Wasu Birane Da Garuruwa Da Makarantu Da KumaTsangayu A Arewacin Najeriya

0
297

Akwai wasu al’amura da ke jawo karkatar makaranta ko masu neman karatun AlÆ™ur’ani zuwa wasu larduna ko biranen fiye da karkatarsu ga wasu lardunan ko biranen.

Ƙaura daga wuri zuwu wani Wurin daban, abu ne da aka san makarantan tsangaya da shi, tun kaka da kakanni. Da yawa za ka ga Wata tsangaya cike da gardawa ko almajirai a lokacin rani; amma da zarar damina ta sauka sai ka neme su ka rasa. Irin wannan na faruwa ne saboda noma da aikin gona don samun ishasshen abinci.

A wani lokaci kuma, makaranci kan yi Æ™aura da almajiransa ko kuma gardi a karan kansa, idan ya sami labarin wata tsangaya mai tashen tara makaranta; ko kuma labarin wani mashahurin alaramma mai baiwa don ya fa’idanta daga baiwar da yake da ita. Yanayin wuri da ni’imarsa ko yalwar ruwa da wadatar Æ™asar noma shi ma wani dalili ne da ke jawo taruwar makaranta.

Irin wannan al’ada ita ake kira yawon bundi a wasu sassa na Arewacin Najeriya, musamman ma Sakkwato da kewayenta. Don Æ™arin haske game da asalin wannan al’ada, sai a duba Babi na HuÉ—u cikin Sashe na Biyu kan É—abi’un makaranta da halayensu cikin zamantakewar tsangaya.

Wata tsohuwar al’ada tsakanin makarantan Arewacin Najeriya ita ce, tafiya Gabas, ma’ana Æ™asar Barno don samun karatu. Don haka ne ma zai yi wuya ka sami wani makaranci a faÉ—in wannan nahiya ta Arewa; wanda bai dangana da Barno ko kewayenta ba ya yin neman karatu. Wannan na komawa ga irin rigayen da Kanem Barno ke da shi wajen karÉ“ar Musulunci da tsohowar alaÆ™ar wannan daula; da Æ™asshen Larabawa, Æ™arnuka masu yawa da suka shuÉ—e.

Ƙasar Barno ta zamo tamkar wata Ka’aba ce ga manema AlÆ™ur’ani. Makaranta, a bisa É—abi’arsu, sun fi son wurin da za su keÉ“ance kansu nesa da jama’a; kodayake buÆ™atun rayuwa na yau da kullum musamman buÆ™atar abinci ya jawo yawaitar almajirai da makaranta cikin birane da garuruwa masu cigaban kasuwanci da tashoshin mota da kasuwanni.

Za mu iya ayyana wasu garuruwa da suka yi fice tuntuni da tara makaranata a Arewacin Najeriya kamar haka:

– Ngazargamu
– Gaidam
– Gashuwa
– Gubuci
– NGuru
– Damaturu
– Takai
– Bama
– Ganjarma
– Birniwa
– Kebberi
– Hadejiya
– Kondiga
– Paki
– Kahutu
– HunÆ™uyi
– Matazu
– Tsakuwa
– MaÆ™arfi
– Kura
– Zangon Daura
– Ningi
– Bunkure
– Illela a Nijar
– Kance a Nijar
– Mutame a Nijar
– Insharuwa da dai sauransu.

Abu ne mai matuÆ™ar muhimmanci sanin yawan tsangayunmu na AlÆ™ur’ani, da yawan malamansu da almajiransu. Wannan ya sa tsohowar gwamnatin jihohin Arewa Æ™arÆ™ashin jagorancin Marigayi Sir Ahmadu Bello; Sardaunan Sakkwato ta aiwatar da wannan Æ™ididdiga a Makarantun AlÆ™ur’ani Bisa Æ™ididdigar Gwamnatin Arewacin Najeriya (1960)

Domin karanta cikakken bayani a kan Gudunmawar Tsangayun AlÆ™ur’ani Wajen Cigaban Al’umma danna nan.

Domin karanta cikakken bayani a kan Mutane Biyar Da Suka Yi kama Da Manzon Allah (S.A.W) danna nan.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun AlÆ™ur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.