Category: Tatsuniyoyi

  • Tatsuniyar Wata Mata Da ’Ya’yanta

    Tatsuniyar Wata Mata Da ’Ya’yanta

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can kudu da garin su Gizo da Koƙi akwai wata mace mai ’ya’ya mata su huɗu, waɗanda ubansu ɗaya. Suna nan zaune cikin jin daɗi, sai ciwo ya kama mijinta, watau uban yaran nan. Da ya ga kamar ba zai tashi ba, sai ya sa aka yi wa ’yan matan nan huɗu aure. Bayan kamar wata uku da aurar da su, sai ya cika.

    Ɗaya daga cikin ’ya’yan nan ta yi aure a garin da ba a barci; ta biyu ta yi aure a garin da ake tsinkar gauta da hanci da tsinkar kuɓewa da ƙirji; ta uku kuma ta yi aure a garin da ba a cin abinci, ba a kashi sai dai a sha romon nama; ta huɗun ta yi aure a garin da ba a kwana a gida sai a can sararin sama. Wata rana sai matar ta shirya za ta ziyarci ’ya’yanta.

    Sai ta ɗauki ƙwarya ta kama hanya sai garin ’yarta ta fari, watau garin da ba a barci. Da ta je gidan ’yarta, sai ’yar ta razana ta ce: “Inna me ya kawo ki garin nan da ba a yin barci?” Tun da tana son ganin ɗiyarta, sai ta ce mata: “Ai tun da babanku ya rasu ban sake barci ba.” Sai ’yar ta ce: “To shi ke nan.” Suka zauna ta yi mata abinci ta ci.

    Da dare ya yi sai suka kama hira a cikin ɗaki. Can sai uwar ta fara gyangyaɗi. Da ’yar ta ga haka, sai ta ce da gyatumarta: “Kada ki yi barci fa.” Sai ta juya suka cigaba da hirarsu da mijinta. Jiki da jini, can sai uwar ta kwanta ta kama barci. Da mijin ’yar ya lura surukarsa ta kwanta tana barci, sai ya fita ya tara mutane ya ce surukarsa ta rasu.

    Da gari ya waye, sai masu haƙa ƙabari suka tafi maƙabarta suka kama aiki. Aka shiga shirye-shiryen binne wannan matar. Data ji hayaniyar mutane, sai ta fito tana yi musu magana, tana cewa ita fa ba ta mutu ba, barci kurum ta yi. To su ba su san barci ba. Sai
    wani daga cikin mutanen da suka taru ya ce wa sauran da ke saurarenta: “Yaya kuke magana da fatalwa bayan kun san ta mutu?

    Mutum zai mutu ya dawo ne?” Wannan abu ya tsorata matar, saboda haka sai ta koma cikin ɗakin ’yarta; sai ’yarta ta ce: “To kin san na gaya miki ba a barci a nan garin; su ba su san barci ba.” Baƙuwar nan ta rasa yadda za ta yi. Idanu suka raina fata. Can dai wata dabara ta faɗo wa ’yar. Ta dubi uwar ta ce: “Zo in fitar da ke ta danga ki gudu, in ba haka ba za su binne ki da rai.”

    Sai ta ja ta suka bi ta bayan gida, ta buɗe mata hanya ta gudu ta nufi garinsu. Bayan kwana ɗaya da komawar matar nan gida, sai ta ce bari ta je garin ’yarta ta biyu, watau garin da ake tsinkar gauta da hanci kuma a tsinki kuɓewa da ƙirji. Sai ta kama hanya har ta isa garin. Da ta isa gidan ’yar, sai ’yar ta ce: “Inna me ya kawo ki nan?

    Kin sani fa a nan garin ba a cin abinci. Kowa sai dai ya tsinki kuɓewa da ƙirji, kuma ya tsinki gauta da hanci. Shi ne iyakar abinda mukan ci. Idan kuma ba ki tsinka ba, to kuwa ba za ki ci komai ba.” Da jin haka sai uwar ta ce: “Haba, ai mu ma a garinmu da ƙirji muke tsinkar kuɓewa, sai da na auri babanku na daina.” Sai ’yar ta ce: “To shi ke nan.”

    Da yamma ta yi duk sauran matan gida suka ɗunguma gona tsinkar kuɓewa tare da baƙuwar. Kowa ya kama yana tsinka, har suka ƙoshi. Amma baƙuwar nan ba ta tsinka ba, ƙirjinta ko ya dame ta da ƙaiƙayi. Haka ta kwana da yunwa. Washe-gari ma kowa ya tsinki kuɓewa da gauta da ƙirjinsa, amma ban da ita.

    Ta sake kwana da yunwa. Da ta ga ta kwana biyu ba ta ci komai ba, sai ta gaya wa ’yar za ta koma gida. Da ’yar ta ji haka, sai ta dubi uwar tace: “To, bari in raka ki.” Sai ta riƙe wa uwarta ƙwaryarta ta raka ta bayan gari, suka yi bankwana, kowa ya koma garin da yake. Da matar nan ta isa gida ta huta kwana ɗaya sai ta shirya ziyartar ’yarta ta uku, watau dai ba ta daddara ba.

    ’Yar kuwatanacan garin da ba a cin nama ne sai dai romo, domin su zubar danama suke yi idan sun dafa. Sai ta haɗa kayanta, ta kamahanyasai garin ’yarta ta uku. Da ta isa sai ’yar ta yi mamakin ganinta, kuma ta ce da ita, “Inna ba za ki iya zama a garin nan ba fa sabodaa nan ba a cin abinci, ba a yin kashi, kuma ba a cin nama sai dai romon naman.”

    To abin ka da wanda ya saba da gardama, sai uwar ta ce: “Haba, ai ni rabona da cin abinci tun sanda babanku ya mutu.” Da ta ji bayanin uwar sai ta ce: “To shi ke nan.” Sai suka zauna. Da lokacin cin abinci ya yi, sai ta ga ’yarta ta dafa nama mai yawa, ta tsiyaye romon, za ta zubar da naman, sai tace: “Haba ’yar nan ai kin gaji, bari in je in zubar miki da shi.” Da ta karɓi nama ta fita bayan gida sai ta zauna ta cinye shi duka.

    Bayan ta dawo sai ’yar ta tambaye ta: “Yaya na ga kin daɗe baki dawo ba?” Da uwar ta ji wannan tambaya sai ta ce: “Ai bayan gari na kai.” Sai ’yar ta ce: “To madalla, hakan ya yi.” Can cikin dare sai uwar ta tashi daga barci ta ce wa ’yar tana jin kashi. Sai ’yar ta ce mata: “Ki tuna fa na gaya miki ba a yin kashi a nan garin, shi ya sa ma ba mu da shadda a nan garin.”

    Da kashin ya matsanta wa uwar, sai ’yar ta ba ta tukunya ta cika ta da kashi; ’yar kuma ta ɓoye tukunyar kashin. Da gari ya waye sai kajin garin suka kama cara da kuka suna cewa: “Kukuruku, an yi kashi a garin nan.” Idan akuya ma za ta yi kuka sai ta ce: “Be, be, be, an yi kashi a garin nan.” Haka dai duk dabbobi suka dinga yin wannan fallasa a cikin kukansu.

    Da abin ya yi yawa sai Sarkin garin ya tara mutanen garinya ce: “Wane ne ya yi kashi a garin nan?” Kowa ya ce bai sani ba. Aka yi ta bincike, kowa yana cewa bai yi kashi ba, kuma ba su san wanda ya yi ba. Da Sarki ya ga magana tana nema ta yi tsawo, sai ya ce: “To za a yi al’adar da aka saba yadda duburar duk wanda ya yi kashin nan za ta riƙa waƙa, kowa ya ji a gari.”

    Sarki ya sa aka yi magani; nan take duburar matar nan ta fara waƙa. Da ’yar ta ji sai ta ce: “Inna zo in raka ki domin kada a sani mu ji kunya.” Nan dai a cikin gaggawa ta tattara kayanta, ta raka ta bakin gari suka yi ban kwana ta tafi bayanta na waƙa. Matar nan tana cikin tafiya a dajin da ke tsakanin garin da ta je da wanda za ta, sai ta haɗu da wani Bafulani yana kiwo; sai yace yana son abin nan da ke yin wannan waƙa mai daɗi haka.

    Sai tace: “Zan ba ka idan za ka ba ni shanu biyu.” Kamar da wasa sai ya amince da hakan. Ta ce masa ya yi kashi ya shafa mata, abin zai koma jikinsa. Sai ya ba ta shanu biyu, kuma ya yi kashi ya dangwala ya shafa mata. A nan take abin ya koma jikinsa, yana waƙa. Sai ya shiga daji da shanunsa yana murna.

    Ita kuwa ta kora shanunta biyu ta shiga gari, ta je gida ta ɗaure kayanta. Bayan kwana biyu sai matar nan ta shiga shirin zuwa wurin ɗaya ’yarta wadda a garin da take aure ake kwana a sama. Shi kenan ta ɗau hanya, tana isa garin ta zarce gidan auren ’yarta. Da ta ga uwarta ta yi murna, amma sai ta ce mata: “Sai dai fa mu a nan garin idan dare ya yi muna tashi sama mu kwana a can ne saboda mayu suna yawan zuwa nan.”

    Sai uwar ta ce: “Ai babu komai, zan yi tsalle in hau sama kamar yadda kowa zai yi.” A nan ne fa ’yar ta ce: “To yi tsallen mu gani.” Kamar da gaske, uwar ta fara gwadawa. Da ta ɗaga ƙafa sai ta faɗi, ta yi ta yi, har ta gaji, kuma ga shi dare ya yi. Tun da an riga an makaro, sai ’yar ta ce wa uwar: “Zan ɓoye ki a cikin ɗaki, amma kada ki yi magana ko da za ki ji ana ta buɗe-buɗe da bincike a ɗakin.

    Domin mayun ne ke neman mutanen da ke kwana a ƙasa su cinye.” Uwar ta amsa mata cewa ba za ta yi magana ba. Can matar tana kwance a ɗaki sai ta ji motsi da ɓuruntu. Sai ta manta da dokar da ’yar ta sa mata ta rashin magana, ta ce: “Wane nenan?” Kafin ta gama rufe baki mayun nan sun afka kanta, sun cinye ta. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Idan ka baƙunci gari ka tarar da mutan garin kowa da wutsiya to kai ma ka sami zangarniya ka saka, sai ka zauna lafiya.
    • Wanda bai ji bari ba, ya ji hoho.
    • Da muguwar rawa, gwamma ƙin tashi

    Danna nan don karanta Tatsuniyar ‘Yan Bakwai Da Aljana

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ‘Yan Bakwai Da Aljana

    Tatsuniyar ‘Yan Bakwai Da Aljana

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can kusa da dajin aljannu wanda aka ce ya yi iyaka da bangon duniya, akwai wata mata mai ’ya’ya maza su bakwai. Ana nan, ana nan sai yaran suka girma, har dai suka isa aure. Da gyatumarsu ta ga sun isa aure, sai ta tara su ta ce: “Ya kamata a ce yanzu kun yi aure, tunda ga shi Allah ya sa duk kun girma, kowa ya mallaki hankalinsa.”

    Da suka ji haka, sai babban cikinsu ya ce wa uwar: “Za mu yi aure, amma muna so a sama mana ’yan mata bakwai waɗanda suke uwarsu ɗaya.” Sai babarsu ta ce: “Kash, amma ai duk garin nan babu irin ’yanmatan da kuke so, sai dai ku tlafi nema wani garin.”

    Sai suka bi maganar mahaifiyarsu, suka shirya suka kama hanya za su neman matan aure. Bayan ’yan bakwai sun bar gari sun kama hanya, sun yi tafiya mai nisa, sai suka haɗu da wata mata da ’yarta ɗaya suna noma. Da ta ga samari bakwai rigis, sai ta ɗaga kai ta dube su tace: “Sannunku samari.” Su kuwa suka amsa gaisuwarta a cikin ladabi.

    Sai ta tambaye su inda za su. Sai babbansu ya ce mata: “Za mu je neman matan aure ne.” Da ta ji haka sai ta ce: “To ga ’yata idan za ku aura.” Tare da ban girma sai ɗaya daga cikinsu ya ce: “A a, muna neman ’yan mata bakwai ne waɗanda suke uwarsu ɗaya kamar mu.” Wannan bayani ya rufe mata baki, sai ta ce: “To, shi ke nan; ni dai
    ’yata ɗaya ce idan za ku karɓe ta.”

    Sai suka ce: “A a, mun gode.” To ashe wannan mata aljana ce ba su sani ba. Da suka yi nisa daga inda take, sai ta yi irin saurin aljannu ta je can gabansu a wata gonar da ’ya’ya mata biyu. Saboda suna da ladabi da girmama manya, a nan ma suka gaishe ta, ba tare da sun san ita ce ba, saboda ta sauya kama. Matar nan ta tambaye su labarinsu, suka faɗa mata tare da bayani a kan abin da suka fito nema.

    Sai ta nuna za ta ba su ’yanmatan nan biyu idan sun amince. A nan ma dai a cikin hikima suka yi mata bayanin cewa ’yan mata bakwai ’yan ciki ɗaya suke nema. Suka wuce suka bar ta a wannan gonar. Da matar nan ta ga sun wuce, sai ta ɓata, ta je gaba ta ƙara sake kamanni. Ta shiga wata gonar tare da ’yan mata uku.

    Haka dai ta dinga yi musu har sai da suka kai biyar. Sai suka ce su fasai sun sami ’yan matan da su ma bakwai ne kamar su. Sai aljana ta sake ɓata, ta rikiɗa ta zama wata mata kyakkyawa mai ’ya’ya mata bakwai suna taya ta noma. Da samari bakwai suka zo za su wuce sai matar ta yi musu sallama. Da suka gaisa sai ta tambaye su inda za su.

    Kamar yadda suka saba yin bayani a baya, sai suka ce za su neman aure ne, to amma sai ’yan matan da zasu aura ɗin sun kai bakwai, kuma ’yan ciki ɗaya kamar su. Da jin haka sai ta ce wa babban cikinsu: “To tun da mun haɗu ni ma ina da ’yan mata bakwai ’yan ciki ɗaya kamar ku, in kun yarda sai in haɗa ku.” Sai baki ɗaya suka amsa mata: “Yawwa; yanzu muka sami matan da za mu aura.”

    Daga nan sai matar nan ta kai su gidanta, ta sa ’yan matan suka yi wa samarin nan ruwa. Da suka ɗebo ruwa suka kawo, sai kowacce ta ba wanda za ta aura; amma fa ruwan ba ruwa ne na gaske ba, duk jini ne, in ban da na ɗan’auta; shi yarinyarsa ba ta kawo masa ruwan jini ba.

    Da ’yan matan suka tafi sai ɗan’autansu ya ce kada su sha ruwan da aka ba su saboda jini ne, ba ruwa ba. Da sauran suka ji haka, sai suka zubar, ya ba su nasa suka sha suka ƙoshi. Can kuma sai ’yan matan suka shiga dafa wa baƙinsu abinci. ’Yan mata shiɗa suka ɗebo naman mutane da uwar ta yi tanadi, suka shiga dafa wa samarinsu; amma ƙaramar cikinsu ta ɗan’auta, sai ta ɗebo naman shanu ta girka wa masoyinta ɗan’auta.

    Da suka dafa abinci suka kawo wa mazajensu, sai da aka zo cin abinci, ɗan’autansu ya ce su zubar da abincin domin da naman mutane a ciki. Da suka zubar sai ya kawo musu nasa suka ci, har suka ƙoshi. Da dare ya yi, sai aka nuna wa kowannensu ɗakinsa shi kaɗai. Amma ɗan’auta da amaryarsa sai suka shiga wata bukka.

    Can bayan duk sauran sun yi barci, sai surukarsu, watau aljana ta fara wasa wuƙarta domin ta riga ta yanke shawara idan dare ya yi za ta yanka su duka. Saboda ɗan’auta ya san abin da matar take son yi, sai ya zagaya ya shiga kowane ɗaki, yana cire wa mazan kayansu yana sa musu na mata, su kuma matan yana sanya musu kayan mazan.

    Da ya gama, ya koma ɗakinsa ya shirya ya kama tona rami har zuwa garinsu. Da ya gama sai ya kwanta yana sauraron matar nan ta dinga shiga ɗaki-ɗaki tana yanka ’ya’yanta ba tare da ta sani ba. Da ɗan’auta ya tabbatar matar ta gama yanke-yanken ta koma, sai ya fita ya tashi duk ’yan’uwansa don su gudu.

    Sai suka shiga ramin da ya tona suka tafi gida. Ita kuwa aljana da gari ya waye sai ta fara buga ƙofofin ’ya’yanta don su tashi, amma shiru. Da ta karairaya ƙofofin ta shiga ɗakunan, sai ta tarar ashe ’ya’yanta ne ta yanka gaba ɗaya. A nan take ta fara kuka. Da ta ɗan huce, sai ta ce sai ta yi maganin yaran nan.

    Sai ta rikiɗa ta zama goɗiya ta shiga garin ’yan bakwai. Da ta je daidai gidansu sai suka gan ta. Sai ɗan’auta ya ce a bar shi ya kama ta, sai babbansu ya ce: “Ai kai ne ƙarami don haka bai kamata ka kama goɗiyar nan ba.” Sai ya bari babbansu ya kama ta ya ɗaure ta cikin gidansu yana kiwonta, har ta yi ƙiba, ta yi kyau.

    Bayan wasu kwanaki sai ɗan’auta ya ce da yayansa: “Yau zan kai maka goɗiyarka rafi.” Sai ya ce: “To, na gode.” Sai ya kwance goɗiya ya kai rafi ya ɗaure a jikin bishiya; sai ya samo wata babbar sanda ya fara jibgar goɗiyar nan yana waƙa yana cewa: “Ba goɗiya ba ce, aljana ce.”

    Ya doke ta sosai har ta rame. Da ya koma gida da goɗiyar sai yayansa ya ga duk jikinta jina-jina, kuma ta rame. Ganin haka sai yayan nasa ya kama shi da faɗa. Sai ɗan’auta ya ce: “To shi ke nan, muna nan da kai za ka zo ka yi da-na-sani.” Washe-gari sai babban wan su ɗan’auta ya hau goɗiyar domin ya kai ta rafi shan ruwa.

    Amma da goɗiyar ta ga sun fita daga cikin gari, sai ta kama sukuwa kamar za ta tashi, ba ta tsaya ba sai a gidan aljanar da ta so yanka su. Tana isa ta zame, ya faɗo ƙasa, kuma ta rikiɗa ta koma siffarta ta aljana. Sai ta dube shi tace: “’Yan banza; ni kuka kashe wa ’ya’ya, to duk sai na cinye ku. Tashi ka jiƙa waccan tokar miyar don zan dafa ka da ita in an jima da daddare.”

    Sai ya tashi ya jiƙa tokar miya; sai aljana ta ce: “Zauna kusa da tokar don da ita zan dafa ka.” A can gida ba a ga yayan ɗan’auta ya dawo ba, sai ɗan’auta ya rikiɗa ya koma ɗan maraƙi ya je gidan aljana. Daga shiga sai ya nufi inda ɗan’uwansa yake zaune, ya ture tokar da ke gabansa.

    Da babban ya ga haka sai ya ce wa aljana: “Kin ga ɗan maraƙi ya zo ya zubar da ruwan tokar.” Sai aljana ta ce: “Maza ka kwashe ka kai can waje, ka dawo ka sake jiƙa wata.” Shi kuwa sai ya bi umarninta. Ya kori ɗan maraƙi waje, sai ya sake jiƙa toka ya zauna a gefe. Yana zaune sai ɗan maraƙi ya sake zuwaya zubar da ruwan tokar.

    Sai ya tashi ya kirawo aljana ya gaya mata cewa ɗan maraƙin nan ya sake zubar da ruwan tokar. Sai aljana ta ce: “To ka kora shi ka kai shi bakin gangaren can mai
    nisa.” Da ya kora ɗan maraƙi har suka yi nisa da gidan aljana, sai ga ɗan maraƙi ya koma ɗan’auta. Sai ya dubi yayansa ya ce: “Ai dama na gaya maka ka yi hankali da goɗiyar nan.”

    Ba dai tare da ɓata lokaci ba sai ya ce da yayansa su tafi gida. Nan da nan suka kama hanya. Can da aljana ta ga shiru, sai ta bi sawu, sai ta ga alama lallai sun gudu. Sai ta ce: “Zan yi maganin ɗan’auta.”A nan take aljana ta rikiɗa, ta zama kyakkyawar budurwa ta shiga garin su ’yan bakwai, tana tafiya har ta kai ƙofar gidansu. Da suka gan ta sai suka ce dukkansu kowa yana son ta, amma daga ƙarshe suka amince a bar wa yayansu ita.

    Suka bar masa, aka ɗaura musu aure. Da dare ya yi suna ɗaki da matarsa sai ya ga ta rikiɗa ta zama aljana; sai ta ce: “Kun ɗauka za ku tsira daga sharri na ne?” Kafin ya ma gane abin da yake ciki, sai ta yi farat ta ƙwaƙwale masa ido, ta tafi da shi. Da gari ya waye aka buga ƙofa, sai aka ji shiru. Ɗan’auta ne ya kira yayansu ya amsa, sai ya gayawa ƙannensa amarya ta ƙwaƙwale masa idanu.

    Ɗan’auta ya ce shi kenan, ya san abin da zai yi; ya kama hanya ya je bakin rafi ya cika cikinsa da ruwa, ya rikiɗa ya zama tsohuwa, ya yafa mayafi ya tafi gidan aljana. Da ya isa ya yi sallama, sai ta amsa. ’Yar tsohuwa ta shiga ta ce wa aljana ta ji an yi mata rasuwa shi ya sa ta zo yi mata gaisuwa, kuma ta ƙara ba ta haƙuri da rashin da ta yi.

    Da aljana ta ji jawabin tsohuwa, sai ta yi mata godiya, kuma tace: “To me zan ba ki ne tsaraba tun da kin zo yi mini ta’aziyya daga nesa?” Sai tsohuwa ta ce: “Haba babu komai, sai dai ina da wata matsala da ta dame ni.” Da aljana ta ji haka sai ta ce: “Wace irin matsala ce?” Sai tsohuwa ta shiga marairaita ta ce wai yau mijinta ya yi shekara da shekaru ba shi da ido, da yana gani ma da tare za su zo gaishe ta.

    Da ta ji wannan sai ta ce wa tsohuwa: “Haba ai babu komai; ina da wasu idanu da na ƙwaƙwalo na zo da su jiya. Sai ki ɗauka, idan kin je gida ki jiƙa su a rama ki sa masa su.”
    ’Yar tsohuwa ta yi godiya, ta ɗebi idanu ta kama hanya. Da ta fita waje sai ta rikiɗa, Ɗan’auta ya koma kamanninsa na farko ya ƙyalkyace da dariya.

    Ashe aljana ta gane shi ne ya zo; sai ta ji haushi ta ce: “Na san yadda zan yi da shi da ’yan’uwansa.” Da ɗan’auta ya je gida, sai ya samo rama ya jiƙa idanun, ya sanyawa yayansa, nan da nan ya fara gani. Ana nan sai wata rana ’yan bakwai suka tafi daji su yanko ciyawa. Da suka yanka, sai kowa ya ɗaure tasa, amma sai ɗan’auta ya ga wani babban maciji ya shiga ta yayansu.

    Sai kawai yace: “Yaya ka bar mini taka zan ɗauka, kai ka ɗauki tawa.” Sai yayan ya amince da maganar ɗan’auta. Sai ɗan’auta ya sami igiya ya ɗaure ciyawar yayan nan tamau, yadda macijin nan ba zai iya motsi ba. Ya yi haka ne domin ya san aljana ce ta zama maciji.

    Da kowa ya ɗauki ciyawarsa suka kama hanyar gida, can sun kusa da gari sai suka tarar an hura wuta tana ci ganga-ganga, abin ban tsoro. Sai ɗan’auta ya jefa ciyawarsa a cikin wutar. Da suka ga haka, sai ’yan’uwansa suka ce: “Me ya sa ka jefa ciyawar ka a cikin wuta?” Sai ya ce: “Ku tsaya za ku gani.” Can da wutar ta lafa, sai ya ɗauki kara ya tona ciyawarsa, sai suka ga macijin nan ya ƙone ƙurmus.

    Mamakin baiwar ɗan’auta ya kama ’yan’uwansa. Shi kuwa ba abin da ya dame shi; sai yace musu: “Mu tafi gida, daga yanzu ƙaryar aljanar nan ta ƙare.” Wannan ne ya sa a ko ina ake tsoron ’yan bakwai. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Ba kullum akan kwana a kan gado ba.
    • Yawan shekaru ba shi ne wayo ba, Allah na yin baiwarsa ga wanda ya so yaro ne shi ko babba.
    • Mugun nufi ba ya kashe ɗan kurciya.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Wata Mayya Da Danta

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Wata Mayya Da Danta

    Tatsuniyar Wata Mayya Da Danta

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wata mayya a wani gari, tana zaune da mijinta, har ta sami rabo. Daga ƙarshe ta haifi ɗanta namiji aka sa masa suna Malgwi. To da man tun tana da cikinsa ubansa ya rasu, ya bar dokinsa, wanda yaron ya gada. Uwar ta kula da dokin har Malgwi ya girma, ya zama saurayi kyakkyawa.

    Wata rana sai wata ƙawar uwar Malgwi ta ziyarci gidansu. Sai ita da baƙuwa suka zauna a tsakar gida suna hira. Sai ƙawar tace da ita: “Ya kamata ki san yadda kika yi da ɗanki tun da ya girma ya kai a cinye shi.” Sai uwar ta ce: “E, ai ina shiri, kuma a daren yau zan gama da shi, na ga ya fara shige-shige.”

    Ashe Malgwi yana bakin ƙofar ɗaki yana jin duk abin da suke faɗa; sai ya fita waje ya sami wuri ya zauna, ya kama kukan zuci yana cewa ashe uwarsa mayya ce bai sani ba? Kuma ƙila ma ita ce ta cinye babansa, yanzu kuma za ta cinye shi. Nan dai ya yanke shawarar barin garin; sai ya je ya kwance dokin da ubansa ya mutu ya bari, ya ɗaura masa sirdi ya hau ya kama hanya, ya bar garin.

    Da uwar Malgwi ta fito daga ɗaki ta ga an kwance doki, sai ta fita tana tambaya ko an ga wanda ya kwance doki. Sai waɗanda suka gani suka gaya mata cewa ɗanta ne ya wuce a kan dokin, ya bar garin. Sai ta koma gida ta sa rigar maitarta, ta fito bin sawun Malgwi. Duk sanda ta yi taku ɗaya sai ta je kusa da shi, shi kuma sai ya ƙara zaburar doki, yana sulalewa yana waƙa yana cewa: “Dokin baba kai ni gari ba kusa ba.”

    Ita kuma uwar tana ba shi amsa tana cewa: “Ga ni nan Malgwi, ga ni nan ɗana.” Haka dai tana gudu ɗuwawunta biyu suna motsi suna waƙa suna cewa: “Ka tumbuɗe ka durje, Da ka faɗi bakin maza.” Ita kuma tana cewa: “Ga ni nan Malgwi, Ga ni nan dana.” Haka ya ci gaba da sukuwa a kan dokin nan.

    In sun haɗu da mutane sun tambaye shi abin da ya sa shi gudu haka sai yace:
    “Abin da ke bayana fi ƙarfin kowa, ku ba ni hanya.” Yana cikin wannan gudun ceton rai, sai wasu mutane suka sake tsai da shi, amma sai ya ƙi tsayawa har dai ya kai gaɓar wani babban gulbi; sai dokin ya tsaya.

    Da Malgwi ya ga dokin ya tsaya, sai ya fara waƙa yana cewa: “Dokin baba kai ni gari, ba kusa ba.” Da doki ya ji waƙa sai ya faɗa cikin ruwa yana ninƙaya har suka haye, kuma suka shiga cikin wani ƙungurmin daji wanda ke cike da aljannu da manyan namun daji. A nan ne fa shi da dokin suka yi cirko-cirko, suka kasa yin gaba, balle kuma baya.

    Da ƙurar hanya ta lafa, sai ga wasu manyan namun daji a tsugune suna kallon Malgwi da dokinsa. Sai suka tambaye shi labarin halin da yake ciki, sai ya yi musu bayani. Da suka ji bayaninsa, sai suka ba shi izini ya sami wuri a gindin wata bishiya da ke kusa ya zauna ya huta. Da ya ɗan zauna yana hutawa, sai namun dajin nan suka ce masa za su taimake shi.

    Ya ɗaure dokinsa, ya yanki ciyawa ya sa a gabansa, doki kuma ya fara ci. Can Malgwi ya fara hutawa, har da ɗan gyangyaɗin gajiya, sai ga uwarsa ta iso inda yake a guje, tana haki da waƙa. Sai ɗaya daga cikin namun dajin nan ya buɗe bakinsa, wanda ya fiƙofar gari girma. Ita kuwa idanunta sun rufe, ga shi ta doshi Malgwi gadan- gadan za ta yi masa rungumar mutuwa irin ta mayu, sai ta faɗa bakin babban naman dajin nan, ya haɗiye ta.

    Bayan ya haɗiye ta, sai ya sami ruwa ya sha, ya yi gyatsa kuma cikinsa ya ɗan ɗaga kaɗan, amma fa bai ƙoshi ba, saboda ya daɗe bai ci komai ba. Sai namun dajin suka dubi Malgwi suka ce masa: “Mun yi maka maganin mayyar nan. Idan ka ga dama sai ka kama hanya ka koma garinku.”

    Da Malgwi ya ji haka, sai ya yi musu godiya; ya kwance dokinsa, ya ɗaura masa sirdi, ya hau, ya haye ruwa, ya kama hanyar garinsu, bai tsaya ba har gida. Ƙurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Makusancinka na iya zama makashinka:
    • Ana zaton wuta a maƙera, ashe tana masaƙa:
    • Mai rabon ganin baɗi, sai ya gani:
    • Ceto daga Ubangiji yakan zo ta kowane hali:
    • Zarmewa wajen kula da yaro takan janyo masa bala’i ta fuskar da ba a zata ba.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Awa Da Dawi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Awa Da Dawi

    Tatsuniyar Awa Da Dawi

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana Awa da Dawi suna kiwo a daji, sai wani abu ya tsoratar da su. Kowa ya kama gabansa domin neman tsira. Suka ɓace wa juna. Da Dawi ya nemi ƙanwarsa bai gan ta ba, sai ya kama hanya ya tafi. Ita kuma ta nemi hanya ta rasa. Ta riga ta ɓata a dajin nan.

    Sai tafiya take ta yi, ba ta san inda za ta ba, har dare ya yi. Da ta gaji, kuma ga dare ya yi, sai ta sami gindin wata bishiya ta kwanta, har gari ya waye. Da sassafe tana kwance sai wata tsohuwa da ta yi sammakon neman ganyen miya ta tarar da ita. Da tsohuwar nan ta ga Awa a kwance sai ta tashe ta daga barci, tace da ita: “Ke yarinya me ya kawo ki nan?”

    Sai Awa ta kwashe labarin yadda suka yi da ɗan’uwanta ta gayawa tsohuwa. Sai tausayinta ya kama tsohuwa, ta dubi Awa tace da ita: “To idan kin yarda ki zo mu tafi da ke gidana.” Nan take Awa ta yarda suka tafi gidan tsohuwa, ta ba ta masauki da abinci. Awa ta ci abinci ta ƙoshi, ta yi wanka ta zauna.

    Da tsohuwa ta kalli Awa, sai ta ga yarinya ta ƙara kyau. Dama yunwa da dauɗa da gajiya da tsoro ne suka ɓoye kyaunta. Sai tsohuwa ta yanke shawarar kai wa Sarkin garin labarin Awa ko zai so ta. Nan da nan ta isa gidan Sarki, ta same shi a fada, ta durƙusa ta yi gaisuwa ta ce: “Ranka ya daɗe, na zo maka da wani albishir idan kana da buƙata.”

    Sarki ya ce: “Albishir na mene ne?” Sai tsohuwa ta ce wa Sarki “Ina da wata kyakkyawar yarinya wadda za ta dace da kai idan za ka yarda ka aure ta.” Sarki na jin haka sai ya ce: “A kawo ta in gan ta.” Da tsohuwa ta ji haka, sai ta je gida ta gaya wa Awa, kuma suka tafi fada tare.

    Da Sarki ya ga Awa sai ya ce zai aure ta. Ba jimawa aka ɗaura musu aure da Sarki, ta tare a gidansa. Bayan wasu ’yan shekaru, sai Awa ta haifi ɗanta aka raɗa masa sunan yayanta wanda ya ɓata, watau Dawi. Ana nan sai Sarki yace kada a riƙa katse ƙashin ɗansa da ƙara domin zai ji masa ciwo, sai dai da hantar sa.

    Haka kuma ake yi. Kullum da safe sai a yanka shanu, a yanke hantar da huhun a ba Awa ta riƙa share wa yaron ƙashi da su. Wata rana sai Awa ta gaya wa Sarki tana so ta ziyarci iyayenta. Sai ya tambayi sunan garinsu, ta faɗa. Sarki ya sa cigiyar wanda ya san garin. Aka yi sa’a, aka samu.

    Sai aka haɗa shi da matar Sarki da doki ya kai ta garinsu. Kafin su tafi sai aka yanka shanu aka zuba mata hanta da huhu a cikin ƙwarya don katse ƙashin ɗan Sarki, aka kawo kayan tsaraba masu yawa aka ba ta. Da Awa da ɗan rakiyarta suka kama hanya, har Allah ya kai su garin lafiya, murna ta kama ta. Sai ta doshi gidan iyayenta, ta shiga.

    Mutanen gidan suka yi murnar ’yarsu ta dawo. Bayan sun huta, sai ta ba su labarin abin da ya faru har zuwa aurenta da Sarkin garin da suke. Iyayenta da sauran danginta suka yi ta murna. Awa ta kawo kayan tsaraba ta ba iyayenta da sauran’yan’uwanta. Suna zaune ana hira sai ɗanta ya yi ƙashi, sai nan da nan ta zaro hanta za ta katse ƙashin yaron da ita.

    Da uwar ta gani sai ta ce: “Me za ki yi da wannan hanta?” Sai Awa ta ce: “Ai da hanta ake katse ƙashin ɗan Sarki, ba a katse masa da ƙara; mahaifinsa ya hana.” Mamaki ya kama mahaifiyar Awa da ta ji wannan batu. Sai ta shiga tunanin cewa ga abin da mutum ba zai iya samu ya ci kullum ba ya zama abin katse ƙashin jikanta.

    Daga nan sai ta shiga ƙulla yadda za ta kwashe hantar ta cinye. Shi ke nan sai uwar ta kira Awa ta ce mata: “Ɗauki gora ki je ki ɗebo mana ruwa a rafi.” Saboda halinta na bin iyaye, sai kawai tace: “To, amma ki kular mini da yaron nan don ba zan je rafi da shi
    ba.” Sai kakar yaron ta ce: “To, zan lura da shi.”

    Da ta ga lallai Awa ta tafi ɗaukar ruwa rafi, sai ta kwashe hantar katse wa ɗan Sarki
    ƙashin da ta zo da ita gaba ɗaya, ta gasa ta cinye. Da yaron ya yi ƙashi kafin Awa ta dawo daga rafi, sai uwar ta ɗauki ƙara ta katse masa da shi.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Tsautsayi ba a sa maka rana.
    • Mai mugun hali tun a duniya sai ya ɗanɗana kuɗarsa.
    • Aikin da ba a yi shi da kyakkyawar niyya ba ƙarshensa nadama.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Maye Da ’Ya’yansa

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Maye Da ’Ya’yansa

    Tatsuniyar Maye Da ’Ya’yansa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum a wani gari da ke gabas da garin nan. Yana da mace ɗaya da ’ya’ya biyu mata. Da suka isa aure Allah ya ba su masoya, aka yi musu aure aka kai kowacce ɗakinta. Bayan ’yan shekaru kowacce ta haifi ’ya’ya. Ana nan, sai aka aika musu uwarsu ta rasu; sai dai su ba su san cewa ubansu maye ne ba, kuma shi ne ma ya cinye uwar tasu.

    Shi ke nan yaran nan suka je gidan ubansu saboda zaman makoki, amma sai suka tarar uban nasu ya cinye gawar uwar tasu, domin yunwar maita ta kama shi, kuma babu wanda zai ci sai gawar. Da ya ji muryar ’ya’yansa, sai ya kulle kansa a cikin ɗaki don kada su gani, su gane.

    Duk sanda suka kai masa abinci, sai yace su ajiye a ƙofar ɗaki. Bayan sun yi kwana biyu a gidan, sai a dare na uku ya tara su, ya fara zaro harshe yana haɗiyar yawu. Sai suka gane cewa shi ya cinye babarsu, kuma yana so su ma ya cinye su. Da man sunan ɗaya Nkwa, ɗaya kuma Sektiraye.

    Sai ya fara kiran su yana cewa: “Nkwa da Sektiraye duk da ’ya’yanku, Ku jira ni ina zuwa, Zan cinye ku, Da man ina jin yunwa.” Da suka ji haka sai suka kama ’ya’yansu suka ɓuya, kuma suka ajiye kabewa a kan gado suka lulluɓe ta. Da dare ya yi tsaka, sai
    kawai ya tashi ya kama cin kabewar da ke kan gado.

    Da ya gane ba nama ba ne, sai haushi ya kama shi. Can kuma sai ɗaya daga cikin jikokinsa ya fara kuka a inda suka ɓuya. Da ya gane inda suka ɓuya, sai ya yi kukan kura ya auka musu, amma bai cafki ko ɗaya ba. Sai ’ya’yan nasa da jikokin suka fito da gudu, suka kama hanyar dajin da ke kusa da garin, shi kumayana bin su.

    Suna cikin gudu a dawan nan sai ya kama ɓarin jikinsa ya cinye, har dai ya zama saura ƙashi a jikinsa kawai. A hakan yake bin su da gudu yana cewa: “Dun kwalak, ka dun kuci kal.” Da suka isa wani guri a cikin dajin, sai suka tarar wuta tana cin ciyawa, sai suka keta ta cikin wutar a guje.

    Saboda yawan wutar, har ta kama cin hanya. Da uban nasu wanda ya zama ƙwarangwal
    ya isa wurin wutar nan, sai ya faɗa cikinta, wuta kuwa ta cinye ƙasusuwansa, ya ƙone ƙurmus. ’Ya’yan nan nasa da jikokinsa sun sami tsira. Da gari ya waye, sai wasu mata masu neman tokar miya suka tarar da tokar wannan maye a kan hanyar, ba su san ta mutum ba ce.

    Sai ɗaya daga cikinsu ta ce su deɓi tokar miya. Sai suka ɗiba, suka koma gida. Sai ɗaya daga cikin matan ta haɗa tokar za ta yi miya da ita. Bayan ta ɗora tukunyar miya da tokar a ciki a kan wuta, sai ta ji miyar tana cewa: “Ki juya ni a hankali, domin wuta ta ƙona ni da yawa.” Da ta ji haka ba ta ce uffan ba, kuma ba ta daina girki ba, har sai da ta gama.

    Da ta gama, ta zuba, ta kai wa mijinta abincinsa a akushinsa. Data je ajiye akushin sai ta ji an ce: “Idan za ki ajiye ni, ki ajiye ni a hankali don wuta ta ƙona ni da yawa?” Da mijin ya ji, sai ya kira matarsa ya ce mata: “Na ji kamar miyar tana magana.” Sai ta dubi mijin tana murmushi ta ce: “Kai anya, ba kunnenka ba ne kuwa?”

    Sai mijin ya sa hannu zai buɗe akushi ya fara cin tuwo da miya, sai miyar ta ce: “Idan za ka deɓe ni, ka deɓe ni a hankali, don wuta ta ƙona ni sosai.” Da mijin ya ji haka, sai ya dubi matar ya ce: “To ashe ke mayya ce ban sani ba.” Sai matar ta ce: “A a ai a cikin jeji na samo tokar miya.”

    Sai mijin ya ɗauki miyar ya kwara mata a ƙirji. Nan take ƙirjinta ya fitar da haƙora gatso-gatso, abin gwanin ban tsoro. Da mijin ya ga haka, sai ya kore ta, sai ta shiga daji, ta koma can da zama. Duk wanda ya je dajin da take zai tarar da ita tana yawo, tana cin fari da kwaɗi. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Tsautsayi ba a sa maka rana.
    • Mai mugun hali tun a duniya sai ya ɗanɗana kuɗarsa.
    • Aikin da ba a yi shi da kyakkyawar niyya ba ƙarshensa nadama.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Binta ’Yar Sarki

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Binta ’Yar Sarki

    Tatsuniyar Binta ’Yar Sarki

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wani Sarki a wani gari mai mata biyu, kowacce tana da’ya. Yarinya ɗaya sunanta Binta, ɗayar kuma Falmata. Sarki yana ji da’ya’yan nan nasa, to amma fa ya fi son Binta don ita ce ƙarama, kuma ’yar amarya.

    Ana nan, rannan sai Sarki ya tafi wani gari mai nisa, kuma zai daɗe a can. Bayan ya tafi da ’yan kwanaki, sai ciwo mai zafi ya kama amaryarsa, watau mahaifiyar Binta. Da ta lura ciwon kamar ba wanda za ta tashi ba, sai ta kira kishiyarta ta gaya mata cewa tana jin ba za ta tashi ba, amma idan ta cika, tana roƙonta ta kula da’ya’yansu cikin amana.

    A cikin tausayi kishiyar ta ce da ita: “Zan yi bakin ƙoƙari na in kula da su.” Bayan kwana biyu da yini ɗaya, sai amaryar Sarki ta rasu. Sarki dai bai dawo daga tafiyar da ya yi ba har wasu ’yan kwanaki suka wuce. Rannan sai kishiyar uwar Binta ta sa ta ɗauko ruwa a rafi a cikin wani masaki, kuma ta gaya mata lallai a rafin Apko mai cinye mutane za ta ɗebo ruwan, watau ba a ɗaya rafin mai lafiya ba.

    Ɗaya rafin mai lafiya wanda daga shi mutanen suke ɗaukar ruwa sunansa Diddire. Binta ta ɗauki masaki ta garzaya wajen kabarin mahaifiyarta, tana kuka tana waƙa, tana cewa:

    “Baba, baba, babar Binta,

    Kishiyarki ta ce in je Apko in ɗebo ruwa,

    In je Apko ko in je Diddire?”
    Daga cikin kabarin sai ta ji mahaifiyarta ta amsa mata dawaƙatana cewa:

    “Ki je Diddire,

    Kada ki je Apko,

    Domin Apko zai apka da ke.”

    Sai Binta ta tafi rafin Diddire ta ɗebo ruwa. Da kishiyar uwarta ta ga ba ta ɗebo ruwan Apko ba, sai ta hau ta da duka. Ta ma zubar da ruwan da ke cikin masakin, ta ce lallai maza ta je ta ɗebo mata ruwa daga kogin Apko, kuma ta gaya mata cewa idan ta kuskura ta ɗebo mata ruwan Diddire, to za ta yanka ta.

    A kan dole Binta ta ɗauki masakin ta tafi rafin Apko ɗiban ruwa. Tana shiga za ta ɗebi ruwan, sai rafin ya cinye ta. Tana nan a cikin ruwa, har wasu ’yan kwanaki. Ita kishiyar uwarta ba ta sa an je nemanta ba, kuma ita ba ta je ba. Ko fadawa ma ba ta gayawa ba, har ranar dawowar Sarki.

    A ranar da Sarki ya dawo sai fadawa da jama’ar gari suka fita bayan gari suna yi masa barka da zuwa. Masu tambura suka goce da kiɗa, ana yi masa kirari ana cewa: “Baban Binta ya dawo, Sarki baban Binta ya dawo.” Da Binta ta ji ana buga tambarin babanta, ga shi kuma ba za ta iya fita daga ruwan ba, sai ta kama kuka da waƙa tana cewa:

    “Falmata ce ’yar Sarki,

    Babanta ya dawo,

    Falmata kin ji daɗi,

    Falmata ’yar Sarki.”

    Sarki ya sa ido ko zai ga Binta a cikin masu tarye, amma bai gan ta ba, kuma ya saɓa idan ya yi tafiya ya dawo akan ɗoro ta a kan doki, a kai ta gabansa, su gaisa. Ya sake dubawa bai ga Binta ba sai Falmata. Sai hankalinsa ya tashi, har dai ya kasa daurewa ya tambayi fadawansa inda Binta take.

    Sai suka ce ai Binta ta ɓata, ba wanda ya san inda take. Suka ƙara da cewa ai ma yau kwana goma sha tara kenan da uwarta ta rasu. Hankalinsa ya tashi, amma ya yi
    ta maza, ya shanye halin damuwar da yake ciki. Da ya shiga gida, sai ya kira uwargidansa, ya tambaye ta inda Binta ta je.

    Sai ta ce ba ta sani ba, tun da dai ta fita yawo ba ta sake komawa gida ba. Yana jin haka, sai ya sa aka shiga neman Binta. Wasu daga masu nemanta suka bi ta rafin Apko. Da fari ba su ga alamun kowa a can ba, to amma daga baya sai suka ji muryar mutum na waƙa a cikin rafin. Da suka kasa kunne da kyau, sai suka ji ana waƙa ana cewa:

    “’Ya’yan uwa kada ku zo Apko,

    Idan kun zo zai apka da ku,

    Ni kishiyar uwa ta aiko ni nan,

    Har ya apka da ni.”

    Da masu nemanta suka ji haka sai kawai suka koma suka shaida wa Sarki abin da suka jiyo a kogin Apko. Sai Sarki yace da su da sauran fadawansa su je tare da shi bakin rafin ya ji. Nan da nan suka dunguma, kuma suka tarar Binta tana yin wannan waƙar. Sarki ya kasa kunne, kuma daga ƙarshe dai ya fahimci cewa muryar Binta ce.

    Sai nan da nan ya ce da Sarkin maroƙa ya shiga gari ya yi yekuwa cewa duk wanda ya fito da Binta dagakogin Apko za a ba shi dawakai da dukiya mai yawa. Da fari ba wanda ya ce zai gwada, amma can sai wani tsoho ya zo ya ce zai shiga ruwan ya tsamo ta. Sai wasu mutanen garin suka ce: “Amma tsohon nan da rigima kake.

    Ga mu nan duk da ƙarfinmu mun kasa, ballantana kai da ka tsufa?” Sai Sarki ya ce: “A bar shi ya gwada.” Tsoho ya faɗa ruwa, zuwa wani ɗan lokaci sai ya fito da Binta a hannunsa. Da Sarki ya ga ’yarsa sai ya ji kamar ya zabura da gudu ya rungume ta saboda murna da farin cikin da yake ciki.

    Amma sai ya nuna halin manya, ya jure. A cikin murna da farin ciki Sarki da fadawansa da jama’arsa suka yi ta gode wa tsohon nan. Da aka koma fada ya sa aka kwanto dawakai Asbin da kili da fari da ja da baƙi da ingarma da kuru da dai dawakai iri-iri masuyawa da dukiyar da ba a taɓa ganin irinta ba a ƙasar, aka ba tsoho.

    Bayan an tashi daga zaman fadanci Sarki ya shiga turakarsa, sai ya kira matarsa da Falmata, ya tambaye su yadda aka yi Binta ta faɗa ruwa. Sai suka yi shiru. Da dai ya gane munafunci suka yi, sai ya kore su, ya ci gaba da rayuwarsa da ’yarsa Binta. Shi ya sa duk wanda ya je garin zai ji ana cewa: “Binta ’Yar Sarki.” Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Alkawari kaya ne.
    • Kowa ya ci amana sai amana ta ci shi.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar ’Ya’yan Sarki Da Ƙadangare

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ’Ya’yan Sarki Da Ƙadangare

    Tatsuniyar ’Ya’yan Sarki Da Ƙadangare

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani Sarki da ’ya’yansa mata su biyu kyawawa. Amma tun suna ƙanana ya hana su fita waje domin tsaron lafiyarsu. Kullum suna gida har suka girma, suka isa aure. Ganin sun kai munzalin aure, sai ya bari suka ɗan fara fita waje.

    Ana nan, rannan dai Sarki ya ce zai aurar da su. Manema suka fito. Wannan ya zo, a ce a a, bai yi ba. Wancan ya zo, a hana shi. Wata rana dai sai Sarki ya ce a tara mutane, duk wanda ya kira sunan ɗaya daga cikinsu, to shi za a ba wadda ya faɗi sunanta. Shi
    ke nan aka sa ranar tara mutane don a ji wanda zai faɗi sunan.

    Matasa da sauran waɗanda ba su wuce auren budurwa ba, kowa ya shiga neman sunayen ’yan matan; abu dai ya gagara. Sai Biri ya sami labari kuma ya ce ya san dabarar da zai yi. Sai ya je ya samo mangwaro nunannu kyawawa guda biyu. Da ya make mangwaron nan biyu, sai ya garzaya cikin lambun Sarki inda yaran suke hira, ya zauna a kan bishiyar da suke zama a gindinta ya shiga jira.

    Da suka fito, sai ɗaya daga cikin ’yan matan ta je gindin bishiyar da Biri yake kai, sai ya jefa mangwaro ɗaya. Da ta gani sai ta ɗauka tace: “Kirindi zo ki ga wani nunannen mangwaro na samu.”Wannan ya sa Biri murna saboda ya ji sunan ɗaya daga cikinsu. Da ɗayar ta doshi wajen wadda ta kira ta don ta je ta ga mangwaron Kirindi, sai ya jefa ɗaya mangwaron, sai ita ma ta ganshi.

    A cikin murna da ɗoki ta ce: “Ai ni ma na samu Karanda.” Biri na ji sai ya kama murna yana cewa: “Yawwa ai ni zan aure su tun da na ji sunayensu.” Bayan lokacin da Sarki ya yanka wa mutane ya cika, sai aka tara mutane ana tambayar su ko sun sami sunan ’yan matan.

    Wannan ya zo ya ce kaza ne, a ce masa a a, wancan ma ya zo bai canka ba. Haka dai aka yi ta fama har aka zo kan malam Biri. Ana zuwa kansa sai aka ji a cikin raɗa saboda tsoro ya ce: “Kirindi da Karanda.” Sai Ƙadangare da ke gefensa ya ji, sai kawai ya yi farat da ƙarfi ya ce: “Kirindi ce da Karanda.”

    To shi kuma Sarki ya riga ya yi alkawarin duk wanda ya faɗi sunayensu, zai ba shi su aure. Ba tare da ɓata lokaci ba, aka ba Kadangare auren ’ya’yan Sarki. Ashe Biri ya ji haushin ƙwacen da Ƙadangare ya yi masa, kuma ya saɓi laya sai ya ɗauki fansa a kan Ƙadangare.

    Saboda haka bayan an gama bikin amaren Ƙadangare sun tare a gidansa, sai
    rannan Biri ya haura dangar gidan gonar Sarki inda Sarki ke kiwo. A cikin dabbobin da Sarki ke kiwo kuwa, akwai wata babbar kazarsa wadda ya fi so a kan duk sauran abubuwan da yake kiwo a gonar.

    Sai Biri ya kama wannan kaza ya yanka, ya fige, ya dafa ya cinye. Da ya cinye ya sha ruwa, sai ya kwashe duk gashinta da ƙasusuwanta ya je ya haura dangar gidan Kadangare ya zuba. Gari na wayewa, sai labari ya je ga Sarki cewa an sace masa kaza. Sai ya sa fadawa su bi gida-gida su nemo kazar nan kafin a zahar.

    Fadawa na shiga gidan Kadangare, sai suka tarar da gashin kazar Sarki da ƙasusuwa. Suna ganin haka, sai suka kai wa Sarki labari. Saboda kunya da kara irin ta manya, da Sarki ya ji cewa a gidan surukinsa ne aka sami gashi da ƙasusuwan kazarsa, sai ya ce a bar maganar, kuma ya hana a hori Kadangare.

    Biri dai bai ji daɗin haka ba. Duk domin ya yi ramuwar gayya, sai ya yanka akuya ya dafa aka yi romo mai kayan yaji. Ya ɗauka ya kai gidan Kadangare, romo da naman akuya suna tafasa saboda zafi. Da Kadangare ya buɗe mazubin, sai ya ga naman akuya da romo, ga ƙamshinsa ya cika gari.

    Sai kwaɗayinsa ya tashi, bai yi wata- wata ba sai ya kai bakinsa. Yana ɗosana bakinsa kuwa sai yaƙone, ya ja baya. Matansa na fitowa sai hankalinsu ya tafi kan mazubin nan. Da suka buɗa, suka ga naman akuya ne a cikin romon da ya sha kayan yaji, sai su ma suka kwasa, suna kai wa bakunansu sai zafi ya sa kowacce ta ƙwala ihu, ta tofar da wanda ta guntsa.

    Dukkansu uku, watau Kadangare da matansa biyu ba wand abai ƙone ba. Da Biri ya ga haka, sai ya fita daga inda ya maƙe, ya kama hanya ya tafi yana dariyar ƙeta da jin daɗi, ya bar su da jinya. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kowa ya cuci wani zai ga mummunan sakamako.
    • Duk abin da ka samu ta hanyar rashin gaskiya ba za ka moreshi ta hanyar jin daɗi ba.
    • An ɓata goma ɗaya ba ta gyaru ba.
    • Rabon kwaɗo ba ya hawa sama.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Tsurondi

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Tsurondi

    Tatsuniyar Tsurondi

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana wani Dodo ya rikiɗa ya zama mutum, ya shiga wani gari neman aure. Da ya je mazaunin wasu mutane sai ya gaishe su. Ya sanar da su cewa shi baƙo ne, amma neman aure ne ya kawo shi garin. Ya ƙara yi musu bayani cewa ya fi son kyakkyawar mace, wadda babu kamar ita a garin.

    Shi ke nan, sai mutanen nan suka yi masa kwatancen gidan wasu ’yan mata biyu, Awa da ƙanwarta Tsurondi. Da ya je gidan ya yi sallama, sai mai gidan ya fito suka gaisa. Daga nan baƙo ya yi wa mai gida bayanin abin da ya kawo shi. Sai uban ’yan matan ya ce: “To bari in turo su, duk wadda tace za ta aure ka sai in ba ka ita.”

    Ya shiga cikin gida. Jim kaɗan sai Awa, watau babbar, ta fito. Da ya gan ta nan take ya ce yana sonta. Da ta gan shi kyakkyawa kuma baƙo ne sai ita ma ta yarda. Aka shirya biki, aka gama. Aka raka su bayan gari ita da mijinta za su tafi garin mijin. Bayan ango da amarya sun kama hanya, sai ƙanwarta Tsurondi ta ce za ta raka ta.

    Amma sai Awa ta ce kada ta bi su. Ƙanwar ta yi juyin duniyar nan, amma Awa ta ƙi yarda. Sai Tsurondi ta zama ƙuda ta faɗa kan kayan amarya, suka kama hanya. Can lokacin da suka isa dokar daji, sai iska ta ɗauke hular ango. Da matarsa Awa ta ga haka sai ta ce: “Mai gida hularka ta faɗi.” Sai ya ce da ita: “A nan na tsince ta da man.

    Haka dai ya yi ta zubar da kayan jikinsa har ya zama tsirara. Sai kawai ya zama wani
    dodo mai babban ƙaho a tsakiyar kansa da doguwar jela mai gasuka kowanne kamar girman adda. Ganin haka ya sa Awa ta razana. Nan take ta ɓarke da kuka, amma fa tana bin sa har suka isa gidansa.

    Bayan sun huta a gidan Dodo, kuma ya fita shan iska, sai ƙanwarta ta rikiɗa zuwa mutum. Da Awa ta gan ta, sai murna da mamaki suka kama ta, kuma ta dubi
    ƙanwar ta ce: “Tsurondi yaya aka yi kika biyo ni?” Sai ta ba ta labarin yadda ta yi. Shi ke nan kullum idan lokacin dawowar Dodo ya kusa, sai ta ɓoye ƙanwarta, kuma in gari ya waye, Dodo ya tafi farauta, sai ta fitar da ƙanwar.

    Haka dai suka yi ta fama har Awa ta sami ciki. Da lokacin haihuwa ya kusa, sai ta ce da ƙanwar ta kama hanya ta je gida ta gaya musu za ta zo haihuwa, amma kuma idan sun isa, a yi dabarar da za a kashe Dodon. A haka suka yi ban kwana. Tsurondi ta zama tsuntsuwa ta tashi sama fir, sai garinsu.

    Tana isa gida ta ba mutanen gari labarin abin da Awa ta aura. Da suka ji haka, sai suka fara shirin kashe Dodo. Suka tona rami a ɗakin mahaifiyar Awa, a daidai inda Dodo zai zauna ranar suna. Da watan haihuwar Awa ya kama, sai ta gaya wa Dodo za ta je gida domin ta haihu a cikin ’yan’uwanta.

    Mijin kuwa ya ba ta izini, har ma ya sa ta a hanya, ta isa gida lafiya. Bayan ’yan makonni da isarta gida, sai ta haihu, kuma aka aika masa ya zo ya ga ɗansa. Sai ya yi murna, kuma ya sa ranar zuwansa. A ranar da Dodo zai isa tun da safe iyayen Awa suka hura wuta a ramin da suka tona. Suka jefa manyan guma-gumai, wuta ta haɗu sosai. Daga nan suka ɗora gadon kara a kan ramin, sannan aka shimfiɗa tabarma a kai.

    Da Dodo ya zo, aka zaunar da shi a kan tabarmar, aka kuma miƙa masa ɗansa domin ya gani. Can sai ya fara ji kamar ana muntsinar sa a duwaiwai, bai san ramin wuta ne a ƙarkashinsa ba. Da wuta ta ci karan, sai suka ɓurma shi da ɗansa. Nan dai ya yi kici -kicin jefo ɗan waje, amma aka sake mayar masa shi, har dai suka ƙone ƙurmus a cikin ramin nan.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kyau ba shi ke kawo daɗin zaman aure ba.
    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Ceto daga Ubangiji ne abin dogaro ba na ɗan’adam ba.
    • Zakaran da Allah ya nufa da cara ko ana muzuru ana shaho sai ya yi.
    • Mai rabon ganin baɗi ko ana ha maza ha mata sai ya gani.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Kurege Da Wayo

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kurege Da Wayo

    Tatsuniyar Kurege Da Wayo

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani lokaci da aka yi yunwa, ba abinci. Wuya ta sa Kura da Maciji da Alade da Kurege suka haɗa kai, suka haɗu domin su haɗa gwiwa su yi noma tare. Sai suka zaɓi wani fili a dajin da suke, suka gyara, ya zama gonarsu.

    Ana nan, jim kaɗan kafin damina ta faɗi, sai Maciji ya ce shi ne zai yi sassabe, watau zai gyara gona, ya sare lallagowa ya kawar da yayi. Alade ya ce: “Ni zan yi mana huda.” Kura ta ce: “Ni zan nome mana gonar.” Kurege kuwa sai ya ce: “Ni kuma zan nemo mana irin shukawa.”

    A daidai lokacin da ya dace, sai Maciji ya tuge bishiyoyin gonar ya ƙone. Alade ya yi musu huda. Kura ta nome. Kurege ya tafi neman irin shuka a kasuwa, sai ya ga wata mata ta tara dawa da masara da gyaɗa da wake. A daidai lokacin da ta tashi tafiya gida sai Kurege ya ruga, ya je gabanta ya kwanta kamar ya mutu.

    Da matar ta gan shi sai ta ce: “Kai ga nama ya samu. To amma fa idan na ɗauka zai cinye mini dawa ta kare da wuri.” Sai ta tafi ta bar Kurege, ba ta ɗauka ba. Da Kurege ya ga haka sai ya tashi ya kama gudu, ya sha gaban matar nan ya kwanta. Da ta ga wannan Kuregen ba ta san na baya ba ne sai ta ce: “Allah ne ya ba ni.”

    Sai ta ɗauki Kurege ta sa a bakin ƙwaryarta, ta shiga gefen daji domin ta samo ɓawon kargo ta ɗaure Kuregen ko ta ji daɗin tafiya da shi gida. A lokacin da ta ajiye ƙwarya ta je ta yo ɓawon kargo sai Kurege ya ɗauki ƙwaryar nan cike da irin dawa ya gudu.

    Da matar nan ta dawo, sai ta ga ba ƙwarya, ba Kurege. Hankalinta ya tashi, kuma ranta ya ɓaci. Haka dai matar nan ta kama hanyar gida da ɗan abin da ba a rasa ba, tana kuka. Shi kuwa Kurege ya kai iri suka shuka tare da abokan nomansa. Ƙurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Idan an hada kai komai zai zo cikin sauki.
    • Iya ruwa fidda kai.
    • Neman araha kan sa mutum ya rasa abin da yake hannunsa.
    • Kwadayi mabudin asara/wahala.

    Karanta Tatsuniyar ƊanAuta Da ’Yar Gwaggo

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ƊanAuta Da ’Yar Gwaggo

    Tatsuniyar ƊanAuta Da ’Yar Gwaggo

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum yana da ’ya’ya biyu mace da namiji. Macen ce babba, namijin ne ƙarami. Ita sunanta ’Yar Gwaggo, shi kuma sunansa Ɗan’auta. Da iyayensu za su rasu sai suka kira ’Yar Gwaggon suka ce: “Za mu bar miki ƙaninki Ɗan’auta. Kada ki ba shi wahala, duk abin da yake so ki ba shi; kuma duk abin da ya ce zai yi, kada ki hana shi; ki bar shi ya yi.”

    ’Yar Gwaggo ta ce: “To na ji.” Sai iyayen suka kwanta, suka rasu. To da ma iyayen sun bar musu dukiyar abinci da kadarori. Bayan ’yan kwanaki da rasuwarsu sai Ɗan’auta yace su tattara dukiyar da abincin da gidan baki ɗaya su ƙona. Sai ’Yar Gwaggo ta ce: “Haba Ɗan’auta, idan muka ƙona kuma me za mu ci, kuma a ina za mu zauna?” Sai Ɗan’auta ya ce: “Ba su baba sun ce idan ina son komai ki ba ni ba, kuma duk abin da zan yi kada ki hana ni?”

    Sai ta ce: “To shi ke nan, ka tashi mu tara kayan a ƙona.” Suka tara kayan da abincinsu rumbu-rumbu, suka ƙona. Da yunwa ta fara damun su sai ’Yar Gwaggo ta ce to su tafi bara. Suka kama hanya har gidan Sarki sai suka tarar da ’ya’yan Sarki suna wasan kirbe-kirbe, sai yace shi ma sai ya yi.

    Sai ’Yar Gwaggo ta ce: “Haba Ɗan’auta, wannan fa gidan Sarki ne, kuma ’ya’yan Sarki suna wasa. Idan aka kama mu fa?” Sai ya ce: “Ba su iya da baba sun ce duk abin da na ce zan yi ki ƙyaleni ba?” Sai ta bar shi ya shiga wasan ’ya’yan Sarki. A cikin wasan ya ɗaga ɗaya daga cikinsu, ya ƙwala da kasa sai cinyarsa ta karye.

    Sai Sarki ya sa fadawa su kama shi. Ganin haka sai ’Yar Gwaggo ta kama hannun ƙanenta suka kama gudu, har cikin jeji, dogarai suna bin su. Can sai suka hau kan wata bishiya, suka ɓuya. Da dogarai suka zo sai suka rasa hanyar da suka bi, sai suka ce bari su huta a gindin bishiyar nan. Su Ɗan’auta na kan bishiyar.

    Da ɗaya daga cikin dogaran ya kwance rawaninsa domin ya sha iska, ga shi ya aske kansa ƙwal-ƙwal yana ƙyalli, sai ɗan’auta ya auna kan dogarin sosai, sai kawai yace wa ’Yar Gwaggo: “Zan yi kashi.” Tsoro ya kama ’Yar Gwaggo, domin idan dogaran nan suka ji motsi za su kama su. Sai ta ce: “Haba Ɗan’auta, idan ka yi kashi za su gan mu, su kama mu fa.”

    Sai ya ce: “Ba iya da baba sun ce duk abin da zan yi ki ƙyale ni ba?” Sai ta ce: “To shi ke nan yi kashinka.” Sai ya tuɓe wandonsa ya auna daidai kan dogari sai ya ɓarke da kashi. Da kashi ya zuba kan dogari sai ya ce: “Wannan wane ɗan iskan tsuntsu ne ya yi mini kashi?”

    Da suka ɗaga kai sama sai ga su Ɗan’auta da ’Yar Gwaggo, sai suka fara sarar bishiya, saura kaɗan ta faɗi, sai ga wata ’yar tsuntsuwa za ta wuce, sai ’Yar Gwaggo ta ce: “‘Yar tsuntsuwa ki taimake mu mana.” Sai tsuntsuwar ta ce: “To ku hau bayana.” Suka hau bayan ’yar tsuntsuwa, ta tashi da su sama suka fara tafiya.

    Bayan sun fara nisa a can sama, sai Ɗan’auta ya ga gindin tsuntsuwa na ta motsi, yana budewa ya rufe. Sai kawai ya ce zai tsokale gindin tsuntsuwa. Yayarsa ta ce: “Haba Ɗan’auta, ita da ta taimake mu. Da an kama mu an kashe. Ka yi haƙuri mana.” Sai ya ce: “Ba inna da baba sun ce idan na ce zan yi abu kada ki hana ni ba?”

    Sai ta ce: “To ka yi.” Sai ya sa kara ya tsokale gindin tsuntsuwa. Sai ta juyar da su, suka faɗa cikin wani babban rafi. Suka yi ta iwo har suka kai bakin ruwa. Sai suka fita a daidai wani ɗan ƙauye. Da suka shiga ƙauyen sai suka fara neman masauki. Sai suka haɗu da wata ’yar tsohuwa suka gaya mata su baƙi ne masu neman masauki.

    Sai tace: “To zan ba ku masauki, amma fa a garin nan ba a fita da daddare don akwai wani dodo da yake cin mutane; har sarki ya yi alƙawari zai ba duk wanda ya kashe dodon rabin gari kuma ya aura masa ’yarsa.” Sai suka ce: “To shi ke nan.” Da dare ya yi sai Ɗan’auta ya ce shi fa sai ya ga dodon da yake hana mutane fita.

    Yayarsa ta yi, ta yi da shi kada ya fita waje, ya hura wuta a gefensa. Da wuta ta ruru, sai ya saka duwatsu bakwai a cikinta, har suka yi jawur. Sai ya zauna a tabarmarsa, ’yar tsohuwa kuma don tsoro sai ta shiga randarta ta buya a ciki. Da dodo ya iso gari ya shiga waƙa yana cewa: “Wa ya yi da ni a garin nan, Wa ya yi da ni, ni dodo in cinye shi?”

    Sai Ɗan’auta ya mayar masa yana cewa: “Na yi da kai a garin nan, Na yi da kai ni Ɗan’auta.” Da tsohuwa ta ji sai ta fara zawo a cikin randar don tsoro. Sai dodo ya nufo inda Ɗan’auta yake. Da Ɗan’auta ya ga ya buɗe baki, sai ya ɗauki dutsen nan da ya yi jawur da wuta, ya jefa a cikin bakin dodo.

    Sai dodon nan ya hadiye. Ya ci gaba da matsowa, shi kuma Ɗan’auta ya ci gaba da jefa duwatsun nan, har ya zo kan na ƙarshe. Da ya jefa na bakwai, sai kawai dodon ya faɗi matacce. Da Ɗan’auta ya ga haka, sai kawai ya koma ya kwanciyarsa. Da gari ya waye sai aka aika wa Sarki cewa an kashe dodon da ke damun mutanen gari.

    Sarki kuwa ya ce duk wanda ya kashe dodon za a ba shi rabin gari, kuma a aura masa ’yar Sarki. To da ma shi Ɗan’auta ya manta takalmansa a inda ya yi faɗa da dodo. Da aka tara mutane suka zo suka yi ta gwada takalma amma bai yi ba, sai da suka nemi baƙin da suke garin.

    Da Ɗan’auta ya gwada takalma sai suka yi daidai da shi. Nan take aka ba shi rabin gari, Sarki kuma ya cika alƙawari, wato ya ba shi auren ’yarsa. Ƙurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Wauta ne a sakar wa yaro linzami ya yi abin da ya ga dama.
    • Mai wayo ya fi mai zafin nama cin nasara.
    • Ya kamata a karɓi bako da hannu bibbiyu don ba a san alhairindazai kawo ba.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Gizo Da Sarki

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu