Abin da Bincike Ya Gano Game Da Matsalolin Aure A Ƙasar Hausa

0
451

Wannan bincike dai ya yi ƙoƙarin binciko wasu muhimman al’amura; game da wasu matsaloli da suka addabi gidajen mafi yawan Hausawa; inda binciken ya gano musabbabinsu ta amfani da wasu waƙoƙin Hausa na Situdiyo.

Matsalolin Aure -Daga cikin abin da binciken ya gano, ya bayyana lalle akwai matsaloli a tsakanin ma’aurata a Ƙasar Hausa, sannan ya fayyace matsalolin ta hanyar amfani da zantukan mawaƙan baka na Situdiyo.

Binciken dai ya gano yadda mawaƙan baka na Situdiyo suke taka muhimmiyar rawa wajen wayar da kan al’umma ta hanyar lalubo matsalolin da suka addabe su, da kuma bayyana su cikin hikimar zance irin tasu.

Har wa yau, binciken ya nuna waƙa yalwatacciyar hanya ce ta isar da saƙo ba jefa nishaɗi kurum a tsakanin al’umma; ta yadda da ita za a iya gano matsalolin da suka dabaibaye al’umma; har ma a yi kirdadon hanyoyin magance matsalolin.

Binciken dai ya ƙara tabbatar da cewa aikin waƙa; aiki ne na fasaha da bincike ta yadda ba haka kawai da ka ake yin waƙa ba; har sai an yi bincike yayin da ake son isar da wani saƙo; ko kuma yin ishara ko hannunka mai sanda ko kuma faɗakarwa a cikin waƙoƙin baka na Situdiyo.

Wani babban abu kuma muhimmi da wannan binciken ya gano shi ne muhimmancin mawaƙa da kuma; ƙoƙarin taƙaituwa zuwa ga abin da suka faɗa a matsayin ita ce matsala ga wani rukuni na al’umma; ko wani abu da yake faruwa a tsakanin al’umma.

To mawaƙa ma na iya tsinkayowa da kuma ayyana basirarsu wajen sanar da jama’a a waƙe.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Nazarin Matsalolin Aure A Ƙasar Hausa Daga Mahangar Zabiya Lawisa da Fatima Jalo wanda Ibrahin Baba (Nayaya) ya wallafa shi.

Domin karanta bayani a kan Ma’anar Aure danna nan

Domin karanta bayani akan Abin da Bincike Ya Gano Game Da Matsalolin Aure A Ƙasar Hausa danna nan

labarin da ya wuceTaƙaitaccen Tarihin Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau
Labarin na GabaTaƙaitaccen Tarihin Samuwar Waƙoƙin Baka a Ƙasar Hausa