Ga ta nan, ga ta nanku.
Wata rana Awa da Dawi suna kiwo a daji, sai wani abu ya tsoratar da su. Kowa ya kama gabansa domin neman tsira. Suka ɓace wa juna. Da Dawi ya nemi ƙanwarsa bai gan ta ba, sai ya kama hanya ya tafi. Ita kuma ta nemi hanya ta rasa. Ta riga ta ɓata a dajin nan.
Sai tafiya take ta yi, ba ta san inda za ta ba, har dare ya yi. Da ta gaji, kuma ga dare ya yi, sai ta sami gindin wata bishiya ta kwanta, har gari ya waye. Da sassafe tana kwance sai wata tsohuwa da ta yi sammakon neman ganyen miya ta tarar da ita. Da tsohuwar nan ta ga Awa a kwance sai ta tashe ta daga barci, tace da ita: “Ke yarinya me ya kawo ki nan?”
Sai Awa ta kwashe labarin yadda suka yi da ɗan’uwanta ta gayawa tsohuwa. Sai tausayinta ya kama tsohuwa, ta dubi Awa tace da ita: “To idan kin yarda ki zo mu tafi da ke gidana.” Nan take Awa ta yarda suka tafi gidan tsohuwa, ta ba ta masauki da abinci. Awa ta ci abinci ta ƙoshi, ta yi wanka ta zauna.
Da tsohuwa ta kalli Awa, sai ta ga yarinya ta ƙara kyau. Dama yunwa da dauɗa da gajiya da tsoro ne suka ɓoye kyaunta. Sai tsohuwa ta yanke shawarar kai wa Sarkin garin labarin Awa ko zai so ta. Nan da nan ta isa gidan Sarki, ta same shi a fada, ta durƙusa ta yi gaisuwa ta ce: “Ranka ya daɗe, na zo maka da wani albishir idan kana da buƙata.”
Sarki ya ce: “Albishir na mene ne?” Sai tsohuwa ta ce wa Sarki “Ina da wata kyakkyawar yarinya wadda za ta dace da kai idan za ka yarda ka aure ta.” Sarki na jin haka sai ya ce: “A kawo ta in gan ta.” Da tsohuwa ta ji haka, sai ta je gida ta gaya wa Awa, kuma suka tafi fada tare.
Da Sarki ya ga Awa sai ya ce zai aure ta. Ba jimawa aka ɗaura musu aure da Sarki, ta tare a gidansa. Bayan wasu ’yan shekaru, sai Awa ta haifi ɗanta aka raɗa masa sunan yayanta wanda ya ɓata, watau Dawi. Ana nan sai Sarki yace kada a riƙa katse ƙashin ɗansa da ƙara domin zai ji masa ciwo, sai dai da hantar sa.
Haka kuma ake yi. Kullum da safe sai a yanka shanu, a yanke hantar da huhun a ba Awa ta riƙa share wa yaron ƙashi da su. Wata rana sai Awa ta gaya wa Sarki tana so ta ziyarci iyayenta. Sai ya tambayi sunan garinsu, ta faɗa. Sarki ya sa cigiyar wanda ya san garin. Aka yi sa’a, aka samu.
Sai aka haɗa shi da matar Sarki da doki ya kai ta garinsu. Kafin su tafi sai aka yanka shanu aka zuba mata hanta da huhu a cikin ƙwarya don katse ƙashin ɗan Sarki, aka kawo kayan tsaraba masu yawa aka ba ta. Da Awa da ɗan rakiyarta suka kama hanya, har Allah ya kai su garin lafiya, murna ta kama ta. Sai ta doshi gidan iyayenta, ta shiga.
Mutanen gidan suka yi murnar ’yarsu ta dawo. Bayan sun huta, sai ta ba su labarin abin da ya faru har zuwa aurenta da Sarkin garin da suke. Iyayenta da sauran danginta suka yi ta murna. Awa ta kawo kayan tsaraba ta ba iyayenta da sauran’yan’uwanta. Suna zaune ana hira sai ɗanta ya yi ƙashi, sai nan da nan ta zaro hanta za ta katse ƙashin yaron da ita.
Da uwar ta gani sai ta ce: “Me za ki yi da wannan hanta?” Sai Awa ta ce: “Ai da hanta ake katse ƙashin ɗan Sarki, ba a katse masa da ƙara; mahaifinsa ya hana.” Mamaki ya kama mahaifiyar Awa da ta ji wannan batu. Sai ta shiga tunanin cewa ga abin da mutum ba zai iya samu ya ci kullum ba ya zama abin katse ƙashin jikanta.
Daga nan sai ta shiga ƙulla yadda za ta kwashe hantar ta cinye. Shi ke nan sai uwar ta kira Awa ta ce mata: “Ɗauki gora ki je ki ɗebo mana ruwa a rafi.” Saboda halinta na bin iyaye, sai kawai tace: “To, amma ki kular mini da yaron nan don ba zan je rafi da shi
ba.” Sai kakar yaron ta ce: “To, zan lura da shi.”
Da ta ga lallai Awa ta tafi ɗaukar ruwa rafi, sai ta kwashe hantar katse wa ɗan Sarki
ƙashin da ta zo da ita gaba ɗaya, ta gasa ta cinye. Da yaron ya yi ƙashi kafin Awa ta dawo daga rafi, sai uwar ta ɗauki ƙara ta katse masa da shi.
Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa
- Kwaɗayi mabuɗin wahala.
- Tsautsayi ba a sa maka rana.
- Mai mugun hali tun a duniya sai ya ɗanɗana kuɗarsa.
- Aikin da ba a yi shi da kyakkyawar niyya ba ƙarshensa nadama.
Danna nan don karanta Tatsuniyar Maye Da ’Ya’yansa
Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.
Edita@rumasau-kallamu










