Tag: ilimi

  • Yadda Ake Addu’ar Nema Wa Yara Samun Karatu Da Raba Su Da Abokanan Banza

    Yadda Ake Addu’ar Nema Wa Yara Samun Karatu Da Raba Su Da Abokanan Banza

    Wannan ita ma addu’a ce da ake karantawa domin nema wa yara shiriyar Ubangiji da samun karatu. Duk mai son Allah ya kintsa masa yara su shiryu, su zama abin koyi a wajen al’umma.

    To sai ya dinga lazumtar karanta musu wannan addu’ar a duk lokutan da ya yi aikin alkhairi; ko kuma bayan sallar asuba, sai ka karanta wannan addu’a ta Nema Wa Yara Samun Karatu Da Rabasu Da Abokanan Banza.

    Ga addu’ar kamar haka:

    Allahumma ahsin ƙulubu awladina wa akhlawahum, wa amla ƙulubahum nuran wa hikmah, allahumma dahhir ƙulubahum minar riya, allahumma hafiz farujahum minaz zina, walluwadi, wassihaƙi wa kullil jara’im. Allahummaj’alhum hafzatan likitabika, wasunnati mabiyyuka (Sallallahu Alaihi Wasallam). Allahummar zuƙ humul ƙana’ata, war ridha. Allahummar zuƙ hubbuka wa hubbub nabiyyuka (Sallallahu Alaihi Wasallam), wa hubbub kullu man yuhibbuka, allahummaftah alaihim abwaba rizƙukal halalu miin wasi’u fadlika wakfihim bihaluka an haramika wa agnihim bifadlika. Allahumma jannibhum rufaƙa’is su’i wal fawaahisha ma zahara minhu wama badan. Allahumma aafihim fi abdanihim wa asma’ihim, wa anfusihim, wa absarihim, wa jawarihim ya arhamur rahimina”.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Addu’ar Ismullahil A’azim danna nan.

  • Yadda Ake Addu’a Ga Cututtuka Ko Kuma Wata Annoba

    Yadda Ake Addu’a Ga Cututtuka Ko Kuma Wata Annoba

    Addu’a Ga Cututtuka; Wannan kuma addu’a ce da aka ce a dunga karanta ta a duk lokacin da wata annoba ta shigo.

    Idan har kana karanta wannan addu’ar, Allah zai tsare shi daga ciwon annoba na zamani, wanda aka sani da wanda ba a sani ba. Duk sanda mutum ya yi sallah ko wani aikin alkhairi, ya dunga karanta wannan addu’a (Addu’a Ga Cututtuka) kamar haka, Allah (Subahanahu Wata’ala) zai kare shi;

    Allahumma inni a’uzhubika minal barasi, wal jununi, wal juzami, wamin sayy’il asqam”.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Nauye-nauyen Rayuwar Aure danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Addu’ar Bushewar Zuciya danna nan.

  • Yadda Ake Addu’ar Bushewar Zuciya

    Yadda Ake Addu’ar Bushewar Zuciya

    Addu’ar Bushewar Zuciya – Wannan addu’ar ma akan karanta ta domin Ubangiji ya ba ka kariya daga dukkan cututtukan zamani da kuma bushewar zuciya.

    Muddin za ka yi wannan addu’ar Bushewar Zuciya; Allah (Subahanahu Wata’ala) ba zai bari ka shiga cikin wani hali na ƙunci a cikin rayuwarka ba, kuma zai tsare ka daga dukkan cututtuka na zamani wanda aka sani da kuma wanda ba a sani ba.

    Ga addu’ar kamar haka:

    Allahumma inni a’uzhubika minal ajzi, wal kasali wal jubni, wal bukhli, wal harami; wal gaflati, wal qaswati, wal ilati, waz zillati, wal maskanati; wa a’uzhubika minal faqari, wal kufri; wal fusuqa, wash shiqaq, wan nifaq, was sum’ati, war riya’a, wa a’uzhubika minas sumami; wal bukami, wal jununi, wal jazami, wal barasi wa sayyi’il asqaam”.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ma’anar Aure danna koren rubutu.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Za ki San Kanki Kafin Ki yi Aure danna koren rubutu.

  • Yadda Za Ki San Kanki Kafin Ki Yi Aure

    Yadda Za Ki San Kanki Kafin Ki Yi Aure

    Mata – Akan so kowacce mace a ce ta san kanta, budurwa ko matar aure ko kuma bazawara, wannan shi ne zai sa ki sami daraja a wajen mijinki.

    Da yawan mata, sun kasu gida huɗu kuma kowacce da hanyar da take bi gurin ta ga ta samu daraja a wajen mijinta; wata hanyar mallaka za ta bi, wata kuma hanyar gyaran jiki; wata kuma hanyar biyayya da kyautatawa, wata kuma wajen kwanciya.

    Ba laifi ba ne, in kin bi hanyoyi uku cikin huɗun nan; wajen ki ga kin samu daraja, kin zama ‘yar lele a wajen mijinki. Bin hanyar mallaka ita ce babbar illa ga mata; don kuwa ita ce ba ta lasting (ƙarko) don tana da iyaka, ba ta ɗorewa.

    Da yawa iyayenmu mata; idan za su aurar da yaransu mata, sun fi damuwa da shirin kayan ɗaki ko kuma shirye-shiryen kayan anko da irin fitar da amarya za ta yi; har ya rage wata uku kafin biki za ki ga ana koya wa ƙawayen amarya irin rawar da za su yi, don su burge ango da abokansa.

    Amma kaɗan ne cikin iyayenmu mata da suke bincikar amarya kama daga lafiyar jikinta da gyarensa; don ta burge mijinta in ta je gidansa.

    Kaɗan ne cikin ‘yan matan da idan suna da matsala suke iya bayyana ta ga iyayensu; wasu yaran sukan ɓoye ta har suje gidan miji da ita.

    Shi yasa da zarar mace ta yi aure sai ka ga kwana kaɗan namiji ya fara juya mata baya; ya fara hantarar ta, yana mata wulaƙanci, don kuwa ya rasa gamsuwar da yake son samu a wajen matarsa; don haka, iyaye ku kula sosai ku rinƙa jan ‘ya’yanku mata a jiki sosai, kuna sanin halin da suke ciki.

    Wannan shi ne zai ba ku dama ba za su rinƙa boye muku sirrinsu ba. Sanin halin da suke ciki shi ne zai ba ku damar ɗaukar mataki kafin ku kai su gidan miji.

    Mata na cewa, “Aure yaƙin mata” .

    Ki zauna da ‘yarki budurwa ki tambaye ta duk abin da yake damun ta da abin da take ji a jikinta da abinda take gani a gabanta kafin ki kai ta gidan miji.

    Kar ki kai ta gidan miji da cuta a jikinta, ya kasance shi kansa mijin ya tsani yarinyar ke kuma yana jin haushin ki.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Za ki Gyara Kanki danna koren rubutu.

  • Yadda Za Ki Gyara Kanki

    Yadda Za Ki Gyara Kanki

    Yadda Za ki Gyara Kanki. Akan so mace ta zauna kamar shinkafa a gidan mijinta; kar ki bari ya daina yinki, kar ki bari ya ƙosa dake.

    Kin san shinkafa za a iya sarrafata ta kowace irin launi. Misali; za a iya yin tuwon shinkafa, jellof, farar shinkafa, dambun shinkafa, fried rice dadai sauransu.

    Shinkafa ce za a shekara da shekaru ana cin ta a gida ba a gaji da ita ba, da zarar an yi sati ɗaya babu ita, ranar hankali ya tashi. Yara da kansu za ka ga suna cewa Daddy ba shinkafa.

    Don haka ki zama kina da dabarar iya kwanciya da mijinki, kullum da irin kwanciyar da za ki yi masa, ta yau daban ta gobe daban.

    Sai ki ga kin daɗe kina zamani a gidan mijinki, sai ki gan ki kullum amarya kike.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Abubuwan Daya Kamata A Sani Game Da Ciwon Sanyi danna nan.

  • Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Ciwon Sanyi

    Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Ciwon Sanyi

    Shi ciwon sanyi wanda Bature ke cewa (S.T.D: Sexual Transmitted Disease) yakan haddasa wa mata matsala daban-daban.

    Kama daga rashin haihuwa, ɗaukewar sha’awa, wasu kuma yakan yi yawa ya taɓa musu ƙoda ya haddasa mata ciwon da Bature yake kira kidney infection; wasu matan kuma ya cire musu sha’awa kwata-kwata.

    Irin wannan matsalar takan iya kama maza su ma, ta haifar musu da wannan matsalolin kamar yadda take haifarwa da mata.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Da Haka Na Gagara wanda Yahaya Ishaq ya wallafa shi; Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Alamomin Ciwon Sanyi Yake danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Maganin Damuwa danna nan

  • Hanyar Warkar Da Ciwon Sanyi Da Maganin Sa

    Hanyar Warkar Da Ciwon Sanyi Da Maganin Sa

    Akwai hanyoyi da mace za ta bi domin rabuwa da wannan mugun ciwon.

    Shawarar farko game da wannan ciwon za ta bi; ko da ma ba ki da wannan ciwon in har an kusa auranki tom ki guji tsarki da ruwan sanyi sannan ki rinƙa yawan yanke farcenki kina wanke hannunki; ko da zai kai ki sosa gabanki kin ga datti ba zai shiga ba.

    Ki samu waɗannan haɗin ki rinƙa wanke gabanki da su;

    • Gishiri
    • Ganyen magarya
    • Ganyen lalle
    • Kanunfari

    Waɗannan za ki rinƙa dafa su ki samo flask ki rinƙa kama ruwa da su a kodayaushe. Sannan pant ɗinki ki rinƙa dafa shi da ruwan zafi da gishiri da Dettol kina wankewa ki sanya a rana ya bushe ki goge su, sun zama sababbi kenan.

    Maganin Ciwon Sanyi

    Ki nemo waɗannan itatuwan ki dafa su dan kawar da ciwon sanyi, musamman ki fara yin su two months kafin bikinki. Da yardar Allah kin rabu da ciwon sanyi, in kin gan ki da shi to sai dai a jikin mijinki kika samu. Shi ma namijin zai iya waɗannan haɗin dan ya rabu da shi.

    Ga abubuwan da za a nema kamar haka;

    • Sayen zogale ma’ana saiwarsa
    • Kanunfari
    • Jema
    • Jar kanwa
    • Gogamaso
    • Kaimin ƙadangare ko kuma ciyawar wutsiyar ƙadangare
    • Cini da zuga, wasu na cewa bini da zugu

    Waɗannan su ne za a tafasa su sosai sai sun fita hayyacinsu sai a tace a zuba a kofi; a sa zuma a sha sau biyu a rana. In Sha Allah za a rabu da matsalar sanyi kowanne iri ne.

    Don karanta cikakken bayani akan Yadda Za ki Kare Kanki Daga Ciwon Sanyi (Toilet Infection) danna nan

    Domin karanta cikakken bayani akan Neman Aure Bisa Koyarwar Musulunci danna nan

    Edita; Rumasa’u Muhammad kallamu

  • Matakan Da Za A Bi Domin Hana Yara Shaye-shaye

    Matakan Da Za A Bi Domin Hana Yara Shaye-shaye

    Akan kai wani mataki duk irin kulawar uwa ko kuma kulawar uba ya zamto yaransu ko yarinyarta ta fanɗare.

    Ka ga yaro ya jefa kansa cikin wannan hatsarin rayuwa, yaro ya rinƙa shaye-shaye sakamakon abokai da ya gamu da su.

    Ga matakan da ake bi In Sha Allah zai daina:

    1. Matakin farko raba shi da abokan hurɗarsa a sama masa wajen sana’a.

    2. Mataki na biyu shi ne ana ɗaukan ayoyin sakina na Al ƙur’ani gaba ɗaya da kuma ayatus Sam, a karanta su a tofa a ruwan sama ko na rijiya, sannan a samu za’afaran da ganyen magarya da muski ɗan kaɗan sai a ba shi ya rinƙa sha da safe da kuma dare.

    Sannan za a iya ɗaukan dukkan nau’in kayan mayen da yake sha a haɗa su guri guda; anemo garin kustul hindi cokali uku da kuma man zaitun da man habba da kuma man kwakwa da na tafarnuwa da na’a na’a a haɗa su guri guda da kayan shaye shaye sannan a rufe a bar su su kwana.

    In gari ya waye a girgizasu sosai, sai a tace sannan a ba shi kafin ya ci abinci. Ana so da ya sha ya yi amai. Wannan haɗin ana so a rinƙa ba shi duk bayan sati uku ko kuma wata ɗaya. Sannan a haɗa da wannan ruwan da aka yi tofin ayoyin a ciki. Insha Allah duk abinda yake sha zai fita daga ransa ya dawo cikakken mutum.

    Minhaj 274
    Ayatus Sakina: Minhaj 255

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Addu’ar Haddar Karatu danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Karatun Manzon Allah danna nan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Addu’a Idan Mutum Yana Cikin Tashin Hankali

    Addu’a Idan Mutum Yana Cikin Tashin Hankali

    Wannan addu’ar za a iya karanta ta idan mutum na cikin mawuyacin hali; ko kuma mace ta rasa mijin aure; ko kuma mutum na cikin yawan bashi ko bashin gidan haya da dai sauran su. 

    An ruwaito daga Hassanul-al-basari, yace wata rana yana cikin tafiya a cikin garin Iraƙ, sai ya ga wani mutum kamar an ciro shi daga ƙabari, hankalinshi a tashe, sai Hassanul-al-basari yake tambayarshi me ya same ka? 

    Sai mutumin yake cewa; labarina akwai tashin hankali a cikinsa, da firgitarwa, amma ka yi alƙawari za ka ɓoye sirrina ba za ka sanar da kowa ba. Sai yace Hajjaj ne ya tsare ni a gidan yari shekaru uku; kuma aka hukunta za a kashe ni tare da wasu.

    Yace ina zaune wata rana a cikin gidan yari sai aka zo aka tafi da wasu mutanen da za a kashe. Bayan an zo an sare musu kai, sai aka dawo aka ce da mu gobe kuma za a kashe ku. Sai na gigice hankalina ya tashi, abinci na kasa ci saboda na san gobe kwana na zai ƙare. Ina cikin tashin hankali har na kasa bacci. Sai gab da asuba bacci ya ɗauke ni, sai na yi mafarki a cikin baccin an ce da ni; tashi ka yi sallah raka’ah biyu 2, idan ka idar da sallar ka karanta wannan addu’ar;

    “Ya manla yashgaluhu shai’un an shai’in, ya man a hada ilmuhu bima zara’a wa bara’a, anta aliun bi khafayatil umuri, muhsy wa sawisus sudur, waanta bil manzalil a’ala, wa ilmuka bil manzilil adna, ta’alaita uluwwun kabira, ya mugithu agithni, wa fukka asri, wakshif durri faƙad naƙida sabri”

    Yace sai na tashi na yi alwala a cikin halin da nake ciki na fargaba, na yi sallah raka’ah biyu 2 kamar yadda na ji a mafarkina, na haddace abinda aka faɗa min a mafarkina, ban bar kalma ɗaya ta kuɓuce min ba daga ciki abin da aka gaya min.

    Wallahi ban kai ƙarshe ba daga cikin kalmomin da na sani sai na ga wani haske, sai na ga wani mutum. Yace koda na kalla, sai na ga ƙofar gidan yarin an buɗe ta, sai kawai na ji an ce tashi ka fita. Shi ne na taso na kama tafiya, Allah ya kawo min mafita, Allah ya warkar da ni damuwa ta, sannan na samu wadata a rayuwa ta.

    Wannan addu’ar duk mutumin da ya samu kansa a cikin wata damuwa ko wani tashin hankali, ko al’amura sun caɓe masa, ya rasa yadda zai yi da kansa, to ya dinga tashi cikin dare ya yi nafila ya karanta wannan addu’ar. Da yaddar Allah, Allah zai kawo masa ƙarshen damuwarsa In Sha Allah.

    An samo wannan addu’ar a cikin littafin MUFATIHUL FARAJ shafi na 108.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Addu’a Idan Mutum Yana Cikin Damuwa danna koren rubutu.

    Don karanta bayani a kan Addu’a Gatan Mumini danna koren rubutu.

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’ar Tashi Daga Bacci

    Yadda Ake Addu’ar Tashi Daga Bacci

    An karɓo daga Aisha (Radiyallahu Anhu) tace Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam); ya kasance yana tashi daga bacci zai karanta wannan addu’a;

    Ga Addu’ar Tashi Daga Bacci kamar haka:

    “La ilaha illa anta subhanakallahumma astagfiruka li zhanbi; wa as’aluka rahmatikallahumma zidni ilman, wala tazig ƙalbi ba’ada iz hadaitani; wahab min ladunka rahmatan innaka antal wahhab” (Abu Dawud)

    Ana so duk wanda ya tashi daga bacci, na safe ne ko na rana ko kuma na yamma to ya karanta wannan addu’ar yayin da ya farka, to Ubangiji zai ba ka kariya daga duk wani abu da zai cutar da kai a ranar kuma Allah zai sa ka samu nutsuwa da wadatar zuciya.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Addu’ar Sauƙin Bashi danna nan.

    Domin karanta bayani a kan Yadda Ake Addu’ar Neman Biyan Bashi danna nan.