda za su iya azumin amma da kyar, sai su ciyar da abinci ga miskinai”. Suratul Baqara aya 184.

    47. Duk jinyar da ba ta da magani ko ta dindindin ko babu maganinta a inda yake, kuma ba shi da ikon zuwa wata ƙasar neman magani, shi ma ciyarwa zai yi.

    Hujja: “Ga waɗanda ba za su iya azumi ba, sai su ciyar da miskinai”. Suratul Baqara aya 184.

    48. Idan mutum yana fama da ciwon saukar suga ko gyanbon ciki mai zafi, zai iya ɗaukar azumi?

    Amsa: likita ne kaɗai zai iya ba shi amsar wannan tambayar, ta halaccin yin azumi ga wanda ke cikin irin wannan jinyar, ko haramcin hakan, kuma wajibi ne ya bi umarnin likita.

    Hujja: Ga waɗanda ba za su iya azumi ba, sai su ciyar da miskinai”. Suratul Baqara aya 184.

    49. Shin ya hallata mai ciki ta ɗauki azumi?

    Amsa: Shari’ah ta ce, “Mai ciki ta haƙura da azumi, saboda ƙoshin lafiyar jaririnta”.

    Hujja: “Duk wanda yake cikin halin rashin lafiya, ya rama bayan sallah”. Suratul Baqara 184.

    50. Shin mai cikin da ta ajiye azumi ciyarwa za ta yi, ko bari za ta yi ta rama bayan ta haihu?

    Amsa: Mai ciki da mai shayarwa, malaman da suka ɗauke su a matsayin marasa lafiya na ɗan lokaci sun ce, “Za ta rama bayan sallah”. Kamar Al-imamu Maalik, malaman da suka ɗauke su a matsayin marasa lafiya, sun ce, “Su ciyar kuma su rama bayan sallah”. Kamar Al-imamu Shafi’i, malaman da suka ɗauke su a matsayin waɗanda ba za su iya azumi ba, bisa uzuri na rauni kamar uzurin tsofaffi sun ce, “Ba za su rama ba, ciyarwa kawai za su yi cikin azumi” Kamar Ibnu Abass, Ibnu Umar.

    Hujja: (Fatawar Ibnu Abbas da Ibnu Imar) littafi Bidaayatul Mujtahid wa Nihaayatul Muqtasid, Ibnu Rushdin.

    51. Idan alfijir ya fito, kuma da janaba a jikina cikin Ramadan, yaya azumina?

    Amsa: babu abin da ya haɗa azuminka da janaba, azuminka yana nan daram.

    Hujja: (fatawar Al-imamun Nawawi, Majmu’ul Fatawa war Rasa’ili Mujalladi na 17).

    52. Idan al ‘ada ta ɗauke, kuma ban yi wanka ba, har alfijir ya fito, shin yaya azumina zai yiwu?

    Amsa: Macen da ta gama al’ada, da wacce ta haihu, jinin ya ɗauke, duk hukuncin su ɗaya da mai janaba, babu komai idan alfijir ya fito ba su yi wanka ba, kuma azuminsu bai ɓaci ba.

    Hujja: (Fatawar A-‘imamun Nawawi, Ajmu’ul Fatawa war Rasa’ili Mujalladi na 17).

    53. Idan Ramadan ya zo, kuma ana bi na bashin azumin Ramadan 5 ko 7 ko 10 na wanda ya wuce, yaya zan yi?

    Amsa: Ba za ka rama ba, har sai Ramadan ɗin da ya zo, ya kare, amma kuma za ka ciyar gwargwadon yawan kwanakin da ake bin ka bashi, a cikin watan Ramadan ɗin da ya zo ya tarar da kai da bashi.

    Hujja: (Mazhabu Malikiyya, Mazhabu Shafi’iyya, Mazhabu Hambaliyya, littafi Nailul Audar na Shaukani).

    54. Ya yawan abin da zan ciyar yake?

    Amsa: Za ka ciyar da abincin da yawan sa ya kai cikin tafin hannunka guda biyu har sau huɗu, shi ne ( Mudun Nabiyi) amma tafukan hannun mutum matsakaici, ba babba can ba, kuma ba ɗan ƙarami ba.

    Hujja: ( haka Anas Ibn Malik ya yi lokacin da ya ciyar saboda tsufa, littafi Nailul Audar na Shaukani).

    55. Su wane ne waɗanda suka cancanta a ciyar?

    Amsa: Za ka ciyar da duk wani mabuƙaci, yaro ko babba mace ko namiji.

    Hujja: “Ka ciyar da miskini ɗaya a rana” marawaici Abu Huraira, littafi Sahihul Bukhari.

    56. Idan ƙasar da nake babu mabuƙata a kusa, zan iya turawa wata ƙasar a ciyar?

    Amsa: Kwarai da gaske, za ka iya turawa da ciyarwa zuwa inda mabuƙata suke.

    Hujja: “Babu wasu mutane dake da buƙatar wannan fiye da ni da iyalina” marawaici Abu Huraira, littafi Sahihul Bukhari.

    57. Zan iya ƙimanta abincin da zan ciyar na bayar da kuɗin a cibiyoyin addini a ciyar min?

    Amsa: Ya halatta ka ba wa cibiyoyin addini kuɗin bisa ƙiyasin abincin da za ka ciyar, sai su ciyar a madadin ka.

    Hujja: (Fatawar Sufyanus Sauri, littafi Arruhu na Ibnu Qayyim.

    58. Wannan ciyarwar mece ce matsayin ta tunda ko na ciyar zan rama bayan sallah?

    Amsa: Matsayin wannan ciyarwar, kaffara ce na ƙin rama azumi da gangan, har wani Ramadan ɗin ya sake zuwa.

    Hujja: (Mazhabu Malikiya, Mazhabu Shafi’iya, Mazhabu Hambaliyya, littafi Nailul Audar na Aliyu Shaukani).

    59. Idan na manta na sha ruwa ko na ci abinci cikin watan Ramadan, yaya azumina?

    Amsa: Wanda duk ya manta ya sha ruwa ko ya ci abinci, azuminsa yana nan daram.

    Hujja: “Wanda ya ci ko ya sha bisa mantuwa cikin Ramadan, ya ƙarasa azuminsa, babu ramuwa a kan shi, Allah ne ya ciyar da shi ya shayar da shi” marawaici Abu Huraira, littafi Sahihul Bukhari.

    60. Idan ana bi na bashin azumin Ramadan 5 ko 7, har wani Ramadan din ya sake zuwa, zan iya ciyar da mutum 5 ɗin ko 7 a rana ɗaya lokaci ɗaya?

    Amsa: Ya halatta mutum ya ciyar da mutane lokaci guda, gwargwadon yawan kwanakin da ake bin shi bashin azumin Ramadan din da ya sha.

    Hujja: “Tafi da wannan, ka ciyar da miskinai sittin” Marawaici Abu Huraira, littafi Sahihul Bukhari.

    61. Idan mutum ya samu kanshi ko ya yi tafiya zuwa inda rana take kaiwa wata shida ko kasa da haka, ba tare da dare ya shigo ba, ko kuma dare yake yin wata shida ko ƙasa da haka, ba tare da rana ta hudo ba, yaya zai yi da azumi?

    Amsa: Idan mutum ya samu kansa a irin waɗannan ƙasashe da ake dare ko rana na tsahon lokaci, zai yi amfani ne da (time zone) wato ƙasashen da lokutansu ya zo ɗaya, amma su suna samun shigowar rana da dare, sai ya ɗauki azumi lokacin da suke ɗauka, ya sha ruwa lokacin da suke sha, haka kuma zai iya amfani da ƙasar da take kusa da su, wacce ba ta da irin wannan yanayin, ya kalli awowin da suke yin azumin Ramadan na wannan shekarar, misali suna yin azumin awa 11 ko 12 a rana, to shi ma haka zai yi, kuma ta fuskar ganin watan Ramadan ma ko Shawwal, haka zai yi.

    Hujja: (Daarul Ifata’i Almisiriya).

    62. Idan mutum zai yi tafiya, ko da a jirgi ne, zai ajiye azumi?

    Amsa: Ita tafiya komai sauƙinta, sunanta tafiya, idan mutum ya ajiye azumi, ya aikata sunna, idan kuma ya yi azuminsa, babu laifi, azuminsa ya yi, sai dai idan yin azumin, zai jefa shi cikin asara, ta rai ko lafiya ko hankali, to a nan, wajibi ne ya ajiye azumin, sai ya rama bayan sallah.

    Hujja: “Shugaban halitta ya sa ankawo masa ruwa a kofi, ya ɗaga sama, yadda kowa zai gani, sannan ya sha a kan hanyarsu ta tafiya, aka ce masa, wasu ba su ajiye azumin ba, ya ce su ne suka zaɓar wa kansu shan wahala”. Marawaici Jabir Ibn Abdullah, littafi Sahihu Muslim.

    63. Mutum zai iya rama wa iyayensa azumin Ramadan?

    Amsa: Tabbas mutum zai iya rama wa iyayensa ko wani nasa azumin Ramadan da ya sha kafin rasuwar sa.

    Hujja: “Wanda duk ya mutu akwai ramuwar azumi a kansa, manema haƙƙin jininsa suna iya rama masa”. Marawaici Ummuna A’isha, littafi Sahihul Bukhari.

    64. Shin mutum zai iya ciyarwa a maimaikon ya rama musu azumin Ramadan ɗin?

    Amsa: Ya halatta mutum ya ciyar da abinci a madadin rama wa iyayens ko wani nasa azumin Ramadan.

    Hujja: (Fatawar Sufyanus Sauri da Hassan, littafi Acrruhu).

    65. Idan mutum ya yi tafiya, sai ya ajiye azuminsa, a lokacin iyalinsa tana al’ada, sai bayan rana ta yi zawali, har azahar ta yi, sai al’adar ta ɗauke, ta yi wankan tsarki, shin ya halatta su yi mu’malar aure da rana?

    Amsa: Ko shakka babu, ya halatta, saboda wannan azumin za su rama shi ne bayan sallah, bisa uzuri da shari’ah ta yi musu, akwai wasu daga cikin malaman dake ganin su haƙura, domin su girmama watan, amma ijtihaadi ne kawai yin hakan, ba wulakanta watan ba ne, hasali ma ibada suka yi, domin abin da suka yi sunansa sunna.

    Hujja: Al ‘lajnatud Da’ima 10202, Majmu’ul Fatawa Ibn Baaz 15/307, Fatawa Siyam Ibn Usaimin 344.

    66. Shin idan mutum yana azumin Ramadan sai ya manta ya kusanci matar shi da rana?

    Amsa: Babu ramuwa, kuma babu kaffara, azuminsa yana nan daram.

    Hujja: Mazhabu Hambaliyya Mazhabu Shafi’iyua, Ibnu Taimayyah, Shaukani, Sun’ani, littafi , Nailul Audar,Subulus Salam.

    67. Shin idan mutum yana cikin kusantar iyalinsa alfijir ya fito, yaya azuminsa?

    Amsa: Daga lokacin da alfijir ya fito, sai ya dakatar daga ci gaba da kusantar ta, babu komai, azumin shi yana nan daram.

    Hujja: Nawawi, Mawurdi, littafi Almajmu’u, Attaju wal iklil li muktasar Khalil.

    68. Idan mutum ya ji kiran sallah na fitowar alfijir ya ci gaba da kusantar iyalinsa da gangan fa?

    Amsa: zai rama wannan azumin bayan sallah, sannan kuma zai yi kaffara.

    Hujja: Nawawi, Mawurdi, littafi Almajmu’u.

    69. Idan mai azumi ya ji kiran sallah, amma bai ci gaba ba, sannan kuma bai zare al’aurarsa daga na iyalinsa ba nan take, har sai bayan mintina biyu ko uku fa?

    Amsa: Zai rama wannan azumin guda ɗaya, amma babu kaffara.

    Hujja: Nawawi mawurdi,

    70. Mece ce ƙiyamul laili?

    Amsa: Ƙiyamul laili ita ce duk sallar da mutum ya yi ta bayan sallar isha’i, ita ce ƙiyamul laili.

    Hujja: (Muhammad Abdus sami’i Aminul Fatawa bi Daaril Ifta’i Almisiriya).

    71. Akwai bambanci tsakanin ƙiyamul laili ne da tarawihi ko asham?

    Amsa: Babu wani bambanci, duk abu ɗaya ne, sunan ne kawai kowanne da abin da yake nufi, idan aka ce ƙiyamul laili, ana nufin tsayuwar sallah cikin dare, tarawihi kuma, sallar da idan mutum ya yi raka’a biyu ko raka’a hudu, yakan ɗan zauna ya huta, kafin ya ci gaba.

    Hujja: Nailul Audar Daarul Ifata’i Almisiriya.

    72. Akwai bambanci ne da tsakanin tarawihi da sallar tahajjud?

    Amsa: A’a. Babu bambanci duk ita ce ƙiyamul laili, fassarar tahajjud tana nufin dagewa ko kokari wajen yin sallar dare, ta hanyar daɗewa a tsaye kana karatun Alƙur’ani.

    Hujja: “Yana ninka yin ibada a goman ƙarshe irin ninkawar da ba ya yi a wasu ranakun”. Marawaici Ummuna A’isha, littafi Sahihu Muslim, Ibn Maajah.

    73. Me yasa aka fi son mai azumi ya dage a goman ƙarshen Ramadan, fiye da goman farko da goman tsakiya?

    Amsa: Ana son mai azumi ya ƙara dagewa ne a goman ƙarshen Ramadan, saboda ninka lada da Allah Azza wa Jalla yake wa bayinsa, ga kuma ‘yanta bayinsa daga shiga wuta da yake ninkawa fiye da goman farko da goman tsakiya. Hujja: Alfatawa 77920 .

    74. Idan mutum ba ya azumi saboda uzuri na shari’ah, shin zai iya duk ibadar da mai azumi yake yi kamar sadaka, ƙiyamul laili, karatun Alƙur’ani, salati, istigifari, da sauran ayyukan lada?

    Amsa: Ko shakka babu, ya halatta ya yi komai idan har yana da damar yi, misali idan mace ce, babu damar ta yi ƙiyamul laili, matsawar uzurinta na rashin tsarki ne.

    Hujja: Alfatawa, Daarul Ifata’i Almisiriya.

    75. Shin idan ana bi na azumin Ramadan da na sha bisa uzurin al’ada, zan iya bari har sai Sha’aban ya zo na rama?

    Amsa: Ƙwarai kuwa, ya halatta macen da ta sha azumi bisa wannan uzurin na al’ada, ta bari har sai Sha’aban ta rama, babu laifi idan ta yi hakan.

    Hujja: Alfatawa 42206, Albayan.

    76. To, idan kuma mijinta ya tuna mata cikin Rajab, ta ce sai a Sha’aban, sai kuma ta ɗauki ciki, har wani Ramadan ɗin ya zo ba ta rama ba fa?

    Amsa: Babu komai na, kaffarar jinkirin ramuwa a kanta.

    Hujja: Alfatawa 42206.

    77. Idan kuma tabari sai sha’aban ta rama sai kuma ta rasu fa?

    Amsa: babu laifi sai arama mata ko aciyar.

    Hujja: Daarul Ifata’i Almisiriya.

    78. Da wane lokaci ne mutum zai yi buɗa baki a shari’ah?

    Amsa: Mutum zai yi buɗa baki ne da zarar rana ta faɗi.

    Hujja: “Idan rana ta ba da baya, ta yi yamma, dare kuma ya ɓullo ta nan, to mai azumi ya buɗe baki”. Marawaici Ibn Umar, littafi Sahihul Bukhari.

    79. Da me aka fi son mai azumi ya yi buɗa baki kafin ya ci abinci sosai?

    Amsa: An fi so mai azumi ya yi buɗa baki da ɗan itace kowanne ne ya samu, ba lalle sai dabino ba, idan babu kuma, ya samu ruwa, ya yi buɗa baki da shi.

    Hujja: “Idan ɗayanku zai yi buɗa baki, ya yi buɗa baki da dabino ko ruwa, domin ruwa na tsarkakewa”. Marawaici Sulaiman Ibnu Aamir, Anas Ibn Malik , littafi Sunan Abu Dawud, Sunan Turmuzi.

    80. Shin akwai addu’a da ake yi kafin mutum ya yi buɗa baki?

    Amsa: Akwai addu’a da mai yin buɗa baki zai yi, amma sai bayan ya yi buɗa bakin ake yin addu’ar.

    Hujja: “Zahabaz zama’u, wabtallatul uruqu, wasabbatal ajaru insha Allah”. Marawaici Ibn Umar, littafi Sunan Abu Dawud, Sunan Nassa’i, Haakim, Baihaqi.

    81. Shin lokacin buɗa baki, lokaci ne na amsa addu’ar mai azumi a kan wata buƙatarsa?

    Amsa: Ko shakka babu, idan mai azumi ya yi buɗa baki, ya yi amfani da wannan damar, ya roƙi Allah Azza wa Jalla buƙatunsa, domin lokaci ne na amsar addu’a.

    Hujja: “Mutum uku addu’arsu ba a dawo musu da ita, Allah yana amsa musu. Mai azumi har sai ya yi buɗa baki”. Marawaici Abu Huraira, littafi Sharhu Mahzab lin Nawawi.

    82. Mene ne ittikaafi?

    Amsa: Shi ne shiga masallaci da niyyar zaman ibada na wasu kwanaki, ba tare da mutum ya fita ko’ina ba.

    Hujja: (littafi Adduru Sinniya, Mausu’a Fiqihiya).

    83. A waɗanne ranaku ne ake yin ittikaafi?

    Amsa: Ana yin ittikaafi ne a goman ƙarshen Ramadan.

    Hujja: “Shugaban halitta yana zaman ibada a masallaci a goman ƙarshen Ramadan, har Allah ya karɓi rayuwarsa”. Marawaici Ummuna A’isha, littafi Sahihu Muslim, Sahihul Bukhari.

    84. Wane lokaci ne ake shiga, sannan wane lokaci ake fita?

    Amsa: Ana shiga ne bayan sallar asuba, wasu malaman kuma sun ce, kafin rana ta faɗi Shugaban halitta yake shiga, wajen zamansa ne, sai bayan sallar asuba yake zuwa, yana fita ne bayan magriba, a daren idi, kafin shigowar yinin idi.

    Hujja: marawaici Abu Huraira littafi Sahihul Bukhari, Sahihu Muslim, Abu Hanifa, Maalik, Sha’fi’i, Ahamad.

    85. Akwai bambanci ne tsakanin yinin idi da daren idi?

    Amsa: Ƙwarai kuwa, domin kowace rana sai daren ya shigo kafin yininta ya shigo, in ban da ranar Arfa, ita kaɗai ce yininta ke riga darenta zuwa.

    86. Shin sai mutum na azumi zai shiga ittikaafi?

    Amsa: Ana shiga ittikaafi ne da azumi.

    Hujja: (Mausu’a Fiqihiya).. “Yana zaman ittikaafi cikin Ramadan”. Marawaici Abu Huraira littafi Sahihul Bukhari, Sahihu Muslim.

    87. A wane masallaci ake son a yi ittikaafi?

    Amsa: Ana so a yi ittikaafi ne, a masallacin da mutum ba zai rasa sallar juma’a ba a jam’i.

    Hujja: (Abu Dawud Assajistan).

    88. Waɗanne abubuwa ne mai ittikaafi zai nisanta?

    Amsa: Mai ittikaafi zai nisanci fita daga inda yake ittikaafi, sai idan fitar ta zamar masa dole.

    Hujja: (Ibnul Munzir)

    89. Shin mace ma za ta iya shiga ittikaafi?

    Amsa: Za ta iya shiga ittikaafi idan ba ta da miji, idan kuma tana da miji, sai idan ya yi mata izini.

    Hujja: “Matan Shugaban halitta sun yi ittikaafi bayansa”. Marawaici Ummuna A’isha. littafi Sahihul Bukhari Sahihu Muslim, Fathul Baari.

    90. Shin akwai wata ibada ce da aka fi son mai ittikaafi ya dinga yi?

    Amsa: Duk ibadar da tafi masa sauƙi a cikin ibadun da yake yi, kafin ya shiga ittikaafi.

    Hujja: (Mausu’a Fiqihiya).

    91. Idan mutum yana ittikaafi, sai janaba ta same shi ta hanyar mafarki, yaya zai yi?

    Amsa: Idan ya farka sai ya je banɗakin masallacin ya yi wanka, idan kuma babu ruwa sai ya yi taimama.

    Hujja: (Fuqhu Maslim Alajnatu Da’ima).

    92. Ana iya kaiwa mai ittikaafi ziyara?

    Amsa: Ana iya kai masa idan buƙatar hakan ta taso, ko a yi masa waya idan bai kashe wayar ba..

    Hujja: Sahihul Bukhari, Fathul Baari.

    93. Shin mai yin ittikaafi zai iya fita ta’aziyya, wacce ta zama masa dole ko dubiyar mara lafiya ko siyan abinci ko biyan buƙata a banɗaki?

    Amsa: Zai iya duk waɗannan abubuwan, haka kawai ne ba a so ya fita.

    Hujja: Sahihul Bukhari, Sahihu Muslim, Almugni li ibni Qudama, Altalqin ala Mazhabi Maalikiya.

    94. Ina son ƙarin bayani a kan bashin (wari) bakin mai azumi da ya fi miski daɗi a wajen Allah Azza wa Jalla.

    Amsa: abin da ake nufi shi ne, zai wayi gari ranar Ƙiyama bakinsa yana ƙamshin turaren da babu irin shi a duniya. Ko kuma zai zama abin da kowane mutum zai yi burin zama ranar Kiyama, saboda darajar da ya samu, saboda wannan bashi bakin nasa, ko kuma zai samu tarin lada ne a kan hakan, saboda babu wani abu mai ƙamshi ko wari a gurin Allah, kowane abu yana kan ɗabi’arsa da ya halicce shi a kai.

    Hujja: (Nailul Audar, Alqaadi Iyaad, Ibnu Abdulbarri).

    95. Me ake nufi da daren lailatul ƙadari?

    Amsa: Daren lailatul ƙadari wani dare ne cikin watan Ramadan da ibada a cikinsa ta yi daidai da ibadar watanni dubu, wanda ya yi daidai da shekara tamanin da uku.

    Hujja: “Lailatul ƙadari kairun min alfi shaharin”. Suratul Qadar aya ta 3.

    96. A wace ranar ce zan nemi wannan dare?

    Amsa: A mara ake neman daren lailatul ƙadari, kamar ranar da azumi ya yi ishirin da biyu (22) da ranar ishirin da huɗu (24) da ranar ishrin da shida (26) da kuma ranar ishrin da takwas (28).

    Hujja: marawaici: Anas ibn Malik , Ibnu Umar, Sahihul Bukhari, Attamhid li ibni Abdulbarri.

    97. Wace alama ce mutum zai gane wannan daren shi ne daren lailatul Ƙadari?.

    Amsa: mutum zai gane wannan daren lailatul Ƙadari ne ta hanyar jin hakan a jikinsa da kuma amincin da zai ji a wannan daren, ya bambanta da na kowanne dare, sannan kuma idan gari ya waye, zai ga rana ta fito haskenta ya yi dishi-dishi.

    Hujja: “Salmum hiya hatt maɗɗala’ill fajar”. Marawaici Ubaiyu Ibnu Kaabin, Sahihu Muslim.

    98. Idan mutum ya dace da daren lailatul ƙadari kuma ya gane cewa wannan shi ne daren lailatul ƙadari,shin akwai wata addu’a ta musamman ne da zai yi?

    Amsa: Zai yi addu’a ne a kan buƙatunsa na duniya da lahira. Ko ya yi addu’ar da Ummuna A’isha ta koya daga Shugaban halitta..

    Hujja: “Allahumma innaka afuwu tuhibbul afuwa, fa afu anni”. Sunan marawaici Ummuna A’isha, Turmuzi, Sunan Nassa’i, Sunan ibn Maajah, Musnadu Ahamad, Ibnu Daqiqul Eidi.

    99. Idan mutum ya karya azumi da gangan mene ne abin da shari’a ta ce ya yi?

    Amsa: Idan mutum ya karya azumi da gangan, zai yi azumin wata biyu a jere ko ya ciyar da mutane sittin ko ya’yanta bawa, wannan ita ce kaffarar laifin da ya aikata na shan ruwa da gangan cikin Ramadan.

    Hujja: marawaici Abu Huraira, littafi Sahihul Bukhari Sahihu Muslim.

    100. Idan ya zaɓi yin azumi sittin yana cikin yi, sai rashin lafiya ta same shi, idan ya ajiye shin sai ya sake daga farko ne?

    Amsa: Idan ya ɗauko yin kaffara nayin azumi sittin, sai ya kamu da rashin lafiya ko ranar sallah layya ta shigo ko al’adarta ta zo, idan mace ce, babu komai, azuminsu na baya bai rushe ba, ɗora lissafi kawai za su yi a kan abin da suka jero, kafin rashin lafiya ko jinin al’ada ko kuma karo da ranar da ba a yin azumi, wato ranar Sallah Babba da Ƙarama.

    Hujja: (Almausu’ah Shaamilah, Fataawas Siyaam).

    101. Shin mace za ta iya shan maganin da zai hana al’adarta zuwa domin ta yi azumin Ramadan gaba ɗaya ko kuma idan akwai kaffara ta azumi sittin, domin ta yi su gaba daya a jere?

    Amsa: Idan har likita ƙwararre ya ce maganin ba zai cutar da ita ba, kamar ya haifar mata da wata illa nan gaba, ba laifi ba ne idan ta sha, amma ta bar tsarin halittarta ta asali da Allah ya yi ta a kai, na tabyi al’ada duk wata, shi ne abin da ya fi.

    Hujja: (Daarul Ifata’i Almisiriya).

    102. Mece ce zakkar fidda-kai?

    Amsa: Zakkar fidda kai, abinci ne da musulmi ke fitarwa ya babwa marasa ƙarfi, domin ya hutar da su daga neman abin da za su ci ranar shagalin sallar buɗa-baki, ranar da kowa yake farin ciki, domin su ma su shiga wannan farin cikin maimaikon su ba zama neman abinbda za su ci.

    103. Wane irin abinci ake bayarwa, kuma yaya yawan abin da za ka fitarwa kowane mutum yake?

    Amsa: Irin abincin da ake ci a yankin da kake zaune, gamagarin abinci ko na musamman gwargwadon wadartarka, ana fitarwa duk mutum ɗaya ciki tafikan hannunka biyu, har sau huɗu, shi ne (Mudun Nabiyi).

    104. Yaushe ake so a fara fitarwa?

    Amsa: Ana fara fitarwa ne tun daga kwanaki biyu kafin sallah.

    105. Su wa yafi cancanta a fitarwa?

    Amsa: Ana fitarwa da duk wani musulmi namiji ko mace, bawa ko ɗan jariri ne ko baligi.

    106. Shin akwai laifi ne idan mutum ya ƙi fitarwa, alhali yana da wadartar yin haka, kuma yaushe ne idan ya fitar ya makara?

    Amsa: Akwai asara mai yawa ga wanda yake da ikon fitarwa, amma ya ƙi fitarwa, idan mutum ya fitar bayan dawowa daga idi, toh abnan ya makara,bko ya fitar ba zakka ya fitar ba, sadaka kawai ya yi.

    107. Shin yin Ummara a watan Ramadan yana da falala ne ta musamman?

    Amsa: Gaskiya ne akwai falala ta musamman fiye da kowace Ummara, sai wacce aka yi da Shugaban halitta.

    108. A wace shekara aka wajabta azumin Ramadan?

    Amsa: An wajabta yin azumin Ramadan ne cikin watan Sha’aban, bayan canza alqibla da kusan wata ɗaya, wasu malaman kuma suka ce bayan watan Sha’aban ya shiga da kwana biyu.

    109. Shekara nawa kenan Shugaban halitta ya yi azumin Ramadan a rayuwarsa?

    Amsa: Ya yi azumin Ramadan ne na tsahon shekara tara.

    110. A cikin azumin Ramadan na shekaru tara da ya yi, sau nawa ya yi azumi talatin, sau nawa ya yi azumi ashirin da tara?

    Amsa: Ya yi azumin Ramadan ashirin da tara sau bakwai, ya yi azumin Ramadan talatin sau biyu.

    111. Waɗanne yaƙe-yaƙe ne Shugaban halitta ya yi, tare da sahabbai a watan Ramadan?

    Amsa: Yaƙi biyu ne kawai ya yi cikin Ramadan, yaƙin Badar babba da fatahu Makka.

    112. Shin Shugaban halitta yana karatun Alƙur’ani na musamman cikin watan Ramadan?

    Amsa: Ƙwarai kuwa, yana tilawar Alƙur’ani cikin watan Ramadan tare da mala’ika Jibrilu.

    113. Shin mene ne hukuncin saukar karatun Alƙur’ani cikin kwanaki uku?

    Amsa: Mustahabbi ne saukar karatun Alƙur’ani cikin kwanaki uku.

    114. Mene ne haramcin saukar karatun Alƙur’ani cikin yini guda?

    Amsa: Ya halatta mutum ya sauke Alƙur’ani cikin yini guda.

    115. Mece ce matsayin saukar karatun Alƙur’ani cikin sallar tarawihi, shin sahabbai sun yi hakan ne?

    Amsa: Saukar Alƙur’ani cikin sallar tarawihi ya hallata, tare da cewa sahabbai ba su yi hakan ba.

    116. Shin ya halatta limamin sallar tarawihi ya dinga sallar tare da Alƙur’ani a hannunsa domin dubawa?

    Amsa: Ya halatta ya yi wa mutane sallar tarawihi da Ƙur’ani a hannunsa da yake dubawa, ba ma sallar nafila ba, har ma ta farilla.

    117. Shin idan hakan ya halatta, mene ne sakamakon kallon takardar Alƙur’anin?

    Amsa: Kallon takardar Alƙur’anin ibada ce, kamar yadda karanta Ƙur’ani yake ibada.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) Yake Shan Ruwa danna nan

  • Abubuwan Da Suke Ɓata Azumi

    Abubuwan Da Suke Ɓata Azumi

    Akwai abubuwan da suke ɓata azumi matuƙar mutum ya aikata su; to azuminsa ya lalace, cikin waɗannan abubuwa, akwai:

    1. Ci ko sha da gangan, idan mai azumi ya ci abinci ko ya sha wani abin sha da gangan, to ya sani azuminsa ya lalace.

    2. Jawo amai da gangan, wanda ya janyo amai da gangan shi ma azuminsa ya lalace. Domin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ambata cikin hadisi cewa, “………… amma wanda ya jawo amai da gangan, to ya yi ramuwa”. (Abu Dawud 2/310, Tirmizi 3/79).

    3. Haila ko nifasi, idan mace ta yi jinin haila ko nifasi cikin wani yanki na yini sawa’un farko ne ko ƙarshe, to azuminta ya warware kuma ramuwa na kanta, idan kuma ta ƙarasa, to bai halatta ba, kuma ba ta da lada. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasalam ya faɗa cikin hadisai da suka zo daga Ibn Umar da Abu Huraira (Radiyallahu Anhu) cewa, “Ashe ba idan mace ta yi haila ba ta sallah, ba ta azumi ba? Suka ce “Haka ne”. Sai ya ce, “Wannan shi ne naƙasu a cikin addininta”. A wata ruwayar ya ce, “Tana zaman kwanaki ba ta sallah, tana shan azumi a Ramadan, to wannan shi ne naƙasu a cikin addininta”. (Muslim 79 – 80).

    Game da umarnin ramuwa kuwa, ya zo cikin hadisin Mu’azat da take cewa; “Na tambayi Nana A’isha na ce mata: “Me ya sa mai haila take rama azumi amma ba ta rama sallah?” Sai ta ce; “Baharuriya ce ke?” Sai na ce “A’a, ni dai ina tambaya ne”. Sai ta ce: “Ya kasance hakan yana samun mu, sai a umarce mu da rama azumi, amma ba a umartar mu da rama sallah”. (Bukhari 4/429, Muslim 335).

    4. Allurar ƙoshi, shi ne shigar da wasu sinadarai masu ƙosar da mutum cikin uwar hanji da nufin ƙosar da maras lafiya, to wannan yana karya azumi, saboda yana shiga ciki ne. Haka zalika idan uwar jini take bi, to ita ma tana karya azumi muddin tana zuwa ne a madadin abinci ko abin sha.

    5. Jima’i, Imam Asshaukani ya ce: “Jima’i babu saɓani kan cewa yana lalata azumi idan ya faru bisa mantuwa, to wasu daga cikin malamai sun haɗa shi da wanda ya ci ko ya sha alhalin ya manta”. Ibnul Ƙayyim ya ce; “Alƙur’ani ya yi nuni cewa jima’i yana karya azumi, kamar ci da sha babu sabani kan hakan”.

    Hadisi ya tabbata daga Abu Huraira (Radiyallahu Anhu) cewa; wani mutim ya zo gun Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Ya Manzon Allah na halaka! Sai Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce masa; “Me ya halakar da kai?”

    Sai mutumin ya ce; “Na sadu da matata cikin Ramadan!” Sai Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce masa; “Za ka iya azumin wata biyu a jere?” Sai ya ce: “A’a”. Sai Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce masa; “Za ka iya ciyar da miskinai sittin?”. Sai ya ce “A’a”. Sai Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce masa “Zauna”.

    Sannan ya zauna; zuwa wani lokaci sai aka zo wa da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) da dabino, sai ya ce; “To ga shi nan, ɗauki ka yi sadaka da shi”. Sai mutumin ya ce; “A tsakanin unguwannin Madina kaf, ba wanda ya kai mu buƙata”. Sai Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya yi murmushi har haƙoransa suka bayyana; sannan ya ce masa “Ɗauki ka ciyar da iyalanka”.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Abubuwan Da Ba Sa Ɓata Azumi danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Laccocin Ramadan Na Mumbarin Jawabi Daga Malamai danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Guziri Ga Mai Azumin Ramadana (Bisa Koyarwar Alƙur’ani Da Sunnah); wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi; Don karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Shin Idan Hakan Ya Halatta, Mene ne Sakamakon Kallon Takardar Alƙur’anin?

    Shin Idan Hakan Ya Halatta, Mene ne Sakamakon Kallon Takardar Alƙur’anin?

    Amsa: Kallon takardar Alƙur’anin ibada ce, kamar yadda karanta Ƙur’ani yake ibada.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Shin Ya Halatta Limamin Sallar Tarawihi Ya Dunga Sallar Tare Da Alƙur’ani A Hannunsa Domin Dubawa? danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Shin Mene ne Hukuncin Saukar Karatun Alƙur’ani Cikin Kwanaki Uku? danna nan.

    Danna link ɗinnan; https://chat.whatsapp.com/JtD82AjZZmo3AtSTaKP05r domin shiga WhatsApp group namu na Ramadan.

  • Shin Ya Halatta Limamin Sallar Tarawihi Ya Dunga Sallar Tare Da Alƙur’ani A Hannunsa Domin Dubawa?

    Shin Ya Halatta Limamin Sallar Tarawihi Ya Dunga Sallar Tare Da Alƙur’ani A Hannunsa Domin Dubawa?

    Amsa: Ya halatta yayiwa mutane sallar tarawihi da Qur’ani a hannunsa da yake dubawa, bama sallar nafila ba, harma ta farilla.

    Domin karanta cikakken bayani akan Shin Idan Hakan Ya Halatta, Menene Sakamakon Kallon Takardar Alƙur’anin? danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Shin Shugaban Halitta Yana Karatun Alƙur’ani Na Musamman Cikin Watan Ramadan? danna nan.

    Danna link ɗinnan; https://chat.whatsapp.com/JtD82AjZZmo3AtSTaKP05r domin shiga WhatsApp group namu na Ramadan.

  • Mece Ce Matsayin Saukar Karatun Alƙur’ani Cikin Sallar Tarawihi, Shin Sahabbai Sun yi Hakan Ne?

    Mece Ce Matsayin Saukar Karatun Alƙur’ani Cikin Sallar Tarawihi, Shin Sahabbai Sun yi Hakan Ne?

    Amsa: Saukar Alƙur’ani cikin sallar tarawihi ya hallata, tare da cewa sahabbai ba su yi hakan ba.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Shin Ya Halatta Limamin Sallar Tarawihi Ya Dunga Sallar Tare Da Alƙur’ani A Hannunsa Domin Dubawa?

    Domin karanta cikakken bayani akan Akwai Bambanci Ne Da Tsakanin Tarawihi Da Sallar Tahajjud? danna nan.

    Danna link ɗinnan; https://chat.whatsapp.com/JtD82AjZZmo3AtSTaKP05r domin shiga WhatsApp group namu na Ramadan.

  • Mene Ne Haramcin Saukar Karatun Alƙur’ani Cikin Yini Guda?

    Mene Ne Haramcin Saukar Karatun Alƙur’ani Cikin Yini Guda?

    Amsa: Ya halatta mutum ya sauke Alƙur’ani cikin yini guda.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Mece Ce Matsayin Saukar Karatun Alƙur’ani Cikin Sallar Tarawihi, Shin Sahabbai Sun yi Hakan Ne? danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Akwai Bambanci Tsakanin Ƙiyamul Laili Ne Da Tarawihi Ko Asham? danna nan.

    Danna link ɗinnan; https://chat.whatsapp.com/JtD82AjZZmo3AtSTaKP05r domin shiga WhatsApp group namu na Ramadan.