Wasu Birane Da Garuruwa Da Makarantu Da KumaTsangayu A Arewacin Najeriya

0
355

Akwai wasu al’amura da ke jawo karkatar makaranta ko masu neman karatun Alƙur’ani zuwa wasu larduna ko biranen fiye da karkatarsu ga wasu lardunan ko biranen.

Ƙaura daga wuri zuwu wani Wurin daban, abu ne da aka san makarantan tsangaya da shi, tun kaka da kakanni. Da yawa za ka ga Wata tsangaya cike da gardawa ko almajirai a lokacin rani; amma da zarar damina ta sauka sai ka neme su ka rasa. Irin wannan na faruwa ne saboda noma da aikin gona don samun ishasshen abinci.

A wani lokaci kuma, makaranci kan yi ƙaura da almajiransa ko kuma gardi a karan kansa, idan ya sami labarin wata tsangaya mai tashen tara makaranta; ko kuma labarin wani mashahurin alaramma mai baiwa don ya fa’idanta daga baiwar da yake da ita. Yanayin wuri da ni’imarsa ko yalwar ruwa da wadatar ƙasar noma shi ma wani dalili ne da ke jawo taruwar makaranta.

Irin wannan al’ada ita ake kira yawon bundi a wasu sassa na Arewacin Najeriya, musamman ma Sakkwato da kewayenta. Don ƙarin haske game da asalin wannan al’ada, sai a duba Babi na Huɗu cikin Sashe na Biyu kan ɗabi’un makaranta da halayensu cikin zamantakewar tsangaya.

Wata tsohuwar al’ada tsakanin makarantan Arewacin Najeriya ita ce, tafiya Gabas, ma’ana ƙasar Barno don samun karatu. Don haka ne ma zai yi wuya ka sami wani makaranci a faɗin wannan nahiya ta Arewa; wanda bai dangana da Barno ko kewayenta ba ya yin neman karatu. Wannan na komawa ga irin rigayen da Kanem Barno ke da shi wajen karɓar Musulunci da tsohowar alaƙar wannan daula; da ƙasshen Larabawa, ƙarnuka masu yawa da suka shuɗe.

Ƙasar Barno ta zamo tamkar wata Ka’aba ce ga manema Alƙur’ani. Makaranta, a bisa ɗabi’arsu, sun fi son wurin da za su keɓance kansu nesa da jama’a; kodayake buƙatun rayuwa na yau da kullum musamman buƙatar abinci ya jawo yawaitar almajirai da makaranta cikin birane da garuruwa masu cigaban kasuwanci da tashoshin mota da kasuwanni.

Za mu iya ayyana wasu garuruwa da suka yi fice tuntuni da tara makaranata a Arewacin Najeriya kamar haka:

– Ngazargamu
– Gaidam
– Gashuwa
– Gubuci
– NGuru
– Damaturu
– Takai
– Bama
– Ganjarma
– Birniwa
– Kebberi
– Hadejiya
– Kondiga
– Paki
– Kahutu
– Hunƙuyi
– Matazu
– Tsakuwa
– Maƙarfi
– Kura
– Zangon Daura
– Ningi
– Bunkure
– Illela a Nijar
– Kance a Nijar
– Mutame a Nijar
– Insharuwa da dai sauransu.

Abu ne mai matuƙar muhimmanci sanin yawan tsangayunmu na Alƙur’ani, da yawan malamansu da almajiransu. Wannan ya sa tsohowar gwamnatin jihohin Arewa ƙarƙashin jagorancin Marigayi Sir Ahmadu Bello; Sardaunan Sakkwato ta aiwatar da wannan ƙididdiga a Makarantun Alƙur’ani Bisa ƙididdigar Gwamnatin Arewacin Najeriya (1960)

Domin karanta cikakken bayani a kan Gudunmawar Tsangayun Alƙur’ani Wajen Cigaban Al’umma danna nan.

Domin karanta cikakken bayani a kan Mutane Biyar Da Suka Yi kama Da Manzon Allah (S.A.W) danna nan.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

labarin da ya wuceZuwan Tajwidi Da Musabaƙa Da Tasirinsa Cikin Tsarin Tsangaya
Labarin na GabaZaman Lafiya Da Iyali