Category: Tatsuniyoyi

  • Ɗan Kutungayya

    Ɗan Kutungayya

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum da ke zaune awani gari mai suna Raƙumawa tare da matarsa da ’ya’yansu su goma sha ɗaya. Rannan sai matar ta haifi ɗa namiji, ya zama na goma sha biyu. Da haihuwar yaro kuwa sai ya yi magana ya ce wa uwarsa: “Kada ma a yi wahalar raɗa mini suna, domin sunana Ɗankutungayya.”

    Ya ƙara da cewa, ragon sunansa ma kada a yanka, a bar masa ya rinƙa hawa. Iyayen suka yi haka, jama’ar gari suna ta mamakin wannan yaro da abubuwan da ya yi. Ana nan, ana nan, sai wata rana yayyen Ɗankutungayya suka shirya za su gidan wata mata da suka saba zuwa gidanta hira da ’ya’yanta su goma sha biyu.

    Sai Ɗankutungayya ya ce zai bi su amma babban wansu ya hana shi bin su. Amma ya bari sai da yayyen suka tafi, sai ya bi su a baya. Da isarsu gidan, sai matar ta yi musu maraba; ta yi musu shimfiɗa, suka zauna; ta kawo musu abinci mai daɗi suka ci, suka fara hira. Amma fa duk zuwan da suke yi gidan ba su san cewa matar nan dodanniya ce ba.

    Suka zauna suna ta hira kamar yadda suka saba kullum. Kuma duk sanda suka yi barci a gidan, Dodanniyar kan tashe su, su tafi gida. Ashe duk wannan dabara ce take yi don su saki jiki da ita, wata rana ta cinye su. Kuma tuni ta yi tanadin manyan tukwanen dafa su, ta sha romo.

    To a daren da suka je tare da Ɗankutungayya ma, duk sauran sun yi barci in ban da shi. Can cikin dare sai ya ji ana wasa wuƙa sai ya ce a ransa: “A a, lafiya kuwa?” Sai ya kwanta ya yi kamar yana barci. Da aka ɗan jima sai ga Dodanniya tana sanɗa, har ta shiga wajen yara.

    Ɗankutungayya yana kallon ta, tana riƙe da wata sharɓeɓiyar wuƙa sai ƙyalli take yi. Da ya ga lallai ta nufi yayyensa, sai ya yi tari da ƙarfi. Da ta ji tarinsa, sai ta koma da sauri. Da aka jima, sai ta sake dawowa; shi kuwa Ɗankutungayya ya ƙara yin tari, ta koma. A zuwanta na uku ne fa da ta ji tarin Ɗankutungayya, sai ta ɓoye wuƙa ta leƙo ta ce: “Kai ɗan samari ba ka barci ne?

    ”Sai ya ce: “Ai ni ba na barci in ba a kan rairayin ƙorama mai sanyi ba.” Da ta ji haka, sai ta ɗauki masaki ta tafi neman rairayin ƙorama. Kafin ta dawo sai Ɗankutungayya ya fito da wata ’yar batta, ya buɗe bakinta, ya zazzago wani magani, ya matsa kusa da wutar da ta hura, ya barbaɗa maganin nan a cikin wutar, sai wani hayaƙi ya tashi.

    Da ’ya’yan Dodanniya da yayyensa suka shaƙi wannan hayaƙi, sai barcin da suke yi ya ƙara nauyi. Nan da nan Ɗankutungayya a cikin sauri irin na hatsabiban mutane ya bi ya tuɓe wa ’ya’yan Dodanniya kayan jikinsu, ya sanya wa yayyensa. Kuma ya tuɓe wa yayyensa nasu kayan, ya sanya wa ’ya’yan Dodanniya.

    Da ya gama wannan aiki sarai, sai ya kwanta, ya shiga jira. Can sai Dodanniya ta dawo, ta kawo rairayi ta ba Ɗankutungayya. Sai ya ce: “Yawwa, iya; na gode. Yanzu zan yi barci.” Da aka jima sai Dodanniya ta dawo da wata sharɓeɓiyar wuƙarta a hannu, ta iske Ɗankutungayya ya yi barci.

    Nan da nan cikin gaggawa da ƙeta ta bi duk ’ya’yanta ta yanke, tana zaton samarin da sukan je hira gidanta ne. Amma ba ta yanka Ɗankutungayya ba, saboda ta ga shi ƙarami ne. Ta ƙyale shi, da nufin ta kiwata shi ya yi ƙiba. Da Dodanniya ta fita za ta fara shirin kwashe naman da take zato ta samu, sai Ɗankutungayya ya zaro battar nan tasa ya sake barbaɗa garin maganin nasa a kan wuta.

    Kafin kifta ido, hayaƙi ya murtuke ɗaki. Cikin gaggawa ya tashi yayyensa, ya gaya musu abin da ya faru, kuma ya ce su yi maza-maza su gudu gida. Ya ce shi zai bi su da gari ya waye, kada su jira shi. Take suka sulale, suka gudu. Da gari ya waye, sai Dodanniya ta zo za ta fara tattara waɗanda ta yanka, a zatonta ’yan’uwan Ɗankutungayya ne.

    Yana ganin ta sai ya kaɗa battarsa, sai ga ragonsa ya zo ya harari Dodanniya, yana yi mata kallon raini ya ce: “To, waɗannan fa ’ya’yanki ne kika yanka. Ba ’yan’uwana ba.” Da ta lura da haka, sai ranta ya ɓaci ta yi wani ƙaraji, ta yi wuf ta kai masa bara za ta cafke shi, sai ya bauɗe.

    Ta sake rarumo shi, amma sai ya ɗare bayan ragonsa. Rago kuwa kamar ya san zancen, sai ya kama sukuwa kamar walƙiya, ya tsere mata fintinkau ya bar ta sororo a cikin baƙin ciki. Dodanniya ta ɗauko ɗan magurjinta na tsafi ta bi ’ya’yanta tana buga wa kowannensu a kai.

    Nan da nan namansu ya zama na tumakai, ta soye suka cinye ita da autarta. Daga nan ta yi alƙawari sai ta rama ƙetar da Dankutungayya ya yi mata. Bayan ’yan kwanaki, sai Dodanniya ta je bakin garin su Ɗankutungayya ta rikiɗe ta zama kanya kuma ta kwanta ’ya’ya da yawa, har sun kusa nuna.

    Da yaran gari suka ga kanyar sai suka yi murna. Da ta nuna, sai wasu daga cikinsu suka dinga kaɗo ’ya’yan suna sha. Har dai wata rana yara da yawa suka hau kanta suna ɗiba. Da Dodanniya ta ga haka sai ta tashi sama da su, ba ta tsaya ba sai a gidanta. Nan da nan ta gaya wa autarta cewa nama ya samu.

    Sai ta umarce ta da ta wanke tukwane. Tana kuwa cikin wanke tukwane sai Ɗankutungayya ya ji labarin abin da ya faru, sai ya rikiɗa, ya zama ɗanmaraki, ya je gidan Dodanniya. Da zuwansa sai ya fara cin shuke-shuken da ke gidan, watau dai yana yi mata ɓarna. Yana cikin wannan ɓarna sai Dodanniya ta ce wa yaran da ta sato, su je su kori ɗan marakin mai yi mata ɓarna.

    Da ya ga sun doshe shi, sai ya ƙi gudu; amma da suka zo dab da shi, sai ya ɗan gudu ya ɗan matsa gaba kaɗan kuma ya ci gaba daɓarna. Yara kuma suka ɗan matsa kusa da shi, ya ɗan ƙara gaba kaɗan. Haka dai ya dinga jan su, har sai da suka yi wa Dodanniya nisa. Sai ya rikiɗa ya zama mutum, ya ce da yaran nan su hanzarta su gudu.

    Ya jaddada musu cewa idan ba su gudu ba, Dodanniya za ta cinye su. Da suka ji haka, sai suka sheka da gudu, suka koma garinsu, suka gaya wa iyayensu abin da ya faru. Shi kuwa Ɗankutungayya sai ya hau ragonsa, ya koma gidan Dodanniya. Da ya tabbatar ta gan shi, sai ya yi mata gwalo ya ce mata: “Na kuɓutar da yara daga sharrinki, sun koma wurin iyayensu.

    Ni ne Ɗankutungayya na yi miki gayyar tawa, wadda ba za ki iya ramawa ba har abada.” Wannan abu da Ɗankutungayya ya yi wa Dodanniya da maganar da ya gaya mata, suka sa ta shiga tunani da ƙulla yadda za ta ɗauki fansa a kansa. Ana nan, sai Dodanniya ta rikiɗa, ta zama mace kyakkyawar gaske, ta ɗauki wani adudu ta je cin kasuwa.

    Masoya suka yi ta kanta, kowa yana so ya aure ta amma ta ce ba wanda za ta aura, sai wanda ya buɗe wannan adudun. Samari da yawa suka gwada, amma duka suka kasa. Bayan ’yan kwanaki, har samari sun fidda rai, sai ɗaya daga cikin yayyen Ɗankutungayya ya ji labari, ya bincika inda take a kasuwa ya je kuma ya gan ta, sai ya ji yana son ta.

    Ita kuma Dodanniya ta gane shi, saboda haka sai ta yi tsafi ta yadda idan ya gwada buɗe adudun zai buɗe. Da zuwansa kuma ya gwada sai adudun ya buɗe, mutane suka yi ta mamaki, shi kuma ya yi murnar samun kyakkyawar mata. Aka ɗaura aure, ba ta jima ba ta tare a gidansa.

    Amma bayan ’yan kwanaki sai ta ƙwakwale wa mijin ido ɗaya, ta tafi da shi ta bar shi da jinya. Ɗankutungayya da jin wannan aika-aikar ya tabbatar da cewa Dodanniya ce. Don haka ya ƙudiri aniyar sai ya ɗauko fansar abin da ta yi wa yayansa. Sai ya rikiɗa ya zama Bafulatana, ya ɗauki nono, ya je gidanta talla.

    Da isarsa sai autar Dodanniya ta fito ta saya. Shi kuma ya yi mata araha. Kullum sai ya kai tallar nono, Dodanniya ba ta gane gogan ne ba. Da haka har Dodanniya ta saba da Bafulatana ƙwarai da gaske. Wata rana sai Bafulatana, watau Ɗankutungayya ya zo gidan Dodanniya a fusace.

    Dodanniya ta tambayi Bafulatana dalilin fushinta, sai ta ce: “Wani mutumwai shi Ɗankumale yake zuwa yana kashe musu shanu. Ga shi yanzu duk sun kusa ƙarewa.” Dodanniya ta ce: “Ke ba sunansa Ɗankumale ba, sunansa Ɗankutungayya. Mugun mutum ne.

    Ba shanunku kaɗai ba, ku kanku ma ku yi hankali da shi. Ni ’ya’yana goma sha ɗaya ya sa na kashe. Kwanan nan ma na kusa makantar da ɗan’uwansa. Kin ga idon yayansa da na ƙwakule.” Sai Bafulatana ta ce: “Tir, da ganin idon lalatacce.” Sai Dodanniya ta ce: “Yau saura kwana uku ma in ba kyanwata idon mugun ta cinye.”

    Bafulatana ta ce: “Kash, da idon nan zai yi wa ƙanena daidai da kin ba ni shi. Shekaran jiya saniya ta harbi idonsa ɗaya ya fashe ya tsiyaye.” Cikin ɗoki da ƙeta Dodanniya ta ce: “Af, don wannan ai sai in ba ki.” Da jin haka sai Bafulatana ta yi farat ta ce: “Ai ko na gode.” Dodanniya ta ƙara yi wa Bafulatana gwaninta, sai ta gaya mata yadda za ta sa masaidon ta ce:

    “A nemo ƙwaiƙwayen kifi guda bakwai da hantar baƙin kare, da ƙiyashi guda bakwai da ƙaucin maƙe, a shanya su bushe, sai a niƙa, a rinƙa sa masa a gurbin idon har kwana uku. A rana ta huɗu, sai a sa idon, zai zauna daram.” Bafulatana, watau Ɗankutungayya, ta amshi ido, ta yi godiya.

    Da ta gusa kaɗan, sai ta tuɓe kayan Fulani, sai ga Ɗankutungayya ya bayyana. Sai ya yi wa Dodanniya gwalo, ya ce: “Kin ga, ni ne Ɗankutungayya.” Sai ya yi wani hatsabibanci ya ɓata, Dodanniya ta daina ganinsa. Bai tsaya a ko’ina ba sai gida. Da ya isa ya yi yadda Dodanniya ta kwatanta masa, idon yayansa kuma yazauna daram, kamar ba a taɓa ƙwakule shi ba.

    Rannan kuma sai Dodanniya ta rikiɗa ta zama kyanwa. Ta kama hanya ba ta tsaya ko’ina ba sai a gidan su Ɗankutungayya. Da shigarta sai ta iske shi yana barci; sai ta lafaba, har ta kai kusa da shimfiɗarsa. Sai ta yi wani ƙaratu irin na tsafinta, ta tofa masa a fuska, sai ya zama ɓera sai ta ɗauke shi ta kai gidanta, ta sa shi a ƙuryar ɗaki.

    Daga nan ta yi masa wani tofin, ya koma mutum.Ita kuma ta rikiɗa ta zama mutum. Sai ta harare shi, fuskarta murtuk, tana cike da fushi, ta ce: “Ɗankutungayya, yau fa ga ni ga ka, ƙaryarka ta ƙare.” Ɗankutungayya bai tsorata ba, kuma bai ce mata komai ba. Can da Dodanniya ta ɗan huta, sai ta sa autarta tsaron Dankutungayya, ita kuma ta kama hanyar kasuwa sayen kayan yaji wanda za ta dafa shi da shi.

    Tafiyarta ke da wuya sai Ɗankutungayya ya yi wa ’yar auta dabara, ya karɓi kayan jikinta ya sa, ita kuma ya sanya mata nasa. Can sai ya ji motsin Dodanniya ta dawo, ya zabura, ya tarye ta yana ƙwaikwayon maganar ’yar auta, yana yi mata maraba. Bayan wani ɗan lokaci kuma sai ga ’yar a cikin kayan Ɗankutungayya, tana yi mata maraba.

    Sai Ɗankutungayya ya dubi Dodanniya ya ce mata: “Ga munafukin nan Ɗankutungayya yana nuna wa wai shi ne ni ’yar autarki har da cewa, ‘Sannu da zuwa inna’. Yau dai ƙaryarsa ta ƙare.” Sai Dodanniya ta ce: “Lallai kam; bar ni da lalatacce!” Nan take ta yi wuf, ta shaƙo ’yarta, ta sa wuƙa ta yanka.

    Tana gamayanke autarta, sai Ɗankutungayya ya buga tsalle gefe, ya kwance zannuwan da ya ɗaura, ya dubi Dodanniyar nan ya ce: “’Yar auta kika yanka, ni ko ni ne Ɗankutungayya, gwanin gayya. Na yi miki gayyar tawa!” Yana gama faɗa mata haka sai ya yi wal, ya ɓace. Dodanniya ta kama ’yarta ta tuɓe kayan jikinta, sai ta ga lallai kuwa autarta ce ta yanka. Nan take sai ta haɗiyi zuciya ta mutu.

    Kurunkus.

    Abubuwan DaLabarin Yake Koyarwa 

    • Kaunar juna da son ’yan’uwa kan ƙara danƙon zumunci. *
    • Mugunta fitsarin faƙo ce kan wanda ya yi take komawa.
    • Dan’uwa rabin jiki.
    • Kaiƙayi koma kan masheƙiya.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Musare Da Hodanego

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Musare Da Hodanego

    Tatsuniyar Musare Da Hodanego

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wani mutum mai mata biyu, da ’ya’ya biyu. Uwargidan tana da ɗanta mai suna Musare; amaryar kuma tana da ’ya wai ita Hodanego. Ana nan har yara suka girma. To da ma shi mahaifinsu yana da dabbobi masu yawa, sai ya ba Musare Akuya guda, ita kuma Hodanego da take ƙarama, ya ba ta Kaza.

    Suna nan, duk sanda Musare ya nemo wa akuyarsa abinci ya zuba mata, sai Hodanego ta saki kazarta ta je ta watsar da abincin. Kullum haka, har dai rannan yunwa ta kashe akuyar Musare. Ya yi haƙuri bai ce komai ba, amma kuma sai kullum ƙanwar ta riƙa yi masa dariya, tana tsokanar sa.

    Daga ƙarshe dai sai ya ɗan yi magana, sai uwar Hodanego ta kama shi da duka. Amma saboda kara irin ta matan kirki, mahaifiyarsa ba ta ce komai ba. Wata rana sai uwar Musare ta kwanta ba lafiya, har jikinta ya fara ruɓewa ta fara wari, sai kishiyarta ta fara yi mata tsiya da ’yan maganganu, har da zagi tana cewa ita fa wari ya fara damun ta a gidan.

    Haka dai, kullum sai Musare da mahaifiyarsa su shiga ɗaki su yi ta kukan baƙin ciki. Da ciwo ya tsananta, sai ta ce da shi: “Ka tashi ka shiga dajin nan ka nemo mini magani.” Sai ya ce da uwar: “To.” Washe-gari da sanyin safiya ya fita, ya kama hanyar dajin don nemo magani.

    Yana cikin dokar daji sai ya haɗu da wata tsohuwa ita kaɗai tana dogara ’yar sanda. Da ta ji motsinsa sai ta ce: “Don Allah ɗan nan ka taimake ni ka ɗora ni kan hanya wadda zan bi
    in shiga gari.” Sai ya dube ta cikin murya lallausa ya ce: “Ayya, ai kin baro hanyar da nisa, amma bari in kai ki.”

    Tsohuwa ta ce: “Yawwa, na gode.” Ya shiga gaba, tana biye da shi har suka isa hanya. Sai tsohuwa ta ce da shi: “Ɗana da ma ina so in gwada kirkinka ne, kuma zan taimake ka a kan abin da ka fito nema.” Mamaki ya kama Musare, sai ya ce: “To.” Sai tsohuwa ta ci gaba da yi masa bayani tace:

    “Ka bi wannan hanyar, kada ka tsaya har sai ka tarar da wata babbar tsamiya, sai ka tsuguna a gindinta ka roƙi duk abinda kake so.” Musare ya yi mata godiya, ya bi inda ta nuna masa har ya isa gindin tsamiyar da ta kwatanta masa. Musare na isa ya tsuguna, ya roƙi maganin ciwon da ke damun mahaifiyarsa.

    Sai kawai ya ga ƙullin magani ya faɗo daga wata sheƙa da ke kan tsamiyar. Ya ɗauka ya yi
    kamar zai miƙe tsaye, sai ya ji an ce: “Idan kana da wani abu da kake buƙata, ka tambaya a ba ka.” Ya waiga bai ga kowa ba, amma sai ya ce: “Ciwon da ke damun uwata ne kan gaba da komai; maganin nan ma ya isa. Na gode.”

    Kafin ya gama rufe baki sai ya ga an fito masa da wani Doki ya sha ado da gwalagwalai da kayan sa wa iri-iri da dukiya mai yawa, sai ya ji an ce: “Dokin da kayan nan duka naka ne.” Ya sake dubawa bai ga kowa ba, sai ya sake yin godiya. Da ya lura dai an sallame shi, sai ya ɗare kan Doki, ya kama hanya bai zame ba sai gida, ya shiga ya ɗaure Doki, ya doshi ɗakin mahaifiyarsa.

    Da ya shiga ɗakin sai ya tarar saboda ƙarfin maganin da aka ba shi, har mahaifiyarsa ta warke. Sai ya ba ta labarin yadda suka yi da tsohuwa. Ita kuma ta gaya masa cewa kishiyarta ma bayan tafiyarsa ta kamu da irin ciwon. Mahaifiyarsa ta yi masa godiya, kuma ta umarce shi da ya kai wa kishiyarta maganin ita ma ta sha.

    Nan take ya ɗauki maganin ya fita tsakar gida, ya kira Hodanego ya ba ta maganin ta kai wa mahaifiyarta. Da kishiyar uwar ta karɓi maganin ta sha, kuma nan take ta warke. Wannan lamari ya sa ta shiga cikin wani hali na jin kunya, sai kawai ta fashe da kuka, ta tashi ta shiga ɗakin uwar Musare tana ba ta haƙuri.

    Ita kuma ta ce da ita ta yafe mata. Da haka suka ci gaba da zama gidan mijinsu, kamar ya da ƙanwa, ba sauran kishi. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kyakkyawar tarbiya jari ce ga mai ita; sai mai tarbiyar ƙwarai ne yake yin afuwa.
    • Idan ka ga mutum mugu kuma maƙetaci to dama ba shi da tarbiya.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Marayu Biyu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Marayu Biyu

    Tatsuniyar Marayu Biyu

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wani mutum shi da matarsa suna zaune cikin farin ciki a wata ’yar unguwa ta mafarauta da ke bakin wani daji. Suna nan sai matar ta sami juna biyu. Bayan’yan watanni ta haifi ɗa namiji. Uwar da mai gidanta suka yi murna ƙwarai, zaman daɗi ya karu a tsakaninsu.

    Bayan matar ta yaye wannan ɗa na fari, sai kuma ta sake samun ciki, amma kuma sai mai gidanta ya rasu kafin ta haihu. Haka dai ta ci gaba da renon yaron da abinda ke cikinta, har Allah ya sa ta haihu lafiya. A haihuwa ta biyukuma ta sami mace.

    Tana zamanta da ’ya’yanta, kullum suna wasansu da’yar ƙiriniyar ƙuruciya irin wadda ba a rasa ba, sai ita ma ciwon ajali ya kama ta. Ta kwanta jinya, sai ta kira ɗanta tace da shi: “Jikina yana gaya mini ciwon nan ba na tashi ba ne.

    Don haka ga ƙanwarka nan, ba ta da kowa a duniyar nan sai kai, ka kula da ita.” Sai ya ce da uwar: “Zan yi bakin ƙoƙarina.” Bayan ’yan kwanaki kaɗan sai ta ce ga garinku nan. Yaran nan ƙanana su biyu suka zama marayu, da ma kuma duk dangin iyayensu sun mutu. Suka zama dai ba su da kowa.

    Duk da cewa yaron nan bai gama ƙwari ba, amma a kullum da safe sai ya shiga daji ya farauto ƙananan dabbobi, ya tsinko ’ya’yan itatuwa su ci, su ƙoshi shi da ƙanwarsa. Haka dai ya ci gaba da renon ƙanwarsa; duk sanda ta fara kuka irin na yarinta, sai ya shiga yi mata waƙar lallashi, yana cewa:

    “Yi shiru ’Yar’auta,

    Ba ni da kowa sai ke,

    Ba ki da kowa sai ni.

    Baba ya tafi tun bara,

    Iya ma ta tafi tun bara,

    Kuma ba su dawo ba.

    Ba dangin uwa, balle na uba,

    Yi shiru ’Yar’auta,

    Yi shiru ƙanwata.”

    Duk sanda ta ji ya yi mata wannan waƙa sai tayi shiru, komai zafin kukan da take yi. A duk lokacin da zai fita daji farauta kuma sai ya ɓoye ƙanwar har ya je ya dawo, kullum haka wata da watanni, har dai ya saba da namun daji, kuma sun lura yakan zuba wani abincin da ya samu a daji a cikin jakarsa ya tafi da shi ƙauyensu.

    Wata rana da ya je farauta ya gama, sai namun daji suka tsare shi da hira. Suna cikin hira sai Zaki yace da shi: “Amma kullum na ga idan ka sami abinci, kakan tafi da shi a jakarka. Ina kake kai wa ne? Ko kana da iyaye ne da kake kai musu?” Sai yaro ya ce ai ba shi da kowa illa ƙanwarsa ɗaya da iyayensu suka rasu suka bar su tare, ya kare da cewa: “Ita nake kai wa abincin nan.”

    Jin wannan bayani ya sa duk suka tausaya masa. Sai ya yi ban kwana da su, ya tafi gida. To ashe Kura ta laɓe ta ji abin da ya faɗa. Wata rana yaro ya tafi farauta kamar yadda ya saba, sai Kura ta laɓaɓa ta je gidansu, ta gano inda ya ɓoye ƙanwarsa ta kama ta ta cinye.

    Da ya dawo gida ya nemi ƙanwarsa inda ya ɓoye ta domin ya ba ta abinci, sai bai gan ta ba, ya kama kuka, ya dai ƙara bincikawa ko ya ganta, amma abin ya ci tura. Amma da ya ɗan duba bayan daki, sai ya ga jini-jini a inda Kura ta cinye ta. Ganin haka ya sa ya koma daji, ya tara namun daji yana tambayar su wanda ya cinye masa ƙanwa daga cikinsu.

    Duk namun dajin da ke wurin kowanne ya ce ba shi ya cinye masa ƙanwa ba. Sai Kurege ya ba Zaki shawara yace: “Ya shugabanmu, ni ina ganin abin da ya kamata ka yi shi ne duk naman dajin da ya je shan ruwa bakin rafi ka tsaya a wurin ka sa ya amayar da abin da ya ci mu gani.”

    Zaki ya amince da wannan shawara, sauran namun daji ma suka yi murna da ita. Da kowa ya yi amai a bakin rafi ba a ga wanda ya yi aman yarinya ba. Har za a baje kowa ya kama hanyarsa, can sai aka ga Kura ta taho tana ɗingishin ƙarya, wai ba ta da lafiya.

    Sai aka gaya mata abinda ake yi, sai ta ce: “Ni da ba ni da lafiya, tun safe ban ci komai ba, balle in yi amai.” Da namun daji suka ji haka sai suka yi shiru. Can sai Kurege ya dubi Zaki ya ce: “Manyan Dawa, da gaskiya ne ba ta ci komai ba, me ya sa za ta zo shan ruwa?Karya take yi; ai dole ta kakaro aman ko da cikinta ba komai.”

    Duk sauran namun dajin nan sai suka ce da Zaki maganar Kurege gaskiya ce. Sai Zaki ya harari Kura, ya daka mata tsawa yace: “Dole sai kin yi amai mun gani; idan ba haka ba kuwa yanzu in kashe ki, mu cinye namanki.”

    Nan da nan Kura ta yi amai, sai ga yarinyar ta fado. Da yaro ya ga Kura ta yi aman ƙanwarsa sai ya ce: “Shi kenan, gaskiya ta tabbatar cewar da aka yi Kura ma-ci amana ce.” Kafin ka ƙifta ido sauran namun dajin nan sun far mata, suka yagalgala ta. Shi kuma yaro ya ɗauki ƙanwarsa, ya wanke ta, sai ga ta ta tashi sumul kamar ba a taɓa ta ba, sai ya sa ta a gaba suka kama hanyar gida.

    Haka ya yi ta renon ta har ta girma, aka aurar da ita. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Gaskiya dokin ƙarfe ce.
    • Karya fure take ba ta ’ya’ya.
    • Macuci ƙarshensa kunyata da halaka.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Wata Mata Da Aljani

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Wata Mata Da Aljani

    Tatsuniyar Wata Mata Da Aljani

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wata mata a wani ɗan ƙauye, wadda ta jima tare da mijinta, amma ba su sami haihuwa ba. Sun nemi maganin samun haihuwa, amma ba su sami biyan buƙata ba, sai suka dangana.

    Ana nan, ana nan, wata rana matar ta je gona tana noma, sai ta ji kukan yaro a gindin wata bishiya. Da ta matsa kusa, sai ta ga wani jariri a cikin tsumma, sai ta ɗauke shi ta goya, ta kuma ɗauki fartanyarta, ta koma gida.

    Da mijinta ya dawo sai ta ɗauko jariri ta kawo masa, tace da shi: “Da man ina da kwantaccen ciki, shi ne yanzu ka ga na haihu a gona.” Mijin ya yi shiru, yana tunani, sai ya ce: “Anya kuwa ke ce kika haifi jaririn nan?” Ta dage cewa ita ce ta haife shi.

    Sai ya ce: “To mun gode wa Allah.” Suka ci gaba da renon yaro, amma duk sanda suka je gona da shi sai ya riƙa kuka ya hana su aiki. Da matar ta ga haka na faruwa kullum, sai ta je cikin danginta ta ɗauko ƙanwarta domin ta riƙa renonsa a gida idan sun tafi gona ita da mijinta.

    Rannan mai gida da matar suka tafi gona suka bar yaro a hannun mai reno. Can sai mai reno ta ga yaron ya rikiɗa, ya zama babban mutum, sai ya yi aman ’yan mata goma sha biyu. Ya buɗe rumbu, kuma ya fito da hatsi suka sussuka suka niƙa, sai ya kwashe garin ya barbaza shi a tsakar gidan; sai kuma ya haɗiye ’yan matan, ya rikiɗa ya koma ƙaramin yaro.

    Can da mai gida da matar suka dawo, suka ga ɓarnar da aka yi musu, sai matar ta kama ƙanwarta da duka wai ta yi mata ɓarna. Yarinya tace ba ita ba ce, yaron ne. Sai yayarta ta ce: “Ta yaya wannan ƙaramin yaro zai buɗe rumbu, ya ɗebo hatsi, ya sussuƙa shi ya niƙe ya zubar?” Ba su dai yarda da bayanin yarinyar ba.

    Haka dai, kullum idan sun fita sai ya yi wata ɓarna, kuma sai matar nan ta doki ƙanwarta. Wata rana matar ta kama ƙanwar tana duka akan ɓarnar da yaron ya yi, sai wata tsohuwa ta kira ta tacemata: “Wannan duka da kike yi wa ƙanwarki fa ba ta da laifi.

    Wannan yaron da yake gidanku ba ki sani ba tsohon aljani ne kika kawo gidan.” Mamaki da tsoro suka kama matar, amma sai tsohuwar ta ci gaba da bayaninta tana cewa: “Idan kina son ki tabbatar, gobe kada ku je gona; bayan gari ya waye ku fita ku ce za ku gona; sai ku zo ku ɓuya a gidana, za ku ga komai da idanunku.”

    Sai ta ce: “To. Allah ya nuna mana goben.” Da gari ya waye mijin da matar suka shirya, kamar za su gona. Da suka fita sai suka ɓuya a gidan tsohuwa. Bayan wani ɗan lokaci sai suka ga yaron ya rikiɗa, ya zama babba; suna gani ya buɗe bakinsa ya yi aman ’yanmata goma, nan da nan ya hau rumbu ya buɗe ya ɗebo hatsi, nan take ’yan matan nan kuma suka sussuƙe hatsin, suka niƙe shi, suka shiga watsar da garin a cikin gida, suna yi suna waƙa.

    Da matar ta ga abin da yaron ya yi sai ta gaya wa mijinta gaskiya da cewa, ai da ma ba ɗanta ba ne, kuma a gona ta tsince shi. Sai mijin ya ce: “Tun farko daman na yi shakka, ga shi ta tabbata ƙarya kika yi mini.” Sai ta faɗi tana kuka, ta shiga hurwa tana ba shi haƙuri, tace: “Ai da wannan ɗa, gara mu zauna babu.”

    Da tsohuwa ta ga abin da ke gudana tsakanin mijin da matar, sai ta ce: “Yanzu abin da za ku yi domin ku rabu da wannan masifa shi ne, ku samo akuya da ƙwaikwaye guda
    bakwai, sai ku ce za ku je ganin gida. Bayan kun kama hanya kun shiga daji, sai ku sami gindin tsamiya ku ce za ku huta.

    Idan kun shimfiɗe yaron sai ku ajiye ƙwaikwayen nan bakwai a gefensa ku ɗaure akuyar a jikin tsamiyar. Can sai ku ce kun yi mantuwa.” Ta ce da su: “Kuna jin abinda nake faɗa?” Suka ce: “Muna ji sarai.” Ta ci gaba da ce wa matar: “Ki ce za ki koma gida ki ɗauko abin da kika manta.

    Daga nan kada ki dawo. Jim kaɗan shi ma mijinki sai ya ce zai bi sawunki saboda kin daɗe. To idan kun tafi kada ku koma; da zarar ya ga kun daɗe zai tashi ya tafi abinsa”. Sai suka yi wa tsohuwa godiya suka koma gida. Da gari ya waye sai matar nan da mijinta suka ce za su ganin gida, sai suka samo duk abubuwan da tsohuwa tace su nemo.

    Da lokacin tafiya ya yi sai suka kama hanya har suka isa gindin wata tsamiya, sai mijin yace ya kamata su huta a nan; suka ɗaure akuya a gindin bishiya suka zauna, can sai mijin ya ce: “Kash!, mun yi mantuwa.”Sai matar ta ce: “To bari in je in ɗauko.”

    Mijin ya ce: “To gara ki yi sauri.” Bayan matar ta tafi, sai ya ce ta daɗe, bari ya bi sawunta. Shi ma ya tashi ya bar wurin. Da ya yi nisa sai ya ɓuya. Yana nan yana kallon gindin tsamiya, can sai ya ga yaro ya rikiɗa ya zama tsoho tukuf da sanda; sai ya kunce akuyar, ya riƙe a hannunsa; kuma ya ga ya ɗebi ƙwaiƙwayen nan bakwai ya kama hanya ya shiga ƙungurmin daji.

    Da mijin nan ya ga haka, sai shi ma ya juya, ya kama hanyar gida. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa
    • Ƙarya da ha’inci masifu ne da ke iya ɓata zamandaakadaɗe cikin amana.
    • Neman afuwa da lafiya su ne kaɗai ke iya magance matsala a zaman amana.
    • Tsintacciyar mage ba ta yin kyanwa.
    • Ƙarya fure take, ba ta ’ya’ya.
    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.
    Danna nan don karanta Tatsuniyar Makauniya Da Ɗanta
    Edita@rumasau-kallamu
  • Tatsuniyar ‘Yar Mowa Da ‘Yar Bora

    Tatsuniyar ‘Yar Mowa Da ‘Yar Bora

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A wani gari an yi wani mutum mai mata biyu da ’ya’ya biyu, ’yan mata; ɗaya sunanta ’Yar Mowa, ɗayar kuma ’Yar Bora. Suna nan, ran nan sai mijinsu ya rasu. Bayan ɗan wani lokaci kuma sai uwar ’Yar Mowa ta rasu, ta bar uwar ’Yar Bora kaɗai. To da ma kafin ta rasu, ta kira kishiyarta tace mata: “Don Allah ga amanar ’yata nan; ki kula da ita.”

    Sai tace: “To.” Amma da ta rasu sai uwar ’Yar Bora ta fara ganawa ’Yar Mowa azaba. Kullum ita ke yin hidimar gida, ba ta da lokacin hutawa. Wata rana da gari ya waye sai aka ga ’Yar Bora ta yi fitsarin kwance, amma sai uwar ’Yar Bora ta ce ai ’Yar Mowa ce ta yi. Saboda haka ta matsa mata sai ta je Rafin Bagaja ta wanke shimfiɗar da aka yi wa fitsari.

    To Ruwan Bagajar nan kuwa yana cin mutane. Amma tunda ba yadda ta iya, sai ta ɗauki shimfiɗa ta kama hanyar rafi. Tana cikin tafiya a daji da ta ga rafi sai ta kama waƙa tana cewa:

    “Kogi, kogi,

    Ko kai ne Ruwan Bagaja,

    Bagajar kauye da ’Yar Sarki,

    Da ’Yar Bora ta yi fitsari,

    Aka ce ni ce,

    Sai na wanke

    A Ruwan Bagaja.”

    Tafiyar ‘Yar Mowa Sai kogi ya ce: “Ni ba ni ne Ruwan Bagaja ba. Ni Ruwan Madara ne. Idan za ki zauna ki sha to.” Sai ta ce ta gode; taci gaba da tafiya. Can sai ta tarar da wani ruwan, sai ta sake maimaita waƙar da ta yi. Sai kogi ya ce mata shi Ruwan Zuma ne. Idan tana so ta zauna ta sha. A nan mata ce ta gode, ta ci gaba da tafiya.

    Sai ta tarar da Kogin Shinkafa da Kaji, sai ta rera waƙar nan, kogi yace mata: “Ni Kogin Shinkafa da Kaji ne. Idan kina so ki zauna ki ci.”A nan ma ta yi godiya, ba ta ci ba; ta yi gaba. Jim kaɗan kuma sai ta tarar da Ruwan Jini. Bayan ya ji bayaninta a cikin waƙa, sai ya ce: “Ni ba Ruwan Bagaja ba ne. Ni Ruwan Jini ne. In za ki sha to.”

    Sai ta ce ta gode ta yi gaba. ’Yar Mowa dai ba ta gaji ba, ta ci gaba da tafiya har ta tarar da wani ruwan. Da ta yi irin waƙar da ta saba sai yace: “Ni ne Ruwan Bagaja; amma ke kuwa wannan yarinya me ya kawo ki wurina inda ba a zuwa?” Sai ta feɗe masa biri har wutsiya a kan abin da ya faru da irin halin da take ciki bayan rasuwar mahaifiyarta.

    Da Ruwan Bagaja ya ji sai ya ce: “To ai sai ki wanke a nan.” Nan take ta yi godiya, ta tsuguna ta wanke shimfiɗa, amma kafin ta gama har dare ya yi. Da ta gama, ta tashi za ta tafi sai kuma ga hadari ya taso, amma kuma ga babu wurin fakewa. Can sai ta hango wata ’yar bukka, ta ko nufi wurinta ta fake.

    Tana zaune a ciki, sai ta ga wata fitila ta kunna kanta da kanta, mamakin wannan ya kama ta, sai kuma ta ga cinya a gefeɗaya. Kafin ta gama mamaki sai kuma ta ga kai shi kaɗai a gefen cinya yana motsi. Sai cinya ta ce da ita: “Kai yanayi miki maraba.”
    Can kuma sai cinya ta yi nata motsin, sai kai yace da ita: “Cinya ma tana yi miki maraba da zuwa.”

    Duka dai yarinya tana amsawa da cewa: “Na gode da wannan maraba.” Suna nan zaune, sai kai ya yi wani motsi, sai cinya ta ce da yarinyar: “Wai yunwa yake ji; ki ɗauki
    wancan kwanon ki ba shi abinci.” Ba tare da wani musu ba, ’Yar Mowa ta tashi ta zuba masa abinci, ta zauna kusa da shi da abincin a kan cinyarta har ya ci ya ƙoshi.

    Sai ya sake yin wani motsin, sai cinya tace da yarinyar: “Wai ki ba shi ruwa.” Nan da nan ta ba shi ruwa. Suna zaune a haka, can sai ga wani wafcecen kumurci ya shigo, amma kuma ba ta ji tsoro ba. Jim kaɗan sai ta ga macijin ya fara aman ƙwaiƙwaye. Ya amayar da uku ƙanana, daga baya ya yi aman wasu manya uku.

    Da ya gama, sai cinya ta yi wani motsi, sai kai ya ce: “Wai idan gari ya waye za ki tafi, ki zaɓi ƙwaiƙwaye uku ki tafi da su, kuma kada ki fasa sai kin isa kusa da garinku.” Ta ce: “To. Na gode, Allah ya kai mu goben.” Da gari yawaye, sai ’Yar Mowa ta tsuguna ta zaɓi ƙwaiƙwaye uku, amma kuma ƙanana ta zaɓa. Ta kama hanya tiryan-tiryan, ta doshi garinsu.

    Sakamakon ‘Yar Mowa 

    Da ta isa bayan gari, sai ta fasa ƙwai ɗaya, sai ta ga ingarman doki da adon kayan ƙawa da sauran kayan alatu iri-iri. Da ta fasa ƙwai na biyu kuma, sai ta ga ’yan mata gomiya goma suna ɗauke da kayan ado da kayan sa wa iri-iri. Da ta fasa ɗayan, sai ga dukiya har da gida ƙerarre, da duk abin da za a nema don jin daɗin duniya a ciki.

    Sai ta yi godiya ga Allah, ta taka ta hau dokin nan, ba ta zame ko’ina ba sai a ƙofar gidansu. Da kishiyar uwar da ’Yar Bora suka gan ta da dukiya da kwalliya kamar sarauniya, sai kishiyar uwar ta nemi sanin yadda ta sami wannan abu haka. A nan ta ba ta labarin zuwanta Ruwan Bagaja, har zuwa inda ta fasa ƙwaiƙwayen nan guda uku. Sai uwar ’Yar Bora ta ce ita ma sai ’yarta ta je washegari, ita ma ta samo nata.

    Tafiyar ‘Yar Bora

    Washe-gari tun da duku-dukun safiya, uwar ’Yar Bora ta tura ta wai don ta je ta wanke shimfiɗa a Ruwan Bagaja. Ita kuwa ta kama hanya. Da ta je Ruwan Madara sai ta yi
    waƙa kamar yadda ’Yar Mowa ta yi. Sai ruwan yace, “Ni Ruwan Madara ne, ba Ruwan Bagaja ba. Amma in kina so, ki zauna ki sha.”Sai ta ce: “To.”

    A nan ta zauna, ta sha madara har sai da ta ƙoshi. Ta tashi ta yi gaba, ko godiya ma ba ta yi ba. Da ta tarar da Rafin Shinkafa da Kaji, sai ta yi masa waƙa. Sai ya ce shi ba Ruwan Bagaja ba ne, Ruwan Shinkafa da Kaji ne; idan za ta ci, ta zauna ta ci. Sai ’Yar Bora ta ce: “Ai ko ba ka faɗa ba zan ci”. Sai tazauna ta ci har ta ƙoshi.

    Ta sami ruwa ta kwankwaɗa, ta yi gaba. Da ta isa Ruwan Jini sai ya ce shi ba Ruwan Bagaja ba ne, shi Ruwan Jini ne. In za ta sha to. Sai ta yi masa gatsine, ta bugi cinya irin yadda masu tsiwa kan yi, tace: “Me zan yi da wani ruwan jini?” Sai ta tofa masa yawu, ta wuce. Da haka dai ’Yar Bora ta ci gaba har ta kai ga Ruwan Bagaja.

    Da ta tambaya ya ce shi ne Ruwan Bagaja, sai shi kuma ya tambaye ta abin da ya kai ta neman Ruwan Bagaja. Sai ta ce ta zo ne ta sami irin dukiyar da ’yar’uwarta ta samu a nan. Sai Ruwan Bagaja yace: “To ga shi kuwa yanzu dare ya fara yi.” Kafin ma ya gama yi mata bayani sai hadari ya taso. Da ta hango wata bukka sai ta je ta shiga ta fake ruwa.

    Can sai fitila ta kunna kanta, sai ta ga cinya a gefe. Sai ta yi kururuwa, a gefe kuma sai
    ta ga kai ya ce da ita: “Kada ki ji tsoro.” Daga nan sai cinya ta yi motsi, sai kai ya ce: “Wai sannunki da zuwa.” Da ta ji haka sai ta yi tsaki, irin wanda ta saba yi wa mutane, ta ce: “Mene ne kuma na wata cinya tace tana gaishe ni?” Da cinya ta ji haka sai ta yi motsi.

    Sai ta dubi yarinyar tace: “Kai ya ce wai ki ba shi abinci yana jin yunwa, ga abincin can ki ɗauko ki ba shi.” A nan ma sai ta sake yin tsaki ta ce: “Kamar ni in ba shi abinci?” Sai ta tashi ta ɗauko abincin. Da ta ga ƙafafun kaji ne da kifi da naman rago da alkaki da nakiya, sai ta zauna ta cinye. Tana cin wannan abinci, sai cinya ta sake yin motsi.

    Shi kuma kai sai ya ce: “Wai ki ba shi ruwa.” Sai ta ce: “Amma fa cinyar nan da raini kike.” Da ta ɗauko ruwan sai kawai ta shanye, ta bar kai bai ci ba, kuma bai sha ba. Suna nan zaune, sai ga ƙaton kumurci ya shigo, sai ’Yar Bora ta ƙwalla ihu. Maciji bai kula ba, ya fara aman ƙwaiƙwaye shiɗa. Uku manya, sauran ukun kuma ƙanana.

    Sai cinya ta yi motsi, sai kai ya ce: “Wai idan za ki tafi gobe ki ɗebi ƙwai uku ƙanana, in kin je bayan garinku sai ki fasa.” Da ta ji haka, sai ta karkace kai irin na marasa kunya tace: “Yau na ji wani abu, ku za ku gaya mini in ɗiba? Ai koba ku faɗa ba zan ɗiba.”

    Sakamakon ‘Yar Bora

    Da gari ya waye, sai ta ɗebi ƙwaiƙwaye uku amma manya, ta tafi. Da ta fara ’yar tafiya sai ta ce: “Yanzu wai har ma sai na je gida zan fasa kayana?” Sai kawai ta fasa ƙwai
    biyu tare. Tana fasawa sai ga jakai da kutare da ƙudaje suna bin ta. Sai ta fasa na uku, sai ga tarkacen shara da tsummokara tili-tili. Sai kutaren nan suka ɗora ta a kan jaki, suna raka ta.

    Kudaje na bin su har gida. Da uwar ta ga ’yarta, sai ta gudu. Da ’yar ta ga uwar tana gudun ta, sai ta ce da ita: “Tsaya mana, ni ce ’yarki fa.” Sai uwar ta ce: “A’a, yau na rabu da ke, ba ni ba ce.” Sai ta gudu ta bar ta da kutarenta da jakan nan da ƙudaje suna ta zaga gari. Mutanen ƙauyukan kusa da su da suka ji labari suka yi ta tururuwa suna zuwa kallo. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Yi wa yara kyakkyawar tarbiya shi ne babban jarin da za su juya don samun kyakkyawar rayuwa.
    • Rashin tarbiya mai kyau shi ne jigon kaiwa ga rashin nasara.
    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Makauniya Da Ɗanta

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Mai Haƙan Ɓera

    Tatsuniyar Mai Haƙan Ɓera

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum da ba ya aikin komai sai ya fita farauta, yana haƙar ramukan Ɓera. Idan ya kamo ɓeraye yakan yanka ya yi bandar naman ya kai kasuwa ya sayar. Wani lokaci yakan fita wannan farauta tare da wani maƙwabcinsa, har ma sun yi suna ƙwarai wajen wannan sana’a tasu.

    Wata rana shi da maƙwabcinsa sun fita farauta, sai suka ga wani babban rami. Da suka tsaya za su haƙa sai maƙwabcin ya ce: “Wannan fa ramin Kura ne bana Ɓera ba. Kada mu tono abin da zai cuce mu.” Sai ya ce da shi: “Kai dai ka cika tsoro, idan dai kai ba za ka haƙa ba, ka tafi ka ba ni wuri.” Da maƙwabcin nasa ya ji haka sai ya tafi abinsa, ya bar shi yana tona ramin.

    Da ramin ya yi zurfi sosai, sai yasa ƙwaryarsa domin ya kama ɓerayen da yake zato suna cikin ramin. Sai ya ji an buge ƙwaryar. Da ya duba sai ya ga ashe Kura ce, har ma ta miƙo ƙafarta waje. Nan da nan ya jefar da kayan haƙan ya kama gudu. Yana cikin gudu ne ya tarar da wasu manoma a gona, sai ya ce da su: “Ku taimake ni ku ɓoye ni mana, ga Kura nan ta biyo ni za ta cinye.”

    Da suka ji haka sai suka ce: “A a, ka yi gaba, ba za mu iyaba.” Haka ya ci gaba da gudu, har ya tarar da wasu mutane masu noma da hanci, ya roƙe su da su ɓoye shi; su ma suka ce ya yi gaba. Ya sake yin gaba da gudu, har ya tarar da masu noma da duwawu, sai ya tsaya ya ce su taimake shi, amma su ma suka ƙi.

    Sai ya ci gaba da gudu, har ya hango wata ’yar bukka sai ya matsa kusa ya leƙa; amma
    ba komai a ciki sai Kunkuru yana zaune. Sai ya dubi Kunkuru ya tambaye shi: “Ina mai bukkar nan? Ina so ya taimake ni ya ɓoye ni.” Sai Kunkuru ya ce: “Ai ni ne mai bukkar, shigo zan ɓoye ka.”Sai mutumin ya ce da Kunkuru: “Manya ma ba su ɓoye ni ba sai kai da karambani za ka ce ka ɓoye ni?”

    Kunkuru ya ce da shi: “Kai dai shigo mana ka gani.” Mai neman Ɓera dai ya tsaya da gardama, har ma ya juya zai tafi, amma kafin ya fara tafiya sai ya hango Kura ta doso bukkar, kuma ya san idan ya fita za ta kama shi. Ai bai san sanda ya kutsa bukkar Kunkuru ba, kuma ya ɓoye shi. Da Kura ta ƙaraso sai ta ce da Kunkuru:

    “Da namana a ɗakin nan.” Kunkuru ya ce: “Babu namanki a ɗakin nan.” A nan Kunkuru da Kura suka kama faɗa, kafin wani ɗan lokaci Kunkuru ya kashe Kura. Da mutumin nan ya ga haka, abin ka da halin ɗan Adam sai kawai ya ce da Kunkuru: “Ni kuma ai nama ya samu a araha; bari ma in feɗe shi, kuma ina son ƙwaryar.”

    Da Kunkuru ya ji haka sai ya ce da shi: “Ka haƙura da fatar Kurar nan mana, ta fi maka amfani. Ka ma kwashe naman nata ga baki ɗaya.” Mutumin nan dai ya ƙi, ya dage shi dai ƙwaryar Kunkuru yake so. Kunkuru dai ya yarda, ya kuma ce da shi: “To, zan haɗa ka da karnuka su raka ka garinku, domin duk sanda fatar Kurar nan za ta cinye ka sai su kama ta da ci.”

    Da ƙyar dai mutumin ya yarda ya tafi da karnukan. Mutumin nan shi da karnuka sun kama hanya sun yi nisa, sai ya ji ya gaji, ya ajiye fata a gindin wata bishiya zai huta. Ajiye ta ke da wuya sai ta fara motsi tana kukan Kura. Da karnuka suka ga haka sai suka rufar mata, suka murƙushe ta, ta daina kukan, kuma ta daina motsi, ya tashi ya ɗauka suka ci gaba da tafiya.

    Bayan wani lokaci kuma, sai ya tsaya zai yi fitsari, fata kuma ta fara motsi. Karnuka kuma suka fara haushi fiye da irin wanda suka yi a baya. Sai mutumin wai ya ji haushi, ya daka musu tsawa, har suka tsorata suka gudu. Kafin ka ƙifta ido, ai fatar nan ta rufe mutumin nan ta cinye shi, kowa ya huta da taurin kansa. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Taurin kai da rashin ɗaukar nasiha babu abinda yake jawo wa mai shi sai cutarwa da faɗawa halaka.
    • Wanda bai ji bari ba, ya ji hoho.
    • Kowa ya ɗebo da zafi, bakinsa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Makauniya Da Ɗanta

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Makauniya Da Ɗanta

    Tatsuniyar Makauniya Da Ɗanta

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A wani ɗan ƙauye da ke yamma da Dajin Kurege, akwai wani manomi da matarsa makauniya. Suna cikin zama irin na rufin asiri, sai Allah ya yi masa cikawa. A lokacin kuwa tana goyon jariri mai suna Zama. Uwar tasa kuwa ta sha wuya wajen renonsa. Kullum sai ta je ta yo bara kafin ta ciyar da kanta da ɗanta.

    Mijinta kuma bai bar dukiya ba sai shanu biyu kawai da Zama ya gada. Ita kuma mace ce mai tsinkaye da riƙon amana, sai ta kai shanun nan wani garke, a rugar wasu makiyaya da ke kusa da ƙauyensu. Ta yi haka ne da nufin a kiwata su, idan yaron ya girma, kuma shanun sun yaɗu, ta nuna masa abin da ubansa ya bar masa.

    Kuma duk abin da ɗanta yake so takan je ta barato masa. Sannu a hankali, yaro ya girma ya isa aure. Wata rana bayan sun ci abincin dare, sai uwar ta kira shi tace: “To, Zama, da ma ina jira ne idan ka yi hankali sosai in danƙa maka abin da ka gada daga mahaifinka. Amma na kai su garke ne, a rugar wasu makiyaya.”

    Da ya ji lafazin mahaifiyarsa, sai ya tambaye ta: “Menene? Wane irin abu ne?” Ta ce: “Shanu biyu ne ya bar maka, amma ban sani ba ko yanzu sun ƙaru?” Sai ta kama hannunsa ta ce: “Mu je inda aka kai shanun, mu jiyo labari.” Ta yi masa kwatancen hanyar da za su bi; suka kama hanya, har ya kai su.

    Mai garke ya yi musu maraba suka gaisa kamar yadda ya kamata, sai makauniya ta tuna masa shanun da ta kawo masa kiwo tun shekarun baya da suka wuce. Sai mai garke ya ce: “Haka aka yi kuwa. Ai yanzu shanu sun hayayyafa, har ma sun kai ashirin.” Da ta ji haka sai ta yi masa godiya, ta ce da shi: “To, ga magajinsu ya kawo ƙarfi, buƙatu sun taso, shi yasa muka zo mu kora su.”

    Sai mai garke ya ware musu shanunsu; suka kama hanyar gida, Zama yana kora su har suka je gida. Bayan sun ɗan huta da kwana biyu, sai uwar tace da Zama: “Ya kamata yanzu kam ka yi aure domin ina so in sami jikan da zan rinƙa wasa da shi.” Sai ya ce da ita: “To, amma fa ni ba zan yi aure a ƙauyen nan ba sai dai daga birni.”

    A kwana a tashi, wata rana sai Zama ya shiga birni, ya je kasuwa; sai ya tarar an sa wata kyakkyawar yarinya a gaba, makaɗa na cashewa, ana yi mata kirari, da waƙe- waƙe. Sai ya tambayi wani ɗan kallo da cewa: “Me yasa aka kewaye wannan yarinya mai kyau kamar aljana, ana yi mata kiɗa da waƙa?” Sai ya ce da shi: “Saboda kyauta ne uwarta tace duk mai son ta, sai ya ba ta duk dukiyar da ya mallaka, kafin ya aure ta.

    Duk masu dukiyar da ke garin nan kuma sun kasa.” Da ya ji haka sai ya yi tsaki, ya ce: “Ni zan aure ta.” Sai ya matsa kusa, ya sa aka yi he!, ya ce: “A gayawa uwar yarinyar cewa ni zan aure ta, kuma zan ba da duk dukiyar da na mallaka.” Wani daga cikin danginta ya ce: “To me ka mallaka?” Zama ya ce: “Ina da riƙaƙƙun shanu ashirin.”

    Sai dangin ya ce: “To, ka je ka kawo su za a ba ka ita.” Da Zama ya ji haka, sai kurum a cikin ɗoki ya koma gida ya gaya wa mahaifiyarsa cewa ya sami wadda zai aura. Uwar ta ce: “Wane sharaɗi iyayenta suka sa maka?” Sai ya ce: “Sun ce sai na ba su duk dukiyata kafin su ba ni ita.”

    Uwar daga farko ta yi murna, amma da ta yi tunani kaɗan sai ta ce: “Kai ɗan nan, wannan fa shi ne iyakar abinda ka mallaka, babu hikima a ce ka ba su ita gaba ɗaya.” Wannan magana dai ba ta shigi yaron ba. Sai kawai yace shi fa sai ya auri wannan yarinyar. Sai uwar ta ce: “Shi kenan, yi abin da kake so.”

    Yaro ya tashi ya kwance shanu ya kora su gidan iyayen yarinyar da zai aura. Suka karɓa suka kuma ba shi yarinyar, aka ɗaura aure ya ɗauki matarsa ya kai ta gidansu, ya je kuma ya sanar da mahaifiyarsa. Ita kuma ta ce da shi: “Ai ya kamata ka kai ni in yi mata barka da zuwa.” Bai yi wata-wata ba ko sai ya kama sandarta ya kai ta har ɗakin amaryar.

    Amma da ta ga mahaifiyar Zama makauniya ce, sai ta ƙi yi mata magana, ta nuna cewa ai ba ta yi wa makafi magana. Uwar kuma ba ta nuna damuwa a kan halayyar surukarta ba, saboda haƙurin da Allah ya ba ta. Ana nan, bayan ’yan kwanaki sai amarya ta ce da Zama: “Ni fa na gaji, ba zan iya ci gaba da girki a gidan nan ba.”Sai ya ce: “To, yaya kike so a yi?”

    Ta ce da shi: “Mai dafa abinci za ka nemo mini.” Da ya ga matarsa ta kafe a kan haka sai ya gayawa mahaifiyarsa. Ita kuma ta ce da shi: “Ba komai, ni zan ci gaba da dafawa; ai da ma tun kafin ta zo, ni nake dafawa.”Haka ta ci gaba da yi musu girki, surukarta kuwa ta ci gaba da zaman ƙwambo.

    Ana nan, sai wata rana matar Zama ta tambayi mijin inda ya samo shanun da ya kai gidansu ya aure ta. Sai ya kwashe labarin yadda ya ci gadon mahaifinsa, ya gaya
    mata. Da ta ji haka sai ta ce: “Ai ba ka da wayo, mahaifiyarka ta cuce ka domin ta ɓoye sauran shanun. Ka je ka bincike ta da kyau, za ta gaya maka inda sauran suke.”

    Nan da nan ya tashi ya je ya sami mahaifiyarsa, ya fara yi mata rashin ladabi da faɗa, wai sai ta fito masa da sauran shanunsa. Ita kuma ta ce da shi: “Haba ɗana, ban ɓoye maka komai ba.” Haka dai Zama ya yi ta yi wa mahaifiyarsa rashin ladabi har tsawon wasu ’yan kwanaki.

    Da matar Zama ta ga bai yi wa mahaifiyarsa wulaƙanci kamar yadda take so ba, sai ta ce da shi: “Ni fa zan koma gidanmu; domin na gaji da zama da makauniya a gidan nan. Yanzu lallai sai ka san inda za ka kai ta, ko kuma ni in tafi gidanmu.” Sai ya ce: “Kada ki damu. Yanzu faɗi yadda kike so a yi da ita.”

    Jin haka fa ya sa ta yi murmushi ta ce: “Ina son ka kai ta cikin jeji inda kuraye suke shan ruwa, sai ka ce ta jira ka, kai kuma ka gudo gida. Washegari sai ka je ka kwaso ƙasusuwanta bayan kuraye sun cinye ta. Daga nan sai ka gaya wa mutane cewa ta yi ɓatan kai ne a jeji, kuraye suka cinye ta.” Ya ce: “Idan na yi haka za ki haƙura da komawa gidanku; za ki zauna da ni?”

    Sai matar ta kashe murya, ta dube shi, ta ce: “Ƙwarai kuwa. Idan ka yi haka, ba inda za ni.” Zama ya je ya ce da mahaifiyarsa: “Yanzu na yi wani tunani ina son ki zo mu je in kai ki inda za ki sami maganin makantarki.” Sai ta ce: “To.” Nan da nan ta shirya a cikin murna, suka kama hanyar daji, har suka kai tsakiya inda kuraye kan taru, ya ajiye ta a gindin wata bishiya, ya ce da ita:

    “Zauna nan, ni kuma zan je neman wani itace da za a haɗa maganin. Idan ban dawo ba, kada ki motsa daga nan.” Ta ce da shi: “To. Na gode Zama, ka kyauta da ka kawo ni
    gidan masu magani.” Shi ko bai ma damu da godiyar da take yi masa ba, sai kawai ya kama hanya ya koma gida ya baro ta a wannan dajin.

    Ita kuwa ta zauna tana jiransa har dare ya yi. Idan ta ji motsi sai ta ce: “Zama ne? Ka dawo?” Sai ta ji kukan kura a bayanta, amma ba ta razana ba. Wannan dajin kuma bayan kuraye da sauran namun da ke dajin, akwai aljanu a wurin da yawa. Aljanun ne ma suka zagaye ta, suna mamakin abin da ya sa ta zo wuri mai hatsari haka.

    Can sai ɗaya daga cikinsu ya rikiɗa ya je ya ce: “Ke matar nan me ya kawo ki nan?” Sai ta ce: “Ɗana ne Zama ya kawo ni, don neman maganin makantar nan tawa.” Sai aljanin nan ya ce: “A a, nan fa mutane ba sa zuwa, domin tsakar daji ne, amma zan taimake ki yadda za ki tafi gida.” Sai ta ce: “A a ɗana ya ce in jira shi a nan; idan na tafi zai yi mini faɗa.

    Gara in jira shi ai zai zo ya same ni.” Da tausayi ya kama aljanin nan, sai ya gaya mata cewa za su warkar mata da makantar. Kamar da wasa, da suka yi wani siddabaru irin nasu, sai kawai ta ga ta fara gani. Buɗe idonta bai sa ta yi niyyar tafiya ba, har gari ya waye ta farka daga barcin da ta yi, ta shiga jiran ɗanta.

    Kafin ya zo sai ta ga shanu masu yawa, garke-garke, ta tambayi aljanin nan da ya rikiɗa ya zama mutum, ko shanun nan na wanene? Sai ya ce da ita, ai nata ne duka, sun ba ta kyauta. Makauniyar nan tana zaune can sai ga Zama ya iso. Ya kuma zo ne don ya kwashe ƙasusuwan mahaifiyarsa saboda ya tabbatar da kuraye sun cinye ta a cikin dare.

    Maimakon haka, sai kawai ya ji ta kira shi daga nesa, saboda jikinta ya ba ta cewa ɗanta ne, ko da yake dai ba ta taɓa ganin sa ba sai wannan rana. Har ya juya zai gudu sai
    ta ce: “A a, kada ka gudu mana. Ni ce mahaifiyarka.” Da ya isa kusa da ita, sai ta kwashe duk labarin abinda ya faru tsakaninta da mutumin da ya taimake ta, ga idanu sun samu, kuma ga shanu.

    Zama ya kora shanu, shi da mahaifiyarsa suka koma gida. Da matarsa ta gan shi da garken shanu, kuma ga mahaifiyarsa tana gani raɗau, sai haushi da mamaki suka kama ta. Shi kuma Zama ya kwashe labari ya gaya mata. Jin haka ya sa ta ce ita ma dole ne ya kai uwarta dajin nan idan yana son zama da ita.

    Sai ya ce: “To, zan yi duka binda kike so, saboda ina son ki.” Bayan kwana uku da dawowar uwar Zama daga dajin mutuwa, matarsa ta tafi garinsu, ta ɗauko uwarta, domin ita ma a kai ta can ta samo shanu. Haka kuwa aka yi ya ɗauke ta ya kai ta daji ya baro. Da ta ji kukan kura na farko, sai ta kiɗime ta kama ihu, ta tsure.

    Nan take kuwa kuraye suka far mata suka cinye ta. Da gari ya waye Zama da matarsa suka kama hanyar daji domin su koro shanun uwar matarsa, amma da suka je inda suka kai ta, sai suka tarar sai ƙasusuwanta; kuraye sun cinye ta, kuma ba shanu. Tun daga dajin matar Zama ta kama kukan baƙin ciki, ta kasa komawa gida ta tare a gindin wata kurna tana ta sharar kuka. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Gaskiya da riƙon amana su ne maganin makirci da makirai.
    • Hassada da ganin ƙyashi su suke sa a faɗa kogin da-na- sani.
    • In za ka gina ramin mugunta, gina gajere.
    • Tun ran gini, tun ran zane.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Sandar Arziƙi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Sandar Arziƙi

    Tatsuniyar Sandar Arziƙi

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can wani gari da ya yi iyaka da ƙasar Aljanu, akwai wani mutum mara sukuni da matarsa, da ɗansu ɗaya. Suna zaune a cikin wannan hali, sai ɗan ya isa aure. Iyayen nasa sai suka ce da shi: “Yanzu ga shi ka isa aure, amma ba mu da abin da za mu aura maka mata da shi.”

    Amma mahaifinsa yana da wata sanda; sai ya ba shi ita yace: “Ka kama hanyar duk garin da ka zaɓa a zuciyarka; sandar za ta zama sanadin yin aurenka.” To, da yake yaron mai biyayya ne, sai ya karɓi sandar ya cewa mahaifansa: “Na gode, kuma na tafi. Allah ya ba ni sa’a.”

    Baki ɗaya suka ce: “Amin.” Yaro yana cikin tafiya a daji, sai ya tarar da wasu mutane suna jifan tsuntsaye. Sai ɗaya daga cikinsu yace: “Kai yaro, ka taimake mu da aron sandar nan taka mu jeho tsuntsu mana.” Ba tare da wani musu ba, sai kawai ya ce: “Ga ta.” Suka karɓa, suka jeho tsuntsaye da yawa da ita.

    Amma kuma sai sandar ta maƙale a jikin rassan bishiyar. Da ya ga sandarsa ta maƙale, sai ya fara waƙa yana cewa: “Tam, tam, Sai kun biya ni sanda ta. Sandata da uwata ta ba ni, Ubana ya ba ni. Takan cishe ni, Tai min aure.” Sai suka ce: “Kash, ga shi kuwa ba mu da komai sai dai mu ba ka tsuntsu ɗaya.”

    Sai ya ce: “To, ku ba ni.” Suka ba shi tsuntsu, ya karɓa ya kama hanya. Yana cikin tafiya sai ya tarar da wata mace ta girka abinci. Sai ta ce da shi: “Kai yaro, ba ni tsuntsun nan naka in gani.” Da ta karɓa, sai kawai ta gyara shi, ta yi miya da shi. Yana ganin haka sai ya ce: “

    Tam, tam, Sai kin biya ni tsuntsuna, Tsuntsuna da maharba suka ba ni, Maharban da suka ɓatar da sandata, Sandata da uwata ta ba ni, Ubana ya ba ni, Yakan cishe ni, Ya yi min aure.” Sai ta ce: “Wayyo samari, ai ban san haka abin yake ba, sai dai ba ni da komai sai tuwon nan da ka gani.”

    Da ya ji haka sai ya karɓi tuwon mara biyar, ya kama hanya riƙe da abinsa. Yana cikin tafiya, sai ya tarar da wasu manoma, sun yi aiki sun gaji; yunwa ta sa sun galabaita. Da suka ga tuwo a wurin yaro, sai suka ce: “Ɗanyaro mu ga tuwon nan mana.” Da suka karɓa sai suka cinye. Da ya ga sun cinye masa tuwo, sai ya fara waƙar da ya saba

    “Tam, tam, Sai kun biya ni tuwona, Tuwona da mai girki ta ba ni, Da ta karɓi tsuntsuna,
    Tsuntsuna da maharba suka ba ni, Maharban da suka ɓatar da sandata, Sandata da uwata ta ba ni, Ubana ya ba ni, Yakan cishe ni, Ya yi min aure.” Sai suka ce: “To ga shi ba mu da komai. Amma in kana son fartanya ko magirbi, sai mu ba ka ɗaya.”

    Da ya ji hakasai ya ce: “Ba komai, ku ba ni magirbi, ya wadatar.” Nan take suka ba shi magirbi ɗaya, ya kama hanya. Yana cikin tafiya, ya kusa isa wani babban birni, sai ya tarar da wasu mutane sun fara haƙa ƙabari za su yi jana’izar wata gawa. Da suka ga magirbi a hannunsa, sai babbansu ya ce: “Yaro ba mu aron magirbin nan mana mu haƙa ƙabari.

    ”Ba wani musu, sai ya ba su. Suna cikin tonon rami, sai magirbin ya kare da ganin haka sai ya fara wakarsa: “Tam, tam, > Sai ka biya ni gawata, > Gawata da masu haƙar ƙabari suka ba ni, > Masu tonon ƙabari da suka karya magirbina, > Magirbina da manoma suka ba ni, > Manoma da suka cinye tuwona, > Tuwona da mai abinci ta ba ni, > Mai abinci da ta karɓi tsuntsuna, > Tsuntsuna da maharba suka ba ni, > Maharba da suka ɓatar da sandata, Sandata dauwatataba ni, > Ubana ya ba ni, > Yakan cishe ni,
    > Ya yi min aure.” >

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Yin biyayya ga magabata tare da jure wahalhalun rayuwa sukan kawo nasara a rayuwa.
    • Mai arziki ko a ƙwara ya sayar da ruwa.
    • Arziki a ƙasa ake tako shi.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Sarkin Maƙera Da Dodo

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Sarkin Maƙera Da Dodo

    Tatsuniyar Sarkin Maƙera Da Dodo

    Ga ta nan, ga ta nanku. A wani ɗan ƙauye, an yi wata mata mai ’ya’ya biyu, mace da namiji. Sunan namijin Fugo shi ne wa; ita kuma macen sunanta Awa, ita ce ƙanwa. Shi Fugo maƙeri ne. Ana nan, sai wata rana wani mutum daga wani gari mai nisa ya zo ya ce yana son ya auri Awa, sai aka yarda, aka ba shi ita.

    Bayan an gama biki, sai ya ɗauki matarsa suka tafi garinsu, wanda ba a bin hanyar zuwansa da rani saboda akwai wani dodo da kan tsare hanyar, ya cinye matafiya duk lokacin rani. Amma kuma da damina ba ya taɓa kowa. Ana nan, ana nan sai a wata damina Fugo ya je garin mijin ƙanwarsa Awa don ya gaishe su.

    Bayan ya dawo da rani sai mahaifiyarsu ta rasu, kuma ana so a aikawa Awa garin da take aure, to amma ba hali saboda a cikin rani ne; kowa yana tsoro kada ya bi hanyar dodon nan ya cinye shi. Ana cikin neman mai zuwa, sai kurciya ta ce za ta je ta gaya wa Awa saƙon. Sai ko aka ba ta saƙo, ta tashi sama, ba ta sauka ba sai a kan ɗakin Awa.

    Awa na kwance a ɗaki, sai ta ji kurciya tana waƙa, tana cewa:

    “Awa, Awa kina barci,

    Ga uwarki can,

    Tana barci tun shekaran jiya,

    Tun shekaran jiya ba ta tashi ba,

    Ki shirya, za ki dakan gero.”

    Sai ta fito ta saurara da kyau, ta fahimci lafazin waƙar kurciya, sai ta fashe da kuka, har da kururuwa. Da mijinta ya ji, sai ya shigo ya tambaye ta abin da ya faru. Sai tace an aiko mata da rasuwar uwarta ne. Da ya ji haka sai yace: “To, ga shi hanya ba za ta biyu ba. Yanzu yaya za a yi?”

    Duk da cewa Awa ta san dodo yana hanya kuma tabbas idan ta bi hanyar zai cinye ta, sai ta ce ita kam lallai sai ta je ta gano kushewar mahaifiyarta tun ba ta daɗe da rasuwa ba. Da mijin Awa ya lura lallai ta tsaya kai da fata sai taje, sai ya ce: “To, shi ke nan, sai mu yi wata dabara, mu yanka miki shanu, mu raba su gida bakwai, idan dodo ya taso zai
    cinye ki, sai ki jefa masa kashi ɗaya.

    Da haka har ya ƙoshi, ke kuma ki isa gida.” Sai Awa ta ce: “To na gode, mai gida.” Aka kama shanu, ya yanka, ya sa aka kasa nama gida bakwai, aka zuba wa Awa a cikin masaki. Da ranar da aka sa ta zo, sai ta kama hanya, ɗauke da masakin nama. Tana cikin tafiya a daji, sai dodon nan kwatsam ya ɓullo, yana tafiya yana waƙa, yana cewa:

    “Maraba, lale, lale,

    Wannan mata, lale,

    Ina za ki je?

    Gaya mini, ina za ki je?”

    Dodon nan baƙi ne ƙirin, ga gashi duguzunzun; abin gwanin ban tsoro. Idan ya buɗe baki sai turiri ke fita. Amma Awa ba ta tsorata ba, sai kawai ma ta mayar masa da waƙa:

    “Ni Awa, ni Awa,

    Zan je makokin mutuwa,

    Mutuwar uwata,

    Zan je kai kayan mutuwa,

    Mutuwar uwata,

    Zan kai kayan miya,

    Kayan miyar mutuwar uwata.”

    Sai dodo ya matso kusa da ita ya ce: “Buɗe in gani; menene a ciki?” Da ta buɗe masaki ya ga naman sa ne, sai ya ce: “Ko dai ki ba ni ko in haɗiye ki.” Sai ta ce: “Idan ka haɗiye ni zan yi maka kuka.” Sai dodon ya ce: “Yi kukan mu ji.” Sai ta ce:

    “Wai, wai, wai, Gari ya yi zafi,

    Uwata ba ta nan,

    Uwata ta tafi lahira.”

    Tana gama waƙar, sai ta ɗauki yankan nama ɗaya ta jefa masa. Da ya tsaya yana ci, sai ta kama hanya tana sauri. Kafin ya cinye ta yi nisa. Da ya cinye, sai ya sake bin ta, ya sha gabanta ya kama waƙa, ita kuma sai ta mayar masa. Duk sanda ta jefa masa naman, sai ta fara gudu, shi kuma ya ɗauki naman ya tsaya ya cinye.

    Da ya cinye sai ya sake bin ta. Haka suka rinƙa yi, har naman ya ƙare. Ba ta yi
    nisa ba sai ta yar da masakin, ta kama gudu. Shi kuma da ya cinye nama, sai ya bi ta. Da ta ga dai ya kusa kamo ta, sai ta hau bishiya, shi kuma ba zai iya hawa ba; sai ya tsaya a gindin bishiyar.

    Can sai ya ɗaga kai ya ce da Awa: “Ki sauko in cinye ki”. Ita kuma ta rasa yadda za ta yi, sai kwatsam ga kurciya ta sauka a kan bishiyar. Sai Awa tace da ita: “Idan na aike ki wurin yayana me za ki ce da shi?” Sai kurciya ta ce: “Zan ce da shi Fugo kana maƙera kana ƙira, amma ƙanwarka tana can a kan bishiya dodo zai cinye ta a dokar daji.”

    Sai Awa ta ce da kurciya: “Yawwa, haka za ki je ki faɗa masa.” Nan take kurciya ta tashi sama, ba ta tsaya a ko’ina ba sai kan bishiyar da ke kusa da maƙerar Fugo. Da saukarta ta fara waƙa tana maimaita saƙon da aka aiko ta sanar wa Fugo. Da ya ji waƙa, sai ya ɗaga kansa sama, ya ga kurciya, ya kuma fahimci abin da ta faɗa.

    Sai ya shiga shiri, domin bai ga ta zama ba, saboda dodo zai kashe masa ƙanwa. Ya ɗebi makamai irin waɗanda yake ƙerawa, kamar masu da kwari da baka da takubba da sauransu, ya kwance karnukan farautarsa guda goma, sai ya ce da kurciya ta tashi sama, zai bi inuwarta har gindin bishiyar da dodo ya tsare masa ƙanwa.

    Haka Fugo ya kama hanya, kurciya na yi masa jagora. Idan ya saki hanya, sai ta yi waƙa, shi kuma ya bi inda ya ji muryarta, har dai suka isa. Suna zuwa, sai suka tarar da dodon a inuwar bishiyar yana barci. Ba tare da jinkiri ba, sai Fugo ya zaro kibiya ya ɗirka wa dodon nan. Kafin ya farka, sai da Fugo ya yi masa ruwan kibau kamar ashirin.

    Da ya farka, kafin ya wartsake Fugo ya jefa masa masu kamar guda tara. Amma duk da haka da ya wartsake sai aka ji yana cewa: “Kai wane cinnaka ne yake damuna?” Shi kuma Fugo sai ya zaro wasu kibau masu dafi, ya dinga ɗana su yana sakar wa dodo ɗaya bayan ɗaya a idonsa na dama, nan take idonsa ya tsiyaye.

    Kafin ya san abinda ake ciki, Fugo ya sake auna ɗaya idon, kuma ba kuskure ya same shi. Shi ma nan take ya tsiyaye, dodo ya zama ba ya iya gani. Tuni dafin kibiyar ya bi jikin dodo, har ya zamanto ba zai iya tashi ba. Sai Fugo ya ce da Awa ta sauko. Sai dodo ya ce: “Ki sauko in cinye ki.” Da Fugo ya ji haka, sai ya zare takobi ya sassare dodo, ya yi masa gunduwa-gunduwa.

    Awa tana gani, amma da ta yunkura za ta sauko, sai guntayen naman dodo suka ce, idan ta sauko za su cinye ta. Da Fugo ya ga haka sai yasa karnukansa suka cinye naman dodon gaba ɗaya, sannan ya ce ƙanwarsa ta sauko. Da ta miƙo ƙafarta za ta sauko, sai ƙasusuwan suka ce, idan ta sauko za su cinye ta. Sai ya sake sa karnukansa suka cinye ƙasusuwan.

    Daga nan kuma ta sake miƙo ƙafarta za ta sauko, sai busasshen jinin dodon da ke ƙasa ya ce, ta sauko ya cinye ta. Daga nan dai sai Fugo ya sa karnukansa suka gwaguye jinin da ya yi kasko a ƙasa, har dai suka tabbatar babu kome a wurin, sai ya ce to ta sauko. A nan ne fa ta sauko lafiya, yasa ta a gaba, suka kama hanyar gida.

    Nan da nan labari ya bazu cewa Fugo Sarkin Maƙera ya kashe dodo, kuma hanya ta yi lafiya, rani da damina, babu sauran fargaba. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Haƙuri da juriya da nuna jarumta sukan sa a shawo kan matsala komai tsaurinta.
    • Farar aniya laya.
    • Mai rabon ganin baɗi ko ana ha-maza-ha-mata sai ya gani.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Umbagila Da Dodo

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Umbagila Da Dodo

    Tatsuniyar Umbagila Da Dodo

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani ƙaramin ƙauye da yake kusa da wani daji ai cike da dodanni. Ɗaya daga cikin dodannin ya matsawa mutanen wannan ƙauyen, yana kama su ya bautar da su. Yakan fita ɗibar kayan miya duk ranar Asabar. Saboda haka mutanen ƙauyen suka daina fita ɗibar kayan miya a ranar da Dodon yake fita domin kada ya kama su ya mayar da su bayi.

    Mutanen da ya kama ne sukan dafa masa abinci da sauran wahalhalun gida na yau da kullum. Ana nan cikin haka shekara da shekaru, sai wata rana wata yarinya wai
    ita Umbagila ta ƙudurce a zuciyarta cewa za ta je ɗebo kayan miya ranar da Dodo yakan je, watau ranar Asabar.

    Sai ta gaya wa uwarta. Da uwar ta ji abin da tace sai ta dube ta ta ce: “Kada ki je domin ranar Asabar Dodo yakan je ɗibar kayan miya, idan kin je zai kama ki.” Umbagila ta ce da uwarta: “Ni dai ki yi min addu’a lallai kam zan je.” Haka dai ta haƙura ta ƙyale ta ta ɗauki ƙwarya ta shiga dajin da mutanen ƙauyen kan je neman kayan miya.

    Tana cikin cirar ganyen lalo da ayayo da karkashi da barkono da sauran kayan miya, kwatsam sai ta ji motsi a bayanta, kafin ta juya sai ta ji Dodo ya cafke ta. Tana ganinta a hannun Dodo sai ta fashe da kuka. Da ya ga ta fara kuka, sai ya ce mata ta daina kuka, idan ta yarda za ta aure shi ba zai cinye ta ba.

    Ba tare da gardama ba Umbagila ta ce da Dodo: “Na yarda in aure ka.” Shi ke nan Dodo ya kai ta gidansa ya ajiye ta, kuma ya ce daga wannan rana ba zai ci abincin da bayi suka dafa ba sai wanda ta dafa. Duk sanda Dodo ya je farauta, ko yawace-yawacensa ya dawo, da ya iso kusa da gida sai ya fara waƙa yana cewa:

    “Umbagila matata,

    Umbagila amaryata,

    Umbagila ina tuwona?”

    Ita kuma da ta ji sai ta amsa masa da cewa:
    “Dodo mijina,

    Ga tuwonka can a bakin randa,

    Ga furarka can a bakin randa,

    Ga ruwan sha nan a bakin randa.”

    Haka dai suka ci gaba da zama da Dodo. To dama Dodo yana da wata hatsabibiyar kaza a gidansa. Wata rana ya tafi yawo, sai Umbagila ta haɗa kayanta za ta gudu. Da kaza ta ga alamar za ta gudu, sai ta kira Dodo tace: “Dodo, Dodo za ta gudu.” Nan da nan ya dawo gida yace: “Na ji labari za ki gudu.”

    Sai ta yi masa murmushi tace: “A a, na shanya kayana ne, kuma yaya zan gudu in bar mijina?” Da ya ji haka sai ya ce: “Yawwa matata, na san ba za ki gudu ba.” Sai ya fita harkokinsa. Kullum idan Umbagilatayi ƙoƙarin gudu, sai kazar nan ta fallasa ta. Rannan dai sai ta zauna ta kama kuka a daidai lokacin da ta san Dodo ya kusa dawowa.

    Da ya shigo gida ya tarar tana kuka sai yace: “Me ya sa ki kuka, matata?” Sai ta ce: “Ina so in ci kaza ne, kuma na san ba ni da wanda zai ba ni ita.” Sai ya ce da ita: “Yanzu  saboda wannan ne kawai kike kuka?” Ta ce: “E, saboda haka ne.”Ya ce: “To, daina kukan haka, zan yanka miki kaza.” Sai ko ya kama kazar nan mai fallasa ya yanka suka cinye.

    Bayan sun cinye, sai Dodo ya fita farauta. Ita kuma ta shiga haɗa kayanta za ta gudu. Sai gashin kazar nan ya kira Dodo yace: “Dodo, Dodo, dawo gida matarka za ta gudu.” Tana jin haka sai ta shiga ɗaki ta ɓarke da kuka. Can Dodo ya iso gida ya tarar da matarsa tana sharar kuka, sai ya nemi jin abin da ke damun ta.

    Ta ce masa: “Bana son ganin gashin kazar nan a gidan nan.” Da jin haka sai ya tattara gashin kazar ya ƙone, ya sa bayinsa suka kwashe tokar suka kuma ƙanƙare jininta daga wurin da aka yanka ta. Washegari da Dodo ya tafi yawonsa, sai Umbagila ta kwashe ’yan komatsenta, ta gudu gidansu, ta kuɓuta daga sharrin wannan Dodo. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Ƙin bin umarnin iyaye yakan janyo wa ɗan ya fuskanci matsaloli masu yawa a rayuwarsa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar ‘Yan Goma Sha Ɗaya

    Edita@rumasau-kallamu