Zuwan Tajwidi Da Musabaƙa Da Tasirinsa Cikin Tsarin Tsangaya

0
418

Tajwidi dai ba sabon al’amari ba ne wajen ma’abota tsangaya, domin kuwa, makaranta da yawa a Maiduguri da Kano sun karɓe shi, kuma sun koye shi tun farko-farkon ƙarni na goma sha tara.

Misali a nan shi ne, Malam Rabi’u Ɗantinki da Malam Ɗankwandarai, waɗanda duka alamajirai ne wajen mashahurin masanin ilmin Tajwidi da ƙira’o’in nan, watau Gwani Hamad.

Hakan kuwa ya yi tasiri da gaske wajen kyautata karatun Alƙur’ani a Kano. A Maiduguri kuwa za mu ga cewa, al’amarin Tajwidi da ilmin ƙira’o’i ya ƙara bunƙasa ne bayan zuwan wasu malamai daga ƙasar Chadi, waɗanda suka yi karatu a wurin Shehun Azahar da ke ƙasar Masar. Waɗannan sun haɗa da Sheikh Daha da kuma Sheikh Hassan bn Umar Almuƙuri.

Duk da wannan alaƙa tsakanin ma’abota tsangaya da Tajwidi tun kimanin shekaru tamanin baya; Tajwidi da ilmin ƙira’a bai yaɗu ya yi tasiri ba, sai bayan zuwan Musabaƙa. A nan ne makaranta masu tilawa mai ƙarfi daga tsangaya; suka riƙa koyon Tajwidi suna yin fice a musabaƙar cikin gida da ma duniya baki ɗaya.

Babu shakka, hakan ya zama sababin tsundumar makaranta fagen neman ilmin fannin Musulunci; wasu ma suka fara danganawa da jami’o’in gida da ma wajen Najeriya, Fitaccen kwatance a nan shi ne Sheikh Ja’afar Mahmud Adam; wanda asalin karatunsa tsangaya ce.

Daga bisani kuma, har ya dangana da Jami’o’in Musulunci da ke Madina da Sudan; don samun digiri na farko da na biyu wato Majistera. A halin yanzu kuma yana ƙoƙarin yin digiri na uku (Doctorate).

Malam Ja’afar a yau ɗaya ne daga fitattun malamai, ba a Kano kawai ba, har ma Najeriya gaba ɗayanta. Baya ga ɗaiɗaikun makarantan da suka faɗa wasu fannoni a sababin Tajwidi da Musabaƙa; da yawan tsangayu a Maiduguri da Kano da kewayensu, sun buɗe ɓangaren Tajwidi wanda aka fi sani da ɓangaren Tahfeez. Babban misali a nan shi ne, Gwani Saleh Ɗanzarga Tahfeez da ke Kano; da kuma Tahfeez ta Sheikh Ghibirima; wadda ake kira Institute for the Memorisation of the Holy Qur’an Nguru.

Duk da irin wannan tasiri da Tajwidi da Musabaƙa suka yi ga tsarin tsangaya a Arewacin Najeriya; har yanzu mafi yawan tsangayu da makaranta suna kan tsohon tsarin karatu bisa ƙarin harshenmu na gargajiya.

Domin karanta cikakken bayani a kan Ma’anar Tsangaya danna nan.

Domin karanta cikakken bayani a kan Ma’anar Waƙafi danna nan.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

labarin da ya wuceGudunmawar Tsangayun Alƙur’ani Wajen Cigaban Al’umma
Labarin na GabaWasu Birane Da Garuruwa Da Makarantu Da KumaTsangayu A Arewacin Najeriya