Tag: ilimi

  • Yadda Sakamakon Zalunci Yake

    Yadda Sakamakon Zalunci Yake

    Shi kuwa zalunci babu abin da yake haifarwa ga azzalumai da ƙasa sai musiba da bala’i a duniya da lahira.

    Sakamakon Zalunci – Kowane irin zalunci babba da ƙarami gamammen zalunci wato zalunci da shugabanni suke yiwa miliyoyin mabiyansu; da kuma zalunci da ɗaiɗaikun mutane suke yi wa junansu, kamar zalunci tsakanin ma’aurata; da ubangida da yaronsa da maƙocin da malami da ɗalibansa da sauran rukunonin al’umma; duka irin waɗannan zalunce-zalunce Allah Ta’ala ba ya barinsu su wuce kawai ba tare da wani sakamako ba.

    Sakamakon wani zalunci yakan kasance hallakar da gaba ɗayan al’umma; kamar yadda ya faru ga Adawa da Samudawa da mutanen Annabi Luɗu. Wani sakamakon yakan tsaya ne kawai a kan wanda ya aikata zalunci shi kaɗai.

    Amma kuma idan mutanen kirki suka rungume hannu suka zura wa azzalumai ido suna sheƙe ayarsu, babu mai kwaɓar su, to sakamakon in ya zo yakan shafi kowa da har managartan, saboda ƙin ɗaukar matakin hana zalunci sakamakon zalunci yakan kasance ta hanyoyi daban-daban kamar talauci mai naci, taɓarɓarewar tsaro, yunwa, azzaluman shugabanni da koma baya da rashin ci gaban al’umma.

    Alƙur’ani mai girma da hadisan manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) cike suke da bayanan mummunan sakamakon azzalumai a duniya da lahira.

    A dunƙule ga abin da suke nunawa;

    1. Allah Ta’ala baya ƙaunar zalunci ba ya kuma ƙaunar azzalumai, yana fushi da su yana la’antarsu.

    2. Zalunci yana janyo musiba a bayan ƙasa kamar girgizar ƙasa, ambaliyar ruwa, tsawa, iska, gobara, yawan mace-mace, annoba, fari da sauransu.

    3. Zalunci yana jefa mutane cikin ɗimuwa da kiɗima da rashin samun shiriya ta yadda za a fita daga halin da ake ciki, haka kuma yakan ƙeƙasar da zuciya, azzalumai su ƙi tuba har su mutu a kan zaluncin su gamu da matsananciyar azaba a lahira. Shi ne ma’anar faɗin Allah Maɗaukaki:”Allah ba ya shiriyar da azzalumai.

    4. Allah Ta’ala ba ya ba da nasara da rinjaye ga azzalumai koda kuwa an ga sun ci wata nasara to ba mai ɗorewa ba ce, kuma abin da zai biyo baya na musiba da sharri ba ƙarami ba ne.

    5. A lahira azzalumai ba za su ji da daɗi ba domin akwai azzaluman da za su shiga wuta har abada ba za su fita ba, waɗansu kuma za su daɗe a cikinta gwargwadon irin zaluncin da suka yi.

    6. Azzalumai ba za su samu rabauta ba a lahira.

    7. Ba za su samu kariyar Allah ba.

    8. Ba za su shiga inuwar Allah ba.

    9. Allah Ta’ala zai haɗa su da waɗanda suka fi ƙarfinsu su gana musu uƙuba.

    10. ƙasar da zalunci ya samu wurin zama, sama da ƙasa ba za ta samu bunƙasa ba, ba za a samu kwanciyar hankali da zaman lafiya ba a cikinta, komai sai ya sukurkuce a yi ta ragabza ba ji ba gani ana ci gaban mai haƙan rijiya.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Nasihohi Goma Ga Masu Kula Da Dukiyar Al’umma danna koren rubutun nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Kura-kuran Masu Bayar Da Tarbiyya. danna koren rubutun nan

  • Nasihohi Goma Ga Masu Kula Da Dukiyar Al’umma

    Nasihohi Goma Ga Masu Kula Da Dukiyar Al’umma

    Duk shugaba ko ma’aikaci ko wani wakilin jama’a da dukiyar al’umma take gilmawa ko shigowa hannunsa to haƙiƙa yana cikin babban haɗarin da babu abinda zai ƙwace shi sai tsananin yaƙi da zuciya wajen kau da kai da haƙuri da kaucewa cin wa wannan dukiya ta hanyar da ba ta halattaba, tare da yawaita addu’ar Allah Ta’ala ya ba shi ikon sauke nauyin da yake kansa da kula da amanar da aka damƙa masa.

    Amfani da wannan nasihohi goma za su taimaka ƙwarai da gaske wajen tabbatar da haka;

    1) Ka kasance mai imani da cewa dukkanin dukiya ta Allah ce shi kaɗai kai matsayin wakili kawai kake, shi ne ma ya sa aka shata maka dokoki da sharaɗai kan yadda za ka yi mu’amala da wannan dukiyar kuma za a bincike ka a kan hakan ranar lahira. Saboda haka ka tabbatar duk abinda zai zo hannunka ka tabbatar halal ne tsantsa kuma ka yi amfani da shi ta hanyar da ta dace da shari’ar Allah Ta’ala.

    2) Ka kasance mai imani na gaskiya mai amana da kamewa da wadatar zuci sannan ka san hukunce-hukuncen musulunci, da suka shafi harkokin dukiya da kula da ita da kuma yin aiki da su.

    3) Ka sani cewa dukkanin ɗan ƙasa yana da haƙƙi a cikin dukiyar ƙasa kai ma ɗaya ne daga cikinsu, saboda haka, kada ka nuna son kai ko son zuciya da bambanci wajen baiwa mai haƙƙi haƙƙinsa.

    4) Ka sani cewa kare dukiyoyin al’umma daga sata, salwanta da lalacewa wajibi ne a kan kowa, musamman ma’aikata da shugabanni. Saboda tsaron dukiyar al’umma yana daga cikin manufofin shari’ar addinin musulunci.

    5) Ka guji cin amana da ɓarnatar da dukiyar al’umma ka sani ranar ƙiyama za a bincike kan duk abinda ka mallaka ka yi bayanin ta yadda ka same shi da kuma yadda ka yi amfani da shi.

    6) Ka guji yin amfani da dukiyar al’umma a kan buƙatunka na ƙashin kanka wanda ba su shafi aikinka ba. Misali kada ka rinƙa amfani da motar ofis wajen kai mata ko yara unguwa ko makaranta, ko ka ɗauki wani abu ka kai gidanka kana amfani da shi, ko kuma ka rinƙa amfani da injina ko kayan aikin ofis ɗinka ko ma’aikatarka.

    7) Ka yi mu’amala da dukiyar al’umma kamar yadda ake mu’amala da dukiyar maraya. Duk abinda mutum ya ci daga dukiyar marayu ba tare da haƙƙi ba, ya ci wuta balbal. Wajibi ne a rinƙa juya dukiyar marayu tana ƙaruwa, kuma a yi saboda Allah ba don neman a biya ka ba, sai dai in ka kasance mabuƙaci to sai a rinƙa biyanka ladan aikinka. To albashin ma’aikaci da shugabanni shi ne a matsayin ladansu.

    8) Ka sani cewa kare dukiyar al’umma wajibi ne akan kowa da kowa da kowa ba wai sai shugabanni ba kawai, saboda haka ya wajaba kowa ya bayar da gudunmawarsa wajen yaƙar ɓarnatar da dukiyoyin al’umma gwargwadon ikonsa.

    9) Ka guji ƙoƙarin tara kuɗi ta hanyar amfani da ofishinka, kada ka yi sata, kada ka danne haƙƙin kowa, kada ka karɓi na goro, kada ka ci hanci da rashawa.

    10) Ka sani cewa Allah Ta’ala zai yi maka hisabi kan duk abinda ka aikata a ranar da dukiya da ‘ya’ya da ‘yan uwa ba za su yi wa mara gaskiya wani amfani ba. Yi ƙoƙari ka bar wa ‘ya’yanka halal komai ƙanƙantarsa sai Allah ya sanya masa albarka ya inganta bayanka.

    Kada ka tara haram ka mutu ka bar magada, ba za su yi albarka ba, kuma bayanka ba zai yi kyau ba. Ɗan uwa ka kula da wannan nasihohi ka yi aiki da su za su amfane ka a duniya da lahira. Allah ya sa mu dace amin.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Hanyoyin Ɓarnatar Da Dukiyar Al’umma danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Cin Mutuncin Mutane Da Sunan Hamayyar Siyasa. danna nan.

    Don karanta bayani a kan Yadda Sakamakon Zalunci Yake danna nan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Hanyoyin Ɓarnatar Da Dukiyar Al’umma

    Hanyoyin Ɓarnatar Da Dukiyar Al’umma

    Akwai hanyoyi da yawa da shugabanni da ma’aikata suke bi wajen ɓarnatar da dukiyoyin al’umma kuma sai Allah ya hukunta su a kansu domin nau’i ne na cin amana da rusa tattalin arziƙin ƙasa.

    Kaɗan daga cikin waɗannan hanyoyi su ne;

    1) Fantamawa da wadaƙar da shugabanni da manyan ma’aikata suke yi; da su da iyalansu da abokansu da surukansu da barorinsu da dukiyar al’umma musamman a lokacin bukukuwansu.

    2) Antaya dukiya ga wanda aka ga dama haka kawai; saboda an ga dama ya zama miloniya ya yi nashe-nashe yana muwalat ya zama kamar wani sabon mutum. A can gefe kuma ga talakawa suna ta kuka wasu ma suna mutuwa; an hana su ɗan abinda za su sayi abinci da magani.

    3) Tara dukiyar ƙasa da taskance ta da hana talakawa da sauran mabuƙata sai dai a yi ta cewa tattalin arziƙin ƙasa ya haɓaka; asusun gwamnati ya cika maƙil da kuɗi; amma babu wani talaka da zai gani a ƙwaryar tuwonsa sai dai a yi ta surutu maras kan gado. Wanda in ba su masu faɗar ba, babu mai fahimtar abinda suke faɗa.

    4) Yin amfani da dukiyar al’umma a kan buƙatun ƙashin kai, kamar motoci, injina; kayan aiki da kuɗin al’umma a gonakinsu, ko ma’aikatunsu ko gidajensu da sauransu.

    5) Fifita manya da masu hannu da shuni a kan waɗanda ba su da komai ko ba su san kowa ba; ta hanyar rage, ko yafe musu haraji ko kuɗin fito ko ɗaukar su ko ‘ya’yansu ko matansu aiki; ko ba su bashi don su juya wataƙila ma a ce an yafe musu.

    6) Kashewa mawaƙa da makaɗa kuɗaɗe masu yawa don kawai neman suna; alhali ga malaman makaranta da likitoci da sauran talakawa suna fama da ƙarancin albashi wanda ya jawo taɓarɓarewar aikin gwamnati da rashin zaman lafiya a ƙasa, sai ka ga a lokaci guda wani mawaƙi ko ɗan bal ko wata ‘yar fim suna zama miloniyoyi a sama.

    7) Kashe kuɗaɗe masu nauyin gaske a kan harkokin zaɓe; waɗanda da za a tsakuro ɗaya bisa ukunsu a sa a ɓangaren ilimi ko noma ko lafiya ko tsaro da an ga canji a rayuwar al’umma.

    Amma ina sai a yi watsi-watsi da waɗannan kuɗaɗe masu ciwon gaske a yi abinda aka ga dama; a ce an zaɓe wane ya ci wane ya faɗi.

    8) Kashe maƙudan kuɗaɗe wajen tarbar shugabanni na gida da na wajen domin ƙawata tituna; tara musu talakawa, shirya abinci da sauran abubuwa na ganin ido sai ka ga a yini ɗaya an kashe miliyoyin nairori na fitar hankali; saboda wai shugaba wane zai kawo ziyara ƙasa ko jiha.

    9) Warewa harkokin wasannin kuɗaɗe masu ɗimbin yawa fiye da kuɗin da aka warewa ma’aikatar lafiya; tsaro, ilimi da sauransu waɗanda suka fi wasanni muhimmanci; amma dai haka suke rufe idanunsu su toshe kunnuwansu su narka kuɗi a can ba ruwan su.

    10) Caɓawa masallatai ado wani lakacin da gwalagwalai amma a yi burus da limamai da ladanai da ma su kansu masallatan masu sallah a wasu masallatan; sai ka ga adon yana shagalar da masu sallah maimakon su tara hankalinsu ga sallarsu; sai su yi ta kallon ƙyale – ƙyalen da aka yi.

    A wasu ƙasashen kuma sai a gina masallaci gari guda amma kuma babu masu sallar, sai dai ‘yan yawon buɗe idanu ne za su rinƙa zuwa suna ɗaukar hotuna a cikinsa.
    Kamar yadda a waɗansu ƙasashen ake ƙawata ƙaburburan shaihunai a kashe miliyoyin daloli domin kawai a samu goyon bayan mabiyan wannan mamacin (shehin).

    11) Rashin kula da aiki ta hanyar zuwa a makare da tashi kafin lokacin ya yi; da ma ƙin yin aikin ai an je wurin aikin sai a ɓuge da hira ko karance-karancen jaridu ko matse-matsen waya da kallon talabijin; ka ga kuɗin da ake kashewa kan waɗannan ayyukan da ma’aikatan kusan duk asarar su ake yi.

    12) Kashe dukiyar al’umma kan bukukuwa na ƙasa ko na siyasa ko bukukuwan da ake danganta su ga addini kamar bikin ranar samun ‘yancin kai, Bikin ranar demokuraɗiyya; bukukuwan mauludin Annabi da na shaihunai, sai ka ga an fitar da miliyoyin kuɗi an yi watandar su, alhali ga lalurorin rayuwa babu cikakkiyar kulawa.

    13) Biyawa ‘yan siyasa da ‘yan jagaliya aikin hajji ba don komai ba sai don kawai sun yi wa shugaba yaƙin neman zaɓe sai ya saka musu da kujerun hajji, waɗansu ma in sun je hajijiya kawai za su yi su dawo. Amma malamai masu koyar da alhazai aikin hajji da likitoci da sauran maa’aikatan da za su taimakawa alhazai su yi ibada cikin nutsuwa da inganci waɗannan babu wani laifi don gwamnati ta biya musu aikin hajji amma a ji tsoron Allah a yi gaskiya da adalci a dubi cancanta wajen zaɓar waɗanda za a biyawa.

    14) Ha’inci wajen ba da kwangila ta hanyar kashe-mu-raba tsakanin ‘yan kwangila da jami’an gwamnati; sai a zaftare kuɗin ko dai a ƙi yin aikin sam ko kuma a yi shi mara inganci ta yadda da an kwana biyu zai tashi daga aiki, in titi ne sai ya ɓaɓɓagure in gini ne ya rushe in wasu injina ne su lalace. Subhanallah.

    15) Wawashe kuɗaɗen al’umma a je a damfare su a bankunan ƙasashen turai, su yi ta gina kansu da su; ‘yan ƙasa kuma suna ta mutuwa. Waɗansu ma sai su je can su kafa masana’antu alhali ga miliyoyin ‘yan ƙasa ba su da aikin yi.

    16) Tarukan siyasa musamman na neman zaɓe da karɓar waɗanda suka baro jam’iyyunsu zuwa jam’iyyar gwamnati; in ka ji yawan kuɗin da ake kashewa a irin wannan harkar abin akwai matuƙar takaici da ɗaure kai.

    17) Ware kuɗi mai yawan gaske da sunan wai za a yi addu’ar neman zaman lafiya ga ƙasa; ko kuma samun nasara a zaɓe. Sai dai abin takaicin shi ne mafi yawancin wannan kuɗi masu addu’ar ta gaske; saboda Allah ko labarinsu ba su ji ballantana su gan su. Sai a a yi dumbuza ana bai wa bokaye da miyagun malamai da matsafa da waɗanda ma ba musulmi ba. In ya zama dole sai an fitar da wannan kuɗi kamata ya yi a bi talakawa da gajiyayyu da malaman zaure da na tsangayu da ɗalibansu a ba su abinda zai faranta musu rayuka su ma su sami sa’ida da walwala to ko ba su yi addu’a ba; Allah zai biya buƙata sakamakon faranta musu da aka yi.

    A gaskiya hanyoyi da waɗansu shuwagabanni suke bai wajen tarwatsa da ɓarna da dukiyar al’umma suna da yawan gaske, abin fa ya zama sai dai a ce innalillahi wa inna ilaihirraji’un.
    Ya Allah ka ba mu ikon gyaran halayen mu, ka yi mana a fuwa da gafara ka a zurtamu da shugabanni managarta masu ƙarfi da amana amin.

    Domin karanta cikakken bayani akan Hidisai Goma Kan Hatsarin Shugabanci danna nan

    Domin karanta cikakken bayani akan Haramcin Zalunci, Tasirin Addu’ar Wanda Aka Zalunta Da Wajabcin Sa danna nan.

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Hidisai Goma Kan Hatsarin Shugabanci

    Hidisai Goma Kan Hatsarin Shugabanci

    Hatsarin Shugabanci: Shugabanci komai ƙanƙantarsa wani nauyi ne babba a kan wanda ya hau kansa, wanda in ba a ɗauke shi an sauke shi daidai ba; in ba a yi gaskiya da adalci ba, in ba a riƙe amana ba; tabbas zai zama nadama da takaici ga wanda ya yi wannan shugabanci.

    Da mun san hatsarin da yake cikin shugabanci koda an yi shi bisa gaskiya da riƙon amana; da babu wanda zai nemi a ba shi shugabanci; da sai an zo ana bin mutum ana haɗa shi da Allah don ya karɓi muƙami yana gudu yana a kai kasuwa. To amma rashin sanin hatsari da yake ciki; da kuma kallon da kwaɗayin ɗan roman da yake cikinsa, shi ne yasa ake ta yin kokawa; har ma ana kashe kuɗaɗe masu ciwo da ma roƙon Allah duk don a ɗare kan karagar mulki.

    Ga wasu daga hadisan da shugaban halitta ya faɗa a kan hatsarin shugabanci:

    Hadisi Na Ɗaya

    An karɓo daga Abdullahi ɗan Umar (Radiyallahu Anhu) ya ce; “Na ji Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yana cewa; “Kowane ɗaya daga cikinku makiyayi ne (shugaba ne) kuma za a tambaye shi a kan waɗanda aka ba shi kiwo; shugaba makiyayi ne kuma za a tambaye shi a kan waɗanda aka ba shi kiwo (mabiyansa), magidanci makiyayi ne a kan iyalansa kuma za a tambaye shi a kansu.

    Matar aure mai kiwo ce a gidan mijinta kuma za a tambaye ta a kan waɗanda aka ba ta kiwo. Yaron gida/kanti makiyayi ne a cikin dukiyar uban gidansa; kuma; kowa za a tambaye shi a kan abin da aka ba shi kiwo. Dukkanninku makiyaya ne, kuma za a yi masa tambaya a kan abin da aka ba shi kiwo.
    Bukhari da Muslim ne suka ruwaito shi.

    Karin Bayani

    Wannan hadisi ne mai girma da muhimmanci wanda ya ƙunshi abubuwa da dama kaɗan daga cikinsu su ne:

    1. shugabanci kalma ce mai faɗi bai taƙaita a kan masu riƙe da madafan mulki ba, a’a duk wani wanda waɗansu suke ƙarƙashinsa komai rashin yawansu to shi ma shugaba ne, kamar yadda hadisin ya faɗa:
    Mai mulki shugaba ne, mai gida shugaba ne a gidansa, matar aure shugaba ce a gidan mijinta, bara ko yaron gida ko angulun kanti, shugaba ne a kan dukiyar uban gidansa. Haka dai har shugaban aji da ɗalibai da na ƙungiyoyi da kwamitoci da sauransu.

    2. Kowa za a yi masa hisabi ranar lahira; za a bincike shi kan yadda ya gudanar da shugabanci da aka ba shi.

    3. Duk azabar da za a yi wa azzalumin shugaba; da kuma falala da rahamar da Allah yake yi wa adalin shugaba zai samu mai gida da uwargida, da yaron gida da sarki har zuwa shugaban ƙasa,babu bambanci, sai dai kuma kayan wani sun fi na wani yawa da nauyi.

    4. A duk lokacin da ake maganar shugabanci yabo ko zargi alhairi ko sharri kafin ka yi tunanin shugaban ƙasa ko gwamna ko sarki ko wani na can sama; ka fara duba kanka ka yi wa kanka hisabi. Shi shugabancin da aka ba ka, kana kula da shi yadda ya kamata? Shin kana ba da haƙƙoƙin da suke kanka?.

    Hadisi Na Biyu A Kan Hatsarin Shugabanci

    An karɓo daga Anas ɗan Malik (Radiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Haƙiƙa Allah zai tambayi kowane makiyayi a kan abin da aka ba shi kiwo, shin ya kiyaye shi ko ya tozarta shi? Har ma za a tambayi mutum a kan iyalansa”.
    Ibn Hibban ne ya rawaito shi a cikin sahihinsa.

    Karin Bayani
    Lallai ne magidanta masu tozarta haƙƙoƙin iyalansu su bar ‘ya’yansu kamar marayu, matansu kamar kuyangi ba tarbiyya ba cikakkiyar lafiya har dabbobin da suke kiwatawa ma sai su fi iyalansu jin daɗinsu, su ji tsoron Allah su riƙe iyalansu da gaskiya su sani cewa amana ce Allah ya damƙa musu kuma za su yi bayani ranar ƙiyama kan wannan amanar.

    Hadisi Na Uku A Kan Hatsarin Shugabanci

    An karɓo daga Abu Hurairah (Radiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Duk wanda ya zama alƙali haƙiƙa an yanka shi ba da wuƙa ba”.
    Abu Dawud da Tirmizi ne suka rawaito shi.

    Karin Bayani

    Duk alƙalin da ya yi rashin gaskiya a kan aikinsa, haƙiƙa ya yi babbar asara ya halaka; ba wai rayuwarsa kawai ya rasa ba, har ma da addininsa wato wanda aka yanka da wuƙa zai fi shi samun sauƙin mutuwa da halaka. Wannan hadisi yana bayanin hatsarin da yake cikin alƙalanci; saboda haka ya zama wajibi ga alƙalai su yi taka tsantsan su rinƙa kwatanta gaskiya da adalci su guji zalunci, da cin hanci da murɗe gaskiya.

    Hadisi Na Huɗu A Kan Hatsarin Shugabanci

    An karɓo daga Auf ɗan Malik (Radiyallahu Anhu) haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; “In kuna so zan ba ku bayani a kan shugabanci ko yaya yake? Sai na ɗaga muryata na ce, “Yaya yake ya Ma’aikin Allah? Sai ya ce: “Farkonsa zargi ne, na biyunsa nadama ce, na ukunsa azaba a ranar ƙiyama sai dai wanda ya yi adalci”.
    Bazzar da Ɗabarani ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Wannan hadisi ne mai ɗimbin fa’ida da bayanin ɗabi’ar mulki duk daga taƙaitattun kalmominsa

    • Mai mulki ba ya kuɓuta daga zargi da tuhuma da munana masa zato daga waɗanda yake mulka; da abokan hamayyarsa komai ƙoƙarinsa na kwatanta gaskiya. Haka zai ta shan suka da ƙalubale ta kowanne ɓangare, dukkanin idanu da kunnuwa suna kansa, komai ya faru shi ne ko bai sani ba, kuma ya fi ƙarfinsa.

    – Yayin da abubuwa suka dagule, matsaloli suka kunno kai ta ko’ina, magoya baya suka fara juya baya ga shugaba, barazana da fargaba ta yawaita a gida da waje, shugaba yakan tsinci kansa a halin da- na-sani, da nadamar karɓar wannan shugabanci.

    – Haka kuma bayan shugaba ya bar mulki musamman in an bi shi da jafa’i da bincike-binciken neman laifi da gazawa, wannan ma yana jefa masu mulki cikin kogin nadamar karɓar mulki.

    – Mafi munin yanayi kuma shi ne, matsananciyar azaba da take jiran azzaluman shugabanni a lahira da tozarta da wulaƙanta tun daga duniya.

    A taƙaice wannan hadisi yana ɗauke da tsoratarwa a kan shugabanci na zalunci da kwaɗaitarwa kan adalci saboda shi adalin shugaba babu ruwansa da wannan azabar.

    Hadisi Na Biyar A Kan Hatsarin Shugabanci

    An karɓo daga Abu Zarr (Radiyallahu Anhu) ya ce; “Na ce ya Ma’aikin Allah shin ba ka ba ni wani muƙami ba? Sai ya ɗora hannunsa a kan kafaɗata, sannan ya ce; “Ya kai Abu Zarrin haƙiƙa kai mutum ne mai rauni, shi kuma shugabanci amana ne, kuma yana jawo kunyata da nadama ranar ƙiyama; sai dai wanda ya kula da haƙƙoƙin shugabanci ya sauke nauyin da yake cikin shugabanci.

    Hadisi Na Shida A Kan Hatsarin Shugabanci

    An karɓo daga gare shi (Abu Zarr) Radiyallahu Anhu, haƙiƙa Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce da shi; “Ya kai Abu Zarr haƙiƙa na ga kai mutum ne mai rauni, kuma ina so gare ka abinda nake so ga kaina. Saboda haka, kada ka shugabanci koda mutum biyu, kuma kada ka karɓi riƙon dukiyar maraya.

    Muslim da Abu Dawud da Hakim ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) shugaba ne da yake lura da halin kowa kuma yake ba shi aikin da ya dace da shi.
    Duk tsoron Allah na mutum da yawan ibadarsa bai kamata a ba shi shugabanci ba, in dai ba shi da ƙarfi da gogewa kan al’amuran mulki. Wannan ne ya sa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ƙi ya ba wa Abu Zarr wani muƙami saboda ya san rauninsa da matsanancin sauƙin kansa da gudun duniya; har ma ya ba shi shawarar cewa ko da shugabancin mutum biyu aka ba shi kada ya karɓa.

    Haka kuma kada ya karɓi ajiyar dukiyar marayu ba don yana tsoron zai cinye ba, a’a sai don gudun kada tausayi ya sa ya yi sadaka da wannan dukiyar.

    Ɗan’uwa idan an faɗa wa Abu Zarr (Radiyallahu Anhu) duk da falalarsa; ina ga mutanen yanzu da za ka ga har kuɗi ake kashewa, ko a yi ta yin rigima a kan neman shugabanci, ba kuma tare da wata cikakkiyar cancanta ko manufa ko tsari ba.

    Hadisi Na Bakwai A Kan Hatsarin Shugabanci

    An karɓo daga Abu Hurairah (Radiyallahu Anhu) haƙiƙa Manzo Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; “Haƙiƙa za ku rinƙa kwaɗayin shugabanci, kuma haƙiƙa zai zama sanadin nadama ranar alƙiyama. Madalla da mai shayarwa tir da mai yayewa”.
    Bukhari da Nasa’i ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Wannan abu da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya faɗa na tsananin kwaɗayin shugabanci kamar a yanzu yake maganar. Sai ka ga ɗaruruwan mutane suna takarar kujera ɗaya; kuma a yanzu kowa so yake ya zama shugaba, sai ka ga komai da shugabansa; kuma har ana rigima a kan wannan shugabanci. Amma duka a ƙarshe nadama ce take biyo baya.
    Mai shayarwa da mai yayewa shugabancin ake nufi, wato kamar yadda yaro yake jin daɗi lokacin da ake shayar da shi, kuma yake shan wahala da fama da laulayi iri-iri lokacin yaye shi to haka daɗin shugabanci yake a farkon da kuma wahala da damuwa da ake shiga in an sauka.

    Hadisi Na Takwas A Kan Hatsarin Shugabanci

    An karɓo daga Abu Hurairah (Radiyallahu Anhu) haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; “Kaicon sarakuna, kaicon wakilai, kaicon amintattu. Wallahi waɗansu mutane (waɗanda suka karɓi shugabanci) a ranar ƙiyama za su yi burin ina ma da a ce a ɗaure gashinsu a jikin tauraron surayya; su yi ta reto tsakanin sama da ƙasa a maimaikon shugabancin da suka riƙe.

    Ibn Hibban da Hakim ne suka rawaito shi.

    Hadisi Na Tara A Kan Hatsarin Shugabanci

    An karɓo daga Abu Huraira (Radiyallahu Anhu) ya ce; “Na ji Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yana cewa; “Zamani ya kusa zuwa da mutum zai yi burin gara a ce ina ma ya faɗo daga tauraron Surayya (zai fi masa sauƙi) a kan mulkin da ya yi komai ƙanƙantarsa”.

    Hakim ne ya rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Waɗannan hadisai guda biyu suna bayanin hatsarin shugabanci ta yadda mutum zai ji a ransa cewa gara a rataye shi da gashinsa a jikin tauraro ya yi ta reto; ko kuma a jefa shi daga can sama ya yi ƙasa ya ratattake a maimakon azabar da za a yi masa; saboda rashin adalci da gaskiya da ya gudanar a shugabancin.

    Hadisi Na Goma A Kan Hatsarin Shugabanci

    An karɓo daga Abdurrahman bin Samura (Radiyallahu Anhu) ya ce; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce da shi; “Ya kai Abdurrahman ɗan Samura kada ka nemi shugabanci, saboda in ya zo maka ba tare da ka nema ba, Allah zai taimake ka a kansa; in kuwa aka ba ka shugabanci saboda nema da ka yi sai Allah ya bar ka da dabararka”.

    Buhari da Muslim ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Duk wanda ya san hatsarin shugabanci da makomarsa; ba zai iya nacewa ya yi ta kokawar sai ya sami muƙami ba. To irin wannan idan aka ga cancantar su aka tilasta musu lallai sai sun karɓi muƙamin za su sami tallafi da agaji daga Allah.
    Wanda kuwa ya nace sai an ba shi muƙami musamman in bai cancanta ba ko kuma yana da wata muguwar manufa a ransa to ba zai yi wani abin kirki ba sai hauma-hauma da zalunci.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Hadisi Na Ɗaya A Kan Haramcin Goyon Bayan Azzaluman Shugabanni danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Shugabanci A Musulunci (Hadisai Tamanin Da Biyu A Kan Shugabanci); wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Yadda Ake Tafiya Sujudah

    Yadda Ake Tafiya Sujudah

    Tafiya Sujudah: Akwai hadisin da ya ce mai sallah ya fara ajiye gwuiwarsa kafin hannayensa. Ruwayar (wa’il ibnu hujur).

    Akwai kuma hadisin da ya ce ; ya fara ajiye hannayensa kafin gwuiwarsa, ruwayar (Abu Huraira); shi ne wasu malaman suka ce; gwuiwar raƙumi a hannunsa take saboda haka, da hannuwanka za ka tafi ba da gwuiwa ba.

    Wasu malaman kuma suka ce; ruwayar (Wa’il ibnu Hujur) ita ce ta zo daidai ruwayar (Abu Huraira); ta zo a baibai ne, saboda haka da gwuiwar ƙafafunsa zai tafi sujuda ba da hannuwansa ba.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Abin Da Ya Kamata Mai Yin Sallah Ya yi Bayan Ya Tafi Sujudah danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Sallar Roƙon Ruwa danna nan.

  • Tatsuniyar Gizo Da Namun Daji

    Tatsuniyar Gizo Da Namun Daji

    Ga ta nan ga ta nan ku

    Gizo ne dai yana son ya ci nama, amma ba shi da shi. Ya rasa yadda zai yi. Sannan ya ce a ransa, “Bari dai in yi wata dabara”. Sai ya sayo goro ya rarraba wa namun daji da tsuntsayen gida. Sai ya fara kai wa kaza, ya ce, “Ga shi, goron wasa ne wanda za a yi a cikin daji, naki ne wannan” .

    Sai kaza ta ce, “To. Amma fa kada ka kai wa muzuru”. Sai ya ce, “Haba, me zai sa in kai masa?” Da gizo ya fita, sai ya shiga gidan muzuru, ya kai masa goro. Sai shi ma muzurun ya ce, “To, amma kada ka kai wa kare”. Sai gizo ya ce, “Haba me zai sa in kai masa?”

    Da dai gizo ya fita, sai ya shiga gidan kare ya ba shi nasa goron. Kare ya ce, “To, amma fa kada ka kai wa kura”. ‘Gizo ya ce, “Haba me zai sa in kai mata?” Da ya fita, sai ya kai wa kura nata goron. Kura ta ce, “To, amma fa kada ka kai wa Zaki”.

    Ya ce, ‘Haba kura, me zai sa in kai wa Zaki?’

    Shi ke nan, sai ya kai wa Zaki nasa goron, ya ce, “Ranka ya daɗe. Wani ɗan wasa za a yi na kawo maka goro”. Da Zaki ya karɓa, sai ya ce, “To, Allah ya kai mu”. Shi ke nan. Da ya fita, sai ya shiga ya kai wa damisa. Damisa ta ce, “In ce ko dai ba ka kai wa Sarki Zaki ba?”
    Sai Gizo ya ce, ‘Haba, haba. Wane ni da gayyatar Sarki?’ Sai damisa ta ce, ‘To, Allah ya kai mu”.

    Da ya fito sai kuma ya shiga gidan giwa ya kai mata nata goron. Sai giwa ta ce, “To, in ce ko baka kai wa manyan dawa ba?’ Ya ce, “Mhm! Yaya zan kai?” Ko kai masa ne ma ai ke zan bai wa ki kai masa “. Shi ke nan. Ana nan ana nan, sai ranar wasa ta zo. Gizo ya bayyana musu wurin da za su haɗu a yi wasan. Ya ce musu, “To, ku tafi zan same ku. Ni daga baya zan taho tare da makaɗa’. Shi ke nan. Sai kaza ta fara tafiya. Ashe ba su sani ba, gizo ya riga su isa can. Sai kaza ta isa can. Gizo ya yi mata maraba. Ya ce,

    “Shiga wannan bukkar kafin su zo”.

    Shi ke nan. Kaza ta shiga, ta zauna. Daga can sai ga muzuru ya taho. Sai Gizo ya gaya wa muzuru cikin raɗa, ‘Maraba’. Shiga tana nan a ciki’. Shi ke nan sai muzuru ya shiga ya tasar wa kaza zai cinye ta. Ya cinye ta. Can kuma sai ga kare ya taho. Shi ma dai Gizo ya gaya masa kamar yadda ya gaya wa muzuru. Sai shi ma karen ya cinye muzuru.

    Daga nan kuma sai ga kura. Ita ma ya gaya mata kamar yadda ya gaya wa kare da muzuru. Sai kura ta shiga ta cinye kare. Kura kuma tana zaune a cikin rumfa. Sai ga Zaki ya taho. shi ma Gizo ya gaya masa haka. Ya shiga ya cinye kura. Daga nan sai ga giwa da damisa sun jero sun taho. Sai Gizo ya ce, “To, ku shiga nan bukkar mana”. Daga shigar su, sai suka kaure da faɗa tun daga cikin rumfar har suka yiwo waje. Idonsu duk ya rufe, suna ta faɗa. Sai Gizo ya samo ganga, ya soma kiɗa yana waƙa:
    Zaki bari, damisa bari.
    Giwa bari.

    Faɗanku na manya,

    Wa yake shiga?
    Sai wawa, sai mahaukaci.
    Sai ko ni da ba ni da hankali.

    Suna ta faɗa, can da giwa ta ga abin ba dama, sai ta fito ta yi tafiyarta gida, ta bar zaki da damisa suna karawa. Sai Gizo ya ci gaba da yi musu waƙa. Ya yi ta yi, su kuma suna ta faɗa. Ashe Gizo da ma ya zo da yaji a ƙunshe. Sai ya ɗauko yajin nan ya barbaɗa musu a idanunsu. Sai fa faɗa ya rincaɓe, idanunsu suka rufe ruf. Daga can sai Gizo ya ɗauko wuƙa ya ce, “Yan banza. Ana so a ci nama an rasa yadda za a yi”. Sai ya kama yankan naman jikinsu yana tarawa, har ya kashe su duka. Sai ya jide naman ya kai gida aka soya masa, ya ci ya ƙoshi, ya ajiye sauran, yana ci lokaci-lokaci.

    Ƙurunƙus.

    Domin karanta Tatsuniyar Ɗankaɗafi danna nan.

    Domin karanta Tatsuniyar Gizo Da Giwa danna nan.

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Addu’o’i Domin Neman Tsari Daga Azzalumai

    Addu’o’i Domin Neman Tsari Daga Azzalumai

    Addu’o’in Tsari Daga Azzalumai; An karɓo daga Abdullahi ɗan Mas’ud (Radiyallahu Anhu) ya ce; Idan ɗayanku yana jin tsoron wani azzalumin shugaba sai ya ce:

    Allahumma rabbussamawatis sab’i, wa rabbul arshil azim, kun li jaran min wa atba’ihi min halƙika minal jinni wal insi an yafruɗa alayya ahadun minhum au an yaɗga, azza jaruka wa jalla sana’uka wa la’ilaha illan anta”.

    Asbahani ne ya ruwaito shi daga Ibn Mas’ud danganta maganar ba ga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) (Mauƙuf).

    An karɓo daga Abdullahi Ibn Abbas (Radiyallahu Anhu) ya ce; “Idan ka je wurin wani shugaba mai kwarjini wanda kake jin tsoron zai afka maka sai ka ce:

    Allah Akbar Allah a’azzu min khalƙihi jami’an, Allahu a’azzu mimma akhafu wa ahzaru, a uzu billahillazi laa ilaaha illaa huwa almumsikus samawati an yaƙa’a na alal ardi illa bi iznihi min sharri abdika wa junudihi wa atba’ihi wa ashya’ihi minal jinni wal insi. Allahumma kun li jaaran min sharrihim jalla sana’uka wa azza jaruka wa tabarakas muka, wa laa ilaahha gairuka”(sau uku).

    Ibn Abi Shaiba ne ya ruwaito shi, daga Ibn Mas’ud.

    Ƙarin Bayani

    Wannan hadisi sahihi ne mauƙufan wato zuwa ga Ibn Mas’ud, amma bai inganta ba zuwa ga Annabi. Haka kuma addu’a ta biyu ta inganta daga Ibn Abbas (Radiyallahu Anhu).
    Addu’o’i ne kyawawa da mutum zai iya yi duk lokacin da ya ji tsoron zaluncin wani azzalumin shugaba. A wurin da babu komai sai a faɗi sunan shugaban.

    Fassara

    Fassarar addu’a ta farko:

    Ya Allah Ubangijin sammai bakwai, Ubangijin Al’arshi; mai girma ka kare ni daga sharrin wane ɗan wane da dukkan mabiyansa daga halittunka aljanu da mutane; kada ka ba wa ɗaya daga cikinsu dama ya afka min ko ya yi min ta’addanci; kariyarka ta buwaya, yabonka ya girmama. Babu wanda ya cancanta a bautawa sai kai.

    Ita kuwa addu’a ta biyu ga fassararta:

    Allah shi ne mafi girma, Allah shi ne mafi buwaya daga halittunsa gaba ɗaya. Allah shi ne mafi buwaya daga abin da nake tsoro da fargaba. Ina neman tsari da Allah wanda babu wanda ya cancanta a bauta wa sai shi; wanda yake riƙe da sammai kada su faɗo kan ƙasa sai da izininsa. Ka kare ni daga sharrin bawanka wane da jami’an tsaronsa da mabiyansa da ma magoya bayansa mutane da aljanu.
    Ya Allah ka kasance mai kariya a gare ni daga sharrinsu, yabonka ya girmama, wanda ka baiwa kariya ya buwaya, sunanka ya yi albarka babu wanda ya cancanta a bautawa sai kai.

    Domin karanta cikakken bayani akan Sahabban Da Suka Fi Kowa Rawaito Hadisai danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Hadisi Na Ɗaya A Kan Haramcin Goyon Bayan Azzaluman Shugabanni danna nan.

  • Falalar Adalci, Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    Falalar Adalci, Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    Hadisi Na Ɗaya A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Jarir ɗan Abdullahi (Radiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Duk wanda ba ya tausayin mutane, Allah ba zai tausaya masa ba”.

    Bukhari da Muslim da Tirmizi ne suka rawaito shi. Ahmad ma ya rawaito shi ya ƙara da cewa: “Wanda ba ya afuwa, Allah ba zai yi masa afuwa ba”.

    Abu Dawud da Tirmizi ne suka rawaito shi.

    Hadisi Na Biyu A kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abdullahi ɗan Amr ɗan Asi (Radiyallahu Anhuma) haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Masu tausayi Allah mai rahama zai tausaya musu. Ku tausayawa na ƙasa da ku, wanda yake sama da ku zai tausaya muku.

    Abu Dawud da Tirmizi ne suka rawaito shi.

    Hadisi Na Uku A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abu Hurairah (Radiyallahu Anhu) ya ce: Na ji mai gaskiya abin gaskatawa mai wannan ɗakin baban Alƙasim (Sallallahu Alaihi Wasallam) yana cewa: “Ba a cire tausayi sai daga zuciyar mara rabo a lahira”.

    Abu Dawud da Tirmizi ne suka rawaito shi.

    Hadisi Na Huɗu A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abdullahi ɗan Abbas (Radiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Ba ya tare da mu wanda ba ya tausayawa ƙaraminmu, kuma ba ya girmama babbanmu, kuma ba ya umarni da kyakkyawan aiki, ba ya hani ga mummuna.

    Tirmizi ne ya rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Waɗannan hadisai guda biyar suna bayyana falalar tausayawa mabiya da jinƙan su da sauran masu rauni da haramcin gallaza musu, suna nuna cewa duk wanda yake da jinƙai da tausayi Allah zai tausaya masa, kuma rashin tausayi alama ce ta rashin imani da rashin rabo a lahira, har ma Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Ba ruwan sa da maƙetaci mugu maras imani da tausayi da kuma wanda ba ya girmama na gaba da shi” .

    Hadisi Na Biyar A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    Hadisi Na Biyar A kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Aliyyu (Radiyallahu Anhu) ya ce: “Maganar ƙarshe da Manzon (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya yi ita ce: “Ku kula da sallah, ku kula da sallah, ku ji tsoron Allah ku kula da haƙƙoƙin waɗanda suke a ƙarƙashinku”.

    Abu Dawud da Ibn Majah ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Wannan hadisi yana daga cikin wasiyyoyin da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya bar wa al’ummarsa dab da wafatinsa. Ya yi wasiyyar a kula da sallah kuma a kula da haƙƙoƙin bayi da barori; da kuma duk waɗanda suke ƙarƙashin mutum.

    Hadisi Na Bakwai A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abdullahi ɗan Amr ɗan Asi (Radiyallahu Ahuma) ya ce; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Haƙiƙa masu adalci za su kasance a kan mimbarai na haske a daman Allah mai rahama; kuma duk hannayensa biyu dama ne. Su ne waɗanda suke yin adalci a cikin hukuncinsu da iyalansu da waɗanda suke jagoranta.

    Muslim da Nasa’i ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Haƙiƙa masu yin adalci da gaskiya a shugabancin da yake kansu da iyalansu suke kaucewa zalunci da nuna bambancin a tsakanin waɗanda suke jagoranta, za su samu babban matsayi a wurin Allah ranar lahira.
    Hannun dama da ya zo a wannan hadisin sifa ce daga siffofin Allah Ta’ala waɗanda ake yin imani da su kamar yadda suka zo, ba tare da an yi musu tawali ko canja su, ko kore su ba, ko kuma kamanta su da sifofin halittu ba.

    Hadisi Na Takwas Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Iyad bin Himar (Radiyallahu Anhu) ya ce: Na ji Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yana cewa; “Yan Aljanna guda uku ne: Mai mulki mai adalci mai dacewa da gaskiya; da mutum mai tausayi mai taushin zuciya ga dukkanin ‘yan uwansa da dukkan musulmi da kuma mutum mai iyali, mai kame kai da wadatar zuci.

    Muslim ne ya rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Falalar da darajar waɗannan mutane uku ta sanya Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya taƙaice ‘yan Aljanna a kansu. Saboda duk wani wanda yake riƙe da wani jagoranci tun daga mai gida da uwargida har zuwa kan shugaban ƙasa ya yi ƙoƙari ya yi adalci ya nemi gaskiya kuma ya yi aiki da ita.

    Kowa ya fitar da mugunta da ƙeta da gaba da ganin ƙyashi daga zuciyarsa, mu kasance masu tausayi da taimako da ƙauna ga dukkan ‘yan uwanmu da gabaki ɗayan musulmi.

    Kowa ya zage damtse ya nemi halal ya kula da iyalansa kuma ya wadatu da abin da Allah ya ba shi ya kasance mai godiya ga Allah ya rinƙa hangen na ƙasa da shi, kada ya rinƙa hangen na sama da shi.
    Waɗannan halaye za su sa mu cancanci shiga Aljannah, kishiyoyinsu kuwa, babu abin da za su jawo mana sai shiga wuta tun daga duniya kafin ta lahira.

    Hadisi Na Tara A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abu Huraira (Radiyallahu Anhu) ya ce; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: Allah Ta’ala yana ƙin mutane huɗu: Ɗan kasuwa mai yawan rantsuwa, da talaka mai girman kai, da tsoho mazinaci da kuma azzalumin shugaba.

    Nasa’i da Ibn Hibban ne suka rawaito shi; Muslim ma ya rawaito makamancinsa, sai dai a ruwayarsa ya ce; “Da talaka mai girman kai da shugaba maƙaryaci”.

    Hadisi Na Goma A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Mu’awiyya (Radiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Ba za a tsarkake al’ummar da ba hukuncin gaskiya a cikinta ba, kuma mai rauni ba ya iya karɓar haƙƙinsa daga mai ƙarfi cikin daɗin rai”.
    Ɗabarani ne ya ruwaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Wannan hadisin Ibn Majah ma ya rawaito shi tare da wata ƙissa mai ban sha’awa kamar haka:

    “Wani baƙauye ya zo wurin Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) domin karɓar bashin da yake bin sa. Ya matsa masa har ya ce: “Ba makawa sai ka biya ni bashina”. Sannan sahabbai suka daka masa tsawa suka ce: “Kasan da wa kake magana kuwa? Sannan ya kada baki ya ce: “To ba haƙƙi nake nema ba? Sai Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce da su: “Don me ba za ku goyi bayansa ba?

    Sannan ya aika wajen Khaulatu ‘yar Ƙaisu ya ce da ita: “Idan kina da dabino ki ba ni rance, kafin a kawo mana dabino mu biya ki”. Sannan ta ce: “An gama ya Ma’aikin Allah, uwata da ubana su zama fansa a gare ka”. Sai ta ba shi ya biya baƙauyen, har ya ba shi wani ya ci, ya ji daɗi, ya ce ka cika min Allah ya cika maka.

    Sai ya ce: “Ai waɗannan (masu cika wa mutane haƙƙoƙinsu) su ne zaɓaɓɓun mutane, haƙiƙa ba a tsarkake al’ummar da mai rauni ba ya samun haƙƙinsa cikin sauƙi daga mai ƙarfi”.

    Allahu Akbar! Ɗan’ uwa yi nazari kan wannan ƙissa dubi matsayin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) dubi kuma wane ne wannan Baƙauyen? Sannan ka dubi abin da ya faru tsakaninsu da kuma abin da ma’aikin Allah ya faɗa, lallai za ka fahimci darussa masu yawa.

    Duk al’ummar da ake rayuwar kashin dankali a cikinta, ake rayuwa irin ta rabon kura; rayuwar da uwa ba kwaɓa, uba ba harara, sai dai kowa ƙarfinsa ya ƙwace shi; maras ƙarfi kuwa sai dai ya yi Allah ya isa, to haƙiƙa wannan al’umma ko ƙasa ko gwamnati ba za ta yi wata daraja da mutunci da kwarjini ba, ballantana ta samu wani tsarki da yabo a wurin Allah da kuma mutane. Wannan zai gaggauta rushewar wannan al’umma da ci bayanta. Auna rayuwarmu a yau da wannan hadisi anya ba mu shiga cikinsa ba kuwa?

    Hadisi Na Goma Sha Ɗaya A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abu Buraida daga mahaifinsa haƙiƙa Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; “Alƙalai iri uku ne: alƙalai biyu ‘yan wuta ne, alƙali ɗaya ɗan Aljanna ne. Alƙalin da ya yi hukunci ba na gaskiya ba, yana sane wannan ɗan wuta ne. Kuma Alƙalin da ba shi da ilmi ya yi hukunci ya halaka haƙƙoƙin mutane shi ma ɗan wuta ne. Alƙalin da ya yi hukunci na gaskiya wannan ɗan Aljanna ne.
    Abu Dawud da Tirmiz da Ibn Majah ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Wannan hadisin yana bayanin matsayin alƙalai a lahira. Duk alƙalin da ya yi zalunci saboda son rai ko wata buƙata ko rashawa da aka ba shi, da kuma alƙalin da bai nuna ba, ba shi da ilmin cancantar alƙalanci aka yi abin da aka yi aka ba shi alƙalanci ya zo yana taɓargaza, waɗannan biyun ‘yan wuta ne.
    Shi kuma alƙalin da ya cancanta kuma yana adalci da gaskiya wannan ɗan Aljanna ne.
    Saboda haka alƙalai su ji tsoron Allah, su yi gaskiya da adalci, su kasance cikin karatu da bincike a kowane lokaci. Su ma masa na da alƙalai su ji tsoron Allah su rinƙa naɗa waɗanda suka cancanta su guji naɗa jiƙaƙƙun mutane don kawai sanayya ko rashawa da sauransu.

    Hadisi Na Goma Sha Biyu Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Ibn Abi Aufa (Radiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Haƙiƙa Allah yana tare da alƙali matuƙar bai yi zalunci ba, idan kuwa ya yi zalunci sai Allah ya rabu da shi sai shaiɗan ya naniƙe masa.
    Tirmizi da Ibn Majah da Ibn Hibban da Hakim ne suka rawaito shi. Sai dai a ruwayar Hakim ya ce: “idan ya yi zalunci sai Allah ya yi watsi da shi”.

    Ahmad da Bazzar da Tabarani ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Allah Ta’ala yana taimaka wa shugabanni da alƙalai masu adalci yana ba su kariya; yana rufa musu asiri ya ɗaukaka su matuƙar sun kama hanyar zalunci da rashin gaskiya; sai Allah ya yi watsi da su ya bar su da dabararsu, su yi ta ɗimuwa da shirme, ga rashin ƙima a idon mutane; sannan in suka tafi a haka, a lahira su haɗu da matsananciyar azaba.

    Hadisi Na Goma Sha Uku Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abu Huraira (Radiyallahu Anhu) daga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; “Duk wanda ya shugabanci mutane goma za a kawo shi ranar ƙiyama a ƙuƙume (ɗaure) kodai adalcinsa ya kwance shi ko kuma zalunci ya halakar da shi.

    Ahmad da Bazzar da Tabarani ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Lallai wannan hadisin tsoratarwa ne mai girma ga shugabanni da masu neman shugabanci. Babban abin tsoron shi ne; hadisin bai taƙaita a kan shugaban ƙasa ko gwamna ko sarki ba, a’a duk wanda ya yi shugabanci daga mutane goma zuwa sama, to za a zo da shi a ɗaɗɗaure ranar ƙiyama cikin kukumi wato za a haɗe hannayensa a kan wuyansa a ɗaure. A haka za a yi masa hisabi in ya yi adalci a kwance shi; in bai yi adalci ba a hakan za a nutsa shi a wuta. Allah ya kiyaye mu Ameen.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Shugabanci A Musulunci (Hadisai Tamanin Da Biyu A kan Shugabanci); wanda Shehu Mansur Dala ya waallafa shi. Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Mazajen Da Nana Khadija Ta Aura Kafin Manzon Allah (S.A.W) danna nan.

  • Hadisai A Kan Kada A Goyi Bayan Mai Laifi

    Hadisai A Kan Kada A Goyi Bayan Mai Laifi

    Hadisi Na Ɗaya A Kan Kada A Goyi Bayan Mai Laifi

    An karɓo daga Abdullahi ɗan Umar (Radiyallahu Anhu) ya ce: Na ji Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yana cewa: “Duk wanda alfarmarsa ta hana a yi wani hukunci na Allah, haƙiƙa ya kishiyanci Allah Ta’ala, kuma duk wanda ya yi husuma a kan ƙarya yana sane, zai kasance cikin fushin Allah Ta’ala, kuma duk wanda ya yi wa wani mumini ƙage, Allah zai zaunar da shi a dagwalon Khabalu (Tafkin da surƙamin ‘yan wuta yake taruwa) har sai ya janye abinda ya faɗa.
    Abu Dawud da Hakim ne suka ruwaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Wannan hadisi ya ƙunshi abubuwa uku muhimmai:

    1- Duk mutumin da ya hana a hukunta mai laifi; saboda matsayinsa to haƙiƙa ya yi daidai da mai ƙalubalantar Allah da kishiyantar sa. Wato ya mayar da kansa kamar wani kishiya ga Allah.

    2- Wanda yake ba da kariya ga mai laifi alhali ya san ba shi da gaskiya; Allah zai ta yin fushi da shi har sai ya janye jikinsa ya bar shari’a ta yi aikinta. Wannan ya haɗa da iyaye da ‘yan uwa da lauyoyi; da sukan kafe su yi ta jayayya a kan kare wanda su da kansu sun san ba shi da gaskiya.

    3- Masu yi wa mutane ƙage da sharri suna cikin babban hatsari; za a jefa su cikin dagwalon da ake tara da tafasa ruwan ciwo da ƙuraje na ‘yan wuta a ranar lahira; har sai sun daina yaɗa shi wanda tun daga nan duniya za a yi hakan in kuwa aka yi sake aka je lahira to fa sai yadda ta yiwu.

    Hadisi Na Biyu A Kan Kada A Goyi Bayan Mai Laifi

    Wani abu da yake kawo cikas ga ci gaba da nagartar kowace gwamnati da al’umma; shi ne neman alfarma da masu faɗa a ji sukan yi, domin a ƙyale masu laifi; ko kuma a sassauta hukuncin da ya dace a yi musu, ta yadda koda an yi hukuncin, sai ya zama kamar wasa. Wannan sai ya ƙarfafa guiwar ‘yan gata su yi ta tafka ta’asa son ransu; har ma aikata laifi ya zama wata burga da nuna isa, wato iya matsayinka ko gatanka, iya damarka ta aikata laifi, ka kwana lafiya. To shi me Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya faɗa kan nemawa masu laifi alfarma a ƙyale su?

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Shugabanci A Musulunci (Hadisai Tamanin Da Biyu A kan Shugabanci); wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi. Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Hadisi Na Ɗaya A Kan Haramcin Goyon Bayan Azzaluman Shugabanni danna nan

  • Yadda Ake Yin Tasbihi A Ruku’u

    Yadda Ake Yin Tasbihi A Ruku’u

    Tasbihi A Ruku’u: Mutum zai yi tasbihi a lokacin da ya yi ruku’u kamar haka; “Subahaana Rabbiyal Azim wabi hamdihi” sau uku ko kasa da uku.

    Ba zai ɗago daga ruku’u ba, har sai kowace gaɓa da ya malƙwasa ta ta koma mazaunin ta shi ne gwargwadon yadda tsayin ruku’un nasa zai zama.

    Haka kuma idan yana ɗagowa daga ruku’u zai ce “Sami Allahu liman hamidah” da zaran ya tsaya daram kuma sai ya ce,

    “Rabbana lakal hamdu ko walakal hamdu”.

    Zai tsaya gwargwadon yadda kowacce gaɓa za ta koma mazauninta kafin ya tafi sujudah.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ɗagowa Daga Ruku’u danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Sallar Alwala Da Falalarta danna nan.