Yadda Ake Sujjadar Tilawa

0
727

Sujjada ce guda ɗaya da ake yi, yayin karanta ko sauraron ayar da sujjadar take a cikin Al-kur’ani. Sujjadar tilawa sunna ce mai ƙarfi, har ma waɗansu malaman suna ɗaukar ta a matsayin wajiba.

Ana yin kabbara yayin sujjada da kuma ɗagowa, ba a sallama, ana yin tasbihi a cikinta ,ana son a faɗi wannan zikirin a cikinta “Sajada wajhi lallazi khalkahu, wasawwarahu wa shaƙƙa sam ahu wa basarahu bi haulihi wa ƙuwwatihi”.
Mafi yawan malamai suna ganin tilas sai da alwala, kuma sai an fuskanci alƙibla; sannan a lokacin da ya halatta a yi nafila ake yinta. Amma Ibn Hamz da Ibn Taimiyya suna ganin duk wannan ba sharaɗi ba ne, tun da dai ba salla ba ce, idan mutum yana sallah sai ya karanta ayar sujjada, zai iya yin sujjadar sannan in ya ɗago ya ƙara karantun ko kuma ya yi ruku’u kawai.

Wuraren da ake yin sujjadar tilawa a Ƙur’ani su ne kamar haka:

Suratul A’araf aya ta 206.
Suratul Ra’ad aya ta 15
Suratul Nahli aya ta 49 – 50
Suratul Isra’I aya ta 109.
Suratul Maryam aya ta 58.
Suratul Hajj aya ta 18.
Suratul Furkan aya ta 60
Suratul Namli aya ta 26.
Suratul Sajda aya ta 15.
Suratul Fussilat aya ta 37/38

Waɗannan wurare babu wani saɓani a kansu tsakanin malamai. Sai kuma wuraren da aka yi saɓani a kansu amma dalilansu sun inganta su ne:

11. Suratul Sa’adi aya ta 24.
12. Suratul Najmi aya ta 62.
13. Suratul Inshiƙaƙi aya ta 21.
14. Suratul Alaƙ aya ta 19.
15. Suratul Hajj aya ta 77.
Waɗannan wurare na ƙarshe, ba a sami hadisi a kansa ba, sai dai an samo sujjada daga sahabbai da dama da kuma tabi’ai.

Domin karanta cikakken bayani a kan Sujjadar Godiya Ga Allah danna nan.

Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi domin karanta cikakken littafin danna nan.

labarin da ya wuceYadda Ake Sallar Roƙon Ruwa
Labarin na GabaYadda Ake Sujjadar Godiya Ga Allah