Tag: ilimi

  • Abin Da Ya Kamata Mai Yin Sallah Ya Yi Bayan Ya Tafi Sujudah

    Abin Da Ya Kamata Mai Yin Sallah Ya Yi Bayan Ya Tafi Sujudah

    Idan zai yi sujudah, ya tabbatar ya yi ne a kan gaɓoɓinsa guda 7.

    1-2 tafukan hannuwansa biyu, idan yana da su.
    3-4 guiwowin ƙafafunsa biyu, idan yana da su.
    5-6 wasu daga cikin yatsun digadigan ƙafafunsa biyu.
    7-tun daga goshinsa har zuwa hancinsa gaɓa ce guda ɗaya.

    Ba aso ya ware yatsun tafikan hannayensa ldan ya yi sujudah; kuma kar ya ajiye tsintsiyar hannuwansa biyu a ƙasa; kar ya boƙalo hannuwansa, kuma kar ya choge su a jikin haƙarƙarinsa.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Karatun Surah A cikin Sallah danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Sallar Kisfewar Rana Da Wata (Zazzaɓin Rana Da Wata) danna nan.

  • Yadda Ake Gyaran Gashi Da Sanya Shi Yayi Tsawo

    Yadda Ake Gyaran Gashi Da Sanya Shi Yayi Tsawo

    Gyaran Gashi Da Tsawo: Zaki samu shinkafa kowace iri ce rabin kofi; ki wanke ta sai ki zuba mata ruwa kofi biyu; sannan ki samu mazubi mai murfi ki rufe kibarshi har tsawon awa 24.

    Sai ki ɗauka ki riƙa murzawa kamar yadda kikeyi in zaki wanke, har tsawon minti goma. Sai ki tace ruwan kisamu costor oil kizuba ƙaramin cokali huɗu aciki sai ki ɗauka ki rinƙa shafawa akan ki.

    Ki tabbatar kin raba kan gida huɗu; sai ki shafa a kowanne bangare; sannan ki ɗaure ki barshi har zuwa safe ki wanke.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Gyaran Gashi danna nan.

  • Guraren Da Aljanu Sukafi Zama

    Guraren Da Aljanu Sukafi Zama

    A wajen zama mun bambanta, sai dai da yawan mu muna rushe musu wurin zamansu sannan mu gina namu, kuma muna sare musu wajen zamansu mu dasa namu.

    Aljanu sun fi zama a cikin daji, saman dutse, saman ɗaki, cikin bola, cikin garken raƙuma, jikin shuri da dai sauransu. Da yawa akwai hatsari da mutum ya ga an share fili a daji ya tsugunna ya yi fitsari ko kashi.

    Akasarin irin wajejen nan aljanu ne suka yi jinya suka warke suka tashi a wajen don haka sai a kiyaye. Akwai waɗanda suke mu’amalantar mu a cikin gida, waɗanda su suke zama a cikin gida kamar yadda muke zama, haka kuma wasu daga cikinsu a hanya muke gamuwa da su, su rako mu har gida. Shi yasa musulunci ya koyar da mu addu’ar da za mu yi in za mu shiga gida da in za mu fita. Ya kamata in za ka bar gida sai ka ce;

    “Bismillahi tawakkaltu alallahi wala haula wala ƙuwwata illa billah, allahumma inni a’uzhu bika an adilla aw udilla, aw azilla aw uzalla, au azlima aw uzlama, aw ajhala aw yujhala alayya”

    Sannan in za ka shiga gida sai ka ce;

    “Bismillahi walajna, wa bismillahi kharajna wa’alal lahi rabbana tawakkalna”

    Amfanin addu’ar nan shi ne ko da aljanu sun biyo ka gida idan ka karanata wannan addu’ar za su ga babu ƙofa a gidanka, ba wurin zama sai su koma. Idan kuma ka yi sakaci wurin karanta ta, to za ka ga ka shiga gida cikin damuwa, da ƙunan rai da tashin hankali da jin haushin mutanen gidan.

    Daga lokacin shi kenan sun sami abinda suke so, ka yi ta faɗa da mutanen gida. Shi yasa musulunci ya koyar da mu hatta abinci in za ka ci ka ce bismillah, Allah ba zai ba su ikon su sa hannu su ci ba. In kuma ka gama cin abincin sai ka karanta wannan addu’ar;

    “Allahumma barik lana fi hi wa ta’amna khairan minhu”

    Idan ka yi wannan addu’ar Allah zai ba ka lada sannan kuma ya sa wa abincin da za ka ci albarka.

    Hatta kaya idan za ka cire, musulunci ya koyar da mu addu’a da ya kamata ka yi don ka samu kariya daga sharrin aljanu da sheɗanu. Don haka in za ka cire kayanka ka ce “bismillah” Allah zai rufe idanun aljanu ba za su ga tsiraicinka ba.

    Haka ɗakin da ya dade a rufe hatsari ne a shiga ba tare da an yi addu’a ba. Ko da shimfiɗa ce aka gyara ta domin a kwanta, musulunci ya koyar da mu ka karkadɗeta sau uku sannan ka yi addu’a ka kwanta. Kuma mu kiyaye zama a kofar ɗaki don wannan ma wurin zamansu ne.

    Sai a kiyayi zubar da ruwan zafi a makwarara, saboda nan ma wajen zamansu ne. Kuma a kiyayi zama a cikin ɗaki mai duhu da kuma yin surutu a bayi da zama kai ba ɗankwali da jiki a bude. Sai mu raba kanmu da yawan kalle-kalle marasa amfani ko jin kade-kade.

    Sannan uwar gida ki tattare kayanki da zarar magariba ta doso kai, ki killace yaranki, ki hana su zama ba riga, sannan a rufe kwanukan da aka ci abinci har dai za a bar su a waje. Wannan duk musulunci ya koyar da mu ne don kulawa da kanmu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Kalolin Aljanu Suke danna koren rubutun nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Addu’ar Samun Lafiya Ga Kowane Irin Ciwo danna koren rubutun nan.

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Yadda Kalolin Aljanu Suke

    Yadda Kalolin Aljanu Suke

    Aljanu kala-kala ne kamar yadda muke nau’in mu kala-kala:

    Ga kalolin Aljanu kamar haka:

    • Jinnul gawas
    • Jinnul ɗayyar
    • Jinnul bait
    • Jinnul jalab wal tahdir
    • Jinnul majus
    • Jinnul yahudi
    • Jinnul nasari
    • Jinnul muslim
    • Jinnul ashiƙ
    • Jinnul kamil
    • Jinnul tabdil
    • Ifritu minal jinn

    Waɗannan su ne kaɗan daga cikin kalolin aljanu, kuma kowanne aljani akwai alamominsa sannan akwai irin nau’in magungunansa. Akwai jinnu da yake kama da mutane sannan akwai jinnu da ake tura shi ya shiga mutum.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Alamomin Jinnu Yake danna koren rubutu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Mutane Biyar Da Suka Yi kama Da Manzon Allah (S.A.W)

  • Yadda Nau’ikan Aljanu Suke

    Yadda Nau’ikan Aljanu Suke

    Kamar yadda muke da mata da maza, haka ma aljanu suke da mata da maza, yara da manya, tsoho da tsohuwa, sarakuna da talakawa, masu arziki da kuma matsiyata kuma musulmai da kafirai.

    Kamar yadda Allah (Subahanahu Wata’ala) ya faɗa acikin Al Ƙur’ani mai girma a cikin suratul jin;

    “Wa’anna minnas salihuna waminna du na zalika kunna ɗara’iƙa ƙidada”

    Domin karanta cikakken bayani akan Guraren Da Aljanu Sukafi Zama danna nan.

    Domin karanta bayani akan Addu’ar Da Ba ta Dawowa In An Yi Ta danna nan

  • Gudumawar Waƙoƙin Baka na Situdiyo Wajen Haɓaka Tattalin Arziki

    Gudumawar Waƙoƙin Baka na Situdiyo Wajen Haɓaka Tattalin Arziki

    Bayan fahimtar tattalin arziki da kuma bayyana matsayin waƙa a wurin Bahaushe; da yadda aka ga mawaƙan da kansu sun ɗauki waƙa a matsayin sana’arsu ta yau da gobe.

    A nan, za mu yi ƙoƙarin ganin irin rawar da waƙoƙin situdiyo suke takawa wajen haɓaka tattalin arziki da bunƙasa shi.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Litttafin Gudumawar Adabin Baka Wajen Haɓaka Tattalin Arziki; Keɓantaccen Nazari Kan Waƙar Baka Ta Situdiyo wanda Ibrahim Baba (Nayaya) ya wallafa shi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Masu Rera Waƙar danna nan

  • Yadda Ake Addu’ar Samun Nutsuwa Da Kwanciyar Hankali Da Wadatar Zuciya

    Yadda Ake Addu’ar Samun Nutsuwa Da Kwanciyar Hankali Da Wadatar Zuciya

    Addu’ar Samun Nutsuwa Da Kwanciyar Hankali – An ruwaito daga Shaddad Ibn Aws, Annabi (Sallallaahu Alaihi Wasallam) ya ce; “Ya Shaddad, idan ka ga mutane suna tara azurfa, zinare ko kuma yaƙutu, to suna tarawa ne don kada su yi talauci “.

    Sai ya ce; “Kai Shaddad, ka da ka tara komai, ka riƙe wannan addu’ar kawai, Allah (Subahanahu Wataa’ala) zai tsare mutuncinka ya rufa maka asiri, ka fi ƙarfin abin da za ka ci, kuma ka zauna lafiya, ni ma a duk lokacin da na yi sallah ina karanta wannan addu’ar;

    “Allahumma inni as’alukath Sabbath fil amr, wal azimatu alar rushdi, wa as’aluka shukra ni’matika wa husna ibdatika, wa as’aluka ƙalban saliman wa lisaanan sadiƙan, wa as’aluka min khairi ma ta’alam, wa a’uzubika min sharri ma ta’lam, wa astgfruka lima ta’lam innaka anta allumul gayub”.

    Wannan Addu’ar Samun Nutsuwa Da Kwanciyar Hankali; an samo ta ne daga WABILUS SAYYIBU MIN KALAMUD DAYYIB.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Kalmomi Guda Biyar Masu Amfani A Duniya Da Lahira danna nan

  • Kalmomi Guda Biyar Masu Amfani A Duniya Da Lahira

    Kalmomi Guda Biyar Masu Amfani A Duniya Da Lahira

    Wannan addu’ar; ana so a dunga karanta ta a duk lokacin da mutum ya tashi daga barci, da kuma lokacin da zai kwanta barci. Insha Allah, Allah zai tsare shi Duniya da Lahira.

    Idan ka karanta, Allah (Subahanahu Wata’ala) ba zai ba da dama wani ɗan Adam ya yi nasara a kanka ba; zai tsare ka daga sharrin dukkan maƙiya da mahassada; Duniya Da Lahira. Sannan Allah (Subahanahu Wata’ala) zai sa ka yi kyakkyawan ƙarshe a rayuwarka.

    Ga Addu’ar Kamar Haka;

    Na Duniya

    1. Hasbiyallahu lidini
    2. Hasbiyallahu liman ahammani
    3. Hasbiyallahu liman baga alayya
    4. Hasbiyallahu liman hasadani
    5. Hasbiyallahu liman kadaniy bisu’in.

    Na Lahira

    1. Hasbiyallahu indal mawt
    2. Hasbiyallahu indal mas’alatu fil ƙabar
    3. Hasbiyallahu indal mizan
    4. Hasbiyallahu indas siraɗi
    5. Hasbiyallahu la’ilaha illallahu alaihi tawakkaltu wa’ilahi unib.

    Wannan addu’ar an samo tane daga cikin littafin MAƘALIDUS SAMAWATI WAL ARDI MA’A HUSNUL MU’MIN.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Addu’a Idan Mutum Yana So Allah Ya Biya Masa Buƙata Cikin Gaggawa danna nan

  • Yadda Ake Addu’a Idan Mutum Yana So Allah Ya Biya Masa Buƙata Cikin Gaggawa

    Yadda Ake Addu’a Idan Mutum Yana So Allah Ya Biya Masa Buƙata Cikin Gaggawa

    Wannan addu’a ita ake kira “gaya wa jini na wuce”; domin biyan buƙata, Wato duk wata buƙata da kake nema wajen Allah (Subahanahu Wata’ala); ko kuma kake son Allah ya biya maka buƙatunka cikin gaggawa; sai ka dage ka ɗauki wannan addu’ar.

    Domin samun biyan buƙata, Za ka tashi cikin dare ka inganta alwalarka sannan ka yi nafila raka’ah biyu 2 ko huɗu 4 ko shida 6 ko takwas 8, sannan ka yi istigfari da salatin Annabi da hailala duk adadin da ya sawwaƙa, sai ka yi sujjada sannan ka karanta; 

    La ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minal zalimin” – (71)

    A cikin sujjada sai ka gaya wa Allah damuwarka sannnan sai ka ɗago ka zauna, sai ka sake istigfari da salatin Annabi da hailala, sai kuma ka karanta suratul Hadid; aya ta ashirin da ɗaya zuwa ta ashirin da huɗu (21-24). Sannan ka karanta wannan addu’ar kamar haka:

    Allahumma inni as’aluka bi’ismukal makhzun walmaknun, addahirul muƙaddis; Alhayyul Ƙayyum, Ar-rahmanur Rahim Zil Jalalu Wal Ikram, An Tusalliya Ala Sayyidin Muhammadin (Sallallahu Alaihi Wasallam); wa’an taf’al bi kasha wa kasha (inda zaka faɗi dukkan buƙatunka), birahmatika ya arhamur rahimin”.

    Wannan addu’ar an samo ta ne a cikin littafin MIFTAHUL KHAIR shafi na ashirin (20).

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Addu’ar Nema Wa Yara Shiriyar Ubangiji danna nan.

  • Yadda Ake Addu’ar Nema Wa Yara Shiriyar Ubangiji

    Yadda Ake Addu’ar Nema Wa Yara Shiriyar Ubangiji

    Shiriyar Ubangiji – Ga wanda yake son Allah (Subahanahu Wata’ala) ya shirya masa yaransa su kintsu, su shiryu, su zama suna kiyaye umarnin ubangiji da kuma sharuɗan da ya gindaya musu.

    Sai ka lazumci karanta musu wannan addu’ar a duk lokacin da ka gabatar da aikin alkhairi: azumi ne ko sallah ko kuma wani aikin alkhairi, sai kasanya su ciki, ka yi wannan addu’ar kamar haka;

    “Allahumma baarik lifi awlaadi warzuƙnibirrahun, allahumma ya mu’alimu Musa allimhum, waya mufahhima Suleimana fahhamhum; waya mu’ti Lukmanal hikimata aatihimul hikmah wa fasla kidab; Allahumma allimhum hikmah wa faslal kidab, allahumma allimhu ma jahilu; wazakkirhun manasu, waftah alaihim min barakatis samawati wal ardi; innaka sami’ul mujib. Allahumma inni as’aluka lahumut tawfiƙ, waƙuwwatul hifzi, wasur’atul faham; wasifa’an nahan, allahummaj’al huddatan muhtadin, la dhalina wala mudhallin; allahumma habbib ilaihimul imana wazayyanahu fi qulubihim akarrahu ilihimul kufra wal fasuwa wal isyaan; waja al hum minar rashidina”.

    Idan har ka karanta wannan addu’ar, da yardar Allah; ‘ya’yanka za su samu shiriyar Ubangiji.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Addu’ar Nema Wa Yara Samun Karatu Da Raba su Da Abokanan Banza danna nan.