Ma’anar Aure

0
1294

Aure wani haɗi ne da ake yin sa tsakanin namiji da matar da ta halatta da aure a gare shi, bayan amincewar su da juna, domin tabbatar da halaccin gudanar da cuɗanya a tsakaninsu, da kuma biya wa junansu buƙatar sha’awa, ba tare da an sami wani zargi ba.

Abubuwan Da Sai da Su Aure Yake Zama Karɓaɓɓe:

A musulunce aure na tabbata ne da tabbatar waɗannan abubuwa masu zuwa kamar haka:
1. Samuwar amincewar waɗanda za a ɗaurawa aure.
2. Waliyyin matar da za a aura.
3. Shaidu.
4. Sadaki.
5. Siga. (wato maganganun da aure yake ɗauruwa da su), kamar mai neman ya ce da waliyyin mace: ‘Ina neman auren wance’. Sai shi kuma waliyyin ya ce: ‘Na aura maka ita.

Domin karanta cikakken bayanin abubuwan da sai da su aure yake zama karɓaɓɓe danna koren rubutun nan.

Wannan bayani an ciro ne da littafin Nagartacciyar Rayuwar Aure wanda Abubakar Abbas ya wallafa shi. domin karanta cikakken littafin danna wannan koren rubutun.

labarin da ya wuceMutum Da Son Zuciya.
Labarin na GabaGano Ciwo Shi Ne Makamar Sanin Maganinsa