Addu’ar Sujjadar Tilawar Alƙur’ani

0
339

“Sujada wajhii lillazii khalaƙahu wa shaƙƙa sam’ahu wa basarahu bi haulihi wa ƙuwwatihi (Fatabaarakal-laahu ahsanul khaaliƙiina)”.

{Fuskata ta yi sujada ga wanda ya halicce ta, kuma ya tsaga ji da gani a gare ta; da iyawarsa da kuma ƙarfinsa. (Allah mafi gwanintar masu halitta, ya girma, kuma alherinsa ya yawaita}.

“Allaahummaktub lii bihaa indaka ajran, wa dha’a annii bihaa wizran waj’ilha lii indaka zukhran, wa taƙabbalhaa minni kamaa taƙabbaltahaa min abdika Dawuda”.

{Ya Allah! Ka rubuta mini lada saboda ita (sujadar), ka kankare min zunubi saboda ita; ka sanya ta ta zamo taskar arziki gare ni a wajen ka, kuma ka karɓe ta daga gare ni kamar yadda ka karɓe ta daga bawanka Dawuda}.

Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Tahiyya danna nan.

Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Tafiya Sujudah danna nan.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunna; wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.