Tatsuniyar Maharbi Da Zaki

0
17

Ga ta nan, ga ta nan ku.

An yi wani maharbi da ke gefen Dajin Shiddar, a can yamma da ƙasar Sarkin aljanu. Wata rana ya fita farauta a daji, sai ya ga wani rami, bai yi wata-wata ba sai ya kutsa kai ya shiga. Ashe ramin nan na Zaki ne. Zaki ko na ganin sa sai ya yo kansa. Mutumin nan ya fito ya kama gudu, har ya fita daga dajin ya shiga karkara.

Zaki dai na bin sa, har ya tarar da wani manomi, ya ce da shi: “Mai gida ka taimake ni.” Manomin ya ce: “Me ya koro ka haka?” A cikin tsoro da ɗimuwa maharbin nan ya ce: “Zaki ne, Manyan Dawa. Sai manomin ya ce: “A gaskiya tun da Zaki ne ya fafaro ka, abin ya fi karfina; ba zan iya taimaka ma ba.”

Da ya ji haka, sai ya ci gaba da gudu. Har dai ya tarar da wani manomin a wata gonar yana tiƙar aiki. Shi ma sai ya ce da shi: “Don girman Allah ka taimake ni mana, Zaki ne ya biyo ni zai kashe ni.” Shi ma dai wannan manomi ya gaya wa maharbi ba zai iya taimakon sa ba, domin Zaki ya fi ƙarfinsa.

Sai maharbin nan ya ci gaba da gudu, har ya tarar da Gizo. Shi ma ya yi masa bayani cewa Zaki ne yake bin sa zai kashe, kuma yana son taimakonsa. Sai Gizo ya yarda zai taimake shi. Nan da nan ya kama shi, ya jefa shi cikin yanar da ya saka. Can sai ga Zakin nan ya tunkaro a guje.

Sai ya tsaya ya tambayi Gizo ko ya ga wani maharbi? Gizo ya ce bai gani ba. Sai Zaki ya fusata, ya ce da Gizo: “To, idan ba ka gan shi ba, kai zan cinye ka.” Kamar da wasa, sai ya kai wa Gizo wawura. To, da man ɓangaren yanar Gizon da Zakin ya auka wa yana da dafi, yanar kuma tana da ƙwarin da ko Zaki ba zai iya tsinka ta ba.

Yanar ta dabaibaye Zaki, dafin jikinta kuma yana daɗa raunana shi. Tausayin Zaki ya kama maharbin nan da Gizo, har suka fara yin ƙoƙarin kuɓutar da shi; to amma saboda dafin yanar nan da kuma shaƙe wuyan Zaki da yanar ta yi, kafin su gama warware yanar har rai ya yi halinsa.

Su kuma manoman da maharbi ya roƙa su taimake shi suka ki, tsegumi ya sa sun biyo bayan Zaki domin su ga yadda zai kashe maharbin nan. Amma da suka isa inda Gizo yake, suka tarar da yanarsa da dafin da ke jikinta, sun halaka Zaki, kuma ga maharbi garau, sai mamaki ya kama su.

Saboda borin kunya, sai ɗaya daga cikinsu ya ce: “Da man ina da niyyar taimakon ka, amma ba ka tsaya ba. Na san kuwa shi Gizo da ya taimake ka, bai fi ni kirki ba.” Sai baki daya suka fashe da dariya, suka fara haƙa ramin da za su binne Zaki don gudun kada ya yi wa Gizo ɗoyi a mazauninsa. Kurunkus.

Abubuwan DaLabarin Yake Koyarwa

  • Rashin kyakkyawan tunani kafin aikata abu yakan jefa mutum cikin halin ƙaƙa-naka-yi.
  • Taimakon Allah yana iya zuwa ta inda ba a zata ba.
  • Kowa ya ɗebo da zafi,

Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

Danna nan don karanta Tatsuniyar Kurege Da Kura

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceTatsuniyar Kurege Da Kura
Labarin na GabaTatsuniyar Janniya
wikiHausa
wikiHausa kundin ilimi (insakulofidiya) ce da ke ilimantar da jama'a yara da manya da maza da mata wajen samun ilimi a saukake, cikin harshen Hausa.