Tag: yadda ake

  • Yadda Ake Duba Katin Ɗan Ƙasa Idan Ya Zama An Kammala Shi

    Yadda Ake Duba Katin Ɗan Ƙasa Idan Ya Zama An Kammala Shi

    Katin Ɗan Ƙasa – Yanzu kana ko kina da damar sanin cewar ko katin na dan ƙasa ya zama an kammala domin karɓa.

    Musamman waɗanda suka daɗe da yin katin ta hanyar bin waɗansu matakai.

    Ga matakan kamar haka:

    1. Ziyarci inda ka yi rijista domin tabbatarwa
    2. Ziyarci shafin http://touch.nimc.gov.ng

    Sai ka cike guraben da aka samar da bayanan da aka buƙata. Kamar sunanka da sunan mahaifi, sannan akwai wurin sanya wata lamba da ake kira da tracking ID, wato lambar bin diddigi sai a danna madannin check.

    Muna fatan waɗannan matakan za su gamsar da kai wajen duba katin ɗan ƙasa naku.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Horon Masu Yi Maka Flashing A Waya danna nan.

  • Yadda Ake Raba Hard Disk Gida Biyu (Partition)

    Yadda Ake Raba Hard Disk Gida Biyu (Partition)

    Akwai bambanci tsakanin formatting (kankare Hard Disk) da kuma Partition (raba Hard Disk). Shi formatting yana kankare dukkan abin da aka zuba a cikin Hard Disk ya koma babu komai a ciki.

    Shi kuwa Partition ba ka dama yake ka raba Hard Disk gida biyu ko fiye da haka, sabo da wani dalili irin wanda mai tambaya ya ce “Ina son in raba Hard Disk ɗina ta yadda zan iya ajiye kayana a cikin ɗaya in kuma ɗora Windows a kan ɗaya ta yadda idan na’urar ta sami matsala nan gaba, ba zan rasa ayyukana ba”.
    Akwai hanyoyi da dama da za a iya bi domin haƙarka ta cimma ruwa, amma yanzu bari mu yi amfani da hanyoyi guda biyu (2) da kowanne ka ɗauka zai kai ka ga biyan bukatarka.
    1. Rabawa lokacin ɗora Windows
    Mu ɗauka ka ɗauko sabuwar na’ura wacce babu kamai a cikin Hard Disk a wannan lokaci, kafin ka iya amfani da ita na’urar dole sai ka ɗaura mata Operating System (Windows).
    Bayan ka sanya CD ko DVD na Windows cikin na’urar za ta yi ƙoƙarin tashi daga wannan CD, idan kuwa daman akwai Windows a kan wannan Hard Disk, to dole sai ka shiga cikin CMOS da BIOS Setting ka canza yanayin tsarin tashin ita wannan na’ura. Dalilin yin hakan kuwa shi ne, idan ba ka canza yanayin abin da za ta tashi da shi ba, domin ita na’ura sai ka gaya mata abin da kake son ta yi kafin ta yi abin da kake son ta yi, kamar an ce mata ta rinka tashi da Hard Disk, to ka ga idan buƙatar ta shiga ta CD ya zo, ka ga dole ka canza mata tsari. Wurin da ake canza wannan tsari shi ne wajan canza setin BIOS/CMOS, idan ba ka san abin da ake nufi da CMOS ko BIOS ba sai ka duba ɗaya daga cikin rubuce-rubucenmu.
    Hanyar da za ta ba ka damar shiga BIOS
    Kowane kamfani da yake ƙera Computer yana da tsari da hanyar da ake shiga wajen shirya BIOS/CMOS (ga wanda yake buƙatar cikakken bayanin yadda BIOS da CMOS ya duba darasinmu na BIOS DA CMOS ƊANJUMA DA ƊANJUMMAI).
    Kusan dukkan Computer da take komai da komai kamfani ɗaya ya yi ta ana kiranta da Branded System wacce da Monitor, da Mouse da Keyboard da System Unit kamfani daya ya yi su, kamar kaga Computer HP ce, ko Dell ko Acer ko Toshiba ko kuma Latptop da dai makamantan su, to su ana latsa F10 ko F2 na jikin Keyboard a zarar ka kunna na’urar. Domin gane yadda za ka iya shiga BIOS ɗinka, lura a lokacin da ka kunna Computer tana rubuta wasu rubutu a ƙasa, kusan su ne farkon rubutun da za ta fara rubutawa kamar haka (F2 Setup) ko (F10 Setup) ko (Del to enter setup)da dai makamantan su. Abin da ake nufi shi ne idan ka latsa wannan Key a daidai wannan lokaci idan ka dace da yin haka, maimakon ta ci gaba da bude Windows sai kawai ta shiga BIOS.
    GARGARDI shiga BIOS yana da hatsari ga wanda bai san yadda zai yi amfani da shi ba, sabo da haka Duniyar Computer ba ta ɗauki alhakin lalacewar na’urarka idan har ka tsallake hanyoyin da ta nuna maka, idan ka shiga wurin. Abin da muka ce a yi, sai a yi shi kawai, idan kuwa ka taɓa wani wuri, wani abu ya ɓaci kada ka ce ba mu faɗa maka ba. A kiyaye.
    Idan kuwa computerka ba Branded ba ce, wato hade-hade ce, to, za ka latsa Delete key (Del) a jikin Keyboard ɗinka domin ya ba ka damar shiga wajen shirya BIOS.
    Bayan ka shiga cikin BIOS Setup, za ka wuce kai tsaye wajen da za ka zaɓi wani abu ne cikin abubuwan da na’ura za ta iya tashi da shi, za ka zaɓa, domin ita na’ura tana iya tashi da abubuwa kusan guda goma (10) wanda duk sanda ta ji ɗaya daga ciki a jikinta idan an ce shi za ta fara nema, idan ba ta gan shi ba, ta nemi na gaba har zuwa na ƙarshe, abubuwan su ne kamar haka: Floppy
    · LS120
    · Hard Disk
    · CDROM
    · USB FDD
    · USB ZIP
    · USB CDROM
    · Legacy LAN
    · Realtech Boot A gidan a laptop ce ko Branded System ce (tun da duk Laptop Branded System ce) za ka wuce wurin da aka rubuta (Storage) (Za ka yi amfani da Keys wanda suke jikin keyboard daga gefen hagunka da alamun mashi guda huɗu, ɗaya na kallon sama ɗaya na kallon ƙasa, ɗaya na kallon dama, ɗaya dayan kuma yana kallon hagu) da zarar ka kai kanshi zai buɗe, daga can ƙasa za ka ga an rubuta (Boot Order) idan ka hau kai, sai ka danna (Enter Key) zai sake fito maka da ɗan ƙaramin falle, wanda za ka ga an rubuta Boot Order, to a nan, za ka ga ɗaya daga cikin waɗancan abubuwa da muka lissafa na Floppy da CDROM da Hard Disk, to ka lura da kyau, wanda ka ga a gefensa an rubuta First, to yana nufin shi ne wanda Computer za ta fara nema idan za ta tashi, nan sai ka canza shi zuwa CDROM idan CDROM din yana haɗe da Computer ne. Amma idan CDROM ɗin irin wanda ake ƙarawa na’ura ce, wato External CDROM za ka zaɓi USB CDROM ne. Idan kuwa irin su Mercury Board ne ko kuma Phoenix da dai makamantan su, su bayan ka samu ka danna Del Key ka shiga cikin BIOS setup, sai ka gangaro zuwa inda ka ga an rubuta Advaced Chipset Features sai ka danna Enter Key a jikin Keyboard zai shigar da kai wani shafi, to, a shafin za ka rubutu a jere da yawa, ka lura da inda aka rubuta First Boot Device idan ka zo kai sai ka danna Enter Key daga nan za ka ga an jero maka waɗancan abubuwan da na’ura ke iya tashi da su, sai ka zaɓi CDROM sannan ka latsa F10 domin ya ajiye canjin da ka yi, sannan ka sake danna F10 domin ya fita daga wannan gida na seta BIOS/CMOS.
    Wannan shi ne a takaice bayanin yadda za ka iya shiga BIOS ka zaɓi abin da kake son na’urarka ta fara nema idan za ta tashi
    Da zarar ka sake kunna na’urar, tun da ka umarci ita na’urar ta tashi ta CDROM, kuma ka riga ka sa mata Windows Installation CD (shine CD da zai ba ka damar ka sawa na’ura window) to, za ma ka ji da kanka CD yana juyawa da karfi, a daidai wannan lokacin, ka lura da kyau za ka ga a jikin Monitor ɗinka an rubuta Press any key to boot from CD a daidai wannan lokacin idan ka latsa ko wani irin Key ne zai shigar da kai tafarkin yadda za ka raba ko kuma sanya Windows a na’urarka. Da zarar ya shiga za ka ga shuɗi (Blue Screen) launi a Monitor ɗinka sai ka bar shi ya gama rubuce-rubucensa har ya tsaya, idan ya tsaya, sai ka bi wannan jerin abin da zan rubuta. Mu ɗauka kana son ka yi installing Windows XP ne.
    1. Enter Key = Wannan shi ne zai ba ka damar cewa kana son ka saka sabon Windows XP a jikin wannan na’ura
    2. F8 Key = bayan ya wuce wancan rubutu zai fito maka da wasu rubuce-rubuce na alkawari da za ka ɗauka tsakanin ka da kamfanin Microsoft da kuma dokokin amfani da kayansu. Danna wannan F8 ɗin da ka yi, ka na gaya musu cewar ka amince da dukkan tsare tsarensu.
    3. ESC Key = bayan ya wuce wancan dokoki zai fito maka da shafin da zai tambaye ka, kana son ka gyara tsohon Window XP da yake cikin wannan na’ura ko kuma kana son ka sa sabon Windows XP ne, ko kuma kana son ka fita da ga Setup ɗin gaba daya? To, latsa ESC dake jikin Keyboard kana gaya mai cewar za ka sa sabon Windows XP ne.
    4. D key = da zarar ka danna ESC zai fito maka da shafin da zai jero maka Hard Disk da suke jikin wannan Computer, a lokacin idan an taɓa Installing Windows a kanta, za ka ga Hard Disk ɗin ya kasu kashi biyu ko fiye da haka, wanda yake da manyan lambobi da wanda yake da ƙnanan lambobi, to kai tunda maƙasudin zuwan ka nan, domin ka raba Hard Disk ɗinka gida biyu ne, to dole ka goge wannan babban Partition. Idan ka hau kan wannan Partition ka danna D key a jikin Keyboard ɗinka, kana nuna cewar ta goge wannan Partition kuma hatsarin dake ciki shi ne, idan kana da mahimman ayyuka a kan wannan Hard Disk to komai fa ya tafi. To, mu ɗauka ba ka buƙatar komai dake kan wannan Hard Disk idan ka latsa D komai ya tafi.
    5. L Key = to bayan ka danna D, sai ka danna L a jikin Keyboard, yin haka kana gayawa ita na’urar cewa ta goge duk abin da ke cikin Hard Disk
    6. C Key = bayan ta gama sharewa, za ta sake dawo da kai wajen nan na farko, inda za ka zaɓi Hard Disk da za ka yi Installation na Windows, to za ka ga Hard Disk ɗin ya koma ɗaya, amma an rubuta a gabansa cewar (Unrecognized) ma’ana na’urar ba ta gane shi ba, a daidai wannan lokaci sai ka latsa C a jikin Keyboard dinka, danna wannan key yana gaya mata cewar kana son ka ƙirƙiri sabon Partition. To, a wannan lokaci sai ka rubuta girman Partition da kake so, idan kana son babba da ƙarami ko kuma kana son dukkansu su zama da girma, iya number da ka rubuta iya girman wannan Partition.
    2. Amfani da Software wajen Partition
    Amma idan kana amfani da ita wannan computer, wataƙila sai yanzu ka gano cewar kana buƙatar ka yi Partition na Hard Disk ɗinka, ga shi kuma akwai muhimman ayyukanka wanda idan ka ce za ka bi waccan hanya ta farko, za ka rasa su, gashi babu inda za ka ajiye su ayyukan naka, idan ka yi amfani da hanya ta farko. To wannan ba matsala ba ce, domin akwai waɗansu Program na musamman da suke yin irin waɗannan ayyuka. Kaɗan daga ciki sun hada da:
    1. Paragon Partition Manager (na kuɗi ne)
    2. Acronist Partition Manager (na kuɗi ne)
    3. Cfdisk (na kyauta ne)
    4. BeOS Partition Manager (kyauta ne)
    5. Logical Disk Manager (Disk Management Console) da makamantan su waɗanda za ka yi amfani da su, su kuma ba ka damar raba Hard Disk ɗinka ko da kuwa gida nawa ne, irin waɗannan program suna da saukin amfani, sannan kuma ba su da matsala wajen kawar da dukkan abin da zai taɓa maka ayyukanka, sannan idan kana son ka ƙara yawan filin Hard Disk ko kuma rage yawan fili da dai makamantansu. Amma wani hanzari ba gudu ba, wasu daga cikin waɗannan Program ba kyauta ake siyar da suba, su na da ɗan kuɗi kaɗan. Za ka iya bincikar Partition Software a internet, da yadda za ka yi amfani da su. Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Samar Da Website Na Kyauta Ta Hanyar Amfani Da Google Site danna nan.
  • Yadda Ake Buɗe Modem Ya Yi Aiki Da Kowanne Irin Layi

    Yadda Ake Buɗe Modem Ya Yi Aiki Da Kowanne Irin Layi

    Modem: Barkan ku da warhaka, ‘yan uwa daliban ilimin fasaha, yau na zo muku da sabon bayani a kan yadda ake buɗe modem ya yi aiki da kowanne irin layi(sim).

    Wanda bayan ka buɗe shi kana da damar sanya dukkanin layin daka ga dama a ciki, domin yin aiki da shi.

    Haka kuma, da yawa wasu sukan bada kuɗaɗe masu yawa wajen ganin sun aiwatar da wannan aiki.

    Amma a wasu lokutan ba a da buƙatar sai an buɗe shi da mabuɗin lambar buɗewa, sai dai a ɗan yi wasu saite-saite kamar yadda zai zo a ƙasa, misali wajen chanja setin na APN, misali idan kana da modem na kamfanin Airtel, sai ka bi wadannan matakai domin saita shi ya yi aiki da layin MTN ko wani layin.

    • A buɗe cikin Airtel Setting wizard.
    • A je cikin Configuration Setting sai ka zaɓi APN.
    • Sannan a chanja sunan APN (misali idan kana son ka sanya layin da ba na Airtel ɗin ba sai ka chanja airtelgprs.com zuwa ga mtngprs, ko makamantan sa).
    • Sai a ajiye Settings ɗin.

    Yanzu sai mutum ya yi connecting ɗin modem nasa zai ga ya yi connecting (wanda wannan yana aiki a cikin modem na Airtel ne kawai – Huawei E1731).

    Hanya Ta Biyu Da Ake Amfani Da Ita Wajen Bude Modem

    Yadda ake yi shi ne, a sami masarrafin (software) na UNIVERSAL MASTER CODE GENERATOR, wanda da yin amfani da wannan za a iya buɗe ZTE, NEC, LGkg110, Nokia, Huawei, VK ne kaɗai.

    Idan ana son a bude daya daga cikin wadannna modem din, sai a bi matakan da zasu zo, a kasa.

    1. Ɗauko Universal Master Code Software.(za ka iya sauke wanann masarrafin daga kan wannan link din. http://www.opendrive.com/files/12363728_miv7O_b84d/UniversalMasterCode.zip ).

    2. Mataki na 2 -> Bayan an ɗauko wannan software ɗin sai a danna kansa sau biyu, wanda ba ya buƙatar wani installation. A duba hoton dake kasa za a ga yazo kamar yadda yake a hoton nan.

    3. Shigar da nambar IMEI number, wacce tazo a jikin modem din.

    4. Yanzu sai ka dannan kan Calculate; zata kirga maka nambar budewar UNLOCK code da kuma nambar sharewa FLASH code.

    Abin Lura:

    Bayan an ƙirga nambar buɗewar Unlock code da kuma nambar sharewa flash code; sai ka sanya wani layin da ba na wannan modem ɗin ba, misali idan modem ɗin na MTN ne sai ka sanya layin GLO ko wani layin daban; bayan ka jona moden ɗinka da computer naka ka sanya shi, zai tambaye ka, ka sanya nambar buɗewar kodai Unlock code ko Flash code, sai ka sanya ɗaya daga cikin abun da ya tambaya, sai ka yi connecting da yanar gizo-gizo, wasu lokutan kuma wasu modem ɗin ba sa buɗuwa da wannan tsarin, sai dai da wata hanyar ta daban.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Menene Shafin Blog danna nan

  • Daga Cikin Addu’o’in Roƙon Ruwa

    Daga Cikin Addu’o’in Roƙon Ruwa

    “Allaahummasƙinaa gaisan mugiisan marii’an marii’a, naafi’an gaira dhaarrin, aajilan gaira aajilin”.

    {Ya Allah! Ka shayar da mu ruwan sama mai yaye tsanani, mai daɗi, mai ni’ima, mai amfani ba mai cutarwa ba, da gaggawa ba da jinkiri ba}.

    “Allaahumma agisnaa, “Allaahumma agisnaa, “Allaahumma agisnaa”.
    {Ya Allah! Ka yi mana agaji (da ruwan sama). Ya Allah! Ka yi mana agaji. Ya Allah! Ka yi mana agaji}.

    “Allaahummasƙi ibaadaka wabahaa’imaka, wanshur rahmataka wa ahyi baladakal mayyiti”.
    {Ya Allah! Ka shayar da bayinka, da dabbobinka; kuma ka yaɗa Rahamarka, ka rayar da ƙeƙasasshiyar ƙasarka}.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Addu’ar Neman tsayar Da Ruwan Sama  danna nan.

    Wannan bayanin an ciro sh ine daga Littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunnah wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Addu’o’in Neman Tsayar Da Ruwan Sama

    Addu’o’in Neman Tsayar Da Ruwan Sama

    “Allaahumma hawaalainaa walaa alainaa, Allaahumma alal akaami wazziraabi, wa buɗuunil waudiyati, wa manaabitis shajari”.{Ya Allah! Ka sanya shi ya zuba a kewayenmu, ba a kanmu ba. Ya Allah! Ka sanya shi a kan jigayi da duwatsu, da cikin rafuka, da wajen saiwoyin itatuwa}.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Addu’ar Ganin Jinjirin Wata danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunnah wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Yadda Ake Addu’ar Ganin Jinjirin Wata

    “Allahu akbar, Allaahumma ahillahu alainaa bil amni wal imani, was salaamati wal Islami, wat taufiiƙi lima tuhibbu Rabbana wa tardhaa, Rabbanaa wa Rabbukal laahu”.
    {Allah ne Mafi girma. Ya Allah! Ka sanya tsayuwarsa a gare mu ta zamo kwanciyar hankali ce da imani, da aminci da Musulunci, da kuma gamon Ƙatar da abin da kake so, ya Ubangijinmu, kuma kake yarda da shi. Ubangijinmu da Ubangijinka (ya kai wannan jinjirin wata!) shi ne Allah}.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Addu’ar Cin Abinci danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunnah wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi.

  • Yadda Ake Gasarar Gyaɗa (Peanut Butter)

    Yadda Ake Gasarar Gyaɗa (Peanut Butter)

    Barkan mu da sake kasancewa a cikin shirinmu na Girke-Girken WikiHausa, wanda muke koyar da ƙayatattun abinci namu na gida Nijeriya da kuma na ƙetare, tare da bayani a kan lafiyarsu cikin harshen Hausa a sauƙaƙe. Tare da ni Hafsat Shettimah.

    A yau za mu koyar da yadda ake yin gasarar gyaɗa (peanut butter) ku biyo ni a sannu domin mu koya tare.

    Ko kun san gyaɗa na ɗauke da sinadarai masu gina jiki, kamar protein, fiber, vitamin E, potassium, magnesium, za mu iya sarrafa gasarar gyaɗa waje abinci kala-kala, kamar; kunun gyaɗa, sandwich ko kuma ana iya ci da biredi da sauransu.

    Abubuwan Buƙata:

    1. Gyaɗa mara ɓawo [kofi ɗaya]
    2. Gishiri
    3. Barkono rabin ƙaramin chokali
    4. Chitta rabin kwatan ƙaramin chokali 1/3.

    Yadda Ake Haɗawa

    1. A cikin tukunya mai zurfi a zuba gyaɗa a soya ta, har sai ta yi kalar ƙasa (wato golden brown)
    2. Sai a juye gyaɗar a matankaɗi, a cire ɓawon jikin, sannan a bakace, har sai ta fita tas.
    3. A zuba kayan ƙamshi a ciki, sannan a markaɗa. Amma kar a saka ruwa
    4. Za a iya ci da biredi, ko yalon Bello, sannan ana iya yin kwaɗo da shi, ko kunun gyaɗa nau’o’in abinci masu lafiya. NOTE:- za a iya kunun da shi.

    Danna koren rubutu domin karanta Yadda Ake Dafaffiyar Gyaɗa da Yadda ake Gyaɗa Marau-marau

  • Abubuwan Da Sai Da Su Aure Yake Zama Karɓaɓɓe

    Abubuwan Da Sai Da Su Aure Yake Zama Karɓaɓɓe

    (1) Samuwar Amincewar Waɗanda Za A Ɗaurawa Aure

    A shari’ance, aure ba ya zama zartacce, abin la’akari da shi, sai idan an sami yardar ma’aurata da kuma amincewarsu. Dalili kuwa faɗar Allah Maɗaukaki: “Ku auri abin da ya kwanta muku a rai daga matan (da suka halatta a gare ku), biyu-biyu ko uku-uku ko kuma hudu-hudu.

    Da kuma hadisin da aka karɓo daga Ukbatu ɗan Amir (Allah ya yarda da shi) ya ce “Haƙiƙa Annabi ( Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ) ya ce: “Da wani mutum (da zai ɗaurawa aure ), ka yarda in aura maka wance? Sai ya ce: “Eh (na yarda)”, sannan Annabi ya ce da matar: “Kin yarda in aura miki wane? Sai ta ce, “Eh (na yarda)”, Sai Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ɗaura musu aure”. ( Baihaƙi da Hakim da wasunsu ne suka rawaito shi ).

    Kuma Abdullahi ɗan Abbas (Allah ya yarda da shi) ya ce: “Haƙiƙa, wata budurwa ta zo wajen Annabi ( Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ) ta ce: mahaifinta ya ɗaura mata aure (Da wani), ba da son ranta ba (nan take) sai Annabi (Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), ya ba ta zaɓin idan ta amince da wanda aka aura mata auren ya ɗauru, idan kuma ba ta son sa, to auren bai ɗauru ba”. ( Ahmad da Abu Dawud da wasunsu ne suka rawaito shi).

    Sannan an karɓo daga Khansa’u ‘yar Khidan (Allah ya yarda da ita) Cewa: mahaifinta ya ɗaura mata aure da wani tana bazawara, ba da son ranta ba, sai ta je ta shaida wa Annabi (Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) sai ya ce, “Auren bai ɗauru ba”. ( Bukhari ne ya rawaito shi ).

    (2) Waliyyin Matar Da Za A Aura

    Waliyyi shi ne mutumin da alhakin aurar da mace yake wuyansu, kamar uba, ko madadinsa, ko shugaban musulmai. Waliyyi ma sharaɗi ne daga sharuɗan da sai da su aure yake ɗauruwa a Musulunce. Saboda haka, bai halatta mace ta aurar da mace ba, kamar yadda bai halatta mace ta yi gaban kanta ta aurar da kanta ga wani ba.

    An karɓo daga Abu Huraira (Allah ya yarda da shi) ya ce: “Manzon Allah ( tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ) ya ce : “Mace ba ta aurar da mace, haka kuma mace ba ta aurar da kanta”. ( Ibn Majah ne ya rawaito shi ). Kuma an karɓo daga Ikrima da Abdullahi ɗan Abbas (Allah ya yarda da su) sun ce: “Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce: ” Babu aure sai da waliyyi”.

    Sannan kuma an karɓo daga A’isha (Allah ya yarda da ita) ta ce: Manzon Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce: “Duk matar da ta yi aure ba da izinin waliyyinta ba, auren ɓatacce ne. Idan kuma wanda ya aure ta a kan hakan, har ya sadu da ita, to, ya ba ta sadakinta, saboda saduwar da ya yi da ita. Idan kuwa mace da waliyyinta suka saɓa, to, shugaban musulmai shi ne waliyyin duk wacce ba ta da waliyyi”. (Abu Dawuda da Ibn Majah ne suka rawaito shi).

    (3) Shaidu

    Su kuwa shaidu su ne adalan mutanen da suke halartar gurin ɗaurin aure, su kuma kasance a gurin a lokacin da za a ɗaura auren. A Musulunce, mutane biyu su ne mafi ƙarancin shaidu game da ɗaurin aure. Saboda hadisin da aka karɓo daga Imran ɗan Husaini, da A’isha (Allah ya yarda da ita) cewa, Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce: “Babu aure sai da waliyyi da kuma shaidu biyu adalai”. (Imam Ahmad ne ya rawaito shi).

    Amfanin Samar Da Shaidu A Aure:

    Yana daga cikin amfanin da samar da shaidu yake da shi:
    1. Kawar da zargin zina, ko daduro tsakanin ma’aurata.
    2. Hana a kira ‘ya’yan da mutum ya Haifa ‘ya’yan zina (shegu).

    (4) Sadaki

    Sadaki shi ne dukiyar aure, wacce mace take cancantarsa daga wajen miji ta dalilin aure. Saboda faɗar Allah Maɗaukaki: “Ku ba wa mata sadakinsu cikin daɗin rai, idan kuma suka sayar muku da wani abu daga cikinsa da sonsu (don kansu), to, ku ci shi (halak malak ) rai kwance”. Da kuma faɗar Allah maɗaukaki: “To, waɗanda kuka ji daɗi da su daga cikinsu (mata) ku ba su sadakinsu (cikakke) tilas”.

    Sannan kuma Allah da hikimarsa da ya yi bayinsa, bai yi su bai ɗaya ba, don haka ma, da ya wajabta musu bayar da sadaki, sai bai iyakance musu shi ba. Saboda ya dace da mai hali da kuma mai ƙaramin ƙarfi. Kowanne gwargwadon halinsa. Don haka, a Musulunce ya halatta mutumin da yake da hali ya dunƙule wasu maƙudan kuɗi ya bayar a matsayin sadakin matar da zai aura.

    Allah Madaukaki ya ce : “Idan kuka yi nufin musanya wata mace a maimakon wata (da kuka saka) alhali kuwa da kun ba wa ɗayarsu (ta farkon) dukiya mai ɗimbin yawa (a matsayin sadakinta), to, kada ku karɓi komai daga cikinsa, shin kwa karɓe shi don zalunci da saɓo mabayyani”.

    Sai dai kuma mafi falalar sadaki shi ne wanda bayaninsa ya zo kamar haka:
    An karɓo daga Ukbatu ɗan Amir (Allah ya yarda da shi) ya ce: Manzon Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) “Ya aura wa wani mutum mace a kan sadakin zobe na ƙarfe”. (Hakim ne yarawaito shi). Bayan haka kuma, shi sadaki haƙƙi ne na matar da aka aura, kamar dai yadda bayani ya gabata. Saboda haka, bai halatta ba ga waninta ya ci wani abu daga cikinsa, sai dai inda izininta.

    To bayan kammalar bayanin waɗannan abubuwa da muka ji, ana so a lokacin da za a gudanar da ɗaurin aure a kwaikwayi Annabi ( Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) a rigayi ɗaurin auren da gabatar da wannan addu’ar kamar haka: An karbo daga Abdullahi ɗan Mas’ud (Allah ya yarda da shi) ya ce: Manzon Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ) ya koya mana yin “Huɗubar Haja” a lokacin ɗaurin aure. Wato:

    “Innal hamdulillahi ta’ala, nahmadhu wanastagiynuhu, wanastagfiruhu, wa na’u’zu billahi min shuruwri anfusina wa min sayyi’a’ti a’a’malina, man yahdihil-llahu fala mudilla-lahu, waman yudlil fala hadiyaya lahu, wa’ashadu an lailahaillallahu wahdahu la shariyka lahu, wa’ashadu anna muhammadan abduhuwarasuluhu.
    Ya ayyuhal lazina a’manuttaƙuwllaha haƙƙa tuƙatuhi wala tamutunna illa wa antum muslimun (Al-i-mran, aya ta (102)

    Ya ayyuhannasu-ttaƙuw rabbakumullazhiy kalaƙakum min nafsin wahida wakalaƙa minha zaujaha wabassa minhuma rajalan kasiran wa nisa’a’wattaƙuwllahal lazhiy tasa’a’luna bihi wal’arhama innallaha kana alaikum raƙiyba (An nisa’i aya (1)

    Ya ayyuhal-lazhina ‘a’manuttaƙuw-llaha wa ƙulu ƙaulan sadhidhan yuslih lakum a’a’malakum wa yagfir lakum zhunubakum waman yuɗi’illaha wa rasuluhu faƙad faza fauzan a’zhima (Al Ahzab) Abu Dawud, da Nisa’i da wasunsu ne suka rawaito shi.
    Sannan kuma ya halatta, bayan gama ɗaura aure, ranar a kai amarya gidan miji, a buga dundufa domin sanar da aure da kuma faranta ran ango. Amma bai halatta a yi rawa ba.

    Ranar Haɗuwar Ango Da Amarya:

    A Musulunce ana so ranar da ango ya fara haɗuwa da amaryasa ko kuma ranar da aka kawo wa ango matarsa gidansa, ya yi ƙoƙarin yin waɗannan abubuwa masu zuwa kamar haka:

    (1) Ango ya jagoranci matarsa su yi Sallah raka’a biyu- nafila don miƙa godiyarsu ga Allah da ya cika musu burinsu kamar yadda Ibn Abi Shaiba ya rawaito.

    (2) Ya ɗora hannunsa a kan goshin matarsa, wato ya karanta ya riƙe, sannan kuma ya karanta wannan addu’a kamar haka:
    “Ya Allah ina roƙonka alherin wannan mata da alherin da ka halicceta a kansa, kuma ina neman tsarinka daga sharrinta da sharrin abin da ka halicceta a kansa”. ( Bukhari a cikin littafinsa da Abu Dawuda da Ibn Majah da wasunsu ne suka rawaito shi ).

    (3) Gabatarwa da amarya wani ɗan abin kusa da baka, kamar yadda Annabi (Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ) ya yi wa matarsa A’isha (Allah ya yarda da ita ).

    (4) Goge baki kafin kwantawa da amarya, domin kawar da wani hamami, ko wari da ka iya tashi daga cikin baki. Kamar yadda aka samu Muslim da Abu Awana sun rawaito Annabi (Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ) ya yi haka.

    (5) Yin addu’ar saduwa da mace, kafin fara saduwa da ita. Addu’ar kuwa ita ce: ” Ya Allah ka nesanta ni daga shaiɗan ka kuma nesanta shaiɗan daga abin da ka azurta ni da shi”.
    Annabi ( Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ) ya ce: Idan Allah ya hukunta wa miji da matarsa samun ɗa a saduwar da suka karanta wannan addu’ar, to, shaiɗan ba zai cutar da ɗan da suka samu ba har abada”. (Bukhari da Muslim da wasunsu ne suka rawaito shi ).

    (6) Yin walima da abin da Allah ya hore, bayan tarewa da saduwa da amarya. Saboda aiwatarwar Annabi da kuma umarnin da ya yi na a yi walima.

    Sannan kuma idan za a kira jama’a walima, to a yi ƙoƙarin ganin an tara waɗanda suke mabuƙata, saboda Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ) yana cewa: ” Mafi sharrin abincin walima, wanda ake kiran (ko gayyatar) mawadata a ƙyale mabuƙata “. (wato a ƙi gayyatarsu). ( Malik da Bukhari da Muslim da wasunsu ne suka rawaito shi ).

    Daga lokacin da Allah ya hukunta wa musulmi aurar wata mace, ko kuma ya hukunta wa musulma auren wani musulmi, to ya zamar musu lallai su san cewa, a Musulunce akwai wasu nauye-nauye da suke tattare da rayuwar da za su fuskanta ta zaman aure, waɗanda suka sha bamban da na irin rayuwar da suka faro a baya ta zaman kaɗaici.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Nauye- Nauyen Rayuwar Aure danna koren rubutun nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Nagartacciyar Rayuwar Aure wanda Abubakar Abbas ya wallafa shi domin karanta cikakken littafin danna koren rubutun nan.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Koyi Da Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wassallam)

    Koyi Da Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wassallam)

    Wajibcin koyin da Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wassallam):

    Ita masa’alar koyi abu ne wanda yake haɗe da halittar ɗan Adam. A farkon rayuwar ɗan Adam yakan fara koyi da duk abin da ya ga ana yi, ko daga wajen wa ya ga abin. Yayin da ya bude ido ya gane iyayensa, to sai kuma ya koma koyi da su. To shi kansa wannan matakin akwai matsalarsa, idan ya zama su iyayen ba a kan shiriya suke ba. Shi ya sa Alƙur’ani ya yi ta fama da masu maƙalƙale wa iyayensu wajen koyi da su a mummunar hanya. Misali, inda Allah (Subahanahu wata ala) yake cewa:

    “Idan aka ce da su: “Ku bi abin da Allah ya saukar. Sai su ce “A’a, mu kawai za mu bi abin da muka saba iyayenmu suke kai ne. (Allah Subahana wata ala ya ce: “Yanzu za su riƙa bin iyayen nasu) Ko da iyayen nasu ba su da hankalin fahimtar abubuwa, kuma ba sa kan shiriya?” (Suratul Baƙarah, aya ta:170).
    Wani lokaci kuma mutum yakan ga wani wanda ya burge shi a wata ƙwarewa ta rayuwa, misali: ƙwararren mai tunani wanda ya ƙirƙiri wata hanya ta rayuwa. (kamar kwamanisanci, ko jari hujja. Ko wanda ya ƙirƙiro wani tsari na shugabanci. (kamar damakwaraɗiyya) ko ƙwararren ɗan siyasa wanda ya yi shuhura. Ko ma ƙwararren ɗan wasa ko ƙwararren jarimi a wani fim ko wasannin kwaikwayo. Idan ba a yi sa’a ba, sai mutum ya kama ɗaya daga cikin waɗannan ya zama abin koyinsa a rayuwa. Ka ga an shiga cikin ɓata marar iyaka.
    Wannan ya sa Allah (Subahanahu wata ala) ya yi ta aiko da manzanni domin a yi koyi da su, Allah (Subahanahu wata ala) yana cewa:
    “Waɗannan su ne waɗanda Allah ya shiryar. Ka yi koyi da shiriyarsu” (Suratul An’am aya ta:90).
    To kasancewar Annabinmu (Sallallahu alaihi wa sallam), shi ne na ƙarshe a cikin manzannin Allah, sai ya zama shi Allah ya sanya mana ya zama abin koyinmu. Allah (Subahanahu wata ala) yana cewa:
    “Haƙiƙa kyakkyawan koyi ya tabbata a gare ku, daga Manzon Allah, ga wanda yake ƙaunar Allah da (kyakkyawar makoma daga) Allah da ranar lahira, kuma, ya ambaci Allah da yawa” (Suratul ahzabi, aya ta:21).
    Wannan ya nuna wajibcin sanya shi abin koyi a dukkanin hanyoyin rayuwa.
    Koyi da Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wassallam) a dukkanin tsare-tsaren rayuwa:
    Duk wanda ya ce shi musulmi ne, to lallai ne abin koyin sa ya zamo Manzon Allah (Sallallahu alaihi wassallam), a dukkanin tsare-tsare na rayuwarsa. Misali: Tsarin Ilmi, tsarin zamantakewa, tsarin Tattalin arziƙi, tsarin siyasa (shugabanci) da tsarin shari’ah. Abin nufi a nan shi ne, duk waɗannan tsare-tsare na rayuwa su zamo a kan tsarin Alƙur’ani da sunnah, bisa fahimtar magabata na ƙwarai. Kada mutum ya zama sai a sallah, Azumi, aikin Haji kaɗai, yake musulmi. Watau ya zama yana bin tsarin da ya saɓawa na Allah. Allah (Subahanahu wata ala) Yana cewa:
    “Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku shiga Musulunci gaba ɗaya (watau ku miƙa wuya gaba ɗaya). Kada ku bi takun sheɗan, ba na Allah ba). Shi abokin gaba ne a gare ku, bayyananne” (suratul BAƙarah, Aya ta: 208).
    Abin taƙaici shi ne, a halin da muke ciki a yanzu, za mu ga cewa a dukkanin tsare-tsare nan na rayuwa babu wanda muke tafiyar da shi a kan tsarin da Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wassallam) ya zo da shi. Misali: Tsarin Ilminmu ba ya koya mana tauhidi da tsoron Allah da ranar lahira da tarbiyyar Musulunci. A tsarin zamantakewa. Idan muka ɗauki zamantakewarmu ta aure da zaman iyali, ba a kan Alƙur’ani da sunnah take ba. Tsarin tattalin arzikinmu cike yake da cin hanci da rashawa, cin riba, gululi’ (Watau satar dukiyar jama’a) da sauransu. Tsarin siyasarmu (shugabanci) tsari ne na Damakwaraɗiiyya, wanda babu Allah a cikinsa. Shi kuwa tsarinmu na shari’ah kowa ya san dokokin ‘yan Adam muke fifitawa a kan dokokin Allah (Subahanahu wata ala). Abin nufi a nan shi ne, son Annabinmu na baka ne kawai. Ba a aikace yake ba. Ga shi kuwa Allah (Subahanahu wata ala) yana cewa:
    “Gaya musu, idan kun kasance kuna son Allah, to ku bi ni, sai Allah ya so ku, ya gafarta muku zunubanku. Allah mai gafara ne, mai rahama” (Suratu Ali Imrana, Aya ta:31)
    Allah (Subahanahu wata ala) yana cewa :“Ka ce musu Idan iyayenku da ‘ya’yanku da ‘yan’uwanku, da matanku, da danginku da dukiyoyinku da kuka nema da hanyar samunku da kuke gudun kada ya yi tasgaro da gidajen da kuke jin daɗinsu, su suka fi soyuwa a gare ku, maimakon Allah da Manzonsa, da ƙoƙarin tabbatar da tsarinsa, to ku zauna, har sai Allah ya zo da lamarinsa (Mutuwa ko halakarwa). Allah ba ya shiryar da mutane fasiƙai” (suratul Taubah, Aya ta:24).

    Wannan duka yana nuna cewa ba za mu zama musulmi ba, sai mun gudanar da kowane ɓangare na rayuwarmu bisa tsarin Allah. Wannan kuma ba zai samu ba sai ta hanyar koyi da Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wassallam), watau ta hanyar ruƙo da alƙur’ani da Sunnah. Annabi(S.A.W) ya ce:
    “Na bar muku nauyaya guda biyu, ba za ku ɓata ba, matuƙar kun yi ruƙo da su: Littafin Allah da sunnata”
    Yadda Sahabbai Suka Yi koyi Da Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wassallam):
    Sahabban Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wassal) sun yi koyi da shi a cikin dukkanin harkokin rayuwarsu. Ba kawai sai a salla, Zakka, Azumi da Hajji kaɗai ba. Ga wasu misalai ‘yan kaɗan da za su nuna mana haka.
    Dab da Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wassallam) zai yi wafati ya zartar da wata rundina ta yaƙi, ƙarƙashin shugabancin Usamatu bin Zaid. Bayan wafatin Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wassallam) sai wasu suke ganin ya kamata a dakatar da wannan runduna tukuna, kasancewar an sami wasu suna ƙin bayar da zakka. Har ma aka zama cikin tsoron kawo hari cikin Madina. Me Abubakar ya yi a matsayinsa na shugaba? Abubakar bai yarda a dakatar da wannan runduna ba. Cewa ya yi:
    “Ba za ta yiwu ba a gare ni na kwance tutar da Manzon Allah (Sallallahu alaihi wassallam) ya ƙulla”.

    Haka nan sauran sahabbai suka goyi bayan Abubakar, Usamatu ya shugabanci wannan yaƙi kuma aka yi gagarumar nasara. Game da Madina kuwa, abin da Abubakar ya yi shi ne, sai ya sanya wasu daga cikin manyan sahabbai suka shugabanci wata runduna domin ba ta kariya, kamar su: Aliyu bin Abi Ɗalib, Zubairu bin Auwam, Sa’adu bin Abi Waƙƙas, Abdullahi bin Mas’ud da Abdur Rahman bin Aufin12.
    Wani abin da Sayyidina Abubakar ya yi (na ruƙo da tsarin Annabi) bayan wafatinsa (Sallallahu alaihi wassallam), wanda yake nuna dagewarsa, shi da sauran sahaban
    Sunnar Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wassallam) (watau tsarin sa na rayuwa) shi ne, wasu Larabawan ƙauye sun ƙi bayar da zakka bayan wafatin Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wassallam). A wannan lokacin cewa ya yi:
    “Wallahi! Idan da za su hana ni dabaibayi, wanda suka kawo wa Manzon Allah (Sallallahu alaihi wassallam), da sai na yaƙe su”.
    Wani abin da za mu sake lura da shi shi ne, yanayin da Nana faɗimah ‘yar Manzon Allah (Sallallahu alaihi wassallam) ta nemi gadon Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wassallam), a nan ma sai ya ce mata ya ji Manzon Allah ya ce:
    “Mu jama’ar Annabawa ba a gadon mu. Abin da muka bari, sadaka ne” (Bukhari da Muslim ne suka ruwaito).
    Wani misali shi ne, wata rana sayyidina Umar ya zo zai sumbaci Hajarul Aswadi sai ya tsaya ya ce:
    “Ni na san kai dutse ne. Ba ka cutarwa, ba ka amfanarwa. In ba domin na ga Annabi (Subahanahu wata ala) ya sumbace ka ba, da ba zan sumbace ka ba”. (Bukhari ne ya ruwaito).
    Wata rana Abdullahi bin Mas’ud ya zo zai shiga masallaci, sai ya ji Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wassallam) yana cewa: “A zauna”. Sai ya zauna a kan dokin ƙofar masallaci. Bai ƙara yin gaba ba ko kaɗan, sabo da cika umarni.
    Haka nan sahabbai suka yi ta koyi da Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wassallam), a dukanin tsare-tsaren rayuwa. Wata rana Abdullahi bin Mugaffal ya ga wani mutum (ko wani ɗan ɗan uwansa), yana yin jifan da ake kira ‘Hazfu (wadda akan sa tsakuwa a tsakanin babban danyatsa da ɗab ali, awulla ta). Sai ya ce da shi: “Manzon Allah (Sallallahu alaihi wassallam) ya hana yin hazfu. Da ya sake ganinsa yana yi sai ya ce: “Ina gaya maka Manzon Allah (Sallallahu alaihi wassallam) ya hana yin hazfu kana sake yi. Ba zan sake yin magana da kai ba, har abada” (Bukhari da Muslim ne suka ruwaito).
    Har ma ta kai cewa wasu daga cikin sahabbai suna koyi da Annabi, hatta a abubuwan da Annabi yakan yi ba da nufin lallai sai an yi koyi da shi ba.
    Abdullahi bin Umar ya shahara game da haka.
    Abdullahi bin Umar ya kasance yana zuwa ƙarƙashin wata bishiya a Madina, ya yi baccin rana. Da aka tambaye shi game da haka, sai ya ce shi kawai ya ga Annabi yana yin baccin rana a ƙarƙashinta.
    Wata rana Abdullahi bin Umar yana cikin tafiya tare da mutane, sai aka ga ya kewaye wani wuri, bai bi ta wurin ba, (Alhali babu komai a wurin), da aka tambaye, shi sai ya ce ya ga Annabi wata rana suna tafiya ya kewaye wurin.
    Haka nan wata rana an ga ya sauka a wani wuri tsakanin Makka da Madina, ya yi salla a daidai wannan wurin suna halin tafiya. Duk da kasancewar a lokacin mutane sun yi masallaci a kusa da wurin shi sai ya ƙi yin salla a masallacin, ya je ya yi a daidai inda Annabi ya yi (Sallallahu alaihi wassallam).

    Domin karanta cikakken bayani akan Muhimmacin Sanin Kamannin Annabi: danna koren rubutu.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga litttafin Mu San Kamannin Annabi (Sallallahu alaihi wassallam) Ɗabi’unsa Da Halayensa Domin Koyi Da shi wanda Dr Yahaya Tanko ya wallafa shi domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Azumin Kwanaki Shida A Watan Shawwal (Sitta Shawwal)

    Azumin Kwanaki Shida A Watan Shawwal (Sitta Shawwal)

    Watan Shawwal shi ne watan Karamar Sallah. Ana so mutum ya yi azumi shida (6) a cikinsa.

    Shi wannan azumi ana iya yinsa a jere, ana kuma iya rarraba shi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Azumin Kwanaki Shida A Watan Shawwal danna nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.