Tag: yadda ake

  • Falalar Adalci, Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    Falalar Adalci, Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    Hadisi Na Ɗaya A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Jarir ɗan Abdullahi (Radiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Duk wanda ba ya tausayin mutane, Allah ba zai tausaya masa ba”.

    Bukhari da Muslim da Tirmizi ne suka rawaito shi. Ahmad ma ya rawaito shi ya ƙara da cewa: “Wanda ba ya afuwa, Allah ba zai yi masa afuwa ba”.

    Abu Dawud da Tirmizi ne suka rawaito shi.

    Hadisi Na Biyu A kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abdullahi ɗan Amr ɗan Asi (Radiyallahu Anhuma) haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Masu tausayi Allah mai rahama zai tausaya musu. Ku tausayawa na ƙasa da ku, wanda yake sama da ku zai tausaya muku.

    Abu Dawud da Tirmizi ne suka rawaito shi.

    Hadisi Na Uku A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abu Hurairah (Radiyallahu Anhu) ya ce: Na ji mai gaskiya abin gaskatawa mai wannan ɗakin baban Alƙasim (Sallallahu Alaihi Wasallam) yana cewa: “Ba a cire tausayi sai daga zuciyar mara rabo a lahira”.

    Abu Dawud da Tirmizi ne suka rawaito shi.

    Hadisi Na Huɗu A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abdullahi ɗan Abbas (Radiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Ba ya tare da mu wanda ba ya tausayawa ƙaraminmu, kuma ba ya girmama babbanmu, kuma ba ya umarni da kyakkyawan aiki, ba ya hani ga mummuna.

    Tirmizi ne ya rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Waɗannan hadisai guda biyar suna bayyana falalar tausayawa mabiya da jinƙan su da sauran masu rauni da haramcin gallaza musu, suna nuna cewa duk wanda yake da jinƙai da tausayi Allah zai tausaya masa, kuma rashin tausayi alama ce ta rashin imani da rashin rabo a lahira, har ma Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Ba ruwan sa da maƙetaci mugu maras imani da tausayi da kuma wanda ba ya girmama na gaba da shi” .

    Hadisi Na Biyar A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    Hadisi Na Biyar A kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Aliyyu (Radiyallahu Anhu) ya ce: “Maganar ƙarshe da Manzon (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya yi ita ce: “Ku kula da sallah, ku kula da sallah, ku ji tsoron Allah ku kula da haƙƙoƙin waɗanda suke a ƙarƙashinku”.

    Abu Dawud da Ibn Majah ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Wannan hadisi yana daga cikin wasiyyoyin da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya bar wa al’ummarsa dab da wafatinsa. Ya yi wasiyyar a kula da sallah kuma a kula da haƙƙoƙin bayi da barori; da kuma duk waɗanda suke ƙarƙashin mutum.

    Hadisi Na Bakwai A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abdullahi ɗan Amr ɗan Asi (Radiyallahu Ahuma) ya ce; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Haƙiƙa masu adalci za su kasance a kan mimbarai na haske a daman Allah mai rahama; kuma duk hannayensa biyu dama ne. Su ne waɗanda suke yin adalci a cikin hukuncinsu da iyalansu da waɗanda suke jagoranta.

    Muslim da Nasa’i ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Haƙiƙa masu yin adalci da gaskiya a shugabancin da yake kansu da iyalansu suke kaucewa zalunci da nuna bambancin a tsakanin waɗanda suke jagoranta, za su samu babban matsayi a wurin Allah ranar lahira.
    Hannun dama da ya zo a wannan hadisin sifa ce daga siffofin Allah Ta’ala waɗanda ake yin imani da su kamar yadda suka zo, ba tare da an yi musu tawali ko canja su, ko kore su ba, ko kuma kamanta su da sifofin halittu ba.

    Hadisi Na Takwas Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Iyad bin Himar (Radiyallahu Anhu) ya ce: Na ji Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yana cewa; “Yan Aljanna guda uku ne: Mai mulki mai adalci mai dacewa da gaskiya; da mutum mai tausayi mai taushin zuciya ga dukkanin ‘yan uwansa da dukkan musulmi da kuma mutum mai iyali, mai kame kai da wadatar zuci.

    Muslim ne ya rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Falalar da darajar waɗannan mutane uku ta sanya Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya taƙaice ‘yan Aljanna a kansu. Saboda duk wani wanda yake riƙe da wani jagoranci tun daga mai gida da uwargida har zuwa kan shugaban ƙasa ya yi ƙoƙari ya yi adalci ya nemi gaskiya kuma ya yi aiki da ita.

    Kowa ya fitar da mugunta da ƙeta da gaba da ganin ƙyashi daga zuciyarsa, mu kasance masu tausayi da taimako da ƙauna ga dukkan ‘yan uwanmu da gabaki ɗayan musulmi.

    Kowa ya zage damtse ya nemi halal ya kula da iyalansa kuma ya wadatu da abin da Allah ya ba shi ya kasance mai godiya ga Allah ya rinƙa hangen na ƙasa da shi, kada ya rinƙa hangen na sama da shi.
    Waɗannan halaye za su sa mu cancanci shiga Aljannah, kishiyoyinsu kuwa, babu abin da za su jawo mana sai shiga wuta tun daga duniya kafin ta lahira.

    Hadisi Na Tara A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abu Huraira (Radiyallahu Anhu) ya ce; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: Allah Ta’ala yana ƙin mutane huɗu: Ɗan kasuwa mai yawan rantsuwa, da talaka mai girman kai, da tsoho mazinaci da kuma azzalumin shugaba.

    Nasa’i da Ibn Hibban ne suka rawaito shi; Muslim ma ya rawaito makamancinsa, sai dai a ruwayarsa ya ce; “Da talaka mai girman kai da shugaba maƙaryaci”.

    Hadisi Na Goma A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Mu’awiyya (Radiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Ba za a tsarkake al’ummar da ba hukuncin gaskiya a cikinta ba, kuma mai rauni ba ya iya karɓar haƙƙinsa daga mai ƙarfi cikin daɗin rai”.
    Ɗabarani ne ya ruwaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Wannan hadisin Ibn Majah ma ya rawaito shi tare da wata ƙissa mai ban sha’awa kamar haka:

    “Wani baƙauye ya zo wurin Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) domin karɓar bashin da yake bin sa. Ya matsa masa har ya ce: “Ba makawa sai ka biya ni bashina”. Sannan sahabbai suka daka masa tsawa suka ce: “Kasan da wa kake magana kuwa? Sannan ya kada baki ya ce: “To ba haƙƙi nake nema ba? Sai Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce da su: “Don me ba za ku goyi bayansa ba?

    Sannan ya aika wajen Khaulatu ‘yar Ƙaisu ya ce da ita: “Idan kina da dabino ki ba ni rance, kafin a kawo mana dabino mu biya ki”. Sannan ta ce: “An gama ya Ma’aikin Allah, uwata da ubana su zama fansa a gare ka”. Sai ta ba shi ya biya baƙauyen, har ya ba shi wani ya ci, ya ji daɗi, ya ce ka cika min Allah ya cika maka.

    Sai ya ce: “Ai waɗannan (masu cika wa mutane haƙƙoƙinsu) su ne zaɓaɓɓun mutane, haƙiƙa ba a tsarkake al’ummar da mai rauni ba ya samun haƙƙinsa cikin sauƙi daga mai ƙarfi”.

    Allahu Akbar! Ɗan’ uwa yi nazari kan wannan ƙissa dubi matsayin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) dubi kuma wane ne wannan Baƙauyen? Sannan ka dubi abin da ya faru tsakaninsu da kuma abin da ma’aikin Allah ya faɗa, lallai za ka fahimci darussa masu yawa.

    Duk al’ummar da ake rayuwar kashin dankali a cikinta, ake rayuwa irin ta rabon kura; rayuwar da uwa ba kwaɓa, uba ba harara, sai dai kowa ƙarfinsa ya ƙwace shi; maras ƙarfi kuwa sai dai ya yi Allah ya isa, to haƙiƙa wannan al’umma ko ƙasa ko gwamnati ba za ta yi wata daraja da mutunci da kwarjini ba, ballantana ta samu wani tsarki da yabo a wurin Allah da kuma mutane. Wannan zai gaggauta rushewar wannan al’umma da ci bayanta. Auna rayuwarmu a yau da wannan hadisi anya ba mu shiga cikinsa ba kuwa?

    Hadisi Na Goma Sha Ɗaya A Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abu Buraida daga mahaifinsa haƙiƙa Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; “Alƙalai iri uku ne: alƙalai biyu ‘yan wuta ne, alƙali ɗaya ɗan Aljanna ne. Alƙalin da ya yi hukunci ba na gaskiya ba, yana sane wannan ɗan wuta ne. Kuma Alƙalin da ba shi da ilmi ya yi hukunci ya halaka haƙƙoƙin mutane shi ma ɗan wuta ne. Alƙalin da ya yi hukunci na gaskiya wannan ɗan Aljanna ne.
    Abu Dawud da Tirmiz da Ibn Majah ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Wannan hadisin yana bayanin matsayin alƙalai a lahira. Duk alƙalin da ya yi zalunci saboda son rai ko wata buƙata ko rashawa da aka ba shi, da kuma alƙalin da bai nuna ba, ba shi da ilmin cancantar alƙalanci aka yi abin da aka yi aka ba shi alƙalanci ya zo yana taɓargaza, waɗannan biyun ‘yan wuta ne.
    Shi kuma alƙalin da ya cancanta kuma yana adalci da gaskiya wannan ɗan Aljanna ne.
    Saboda haka alƙalai su ji tsoron Allah, su yi gaskiya da adalci, su kasance cikin karatu da bincike a kowane lokaci. Su ma masa na da alƙalai su ji tsoron Allah su rinƙa naɗa waɗanda suka cancanta su guji naɗa jiƙaƙƙun mutane don kawai sanayya ko rashawa da sauransu.

    Hadisi Na Goma Sha Biyu Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Ibn Abi Aufa (Radiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Haƙiƙa Allah yana tare da alƙali matuƙar bai yi zalunci ba, idan kuwa ya yi zalunci sai Allah ya rabu da shi sai shaiɗan ya naniƙe masa.
    Tirmizi da Ibn Majah da Ibn Hibban da Hakim ne suka rawaito shi. Sai dai a ruwayar Hakim ya ce: “idan ya yi zalunci sai Allah ya yi watsi da shi”.

    Ahmad da Bazzar da Tabarani ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Allah Ta’ala yana taimaka wa shugabanni da alƙalai masu adalci yana ba su kariya; yana rufa musu asiri ya ɗaukaka su matuƙar sun kama hanyar zalunci da rashin gaskiya; sai Allah ya yi watsi da su ya bar su da dabararsu, su yi ta ɗimuwa da shirme, ga rashin ƙima a idon mutane; sannan in suka tafi a haka, a lahira su haɗu da matsananciyar azaba.

    Hadisi Na Goma Sha Uku Kan Falalar Adalci Da Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu

    An karɓo daga Abu Huraira (Radiyallahu Anhu) daga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; “Duk wanda ya shugabanci mutane goma za a kawo shi ranar ƙiyama a ƙuƙume (ɗaure) kodai adalcinsa ya kwance shi ko kuma zalunci ya halakar da shi.

    Ahmad da Bazzar da Tabarani ne suka rawaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Lallai wannan hadisin tsoratarwa ne mai girma ga shugabanni da masu neman shugabanci. Babban abin tsoron shi ne; hadisin bai taƙaita a kan shugaban ƙasa ko gwamna ko sarki ba, a’a duk wanda ya yi shugabanci daga mutane goma zuwa sama, to za a zo da shi a ɗaɗɗaure ranar ƙiyama cikin kukumi wato za a haɗe hannayensa a kan wuyansa a ɗaure. A haka za a yi masa hisabi in ya yi adalci a kwance shi; in bai yi adalci ba a hakan za a nutsa shi a wuta. Allah ya kiyaye mu Ameen.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Shugabanci A Musulunci (Hadisai Tamanin Da Biyu A kan Shugabanci); wanda Shehu Mansur Dala ya waallafa shi. Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Mazajen Da Nana Khadija Ta Aura Kafin Manzon Allah (S.A.W) danna nan.

  • Hadisai A Kan Kada A Goyi Bayan Mai Laifi

    Hadisai A Kan Kada A Goyi Bayan Mai Laifi

    Hadisi Na Ɗaya A Kan Kada A Goyi Bayan Mai Laifi

    An karɓo daga Abdullahi ɗan Umar (Radiyallahu Anhu) ya ce: Na ji Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yana cewa: “Duk wanda alfarmarsa ta hana a yi wani hukunci na Allah, haƙiƙa ya kishiyanci Allah Ta’ala, kuma duk wanda ya yi husuma a kan ƙarya yana sane, zai kasance cikin fushin Allah Ta’ala, kuma duk wanda ya yi wa wani mumini ƙage, Allah zai zaunar da shi a dagwalon Khabalu (Tafkin da surƙamin ‘yan wuta yake taruwa) har sai ya janye abinda ya faɗa.
    Abu Dawud da Hakim ne suka ruwaito shi.

    Ƙarin Bayani

    Wannan hadisi ya ƙunshi abubuwa uku muhimmai:

    1- Duk mutumin da ya hana a hukunta mai laifi; saboda matsayinsa to haƙiƙa ya yi daidai da mai ƙalubalantar Allah da kishiyantar sa. Wato ya mayar da kansa kamar wani kishiya ga Allah.

    2- Wanda yake ba da kariya ga mai laifi alhali ya san ba shi da gaskiya; Allah zai ta yin fushi da shi har sai ya janye jikinsa ya bar shari’a ta yi aikinta. Wannan ya haɗa da iyaye da ‘yan uwa da lauyoyi; da sukan kafe su yi ta jayayya a kan kare wanda su da kansu sun san ba shi da gaskiya.

    3- Masu yi wa mutane ƙage da sharri suna cikin babban hatsari; za a jefa su cikin dagwalon da ake tara da tafasa ruwan ciwo da ƙuraje na ‘yan wuta a ranar lahira; har sai sun daina yaɗa shi wanda tun daga nan duniya za a yi hakan in kuwa aka yi sake aka je lahira to fa sai yadda ta yiwu.

    Hadisi Na Biyu A Kan Kada A Goyi Bayan Mai Laifi

    Wani abu da yake kawo cikas ga ci gaba da nagartar kowace gwamnati da al’umma; shi ne neman alfarma da masu faɗa a ji sukan yi, domin a ƙyale masu laifi; ko kuma a sassauta hukuncin da ya dace a yi musu, ta yadda koda an yi hukuncin, sai ya zama kamar wasa. Wannan sai ya ƙarfafa guiwar ‘yan gata su yi ta tafka ta’asa son ransu; har ma aikata laifi ya zama wata burga da nuna isa, wato iya matsayinka ko gatanka, iya damarka ta aikata laifi, ka kwana lafiya. To shi me Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya faɗa kan nemawa masu laifi alfarma a ƙyale su?

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Shugabanci A Musulunci (Hadisai Tamanin Da Biyu A kan Shugabanci); wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi. Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Hadisi Na Ɗaya A Kan Haramcin Goyon Bayan Azzaluman Shugabanni danna nan

  • Yadda Ake Yin Tasbihi A Ruku’u

    Yadda Ake Yin Tasbihi A Ruku’u

    Tasbihi A Ruku’u: Mutum zai yi tasbihi a lokacin da ya yi ruku’u kamar haka; “Subahaana Rabbiyal Azim wabi hamdihi” sau uku ko kasa da uku.

    Ba zai ɗago daga ruku’u ba, har sai kowace gaɓa da ya malƙwasa ta ta koma mazaunin ta shi ne gwargwadon yadda tsayin ruku’un nasa zai zama.

    Haka kuma idan yana ɗagowa daga ruku’u zai ce “Sami Allahu liman hamidah” da zaran ya tsaya daram kuma sai ya ce,

    “Rabbana lakal hamdu ko walakal hamdu”.

    Zai tsaya gwargwadon yadda kowacce gaɓa za ta koma mazauninta kafin ya tafi sujudah.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ɗagowa Daga Ruku’u danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Sallar Alwala Da Falalarta danna nan.

  • Abin Da Ya Kamata Mai Yin Sallah Ya Yi Bayan Ya Tafi Sujudah

    Abin Da Ya Kamata Mai Yin Sallah Ya Yi Bayan Ya Tafi Sujudah

    Idan zai yi sujudah, ya tabbatar ya yi ne a kan gaɓoɓinsa guda 7.

    1-2 tafukan hannuwansa biyu, idan yana da su.
    3-4 guiwowin ƙafafunsa biyu, idan yana da su.
    5-6 wasu daga cikin yatsun digadigan ƙafafunsa biyu.
    7-tun daga goshinsa har zuwa hancinsa gaɓa ce guda ɗaya.

    Ba aso ya ware yatsun tafikan hannayensa ldan ya yi sujudah; kuma kar ya ajiye tsintsiyar hannuwansa biyu a ƙasa; kar ya boƙalo hannuwansa, kuma kar ya choge su a jikin haƙarƙarinsa.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Karatun Surah A cikin Sallah danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Sallar Kisfewar Rana Da Wata (Zazzaɓin Rana Da Wata) danna nan.

  • Yadda Ake Yin Ruku’u

    Yadda Ake Yin Ruku’u

    Bayan ƙare karatun surah; mutum zai yi ruku’u kamar haka, zai ɗora tafukan hannayensa biyu; yana mai ware ‘yan yatsun hannuwan nasa a kan gwuiwowin ƙafafunsa biyu;

    Zai miƙar da bayansa, sannan zai daidaita kansa, ba tare da ya lanƙwasa shi ko ya ɗago shi ba; sannan zai shigar da gwuiwar hannuwan nasa daidai gwargwadon yadda ba zai cutar da abokanan sahun sallah ba.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Yin Tasbihi A Ruku’u danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Sujjadar Tilawa danna nan.

  • Karatun Surah A Cikin Sallah

    Karatun Surah A Cikin Sallah

    Bayan karatun Fatiha , sai karatun surah; mutum zai karanta abin da ya sawwaƙa tare da shi na surah; ko ayoyi ko ya fara wata surar ya manta sai ya canza wata.

    Ko ya karanta farkon surah ya tsallaka tsakiya ko ƙarshenta, duk ya hallatta ga mai yin sallah; ana so lokacin da yake karatun ko limamin da yake bi sallah yake karatun; ya dinga tadabburin Alƙur’ani wato fahimtar saƙon, idan ɗalibin ilmin addinni ne; idan kuma ba ɗalibin ilmi ba ne, sai ya yi ƙoƙarin sauraren karatun cikin nutsuwa.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Yin Ruku’u danna nan

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Sujjadar Godiya Ga Allah danna nan

  • Yadda Ake Gyaran Gashi Da Sanya Shi Yayi Tsawo

    Yadda Ake Gyaran Gashi Da Sanya Shi Yayi Tsawo

    Gyaran Gashi Da Tsawo: Zaki samu shinkafa kowace iri ce rabin kofi; ki wanke ta sai ki zuba mata ruwa kofi biyu; sannan ki samu mazubi mai murfi ki rufe kibarshi har tsawon awa 24.

    Sai ki ɗauka ki riƙa murzawa kamar yadda kikeyi in zaki wanke, har tsawon minti goma. Sai ki tace ruwan kisamu costor oil kizuba ƙaramin cokali huɗu aciki sai ki ɗauka ki rinƙa shafawa akan ki.

    Ki tabbatar kin raba kan gida huɗu; sai ki shafa a kowanne bangare; sannan ki ɗaure ki barshi har zuwa safe ki wanke.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Gyaran Gashi danna nan.

  • Yadda Ake Warkar Da Kambun Baka Ko Maita

    Yadda Ake Warkar Da Kambun Baka Ko Maita

    Yayin da aka tabbatar da mayu sun kama mutum; ko kuma kambun baka ne ya kama mutum; akan umarce shi da ya yi wanka; sannan ya yi alwala sai ya karanta waɗannan ayoyin kamar haka;

    • Fatihatul kitab
    • Ayatul kursiyyu
    • Ƙarshen suratul ? Baƙarah wato Amanar rasul
    • Suratun Nas
    • Suratul Falaƙ
    • Sannan ya tofa a cikin ruwa ya sha sai kuma ya tofa a hannunsa ya shafe jikinsa. Sannan zai iya karanta su a cikin man zaitun sai ya rinƙa shafawa. Da yardar Allah nan take zai samu lafiya.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Addu’ar Kariya Daga Sharrin Maƙiya danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Addu’ar Samun Farin Jini Da Kwar Jini A wajen Al’umma danna nan 

    Edita; Rumasa’u Muhammada Kallamu

  • Guraren Da Aljanu Sukafi Zama

    Guraren Da Aljanu Sukafi Zama

    A wajen zama mun bambanta, sai dai da yawan mu muna rushe musu wurin zamansu sannan mu gina namu, kuma muna sare musu wajen zamansu mu dasa namu.

    Aljanu sun fi zama a cikin daji, saman dutse, saman ɗaki, cikin bola, cikin garken raƙuma, jikin shuri da dai sauransu. Da yawa akwai hatsari da mutum ya ga an share fili a daji ya tsugunna ya yi fitsari ko kashi.

    Akasarin irin wajejen nan aljanu ne suka yi jinya suka warke suka tashi a wajen don haka sai a kiyaye. Akwai waɗanda suke mu’amalantar mu a cikin gida, waɗanda su suke zama a cikin gida kamar yadda muke zama, haka kuma wasu daga cikinsu a hanya muke gamuwa da su, su rako mu har gida. Shi yasa musulunci ya koyar da mu addu’ar da za mu yi in za mu shiga gida da in za mu fita. Ya kamata in za ka bar gida sai ka ce;

    “Bismillahi tawakkaltu alallahi wala haula wala ƙuwwata illa billah, allahumma inni a’uzhu bika an adilla aw udilla, aw azilla aw uzalla, au azlima aw uzlama, aw ajhala aw yujhala alayya”

    Sannan in za ka shiga gida sai ka ce;

    “Bismillahi walajna, wa bismillahi kharajna wa’alal lahi rabbana tawakkalna”

    Amfanin addu’ar nan shi ne ko da aljanu sun biyo ka gida idan ka karanata wannan addu’ar za su ga babu ƙofa a gidanka, ba wurin zama sai su koma. Idan kuma ka yi sakaci wurin karanta ta, to za ka ga ka shiga gida cikin damuwa, da ƙunan rai da tashin hankali da jin haushin mutanen gidan.

    Daga lokacin shi kenan sun sami abinda suke so, ka yi ta faɗa da mutanen gida. Shi yasa musulunci ya koyar da mu hatta abinci in za ka ci ka ce bismillah, Allah ba zai ba su ikon su sa hannu su ci ba. In kuma ka gama cin abincin sai ka karanta wannan addu’ar;

    “Allahumma barik lana fi hi wa ta’amna khairan minhu”

    Idan ka yi wannan addu’ar Allah zai ba ka lada sannan kuma ya sa wa abincin da za ka ci albarka.

    Hatta kaya idan za ka cire, musulunci ya koyar da mu addu’a da ya kamata ka yi don ka samu kariya daga sharrin aljanu da sheɗanu. Don haka in za ka cire kayanka ka ce “bismillah” Allah zai rufe idanun aljanu ba za su ga tsiraicinka ba.

    Haka ɗakin da ya dade a rufe hatsari ne a shiga ba tare da an yi addu’a ba. Ko da shimfiɗa ce aka gyara ta domin a kwanta, musulunci ya koyar da mu ka karkadɗeta sau uku sannan ka yi addu’a ka kwanta. Kuma mu kiyaye zama a kofar ɗaki don wannan ma wurin zamansu ne.

    Sai a kiyayi zubar da ruwan zafi a makwarara, saboda nan ma wajen zamansu ne. Kuma a kiyayi zama a cikin ɗaki mai duhu da kuma yin surutu a bayi da zama kai ba ɗankwali da jiki a bude. Sai mu raba kanmu da yawan kalle-kalle marasa amfani ko jin kade-kade.

    Sannan uwar gida ki tattare kayanki da zarar magariba ta doso kai, ki killace yaranki, ki hana su zama ba riga, sannan a rufe kwanukan da aka ci abinci har dai za a bar su a waje. Wannan duk musulunci ya koyar da mu ne don kulawa da kanmu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Kalolin Aljanu Suke danna koren rubutun nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Addu’ar Samun Lafiya Ga Kowane Irin Ciwo danna koren rubutun nan.

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Yadda Kalolin Aljanu Suke

    Yadda Kalolin Aljanu Suke

    Aljanu kala-kala ne kamar yadda muke nau’in mu kala-kala:

    Ga kalolin Aljanu kamar haka:

    • Jinnul gawas
    • Jinnul ɗayyar
    • Jinnul bait
    • Jinnul jalab wal tahdir
    • Jinnul majus
    • Jinnul yahudi
    • Jinnul nasari
    • Jinnul muslim
    • Jinnul ashiƙ
    • Jinnul kamil
    • Jinnul tabdil
    • Ifritu minal jinn

    Waɗannan su ne kaɗan daga cikin kalolin aljanu, kuma kowanne aljani akwai alamominsa sannan akwai irin nau’in magungunansa. Akwai jinnu da yake kama da mutane sannan akwai jinnu da ake tura shi ya shiga mutum.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Alamomin Jinnu Yake danna koren rubutu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Mutane Biyar Da Suka Yi kama Da Manzon Allah (S.A.W)