Tag: yadda ake

  • Yadda Za Ki San Kanki Kafin Ki Yi Aure

    Yadda Za Ki San Kanki Kafin Ki Yi Aure

    Mata – Akan so kowacce mace a ce ta san kanta, budurwa ko matar aure ko kuma bazawara, wannan shi ne zai sa ki sami daraja a wajen mijinki.

    Da yawan mata, sun kasu gida huɗu kuma kowacce da hanyar da take bi gurin ta ga ta samu daraja a wajen mijinta; wata hanyar mallaka za ta bi, wata kuma hanyar gyaran jiki; wata kuma hanyar biyayya da kyautatawa, wata kuma wajen kwanciya.

    Ba laifi ba ne, in kin bi hanyoyi uku cikin huɗun nan; wajen ki ga kin samu daraja, kin zama ‘yar lele a wajen mijinki. Bin hanyar mallaka ita ce babbar illa ga mata; don kuwa ita ce ba ta lasting (ƙarko) don tana da iyaka, ba ta ɗorewa.

    Da yawa iyayenmu mata; idan za su aurar da yaransu mata, sun fi damuwa da shirin kayan ɗaki ko kuma shirye-shiryen kayan anko da irin fitar da amarya za ta yi; har ya rage wata uku kafin biki za ki ga ana koya wa ƙawayen amarya irin rawar da za su yi, don su burge ango da abokansa.

    Amma kaɗan ne cikin iyayenmu mata da suke bincikar amarya kama daga lafiyar jikinta da gyarensa; don ta burge mijinta in ta je gidansa.

    Kaɗan ne cikin ‘yan matan da idan suna da matsala suke iya bayyana ta ga iyayensu; wasu yaran sukan ɓoye ta har suje gidan miji da ita.

    Shi yasa da zarar mace ta yi aure sai ka ga kwana kaɗan namiji ya fara juya mata baya; ya fara hantarar ta, yana mata wulaƙanci, don kuwa ya rasa gamsuwar da yake son samu a wajen matarsa; don haka, iyaye ku kula sosai ku rinƙa jan ‘ya’yanku mata a jiki sosai, kuna sanin halin da suke ciki.

    Wannan shi ne zai ba ku dama ba za su rinƙa boye muku sirrinsu ba. Sanin halin da suke ciki shi ne zai ba ku damar ɗaukar mataki kafin ku kai su gidan miji.

    Mata na cewa, “Aure yaƙin mata” .

    Ki zauna da ‘yarki budurwa ki tambaye ta duk abin da yake damun ta da abin da take ji a jikinta da abinda take gani a gabanta kafin ki kai ta gidan miji.

    Kar ki kai ta gidan miji da cuta a jikinta, ya kasance shi kansa mijin ya tsani yarinyar ke kuma yana jin haushin ki.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Za ki Gyara Kanki danna koren rubutu.

  • Yadda Za Ki Gyara Kanki

    Yadda Za Ki Gyara Kanki

    Yadda Za ki Gyara Kanki. Akan so mace ta zauna kamar shinkafa a gidan mijinta; kar ki bari ya daina yinki, kar ki bari ya ƙosa dake.

    Kin san shinkafa za a iya sarrafata ta kowace irin launi. Misali; za a iya yin tuwon shinkafa, jellof, farar shinkafa, dambun shinkafa, fried rice dadai sauransu.

    Shinkafa ce za a shekara da shekaru ana cin ta a gida ba a gaji da ita ba, da zarar an yi sati ɗaya babu ita, ranar hankali ya tashi. Yara da kansu za ka ga suna cewa Daddy ba shinkafa.

    Don haka ki zama kina da dabarar iya kwanciya da mijinki, kullum da irin kwanciyar da za ki yi masa, ta yau daban ta gobe daban.

    Sai ki ga kin daɗe kina zamani a gidan mijinki, sai ki gan ki kullum amarya kike.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Abubuwan Daya Kamata A Sani Game Da Ciwon Sanyi danna nan.

  • Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Ciwon Sanyi

    Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Ciwon Sanyi

    Shi ciwon sanyi wanda Bature ke cewa (S.T.D: Sexual Transmitted Disease) yakan haddasa wa mata matsala daban-daban.

    Kama daga rashin haihuwa, ɗaukewar sha’awa, wasu kuma yakan yi yawa ya taɓa musu ƙoda ya haddasa mata ciwon da Bature yake kira kidney infection; wasu matan kuma ya cire musu sha’awa kwata-kwata.

    Irin wannan matsalar takan iya kama maza su ma, ta haifar musu da wannan matsalolin kamar yadda take haifarwa da mata.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Da Haka Na Gagara wanda Yahaya Ishaq ya wallafa shi; Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Alamomin Ciwon Sanyi Yake danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Maganin Damuwa danna nan

  • Addu’a Ga Yaran Da Ba Sa Ji

    Addu’a Ga Yaran Da Ba Sa Ji

    Yaron da ake gani ya ɗauko hanyar lalacewa ba ya jin magana; ba a sa shi ya yi kuma ba a sa shi ya bari, to ga wata tajriba da ya kamata uwa ta yi wa yaranta.

    Ranar Juma’a rana ce mai tsada. Shi ne lokacin sallar la’asar, duk addu’ar da kika yi a lokacin tana da tasiri ga wanda aka yi wa. A wata ruyuwar ma an ce Annabi Yaƙuba (Alaihis Salam) ya yi wa ‘ya’yansa addu’ar neman gafarar kuskuren da suka aikatawa ɗan uwansu Yusuf bayan Allah ya bayyanar da shi, don haka lokaci ne mai daraja.

    Ana son bayan kin yi sallar la’asar ki sami ruwan zamzam ko kuma na rijiya ko kuma wanda kika yi alwala kika rage.

    Bayan kin idar da sallarki cikin addu’arki sai ki karanta wannan addu’ar kamar haka;

    “Ya maliku yaumud din, iyyaka na’abudu wa iyyaka nasta’in, ihdina siraɗal mustaƙim, siraɗal ladhina an amta alaihim, gairil magdubi alaihim waladdaaliin”

    Sai ki roƙi Allah ya tsare miki yaranki ko yarinyarki tare da kiran sunanta ko sunanshi. Ki yi shi adadi mai yawa kya iya yin ɗari 100, kina karantawa kina tofawa cikin ruwan. In kin gama sai ki ƙara tahiya ita ma ƙafa ɗari 100 ki tofa cikin ruwan. Akan so kullum ki yi wannan har sai wata Juma’ar ta zagayo, kina yi kina tara ruwa. In kin gama sai ki rinƙa ba shi ruwan yana sha da safe kafin ya ci abinci haka da daddare kafin ya kwanta bacci. Inkuma ya yi kangarewar da ba zai sha ba, sai ki sarrafa masa a cikin abinci ya ci ya sha. Za ki ga mamaki yadda yaronki zai koma In Sha Allah.

    Domin karanta cikakken bayani akan Matakan Da Za A Bi Domin Hana Yara Shaye-shaye danna nan.

    Don karanta Hukunce-hukuncen Ƙananan Yara danna nan 

     

     

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Matakan Da Za A Bi Domin Hana Yara Shaye-shaye

    Matakan Da Za A Bi Domin Hana Yara Shaye-shaye

    Akan kai wani mataki duk irin kulawar uwa ko kuma kulawar uba ya zamto yaransu ko yarinyarta ta fanɗare.

    Ka ga yaro ya jefa kansa cikin wannan hatsarin rayuwa, yaro ya rinƙa shaye-shaye sakamakon abokai da ya gamu da su.

    Ga matakan da ake bi In Sha Allah zai daina:

    1. Matakin farko raba shi da abokan hurɗarsa a sama masa wajen sana’a.

    2. Mataki na biyu shi ne ana ɗaukan ayoyin sakina na Al ƙur’ani gaba ɗaya da kuma ayatus Sam, a karanta su a tofa a ruwan sama ko na rijiya, sannan a samu za’afaran da ganyen magarya da muski ɗan kaɗan sai a ba shi ya rinƙa sha da safe da kuma dare.

    Sannan za a iya ɗaukan dukkan nau’in kayan mayen da yake sha a haɗa su guri guda; anemo garin kustul hindi cokali uku da kuma man zaitun da man habba da kuma man kwakwa da na tafarnuwa da na’a na’a a haɗa su guri guda da kayan shaye shaye sannan a rufe a bar su su kwana.

    In gari ya waye a girgizasu sosai, sai a tace sannan a ba shi kafin ya ci abinci. Ana so da ya sha ya yi amai. Wannan haɗin ana so a rinƙa ba shi duk bayan sati uku ko kuma wata ɗaya. Sannan a haɗa da wannan ruwan da aka yi tofin ayoyin a ciki. Insha Allah duk abinda yake sha zai fita daga ransa ya dawo cikakken mutum.

    Minhaj 274
    Ayatus Sakina: Minhaj 255

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Addu’ar Haddar Karatu danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Karatun Manzon Allah danna nan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Addu’a Idan Mutum Yana Cikin Tashin Hankali

    Addu’a Idan Mutum Yana Cikin Tashin Hankali

    Wannan addu’ar za a iya karanta ta idan mutum na cikin mawuyacin hali; ko kuma mace ta rasa mijin aure; ko kuma mutum na cikin yawan bashi ko bashin gidan haya da dai sauran su. 

    An ruwaito daga Hassanul-al-basari, yace wata rana yana cikin tafiya a cikin garin Iraƙ, sai ya ga wani mutum kamar an ciro shi daga ƙabari, hankalinshi a tashe, sai Hassanul-al-basari yake tambayarshi me ya same ka? 

    Sai mutumin yake cewa; labarina akwai tashin hankali a cikinsa, da firgitarwa, amma ka yi alƙawari za ka ɓoye sirrina ba za ka sanar da kowa ba. Sai yace Hajjaj ne ya tsare ni a gidan yari shekaru uku; kuma aka hukunta za a kashe ni tare da wasu.

    Yace ina zaune wata rana a cikin gidan yari sai aka zo aka tafi da wasu mutanen da za a kashe. Bayan an zo an sare musu kai, sai aka dawo aka ce da mu gobe kuma za a kashe ku. Sai na gigice hankalina ya tashi, abinci na kasa ci saboda na san gobe kwana na zai ƙare. Ina cikin tashin hankali har na kasa bacci. Sai gab da asuba bacci ya ɗauke ni, sai na yi mafarki a cikin baccin an ce da ni; tashi ka yi sallah raka’ah biyu 2, idan ka idar da sallar ka karanta wannan addu’ar;

    “Ya manla yashgaluhu shai’un an shai’in, ya man a hada ilmuhu bima zara’a wa bara’a, anta aliun bi khafayatil umuri, muhsy wa sawisus sudur, waanta bil manzalil a’ala, wa ilmuka bil manzilil adna, ta’alaita uluwwun kabira, ya mugithu agithni, wa fukka asri, wakshif durri faƙad naƙida sabri”

    Yace sai na tashi na yi alwala a cikin halin da nake ciki na fargaba, na yi sallah raka’ah biyu 2 kamar yadda na ji a mafarkina, na haddace abinda aka faɗa min a mafarkina, ban bar kalma ɗaya ta kuɓuce min ba daga ciki abin da aka gaya min.

    Wallahi ban kai ƙarshe ba daga cikin kalmomin da na sani sai na ga wani haske, sai na ga wani mutum. Yace koda na kalla, sai na ga ƙofar gidan yarin an buɗe ta, sai kawai na ji an ce tashi ka fita. Shi ne na taso na kama tafiya, Allah ya kawo min mafita, Allah ya warkar da ni damuwa ta, sannan na samu wadata a rayuwa ta.

    Wannan addu’ar duk mutumin da ya samu kansa a cikin wata damuwa ko wani tashin hankali, ko al’amura sun caɓe masa, ya rasa yadda zai yi da kansa, to ya dinga tashi cikin dare ya yi nafila ya karanta wannan addu’ar. Da yaddar Allah, Allah zai kawo masa ƙarshen damuwarsa In Sha Allah.

    An samo wannan addu’ar a cikin littafin MUFATIHUL FARAJ shafi na 108.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Addu’a Idan Mutum Yana Cikin Damuwa danna koren rubutu.

    Don karanta bayani a kan Addu’a Gatan Mumini danna koren rubutu.

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Addu’ar Neman Falala

    Addu’ar Neman Falala

    Wannan addu’a ana yin ta domin neman falala da buɗi akan abinda ka sa a gaba, karatu ko kasuwanci.

    Akan so ka zama mai yawan salatul-duha; kamar yadda aka ruwaito daga Abu Hurairah (Radiyallahu Anhu) yace; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya min wasicci da abubuwa guda uku (3) su ne salatul-duha, sallah raka’ah huɗu lokacin da rana ta fito (da ƙarfe 9 zuwa 10 na safe); Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) yace; ta fi duniya da abunda ke cikinta da kuma yin azumi uku a kowane wata; da kuma salatul-witr, shafa’i da witr kafin a kwanta bacci.

    A yi sa’a ma’abocin yin salatul-duha ne kafin ka fita harkokin ka ka yi sallar raka’ah biyu ko huɗu. Bayan ka yi sallama, kayi salatin Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) da hailala sai ka karanta wannan addu’ar kamar haka;

    “Allahummaj al awwala hazan nahar salaahan, wa ausadahu falaahan, wa akhiruhu najaahan, as aluka khaira dunya wal akhira, ya arhamur rahimin. Labbaika lahumma labbaik, wa sa’daika wal khairu fi yadaka, wa minka ilaika”

    Wannan Addu’ar Neman Falala; An samo ta ne daga littafin DUA’U YARFA’U BALA’I, shafi na 49.

    Don karanta bayani akan Falalar Tafiya Masallaci danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Addu’ar Da Abi Zaril Gaffari Yake Yi danna nan.

  • Yadda Ake Addu’ar Tashi Daga Bacci

    Yadda Ake Addu’ar Tashi Daga Bacci

    An karɓo daga Aisha (Radiyallahu Anhu) tace Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam); ya kasance yana tashi daga bacci zai karanta wannan addu’a;

    Ga Addu’ar Tashi Daga Bacci kamar haka:

    “La ilaha illa anta subhanakallahumma astagfiruka li zhanbi; wa as’aluka rahmatikallahumma zidni ilman, wala tazig ƙalbi ba’ada iz hadaitani; wahab min ladunka rahmatan innaka antal wahhab” (Abu Dawud)

    Ana so duk wanda ya tashi daga bacci, na safe ne ko na rana ko kuma na yamma to ya karanta wannan addu’ar yayin da ya farka, to Ubangiji zai ba ka kariya daga duk wani abu da zai cutar da kai a ranar kuma Allah zai sa ka samu nutsuwa da wadatar zuciya.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Addu’ar Sauƙin Bashi danna nan.

    Domin karanta bayani a kan Yadda Ake Addu’ar Neman Biyan Bashi danna nan.

  • Yadda Ake Addu’ar Biyan Bashi

    Yadda Ake Addu’ar Biyan Bashi

    Addu’ar Biyan Bashi – Wannan addu’a ce ga wanda bashi ya yi wa yawa, yana so ya biya, ko kuma mutum na cikin tsanannin ƙuncin rayuwa.

    Akan so ka tashi cikin dare, ko kuma wani lokacin ka yi alwala, ka yi sallah raka’a biyu; sannan ka karanta wannan addu’a;

    Bismillahir rahmanir rahim, allahummag firli zanbi, wa was’is khulƙi, wa ɗayyib li kasbi, wa ƙanni’ni bima razaƙtani, wala tuzhib ƙalbi ila shai’in sarraftahu anni”.

    Sannan ana so duk lokacin da ka idar da sallar asuba, ko kuma wata sallah cikin salloli biyar, to ka yawaita karanta wannan addu’ar. Yawaita karanta wannan addu’ar yakan sa Allah (Subhanahu Wata’ala) ya warware maka dukkan bashin dake kanka. Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ne ya bai wa Sayyidina Aliyu (Radiyallahu Anhu). Ya ce da shi; “Shin ina so in ba ka tumaki guda dubu biyar, ko kuma na ba ka wasu kalmomi biyar. Sai sayyidina Aliyu ya ce,” Ya Rasulullahi ka ba ni kalmomi guda biyar, sai sun fi dabbobi dubu biyar”.

    Addu’ar Biyan Bashi – An samo wannan addu’ar ne a cikin littafin Miftahul Farj, shafi na 110.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Addu’ar Biyan Buƙata A Wajen Allah (S.W.T) danna nan.

    Don karanta bayani a kan Lokuta Zaɓɓaɓu Na Karɓan Addu’a danna nan

  • Falalar Tafiya Masallaci

    Falalar Tafiya Masallaci

    Tafiya masallaci domin yin ɗaya daga cikin salloli biyar bayan alwala. A lokacin da mutum ya ƙare alwala, idan namiji ne, duk takun da zai yi ko ɗaga ƙafa yayin tafiyar; sai an ɗaga darajarsa, an yafe masa zunubansa; haka ma kuma mace lokacin da take tafiya wajen da za ta yi sallah, ita nan ne masallacinta.

    Ana so mutum ya yi tafiya cikin nutsuwa domin tara lada mai yawa. Isowar sa masallaci ko kuma isowar ta wajen da take yin sallah, idan da dama, ana so a yi nafila raka’a 2 kafin sallar farilla.

    Ga sunayen nafilfilin salloli biyar da yadda ake gabatar da su.

    Ana kiran su da Larabci (Assunanur rawaatibi, Assunanun attabi’atu lil fara’idi). Ma’anar su a harshen Hausa ita ce, jerarrun sunnoni.

    Idan da Asuba ne ana yin raka’a biyu, wacce ake kiranta da Larabci (raka’ataanil fajri) ma’ana raka’a biyu lokacin fitowar alfijir, in Azahar ne ana yin raka’a biyu ko huɗu kafin sallar Azahar, sannan kuma raka’a biyu bayan sallar azahar.

    Idan da La’asar ne kuma raka’a biyu kafin sallar La’asar; in Magriba ce raka’a biyu bayan sallar Magriba, da isha’i kuma raka’a biyu bayan sallar Isha’i.

    Shi ne yawan su ya kai raka’a 14 idan mutum ya yi huɗu kafin Azahar, idan kuma biyu ya yi, sun tashi raka’a 12 kenan.

    Idan mutum ya yi sallama, yana zaune inda yake bayan nafila kafin sallar farilla; mala’iku za su dinga masa addu’a suna cewa Allah ya masa rahama; ya masa gafara, ya yi sallah masa afuwa matsawar bai yi hadasi ba kuma bai cuci wani a lokacin;wannan falalar duk ɗaya ne ga mace ko na miji.

    Domin karanta bayani a kan Fa’idojin Da Sallar Nafila Ta Ƙunsa danna nan

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Sallar Tahajjudi danna nan