Tag: ilimi

  • Alamomin Tashin Ƙiyama

    Alamomin Tashin Ƙiyama

    A jikina na ji kamar ƙarshen rayuwata ya zo dab da barin duniyar nan fa; domin na ga alamu sun nuna cewa, duniya ta zo ƙarshe, kamar yadda Manzo (SAW) ya faɗa.

    “Idan ƙarshen duniya ya zo, za ka ga alamu kamar haka:”

    1. Masu kuɗi za su zama marasa godiyar Allah.

    2. Ana gasar gina manyan gidaje.

    3. Baiwa za ta zama sarauniya.

    4. Zina za ta zama abin kwalliya ga al’ummah.

    5. Za a yawaita zubar da jinin salihan bayi.

    6. Azzaluman mutane za su zama shugabanni.

    7. Lokaci zai zama gajere, (Da zarar gari ya waye, sai ka ga dare ya yi).

    8. Za ka ga ɗan uwa yana gudun ɗan Uwansa.

    9. Addinin Musulunci zai kasu kashi-kashi.

    10. Malaman Addina za su zamo masu son duniya da abin da ke Cikinta.

    Innalillahi wa innah ilaihi raju’un…! Tabbass waɗannan

    alamomin sun bayyana dukkan su,

    ni yanzu tunanina yaushe zan mutu, yau ko gobe?

    Kashe ni za a yi, ko rashin lafiya zan yi, ko hatsarin mota zan yi, ko zan faɗa cikin rami in mutu? Ko gobara ce sanadina, ko kuma haka kawai zan mutu?
    Allahu A’alam.

    Allah ka sa mu yi kyakkyawan ƙarshe, Allah Ka sa mu mutu da kalmar shahada, Amin summa Amin!

    Idan na taɓa zaluntar ka/ki ina neman gafarar ka/ki kafin in koma ga Allah, domin na ji Allah ya ce, “Ba ya yafe laifin da ke tsakanin bawa da bawa.”

    Tunatarwa

    An kawo Facebook, ka iya,
    An kawo WhatsApp, ka iya,
    An kawo Instagram, ka iya,
    An kawo Twitter, Ka ƙware,
    ko wane irin Chatting, Ka iya.

    Shin ka ƙware wajen karanta Alƙur’ani da sanin Tajwidinsa?

    Kuma duk ya riga su jimawa a duniyar nan.
    Ɗan uwa haƙiƙa akwai babbar asara, idan ba ka iya karanta Ƙur’ani ba, ko daidai da hizif 1 ne.

    Manzon Allah (S.A.W) ya ce:- Azumi da Ƙur’ani suna ceto ranar Alƙiyama ga ma’abotan su.

    ‘Yan uwa, mu kasance ma’abota Ƙur’ani, ba ma’abota social media ba.

    Tunatarwa ce!

    Domin karanta cikakken bayani a kan Kalmomi Guda Biyar Masu Amfani A Duniya Da Lahira danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Abin Lura Idan ƊanKa Ko ‘YarKa Sun Kai Shekarun Farko Na Tashen Balaga danna nan.

  • Ciwon Suga (Diabetes)

    Ciwon Suga (Diabetes)

    Ciwon suga sinadari ne mai matuƙar amfani a jikin mutum. Ana samun sa daga abincin da muke ci da kuma abubuwan da muke sha.

    Idan suga ya yi yawa, ko kuma ya yi kaɗan a jikin mutum, ana iya kamuwa da rashin lafiya wadda za ta iya sanadiyar mutuwar mutum idan ba a ɗau mataki ba.

    Akwai wani sinadari da ake kira insulin a jikin ɗan Adam. Sinadarin insulin shi ne yake kula da daidaituwar sinadarin suga a cikin jini. Idan mutum ya ci abinci mai dauke da sinadarin suga (carbohydrate), sai sugan ya koma cikin jini bayan ya narke. 

    Sai sinadarin insulin ya zo ya daidaita suga, domin kada sugan ya cutar da jiki. 

    Ma’anar ciwon suga, cuta ce wadda take faruwa sanadiyyar ƙaruwar yawan sinadarin sikari (suga) a cikin jini na tsawon lokaci. Cutar tana faruwa ne idan jikin mutum ya daina samar da sinadarin insulin, ko kuma insuin ɗin ya daina aiki gaba ɗaya.

    Rabe-raben Ciwon Suga

    Rabe-raben ciwon suga suna da yawa, amma za mu yi magana a kan guda uka kawai:

    1. Type I Diabetes

    Wannan nau’in ciwon sugan, yana faruwa ne idan jikin mutum ya daina samar da sinadarin insulin.

    Idan sugan  mai wannan nau’in ciwon sugan ya ƙaru, ba zai sauka ba, saboda babu insulin. Idan kuwa ana so ya sauka, to dole sai an yi allurar insulin.

    Wannan nau’in  ya fi kama yara. Haƙiƙanin abin da yake janyo wannin  nau’in ciwon ba a san shi ba, amma dai an tabbatar da cewa ana iya gadon ciwon daga wurin mahaifa(iyaye)

    2. Type 2 Diabetes

    Wannan nau’in yana farawa ne idan sinadain insulin ya daina aiki, ko kuma aikinsa ya ragu. Idan sugan mai wannan nau’in ya ƙara, ba zai sauka ba, har sai an sha maganin da zai dawo da aikin insulin.

    Wannan nau’in ya fi kama manya.

    Abubawan da suke janyo haɗarin kamuwa da wannan nau’in sun haɗa da:

    Ƙiba: Ƙiba mara misali, musamman wadda ta haura ma’aunin Body Mass Index (BMI) 3okg/M2.

    Rashin kazar-kazar: Waɗanda ko yaushe a zaune suke, ba sa kai-kawo, ba sa aiki kuma ba sa son aiki.

    Cin abincin da ba shi da inganci a likitance: Yawan cin abinci, musamman wanda yake ɗauke da sinadaran cholesterol, suga, fat masu yawa a cikin su. Misali butter, chees, lemukan roba da na gwangwani, Askirin (lce cream) da sauransu.

    Shan giya

    Gado: Idan mahaifi ko mahaifiya suna da ciwon suga.

    3. Gestational Diabetes

    Wannan nau’in ciwon suga yana faruwa ne ga masu juna biyu (ciki).

    Yanayin su ɗaya da Type 2 Dm. Sai dai ana warkewa daga wannan nau’in bayan an haihu. Ana iya ba su magani su sha, ko kuma a yi musu allurar insulin idan ana so suga ya daidaita.

    Alamomin ciwon suga

    i. Yawan fitsari  fiye da misali.

    ii. Yawan shan ruwa fiye da misali.

    iii. Yawan cin abinci fiye da misali.

    Illolin ciwon suga

    Masu gajeren zango: Su ne waɗanda suke faruwa a ɗan ƙanƙanin lokaci, kuma suna iya sanadiyyar mutuwar mutum nan take. Sun haɗa da:

    a. Suga ya yi yawa sosai a jinin mutum, yawan da ya wuce hankali; irin wannan matsalar tana janyo mutum ya yanke jiki ya faɗi ko kuma mutum ya rasa ransa a nan take.

    b. Suga ya yi ƙasa; wannan idan mutum yana shan maganin suga ko allurar cutar suga (insulin) fiye da yadda jikinsa yake buƙata; yana iya janyowa mutum ya yanke jiki ya faɗi ko kuma ya fita daga hayyacinsa.

    Masu dogon zango: Su ne waɗanda suke faruwa bayan mutum ya daɗe da ciwon suga a jikinsa.

    Misali:

    Ciwon ƙoda.

    Ciwo ko kuma gyambon ƙafa, wanda zai iya janyowa a yankewa mutum ƙafa.

    Ciwon ido wanda zai iya janyowa mutum ya makance.

    Ciwon zuciya.

    Cutar shanyewa ɓarin jiki

    Da sauransa.

    Magani/Shawarwari

    Magungunan ciwon suga, kala biyu ne. Akwai na ƙwaya da kuma allura.

    Idan mutum yana da ciwon suga, yana da matuƙar muhimmanci ya dinga yin waɗannan ababuwan:

    Shan magani ko yin allura a kan ƙa’ida.

    Yawan duba sinadarin suga akai-akai.

    Yawan motsa jiki a ƙalla san huɗu a sati kamar tafiyar ƙasa ta tsawon minti talatin.

    Daina shan giya

    Rage shan kayan zaƙi masamman lemukan gwangwani ko na roba.

    Rage cika ciki da abinci mai sinadain sikar (carbohydrate) a ciki kamar shinkafa, tuwo, masara, doya da sauransu.

    Yawaita cin ganyayyaki kamar su alayyahu, zogale, rama, ganyan salak da sauransu.

    Kammalawa

    Ciwon suga ciwon ne mai haɗarin gaske. Har yanza babu maganin da yake warkar da ciwon gaba ɗaya.

    Amma ana iya shan magani ko ayi allura domin a zauna lafiya. Don haka shan magani da zuwa asibiti ya zama wajibi ga duk mai cutar.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Mene Ne Hawan Jini (HYPER TENSION) danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Mene Ne Ciwon Sikila (SICKLE CELL DISEASE) danna nan.

  • Abin Lura Idan ‘Ɗan Ka Ko ‘Yar Ka Sun Kai Shekarun Farko Na Tashen Balaga

    Abin Lura Idan ‘Ɗan Ka Ko ‘Yar Ka Sun Kai Shekarun Farko Na Tashen Balaga

    Idan ‘ɗan ka ko ‘yar ka sun kai shekarun farko na tashen balaga, to ka lura da waɗannan:

    1. Duk lokacin da yaro ko yarinya suka kai matakin tashen balaga wato “early adolescence”, musamman daga shekara 11, 12 zuwa 13… 18… To wannan shi ne lokaci mafi hatsari ga yara da iyayensu.

    2. A lokacin ne yaro yake samun zama na gari ko na banza, me amfanar da al’umma ko me cutar da su.

    3. Yaro ya fi tasirantuwa da abokan sa ko kawayen ta fiye da malaman sa ko mahaifan sa.

    4. Yaro yana jin shima daidai yake da kowa a duniya, kuma zai iya yin komai kamar yadda kowa yake yi, haka ita ma yarinyar.

    5. A lokacin ne yaro yake neman ‘yanci daga ikon mahaifan sa a kan sa. Yana son ɗakin sa daban, wajen kwanciyar sa daban, abinci, kayan sakawa da aski sai wanda ran sa yake so.

    6. A lokacin ne yake jin karfin sa ya kawo, kuma zai iya ja da kowa.

    7. A lokacin yaro komai yana yin sa ne gaga-gaga, ba kan gado babu nutsuwa, kuma ba wanda ya isa ya hana shi (a tinaninsa), idan kuma iyaye ba su bi hanyar da ta dace ba, to za su sha wahala da shi/ita.

    Mafita:

    1. Iyaye su ja yaron su a jiki, kuma su yi amfani da hikima wajen yi masa gyara da tarbiyyar sa.

    2. Kar su nuna masa ƙarfi ko iko, domin zai iya bauɗare musu, a ƙarshe ya haifar musu da hawan jini.

    3. A kula sosai da su waye abokan sa, ko ƙawayen ta. A haɗa shi da na gari, a raba shi da na banza.

    4. A samar masa da aikin yi, wajen nuna masa yadda zai dogara da kan sa (koda kuwa dan masu kuɗi ne shi).

    5. A tsara masa ayyukan da zai ke yi a kullun tun daga safe zuwa rana, i.e. makaranta, barci, cin abinci, ziyara, hutu, da sauran su.

    6. Iyaye su zama abokan ‘yayan su wajen bincikar matsalolin ‘yayan, da magance musu ita.

    7. Kada a hana yaro wani abu, face sai an maye masa gurbin sa da wani, idan ba haka ba, to zai yi wanda aka hana shi muni.

    8. Kar ayi amfani da karfi, da duka, da tsattsauran hukunci wajen ladabtar da shi; har sai idan abu ya ta’azzara, sai a je da shi guidance and counseling domin neman shawarwari.

    9. A rinka tunatar da su ayoyin Alƙur’ani da Hadisan Manzo S.A.W da sukai magana akan biyayyar iyaye.

    10. Sannan a rinƙa haɗawa da Addu’ar nema musu shiriya da nagarta a wajen ALLAH (SWT)
    Wallaahu A’alam.

    ALLAH Ka shiryar da mu da su a kan hanyar Ka Madaidaiciya……

    Domin karanta cikakken bayani akan Haƙƙoƙin Ƙananan Yara A Musulunci danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Addu’ar Nema Wa Yara Samun Karatu Da Raba Su Da Abokanan Banza danna nan.

  • Tarihin Dutsen Dala Da Rayuwa A Kewayensa

    Tarihin Dutsen Dala Da Rayuwa A Kewayensa

    Dala

    An fara ambatar Kano da sunan Jihar Kano daga lokacin da sojoji suka karɓi mulkin ƙasar nan, kuma suka yayyanka ƙasar zuwa jihohi, kafin wannan lokaci, cewa ake da ita lardin Kano, ko kuma a ce Kano da maƙwabtanta.

    Shi wannan birnin na Kano, ya kafu ne tun lokacin da ba a sani ba, wanda hakan yasa aka samu mabambantan ra’ayoyi dangane da lokacin da Kano ta kafu, wasu suna cewa, “Kano ta kafu ne tun lokacin da ba a sani ba”. Yayin da wasu suke cewa, “Ta kafu ne tun lokacin jahiliya, kafin zuwan Musulunci”. Wasu ɓangaren suna cewa, “Ta kafu ne tun shekara ta 208 A.H (bayan Hijira), wasu sun ce a shekara ta 303 A.H. ko shekara ta 444 A.H. ko kuwa 906 A.D.

    Kamar yadda aka yi saɓani a kan mazaunan ta na farko, inda wasu suka ce mutanen Gaya ne, waɗanda suke zuwa daga alkaryar Gaya, don ɗibar tama; a yayin da damuna ta sauka, sai suka zauna daga yammacin Dala; da wasu manyan rahoniyoyinsu masu kama da tsawon mutum, suna dafa tama a ciki bayan sun yi tsafe-tsafensu, idan ta haɗu, sai su yi ƙarfe da ita, ƙarfen shi ne suke ƙera kayen noma da yaƙi da kuma farauta, sai su bayar a musanya musu, a ba su abinci da sauran kayan buƙatu, waɗannan makera har yanzu akwai zuriyarsu suna yin ƙira.

    Kuma, wasu ko sun ce ‘yan farauta ne, waɗanda suka haɗu da mutunen da suka tarar, suka yi ‘yar alkarya ƙarama, waɗannan su ne iyalan ƙasaitaccen mutumin nan da ake kira da ‘Dala’, wanda Dutsen Dala ya samo sunansa daga gare shi, don ya zauna a kan saman ‘Dala’ shi da iyalansa.

    Bayan da Kanoki ya dawo Dala ya zauna, sai kasuwa ta buɗe masa. Mutane daga ko’ina suka riƙa zuwa wajensa, suna sayen kayan noma da na farauta da na aikin gidaje.

    Wannan kasuwa sai ta jawo masa ƙabilu iri daban-daban, waɗanda suka yiwo ƙaura, suka zo wajensa don su zauna tare da shi. To da yake kowace ƙabila takan zo da abin da Allah ya hore mata na sana’a, sai  masana’antu suka tashi a gurin. Masakar tufafi da marina da majema duk suka yawaita.

    Wannan ƙaramin buɗi na arzikin ƙasa, shi ne ya kawo kafa birnin Kano a gindin Dala, wanda ya ƙunshi dangin ƙabilu sha ɗaya. Kuma kowace ƙabila tana da sana’ar da ta kware a kai. Saboda sunan wannan makeri Kanoki da ya farazama a gurin ake kiran gurin Kano, kuma ƙabilarsa aka dinga kiranta Abagayawa.

    Wannan ƙaramin juyi, ana zaton ya faru ne a tsakanin ƙarni na 5-6 daga haihuwar Annabi Isa (A.S) kuma su waɗannan ƙabilu guda goma sha ɗaya da suka kafa wannan birni a gindin Dala, za ka karanta su a nan gaba kaɗan, kamar yadda tarihin Kano ya ambace su.

    Wani abin sha’awa cikin rayuwar waɗannan ƙabilu   shi   ne,  zaman   lafiya   da   haɗin kai na taimakon   juna.   Tun da dabarar yin sarki, a matsayin shugaban kowa da kowa, ba ta zo ba, to limamin addininsu shi ne shugabansu. A lokacin ruwan Jakara suke bautawa kuma Mazauda shi ne limanin bautar  Jakara,  saboda haka, ya zama shugaba.

    To cikin waɗannan mutane ne, Dala ya zo ya zauna tare da su a kan dutsen Dala. An ce Dala ya zo wannan wuri tare da ‘ya’yansa guda bakwai, huɗu maza uku mata. Sunan babban su Gargaji, shi ne kakan Buzami uban   Barbushe, kuma Barbushe shi ne ya gaje shi daga baya.

    Daga Ina Dala Ya Zo?

    Malaman tarihin Kano irin su Alkali Zangi Waziri Abubakar ba su yi nishaɗi mai yawa ba, tare da labarin Dala da iyalinsa, balle a san daga ina ya zo, kuma shi wane ne kafin ya zo ɗin. Idan ban da  littafin  Tarihin  Kano  na  Muhammadu Bello (Sarkin Kano  1883-1892) ba wanda ya faɗi labarin Dala. Ko shi ma wannan littafin, bai faɗi wani abu mai tsawo ba a kan zuwan Dala nan ƙasar . Abin da littafin kawai ya faɗa shi ne:

    “Shi Dala mutum ne baƙi kuma ƙaƙƙarfa, kuma mafarauci kwarai. Domin shi yakan kashe giwa da sandarsa, ya dauko ta a kansa, ya yi tafiya da ita kamar mil tara. Ya zo garin nan ba a san asalinsa ba. Da ya zo ya gina gidansa a Dutsen Dala, ya zauna a kanta shi kaɗai tare da matansa da ‘ya’yansa bakwai, huɗu maza, uku mata. Sunan babbansu Gargaji, shi ne kakan Buzami uban Barbushe. Barbushe ne ya gaji halayen Dala daga sanin dukkan dangogin tsafi da al’ajubansa da sihirinsa da rinjaye ga ‘yan uwansa, domin haka, ya zama shugabansu!”

    To wannan abin da aka kawo maka cikin littafin Tarihin Kano game da Dala, shi ne kawai abin da za ka ji game da shi, ba daɗi ba ragi, Wannan kuwa ɗan bayani na Dala, ba zai ƙosar da duk wani almajirin Tarihin Kano ba. Kuma tun da yake babu   littattafai a ƙasar  Hausa a  yanzu, waɗanda za su taimake mu, su ba mu haske don mu san daga ina Dala ya fito, kuma da inda ya koyi sihirinsa da dabarar sarrafa su, don neman mu san daga inda ya fito.

    To dole ne mu yi namu ƙoƙarin, Idan ka yi tsokaci mai nisa cikin abin nan da littafin Tarihin Kano ya faɗa game da Dala, za ka ga shi wannan mutum, ya zo da abubuwa uku waɗanda ba a san su a nan ƙasar ba, kafin zuwansa, kuma su waɗannan abubuwa da ya zo da su, su suka sa ya sami shugabancin matsafan wannan guri, har ya bar wa jikansa Barbushe wannan shugabanci.

    Su waɗannan sababbin abubuwan dai da Dala ya kawo su ne:

    1. Dabarun gina wa gunki ɗaki na musamman, da sa masa ranar bauta, da sallar idi biyu; ƙaramar salla da babbar salla, kamar yadda ake bauta a Ka’aba a ƙasar Larabawa a zamanin jahiliyya.
    2. Dabarar sihirce-sihirce da tsafe-tsafe wanda ta burge mazauna wannan wuri, har suka yi wa Dala mubaya’a suka bi jikansa Barbushe da gunkinsa Tsumburbura bi na haƙiƙa.
    3. Dabarar sarrafa giwa wadda ta nuna cewa dama can kafin Dala ya zo nan kasar, ya san giwa da yadda ake sarrafa ta. Tun da yake waɗannan abubuwa da muka lissafa haka suke ga Dala, to shi Dalan daga ina ya fito? Kuma a ina ya sami sanin waɗannan dabaru nasa da aka ambata a sama?

    Shehu Nasiru Kabara ya gaya min cewa, Dala ya zo ne daga tsibirin Dahlak na Rasar Habasha. Wannan tsibiri a bakin kogin Maliya yake, kuma a yanzu yana cikin Kasar Eritrea ne. To ka ga ashe Dala ya fito ne daga cikin ƙasashen gabas, waɗanda suka sami ci gaba wajen ilmin sihiri da tsafi da bautar gumaka da farauta irin ta wancan lokaci fiye da na mazaunan Kano na farko.

    Don haka suka bi shi dole, ba don ra’ayi ba.

    Amma a nazarin da Lugard  ya yi a kan tarihin Hausawa a cikin littafinsa mai suna Tropical Dependence ya ce, “Masu irin wannan addini na gunkin tsumburbura watakila Kibdawan Misira ne na ƙabilar Phonecian, wato Banu Kan’ana kamar yadda aka san su a ƙasar Hausa. Sabooda haka, Dala da jikansa Barbushe ana zaton kibɗawan Misira ne suka yiwo ƙaura daga tsibirin Dahlak na kogin Baharul Maliya, wanda a wannan lokacin a ƙarƙashin mulkin Fir’aun bin Inf yake. Da suka zo nan, suka mallake mutanen wannan   ƙasa na   farko;   ƙabilun  Kwararrafa saboda ci gabansu da ƙwarewarsu wajen tsafi da farautar giwa.

    Zuwan Dala Da Aikin Hajji A Kano

    Zuwan Dala wannan garin tare da iyalinsa da sauran jama’a da ya zo da su, ya kawo ci gaban mazauna wannan wuri na asali. Da farko dai, an samu auratayya tsakanin iyalinsa da mutanen wannan guri, wanda daga ƙarshe ta haɗe mutanen, har aka san su da ƙabilar Dala. Na biyu kuma Dala ya zo da sabuwar bautar gunki irin wadda ake yi a Makka ta su Lata da Uzza kafin Musulunci ya bayyana”.

    Haka kuma, shi ne ya fara gina wa gunki ɗakin bauta mai kusurwa guda huɗu wanda ba mai shiga sai shi kaɗai, ya kirawo wannan gunki nasa Tsumburbura, (watakila wannan ya yi  kama da Kulaista Abraha Sarkin Yaman).

    Bayan wannan, Dala ya sa wa wannan gunki nasa bikin idi a kowacce shekara wanda ake yi a daidai da lokacin da ake hawan Arfa da Babbar salla a Makka. Waɗannan sababbin  abubuwa  sun  bai  wa  Dala ƙarfin ɗaukaka   daga   mabiyansa   na   ko’ina   na ƙasar Kano. Wannan ɗaukaka ta Dala, ita ce ta haɓaka, har ta zama gadon gargajiya da ɗan jikansa, Barbushe ya gaji duk sihirinsa da tsafinsa, bayan shi ya mutu.

    Game kuma da irin addinin da Dala ya zo da shi wanda ya sha bamban da bautar Jakara, ga abin da Malam Adamu naMa’aji ya fada a kai:

    “Ana yin  bikin  Idi sau  ɗaya  a shekara, a (Dala), daidai da lokacin da ake yin Sallar Id-el- Adha a watan Zul Hajj a Makka. A ranar sallar Idi Barbushe, wanda shi ne babban Limami, shi yake jan duk mahajjata zuwa ɗakin gunkinsu, yana rike da baƙin bunsuru na layya. Idan an yanka wannan bunsuru, sai a zuba jininsa a cikin wata gidauniya, wadda aka ajiye a gaban gunkin.

    To, a nan ne Barbushe zai saurari abin da gidauniyar za ta yi. Idan jinin ya yi sanyi a cikin gidauniyar to, alama ce ta komai zai daidaita a sami zaman lafiya da arziki a wannan shekara. Idan kuma jinin ya yi zafi to alama ce ta abin da zai faru a wannan shekara na dangin masifu. Yawan zafin jinin yawan abin da zai faru kenan ko, yaƙi ko annoba ko yunwa. Daga nan sai Barbushe ya shaida wa maƙarrabansa abin da ya gani na masifar da za ta afku, da kuma lokacin da za ta afku din.

    Sannan kuma sai ya ba da umarnin kowane mahajjaci ya yi layya da abin da ya zo da shi don a roki gumaka su kare masifar da za ta zo, ko su rage ta, ta yi wa mutane sauƙi yadda za su iya jure ta”. Wani abin sha’awa a nan shi ne, irin wannan bauta da ake yi a Kano, ita Larabawa suke yi wa Lata da Uzza a Ka’aba a Makka, kafin bayyanar addinin Musulunci.

    A cikin littafinsa mai suna Nuril Yakeen Fi Sirat Sayyadil-Mursalin, Sheikh Muhammad al-Hadhari ya bayyana irin gidauniyar da ake zuba jinin bautar gunki a Makka ta waccan lokacin, ya ce sunan gidauniyar “al-Nasab”, kuma dutse ne aka fafe shi ya zama gurin zuba jinin bauta. Koda yake a nan Malam Adamu na Ma’aji, bai faɗi sunan gidauniyar tsafi ta Barbushe ba, bai kuma faɗi siffarta ba, wataƙila gidauniyar tsafin Barbushe ta ƙarfe ce, wadda mutanen Kano suka ƙera masa, don irin wannan ibada ta gumaka.

    Wannan siffar bautar gunkin Tsumburbura da Malam Adamu na Ma’aji ya bayyana, ta yi daidai da abin da littafin Tarihin Kano ya bayyana game da Idin da ake yi a Dala a wancan lokaci, kuma ga abin da littafin ya ce: Ya fara da nahiyoyin da ake tahowa Dala domin bikin Idi biyu; sallah karama da Sallah babba.“Tun daga Tudu zuwa Danbakoshi, daga Duji zuwa Dankwai, dukkansu suna taruwa wurin Barbushe daren sallah biyu, domin shi ne babbansu cikin tsafi.

    Sunan wurin da gunkinsa yake “Kakuwa”, sunansa kuwa “Tsumburbura domin itaciya ce da ake ambaton ta “Shamus”, sunan mutumin da yake a zaune a karkashinta dare da rana “Mai Tsumburbura”. An kewaye itaciyar da gini, babu mai shiga cikin ginin sai Barbushe, dukkan wanda ya shiga sai ya mutu nan da nan.

    Barbushe kuma ba ya saukowa daga dutsen Dala sai idan ranakun Idi biyu sun kusato. Sa’an nan mutane su zo masa daga gabas da yamma, kudu da arewa, maza da mata. Daga cikinsu wadansu su zo da bakin kare, wadansu da bakar kaza, wadansu da bakiin bunsuru“.

    Wannan ita ce siffar gunkin Barbushe da masu bauta masa da kuma lokacin da suke yin wannan bauta, wato Salla babba da Salla ƙarama ko Kuma mu ce Hajji da Umra, kamar yadda ake yin su a Makka ta lokacin Jahiliyya.

    Ban da wannan kuma ga yadda suke yin hawan arfa  da Ɗawafi i na jahiliyya, bayan su kuma su yi layya “Idan sun taru a ƙarƙashin dutsen Dala ranar jajibri (ranar Arfa) bayan la’asar, sa’an nan Barbushe ya fito daga gidansa da Isha tare da makaɗansa (na Kuru da Gunduwa da Tsintsima). Ya riƙa kururuwa da ƙarfi yana cewa; “Babban Jimina akasa mun gama karaga ga laya Tsumburbura”.

    Mutane kuma su ce, ga Tsumbirbirar Kanawa, ga wajen Dala”. Bayan wannan ya sauko su tafi tare da shi zuwa wurin gunki. Da isa wurin gunkin, kowa ya yanka abin da ya zo da shi, sannan Barbushe ya shiga cikin ginin shi kaɗai yana cewa, Magajin Dala, da kun ƙi da kun so ku bi, ni ba ra’ayi ba‘. Su kuma su ce,

    “Maigida bisa kan dutse, ubangijin Mama, bi mun bi ka, ba a ra ‘ayi ba”. Suna faɗar wannan suna kewaye ginin (suna dawafi) har hudowar alfijir, sa ‘an nan su tsaya tsirara su ci abinci.

    Ya fito, ya ba su labarin dukkan abin da zai faru cikin dukkan wannan shekara, har da bakon da zai fuskanto zuwa wannan gari, ko na alheri ne ko na sharri ne. Shi ne ma ya ba su labarin gushewar mulkinsu da sarewar itaciyarsu da Konewarta da ginin wannan masallaci.

    Kuma ya ce musu wani mutum zai zo wannan gari tare da rundunarsa, ya mallake mu”. Suka ce masa “don me ka fadi wannan? Wannan magana ce mummuna, ya yi shiru. Sa’an nan ya ce da sannu ku gan shi da alfarmar Tsumbirbura! Idan bai zo a zamaninku ba, ya zo a zamanin ‘ya’yanku, ya mallaki dukkan wanda ya samu a cikin wannan ƙasa dukkanta, ya sa a manta da ku duk da jama’arku, ya kuma bayyana da ƙabilar tasa zamani mai tsawo.”

    Wannan duba na Barbushe bai yi wa mabiyansa daɗi ba, don haka suka yi bakin ciki kwarai suka ce masa, “Yaya za mu yi mu kawar da wannan al’amari? Ya ba su amsa da cewa ba yadda za ku yi, sai hakuri. Watakila Barbushe ya hango wani gagarumin juyi, wanda ƙabilar Madatai za ta zo da shi wanda zai haɗiye ƙabila tasa da sannu, shi ya sa ya yi wannan duba cikin tsafinsa, ya ga abin da ya gani na wannan juyi, ya gaya wa mabiyansa.

    Kogin Jakara

    Koda yake waɗannan ƙabilu ba lokaci ɗaya suka zo Kano ba, kuma ba gaba ɗaya suka zo ba, a’a kaɗan-kaɗan suka dinga zuwa, har suka taru suka yi ƙungiya iri biyu, kungiyar Dala ta masu bautar gunki, wato Tsumburbura da kungiyar ‘Yan farauta. Lokacin da wadannan kungiyoyi suke zaune a Kano suna zaune kusa da juna, amma kogin Jakara da manya-manyan itatuwan da suke kewaye da kogin su ne suka raba su, ƙabilar Dala tana arewa da ita, ƙabilar Madatai tana kudu da ita.

    Ita dai Jakara wata ƙorama ce wadda ta faro daga wani guri, yammacin birni, wanda ake kira Bulbula, a Aisami, gabas da Gwauron Dutse. Ta keta ta Dausayi ta Karofin Wanka-da-Shuni, ta cikin Kasuwar kurmi, ta yi gabas har ta je Wasai ta garin Minjibir, ta miƙe da tafiya har ta kai Duku, ta ƙasar Garkin Dirani, inda ta ƙare , ba ta sake tafiya ko’ina ba.

    Wannan ƙorama da duhuwarta, su ne suka raba waɗannan ƙabilu gudu biyu, kamar yadda muka faɗa a baya. To su waɗannan ƙabilu tun zuwan su, sun tarar da mazauna wannan guri na asali, suka zauna tare da su, suka koya musu irin sababbin dabarun zaman duniya da suka zo da su inda suka yiwo ƙaura, waɗanda mazauna wannan guri na asali ba su san su ba.

    Kafin Dala, kakan Barbushe ubangijin Tsumburbura, ya zo wannan gari, akwai mutane da suke zaune a nan suna rayuwa irin tasu.

    Mutanen da suke zaune a wannan guri, kafin zuwan Dala Kabilu ne iri daban-daban, kuma suna zaune ne zama irin na rinji. Zaman rinji shi ne zaman da kowane maigida yake zaune da ƙungiyarsa, a waje ɗaya, wadda ta haɗa gidansa da gidan ‘ya’yansa da na ƙannensa da kuma na barorinsa, ko kuma na waɗansu mutane daban da suka kawo caffa gurinsa don ya riƙe su, kamar ‘ya’yansa.

    Kowane rinji akwai sana’ar da aka san shi da ita, kuma mutanen da suke zaune cikin rinjin an san iyakar wuraren da suka mallaka don noma da waɗansu ayyuka na sana’a.

    Kamar yadda littafin Tarihin Kano ya fada, wasu daga cikin mutanen da Dala ya samu a nan, suna zaune ne kusa da kan Dutsen Dala, inda shi kansa ya hau ya gina nasa gidan. Waɗannan mutane kamar yadda Tarihin Kano ya bayyana, su ne: Gunzago mai gida a ƙarƙashin Goron-Dutse a Ga-giwa, wanda yake kama giwa da igiya don ƙarfinsa da Gubanasu da Ibrahim da Bardoje da Nisau da Kamfatsu da  Duje da Janberi da Gamakora da Gaftaro da Hangugu da Kar-dangi.

    Waɗannan mutane su ne littafin Tarihin Kano ya bayyana su da cewa su ne muƙarraban Barbushe, jikan Dala. Wataƙila ma auratayya ce ta haɗa kakanninsu da ƙabilar Dala; wadda ya zo da ita, har wannan dangantaka ta shiga tsakaninsu.

    Har ila yau; akwai wasu Rinjinan (Rijau) da shugabanninsu suka yi caffa ga Dala da gunkinsa; koda yake su ma zaman kansu suke yi, kuma nesa da Dala suke. Waɗannan kabilu su ne:
    1. Ƙabilar Danburu wanda yake zauna a Jigirya, wajen mil goma gabas da Dala.
    2. Ƙabilar Jandamisa wanda ake kira Ruma. Shi kuwa a kan Dutsen Magwam yake, wato Nassarawa ta yanzu; kuma ƙabilar wannan mutum wato Rumawa sun fi kowace ƙabila yawa a Kano a wancan lokacin. Domin su ne suka yaɗu tun daga inda suke, har zuwa Salanta wato kudu da Dala kamar mil goma.
    3. Ƙabilar Hambarau waɗanda suke zaune a kan Dutsen Tanagar.
    4. Ƙabilar Nisau wadanda suka zauna a kan Dutsen Fanisau. Shi Nisau shi ne uban Gumban ɗaya daga cikin manyan da suke bin Tsumburbura da Barbushe.

    Domin karanta cikakken bayani akan Taƙaitaccen Tarihin Kano Kashi Na Ɗaya(1) danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Taƙaitaccen Tarihin Ƙasar Hausa danna nan.

  • Kaffarar Azumin Ramadan

    Kaffarar Azumin Ramadan

    Game da kaffara kuwa; ya gabata cikin hadisin Abu Hurairah (Radiyallahu Anhu); inda wani mutum ya sadu da iyalinsa da tsakar rana a watan azumin Ramadan; kuma aka ce akwai ramuwar kaffara a kan sa, wato ‘yanta wuyaye, idan bai samu dama ba; to azumin watanni biyu a jere; idan kuma ba zai iya ba; to ya ciyar da miskinai sittin.

    An ce, kaffarar jima’i a kan zaɓi ake yi ba a tartibi (jere) ba; sai dai waɗanda suka rawaito tartibin sun fi yawa. Saboda haka ruwayarsu ta fi rinjaye saboda sun fi yawa, kuma suna da ƙarin masaniya (ilimi) sama da ragowar; inda suka yi ittifaƙi kan cewa azumin wanda ya yi jima’i ya warware; wanda hakan ba ta samu ba cikin ragowar ruwayar, kuma wanda ya sani hujja ne a kan wanda bai sani ba; kuma daga cikin abin da ke rinjayar da tartwikiibin cewa ya fi taka tsantsan kuma riƙo da shi ya isar; idan mun ce zaɓi ne ko ba zaƙi ba, saɓanin idan muka riƙi ragowar hadisan.

    Haka kuma wanda kaffara ta hau kansa, kuma ya kasa ‘yanta wuyaye ko yin azumi ko ciyarwa; to za ta sauƙa daga kansa, saboda ba a kallafa abu sai har idan za a iya. Allah Maɗaukakin Sarki ya ce:

    “Allah ba ya kallafawa rai abu face wanda za ta iya”. (Baqara: 286).

    Kuma ga dalilin aikin Ma’aiki (Sallallahu Alaihi Wasalam); wato inda Ya ɗauke kaffara kan mutumin nan yayin da ya gaya masa wahalar da yake ciki, har ma ya ba shi dabino akan ya je ya ciyar da iyalansa.

    Sannan kaffara ba ta hawa kan macen da mijinta ya neme ta; saboda Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) an ba shi labarin abin da ya faru tsakanin wannan mutumi da matarsa, amma bai wajabta mata kaffara ba, sai guda ɗaya (wato ramuwar azumin). Allahu a’alam.

    Domin karanta cikakken bayani akan Ramuwar Azumin Ramadan danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Raya Daren Lailatul ƙadari danna nan.

    Wannan bayanin anciro shine daga Littafin Guziri Ga Mai Azumin Ramadana (Bisa Koyarwar Alƙur’ani Da Sunnah); wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi; Don karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Yadda Al’ada (Jinin Haila) Yake

    Yadda Al’ada (Jinin Haila) Yake

    A wannan shafin za mu tattauna akan abubuwan da suka shafi al’adar ‘ya mace. Yadda zaki san in al’adarki daidai take ko kuma kina da matsala. Abubuwan da za kiyi amfani dasu idan kina al’ada kamar: Auduga (Pad) da tsumma da sauransu. Yadda zaki tsaftace jikinki da suturar ki idan kina al’ada.

    Mecece Al’ada?

    Ita al’ada jini ne ko kuma gudan jinni wanda yake fitowa daga mahaifa a jikin mace. Al’ada na zuwar wa mace duk wata. Aduk sanda kika ga irin wannan jinin to shi ake nufi da al’ada.

    Me Ake Nufi Da Lokacin Al’ada (Jinin Haila)

    Lokacin Al’ada lokaci ne da yake shiryawa jikin mace ɗaukar ciki duk wata. Lokacin al’ada na amfani da abubuwa guda biyu irin su estrogen da progesterone.

    Bayaninsu ya tafi kamar haka: A jikin mace akwai ƙwayaye guda biyu, kuma kowanne yana riƙe da ƙwayaye ba adadi a cikinsa, kwayayen ƙananu ne, wanda idanu baza su iya ganin sa ba, sai da taimakon na’urar gani. Lokacin al’ada, ƙwayayen suna girma, wanda hakan shi yake nufin cewa maniyi yake jira su haɗu, su haifar da ɗa.

    Bayan mace ta gama al’adar ta, akwai wani mataki da zata shiga, wanda ake kira da “Ovulation”. Da yawan mata basa sanin lokacin da sukeyin ovulating, saboda ba abu bane da mutum zai tayar da hankalin sa. Alamomin ovulation su ne; ciwo a ƙasan mara, wanda zaki ji a ɓari ɗaya ko duka biyun. A turance; bloating, spotting da sauransu.

    Lokutan Da Al’ada Take Farawa Da Kuma Tsayawa

    A wani lokacin girman ‘ya mace, wasu matan suna fara al’ada a shekara sha biyu zuwa sha huɗu. Amma wasu suna ganin nasu da wuri, tunda yanayin jiki ba ɗaya bane; kuma babu tabbacin ga lokacin da zaki ga al’adar. Amma idan baki ga al’adar kiba, har kika kai shekara goma sha shida (16), to ki tuntuɓi likita.

    Yawancin mutane suna daina ganin al’adarsu idan sun kai kimanin shekaru arba’in da biyar (45) ko hamsin da biyar (55), wanda aka fi sani da menopause (lokacin da mace zata daina al’ada). Al’adar mace tana farawa da tsayawa, kamar yadda ragowar mutane suke yi. Amma taƙaitaccen lokacin dainawa shi ne daga shekara arba’in da biyar zuwa hamsin da biyar.

    Abubuwan Da Mace Zata Iya Amfani Dasu Idan Tana Al’ada

    Mace idan tana Al’ada zata iya amfani da su audugar mata da tissue da tsumma da sauransu. Su waɗannan da aka lissafo, suna da inganci a rayuwar mace. Su suke taimakawa wajen tsafta da kuma hana jinin ya ɓata jikin ki.

    1. Audugar mata (Pad): Auduga ce mai fiffike guda biyu, wadda zaki yi amfani da ita wajen hana jinin ya ɓata jikinki. Ita ce mafi ingancin auduga da zaki iya amfani da ita, suna nan kala-kala kamar su: Lady Care da Virony da Always da Molped da 7-layer da sauransu.

    2. Tissue: Zaki iya amfani da wannan idan al’ada ta same ki a waje, ko kuma bakya ɗiga da yawa, amma ba ta ɗaya daga cikin audugar mata da take da kyan amfani. Ita amfanin ta yafi zuwa idan audugar ki ta ƙare, to sai ki yi amfani da shi.

    3. Tsumma: Shi ma amfanin su ɗaya da audugar mata, amma shi wannan zaki wanke shi ne duk sanda kika cire shi.

    Hanyoyin Da Zaki Bi Wajen Tsaftace Jikinki Idan Kina Al’ada

    Idan kina amfani da pad ne, to duk bayan awa shida (6) zuwa takwas (8) ki tabbata kin cire, kin saka wani, idan kuma kina zuba da yawa, to ki dunga cirewa da zarar kin ji ta jiƙe.

    Masu amfani da tsumma kuma, su dunga wankewa, basai sun jira ya jiƙe ba, don da zarar kin jira ya jiƙe, zai iya ɓata ki, kuma abinda ake gudu kenan.

    Tissue kuma bashi da tsayayyen lokaci, tunda shi kamar na agaji ne, zaki iya cire shi duk sanda kika so, ko kike buƙata, amma ki tabbatar bai jiƙe sosai ba.

    Zaki iya amfani da miski ko turare wanda zaki shafa a jikinki, don kashe ƙarni.

    Wanke hannu a duk lokacin da zaki canza, ko bayan kin canza na da matuƙar muhimmanci.

    Yadda Zaki Tsaftace Jikin ki Bayan Kin Gama Al’ada

    Wanke hannu da sabulu mai ƙamshi ko kuma wanka da su turaren wanka.

    Yin wankan tsarki

    Ki sa miski a auduga sai kisa a pant ɗinki da sauransu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Yin Wankan Tsarki Bayan Angama Al’ada danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Ciwon Mara Lokacin Al’ada danna nan.

    Don shiga WhatsApp Group ɗinmu na Tsaftar Mata, ku danna nan.

  • Wa ya Kamata In Bayyana Wa Sirrina Idan Na Fara Al’ada

    Wa ya Kamata In Bayyana Wa Sirrina Idan Na Fara Al’ada

    Da yawa mata idan sun fara al’ada, kunya suke ji su bayyana, wasu da dama ba sa iya faɗa wa iyayensu ko kuma wasu manya ko kuma makusanta.

    A wannan shafin namu, zamu bayyana yadda zaki cire kunya, ki faɗa wa iyayen ki; ko wasu manya da zasu baki shawara dangane da yadda zaki fuskanci matsalar.

    Ga kaɗan daga cikin irin tambayoyi da amsoshin su:

    1. Wa zan tunkara dangane da canjin da na fara fuskanta a jiki na?

    Yanayin da kike fuskanta dangane da canjin jikin ki ba abu bane mawuyaci. Idan kina da tambayoyi akan canjin jikin ki, ko yanayin al’adarki; yana da matuƙar muhimmanci ki fito ki bayyana wa mahaifiyyar ki ko yayyan ki ko malamai; kokuma wasu manya da kika sani, don su ɗora ki akan hanyar da ta fi dacewa da ke.

    Duk wacce kika gani ta wuce shekarun ki, to tabbas ta ɗanɗana irin abinda kike fuskanta a yanzu; kuma koda ace basu sani ba, zasu ɗora ki akan tafarkin da zaki fahimta, ko kuma suhaɗa ki da waɗanda suka sani.

    2. Ya zan yi idan na kasa tunkarar iyaye na?

    Jin kunya wajen tattauna maganar da ta danganci al’ada ga iyaye, ba abu bane maiwuya. Yawancin mutane sun fuskanci irin haka, kuma suna son ki; kuma suna son su taimake ki. Su kansu iyaye; zasu ji daɗi idan kika fuskance su da irin wannan maganar. A lokacin zasu ƙara baki kulawar da kike buƙata, su ƙara nusar dake me rayuwar ta ƙunsa.

    Wasu lokutan yana da muhimmanci ki tanadi tambayoyin da zaki yi musu, don ki samu amsoshin su a lokaci ɗaya.

    Gakaɗan daga cikin yadda zaki iya fara tattaunawar:

    • Zaki iya yin alama da ido, ko kuma zirga-zirga a gaban su, don su fuskanci kina da magana; daga nan su da kansu zasu tambaya, su ce, “LAFIYA”; a nan zaki matsa kusa dasu, sai ki fayyace musu abin da ke birnin zuciyarki baki ɗaya.
    • Idan kin san sun riga da sun sani; zaki iya zuwa gurin su, kice kina jin ba daɗi ne, shi ne kike son ki tattauna matsalar dasu ko akwai mafita.
    • Kiyi tunanin tambayoyin da kike son yi, ki rubata su a takarda, ki tabbata babu wasu-wasi a zuciyarki; sai ki basu takardar, su zasu neme ki.
    • Idan kuma baza ki iya yi wa iyaye magana ba, zaki iya samun yayar ki, ko kaka ko malaman islamiyya ko manya a jihar, ko kuma ki ziyarci asibiti.

    3. Ta yaya zan san lokacin da ya kamata na ziyarci asibiti?

    Lokuta da dama, yana da wuya a tattance in kina da lafiya ko akasin haka; ta yaya zaki san ya kamata ki tattauna da likita?

    Muhimmiyar hanya ita ce, ki fara tattaunawa da iyaye ko kuma yayyan ki ko manya da kika yarda dasu. Sun ɗanɗana dayawa daga cikin abubuwan da kike fuskanta yanzu, don haka, zasu baki shawarar da takamata.

    Idan baki da likita, zaki iya zuwa ɗaya daga cikin asibitocin da ke kusa da ke (ƙwararru), kuma karki manta asibiti basa son tambayoyi marasa ma’ana, don aikinsu shine; su taimaka wa al’umma.

    Babu wanda ya kai likita riƙe sirri, don haka, kar ki ji kunyar faɗa musu abubuwan da ke damunki, don su zasu taimaka miki sosai.

    Bin ƙa’idojina da matuƙar muhimmanci, don su za su taimaka wajen ƙara koyar da ke abubuwan da ya shafi jikinki.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Wankan Tsarki Bayan An Gama Al’ada (2) danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Jinin Haila (Jinin Al’ada) danna nan.

    Don shiga WhatsApp Group ɗinmu na Tsaftar Mata, ku danna nan.

  • Samar Da Tsangayun Gwaji Na Gwamnati

    Samar Da Tsangayun Gwaji Na Gwamnati

    Ya zama wajibi ga dukkan jihar dake son bunƙasa tsangayun Alƙur’ani da inganta rayuwar almajirai, bayan ta ba da dukkan kulawar da ta gabata, ta samar da tsangayar Gwamnati ta Musamman (Model Tsangaya).

    Wadda za ta zama misali ga sauran alarammomi, kuma ta cike giɓin da ke tsakanin tsangayu da sauran takwarorinsu ‘yan zamani ma’ana ‘yan boko.

    Ya kamata yanayin wannan tsagaya ta gwaji, kada ta fita daga irin yanayin Tsagayunmu na gargajiya, musamman tsarin karatu da hura wuta da amfani da alluna da sauran fuskokin karatun tsangaya.

    Abubuwan da gwamnati za ta samar sun haɗa da:

    1. Muhalli mai yalwa da ɗakunan kwanan almajirai, da wurin darasu da Masallaci da kuma banɗakuna.
    2. Gina gidan alaramma da na mataimakansa.
    3. Gina wurin koyan sana’o’i dabam-dabam.
    4. Samar da katafariyar gona kusa da tsangaya da shanun huɗa da amalanke da kaltibeta da kuma ɓangaren kiwon kaji ko dabbobi.
    5. Samar da ɗakin shan magani.
    6. Samar da ofishin babban jami’in gwamnati. (Officer in Charge/Director) daga Ma’aikatar Kula da Al’amuran Makarantun Alƙur’ani.

    Wannan ofishi, shi zai riƙa tattara bayanai da adana su, da kuma bibiyar halin da tsangaya ke ciki. Kuma shi ne mai alhakin bayar da shaidar karatu ga almajirin da ya kammala a hukumance.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Manhajar Tsangayar Gwaji danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Neman Laƙani Da Asiri Ya Shiga Tsangayu danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya, Tarihinsu Da Zamantakewarsu Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan

  • Yadda Ake Wankan Tsarki Bayan An Gama Al’ada (2)

    Yadda Ake Wankan Tsarki Bayan An Gama Al’ada (2)

    Shi yin wankan tsarki alama ce da take nuna cewa an gama al’ada, za ki fara sallah; wadda ya wajabta a kan ko wacce mace, idan ta gama ta yi shi.

    Ruwa me tsafta, mara kala, farin ruwa a buta.

    Ɗaukan niyya, za ki fara da cewa (Bismillahi rahmanirrahim, na yi niyyar yin wanka, haila domin tsarkake kaina)

    Sai ki wanke hannunki sau uku

    Za ki wanke abin da ya yi daga cibiya zuwa gwuiwar ƙafa, saboda duk wata ƙazanta a tsakankanin nan take; bayan kin kammala, sai ki sake wanke hannun ki sau uku.

    Za ki yi Bisimillah, sai ki yi yadda ake alwala, amma ba za ki wanke ƙafa ba.

    Bayan kin kammala alwala, sai ki ɗebo ruwa, ki wanke saman kanki zuwa wuya; (wanki ba me sabulu ba, kuma ba shafawa za ki yi ba, wankewa mai kyau sau uku).

    A wannan gaɓar, za ki raba jikinki gida biyu, wato dama da hagu.

    Sai ki fara da wanke ɓarin dama, daga kafaɗa gaba da baya, harda hannaye zuwa ƙafafu.

    Sai kizo ki wanke ɓarin hagu, daga kafaɗa gaba da baya, harda hannaye zuwa ƙafafu.

    Bayan kin kammala, sai ki zo ki wanke ƙafa (Ma’ana kin cika da alwala kenan).

    Ƙarin Haske:

    Alwalar da kika yi da farko, ba ki wanke ƙafa ba, to bayan da kin gama wanka kika zo kika wanke ƙafa daga ƙarshe, za ki iya sallah da alwalar da kika yi, tunda tsaftatacciya ce, amma ba ta cikin ƙa’ida, cewa sai daga baya za a dunga wanke ƙafa.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Fara Jinin Haila Da Bayanin Siffofinsa danna nan.

  • Yadda Ake Yin Wankan Tsarki Bayan An Gama Al’ada

    Yadda Ake Yin Wankan Tsarki Bayan An Gama Al’ada

    1. Za ta jiƙa tafikan hannayenta da ruwa, sai ta ɗan bubbuga tafikan hannayenta a kanta; sannan ta wanke daga cibiya zuwa gwuiwar ƙafafunta; sannan sai ta ɗebo ruwa cikin tafikan hannayenta biyu, ta wanke kanta, za ta maimaita hakan ne sau uku.

    Sai ta wanke gaɓoɓin alwala, kowanne sau ɗaya; sannan sai ta wanke saman jikinta, daga kafaɗarta zuwa cibiyarta ɓangaren dama. Sai ta maimaita hakan a ɓangaren hagu; sannan ta wanke ƙasan jikinta, daga gwuiwa zuwa idan sawu ɓangaren dama; sai ta maimaita hakan a ɓangaren hagu; sannan ta wanke ƙafafun ta dama da hagu sannan ta kwara ragowar ruwan a gaba ɗaya jikinta.

    Wannan shi ake kira (Sifatul Kamal) wato kalar wanka mai tsari.

    2. Za ta jiƙa tafikan hannayenta da ruwa, sai ta bubbuga tafikan hannayen nata a kanta, saboda kiyaye lafiyar jikinta; sannan ta buɗe shawa ko ta shiga cikin baho ko daro; ko kuma ta juye ruwan bokitin a jinkita, yadda za ta game ko’ina da ina na jikin nata da ruwa.

    Wannan shi ake kira (Sifatul Ijiza’i) wato kalar wankan da shi ma ya wadartar.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Hukunce-hukuncen Jinin Haila Da Na Biƙi danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Wankan Tsarki Bayan An Gama Al’ada (2) danna nan.