Tag: tatsuniya

  • Tatsuniyar Maye Da ’Ya’yansa

    Tatsuniyar Maye Da ’Ya’yansa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum a wani gari da ke gabas da garin nan. Yana da mace ɗaya da ’ya’ya biyu mata. Da suka isa aure Allah ya ba su masoya, aka yi musu aure aka kai kowacce ɗakinta. Bayan ’yan shekaru kowacce ta haifi ’ya’ya. Ana nan, sai aka aika musu uwarsu ta rasu; sai dai su ba su san cewa ubansu maye ne ba, kuma shi ne ma ya cinye uwar tasu.

    Shi ke nan yaran nan suka je gidan ubansu saboda zaman makoki, amma sai suka tarar uban nasu ya cinye gawar uwar tasu, domin yunwar maita ta kama shi, kuma babu wanda zai ci sai gawar. Da ya ji muryar ’ya’yansa, sai ya kulle kansa a cikin ɗaki don kada su gani, su gane.

    Duk sanda suka kai masa abinci, sai yace su ajiye a ƙofar ɗaki. Bayan sun yi kwana biyu a gidan, sai a dare na uku ya tara su, ya fara zaro harshe yana haɗiyar yawu. Sai suka gane cewa shi ya cinye babarsu, kuma yana so su ma ya cinye su. Da man sunan ɗaya Nkwa, ɗaya kuma Sektiraye.

    Sai ya fara kiran su yana cewa: “Nkwa da Sektiraye duk da ’ya’yanku, Ku jira ni ina zuwa, Zan cinye ku, Da man ina jin yunwa.” Da suka ji haka sai suka kama ’ya’yansu suka ɓuya, kuma suka ajiye kabewa a kan gado suka lulluɓe ta. Da dare ya yi tsaka, sai
    kawai ya tashi ya kama cin kabewar da ke kan gado.

    Da ya gane ba nama ba ne, sai haushi ya kama shi. Can kuma sai ɗaya daga cikin jikokinsa ya fara kuka a inda suka ɓuya. Da ya gane inda suka ɓuya, sai ya yi kukan kura ya auka musu, amma bai cafki ko ɗaya ba. Sai ’ya’yan nasa da jikokin suka fito da gudu, suka kama hanyar dajin da ke kusa da garin, shi kumayana bin su.

    Suna cikin gudu a dawan nan sai ya kama ɓarin jikinsa ya cinye, har dai ya zama saura ƙashi a jikinsa kawai. A hakan yake bin su da gudu yana cewa: “Dun kwalak, ka dun kuci kal.” Da suka isa wani guri a cikin dajin, sai suka tarar wuta tana cin ciyawa, sai suka keta ta cikin wutar a guje.

    Saboda yawan wutar, har ta kama cin hanya. Da uban nasu wanda ya zama ƙwarangwal
    ya isa wurin wutar nan, sai ya faɗa cikinta, wuta kuwa ta cinye ƙasusuwansa, ya ƙone ƙurmus. ’Ya’yan nan nasa da jikokinsa sun sami tsira. Da gari ya waye, sai wasu mata masu neman tokar miya suka tarar da tokar wannan maye a kan hanyar, ba su san ta mutum ba ce.

    Sai ɗaya daga cikinsu ta ce su deɓi tokar miya. Sai suka ɗiba, suka koma gida. Sai ɗaya daga cikin matan ta haɗa tokar za ta yi miya da ita. Bayan ta ɗora tukunyar miya da tokar a ciki a kan wuta, sai ta ji miyar tana cewa: “Ki juya ni a hankali, domin wuta ta ƙona ni da yawa.” Da ta ji haka ba ta ce uffan ba, kuma ba ta daina girki ba, har sai da ta gama.

    Da ta gama, ta zuba, ta kai wa mijinta abincinsa a akushinsa. Data je ajiye akushin sai ta ji an ce: “Idan za ki ajiye ni, ki ajiye ni a hankali don wuta ta ƙona ni da yawa?” Da mijin ya ji, sai ya kira matarsa ya ce mata: “Na ji kamar miyar tana magana.” Sai ta dubi mijin tana murmushi ta ce: “Kai anya, ba kunnenka ba ne kuwa?”

    Sai mijin ya sa hannu zai buɗe akushi ya fara cin tuwo da miya, sai miyar ta ce: “Idan za ka deɓe ni, ka deɓe ni a hankali, don wuta ta ƙona ni sosai.” Da mijin ya ji haka, sai ya dubi matar ya ce: “To ashe ke mayya ce ban sani ba.” Sai matar ta ce: “A a ai a cikin jeji na samo tokar miya.”

    Sai mijin ya ɗauki miyar ya kwara mata a ƙirji. Nan take ƙirjinta ya fitar da haƙora gatso-gatso, abin gwanin ban tsoro. Da mijin ya ga haka, sai ya kore ta, sai ta shiga daji, ta koma can da zama. Duk wanda ya je dajin da take zai tarar da ita tana yawo, tana cin fari da kwaɗi. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Tsautsayi ba a sa maka rana.
    • Mai mugun hali tun a duniya sai ya ɗanɗana kuɗarsa.
    • Aikin da ba a yi shi da kyakkyawar niyya ba ƙarshensa nadama.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Binta ’Yar Sarki

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Binta ’Yar Sarki

    Tatsuniyar Binta ’Yar Sarki

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wani Sarki a wani gari mai mata biyu, kowacce tana da’ya. Yarinya ɗaya sunanta Binta, ɗayar kuma Falmata. Sarki yana ji da’ya’yan nan nasa, to amma fa ya fi son Binta don ita ce ƙarama, kuma ’yar amarya.

    Ana nan, rannan sai Sarki ya tafi wani gari mai nisa, kuma zai daɗe a can. Bayan ya tafi da ’yan kwanaki, sai ciwo mai zafi ya kama amaryarsa, watau mahaifiyar Binta. Da ta lura ciwon kamar ba wanda za ta tashi ba, sai ta kira kishiyarta ta gaya mata cewa tana jin ba za ta tashi ba, amma idan ta cika, tana roƙonta ta kula da’ya’yansu cikin amana.

    A cikin tausayi kishiyar ta ce da ita: “Zan yi bakin ƙoƙari na in kula da su.” Bayan kwana biyu da yini ɗaya, sai amaryar Sarki ta rasu. Sarki dai bai dawo daga tafiyar da ya yi ba har wasu ’yan kwanaki suka wuce. Rannan sai kishiyar uwar Binta ta sa ta ɗauko ruwa a rafi a cikin wani masaki, kuma ta gaya mata lallai a rafin Apko mai cinye mutane za ta ɗebo ruwan, watau ba a ɗaya rafin mai lafiya ba.

    Ɗaya rafin mai lafiya wanda daga shi mutanen suke ɗaukar ruwa sunansa Diddire. Binta ta ɗauki masaki ta garzaya wajen kabarin mahaifiyarta, tana kuka tana waƙa, tana cewa:

    “Baba, baba, babar Binta,

    Kishiyarki ta ce in je Apko in ɗebo ruwa,

    In je Apko ko in je Diddire?”
    Daga cikin kabarin sai ta ji mahaifiyarta ta amsa mata dawaƙatana cewa:

    “Ki je Diddire,

    Kada ki je Apko,

    Domin Apko zai apka da ke.”

    Sai Binta ta tafi rafin Diddire ta ɗebo ruwa. Da kishiyar uwarta ta ga ba ta ɗebo ruwan Apko ba, sai ta hau ta da duka. Ta ma zubar da ruwan da ke cikin masakin, ta ce lallai maza ta je ta ɗebo mata ruwa daga kogin Apko, kuma ta gaya mata cewa idan ta kuskura ta ɗebo mata ruwan Diddire, to za ta yanka ta.

    A kan dole Binta ta ɗauki masakin ta tafi rafin Apko ɗiban ruwa. Tana shiga za ta ɗebi ruwan, sai rafin ya cinye ta. Tana nan a cikin ruwa, har wasu ’yan kwanaki. Ita kishiyar uwarta ba ta sa an je nemanta ba, kuma ita ba ta je ba. Ko fadawa ma ba ta gayawa ba, har ranar dawowar Sarki.

    A ranar da Sarki ya dawo sai fadawa da jama’ar gari suka fita bayan gari suna yi masa barka da zuwa. Masu tambura suka goce da kiɗa, ana yi masa kirari ana cewa: “Baban Binta ya dawo, Sarki baban Binta ya dawo.” Da Binta ta ji ana buga tambarin babanta, ga shi kuma ba za ta iya fita daga ruwan ba, sai ta kama kuka da waƙa tana cewa:

    “Falmata ce ’yar Sarki,

    Babanta ya dawo,

    Falmata kin ji daɗi,

    Falmata ’yar Sarki.”

    Sarki ya sa ido ko zai ga Binta a cikin masu tarye, amma bai gan ta ba, kuma ya saɓa idan ya yi tafiya ya dawo akan ɗoro ta a kan doki, a kai ta gabansa, su gaisa. Ya sake dubawa bai ga Binta ba sai Falmata. Sai hankalinsa ya tashi, har dai ya kasa daurewa ya tambayi fadawansa inda Binta take.

    Sai suka ce ai Binta ta ɓata, ba wanda ya san inda take. Suka ƙara da cewa ai ma yau kwana goma sha tara kenan da uwarta ta rasu. Hankalinsa ya tashi, amma ya yi
    ta maza, ya shanye halin damuwar da yake ciki. Da ya shiga gida, sai ya kira uwargidansa, ya tambaye ta inda Binta ta je.

    Sai ta ce ba ta sani ba, tun da dai ta fita yawo ba ta sake komawa gida ba. Yana jin haka, sai ya sa aka shiga neman Binta. Wasu daga masu nemanta suka bi ta rafin Apko. Da fari ba su ga alamun kowa a can ba, to amma daga baya sai suka ji muryar mutum na waƙa a cikin rafin. Da suka kasa kunne da kyau, sai suka ji ana waƙa ana cewa:

    “’Ya’yan uwa kada ku zo Apko,

    Idan kun zo zai apka da ku,

    Ni kishiyar uwa ta aiko ni nan,

    Har ya apka da ni.”

    Da masu nemanta suka ji haka sai kawai suka koma suka shaida wa Sarki abin da suka jiyo a kogin Apko. Sai Sarki yace da su da sauran fadawansa su je tare da shi bakin rafin ya ji. Nan da nan suka dunguma, kuma suka tarar Binta tana yin wannan waƙar. Sarki ya kasa kunne, kuma daga ƙarshe dai ya fahimci cewa muryar Binta ce.

    Sai nan da nan ya ce da Sarkin maroƙa ya shiga gari ya yi yekuwa cewa duk wanda ya fito da Binta dagakogin Apko za a ba shi dawakai da dukiya mai yawa. Da fari ba wanda ya ce zai gwada, amma can sai wani tsoho ya zo ya ce zai shiga ruwan ya tsamo ta. Sai wasu mutanen garin suka ce: “Amma tsohon nan da rigima kake.

    Ga mu nan duk da ƙarfinmu mun kasa, ballantana kai da ka tsufa?” Sai Sarki ya ce: “A bar shi ya gwada.” Tsoho ya faɗa ruwa, zuwa wani ɗan lokaci sai ya fito da Binta a hannunsa. Da Sarki ya ga ’yarsa sai ya ji kamar ya zabura da gudu ya rungume ta saboda murna da farin cikin da yake ciki.

    Amma sai ya nuna halin manya, ya jure. A cikin murna da farin ciki Sarki da fadawansa da jama’arsa suka yi ta gode wa tsohon nan. Da aka koma fada ya sa aka kwanto dawakai Asbin da kili da fari da ja da baƙi da ingarma da kuru da dai dawakai iri-iri masuyawa da dukiyar da ba a taɓa ganin irinta ba a ƙasar, aka ba tsoho.

    Bayan an tashi daga zaman fadanci Sarki ya shiga turakarsa, sai ya kira matarsa da Falmata, ya tambaye su yadda aka yi Binta ta faɗa ruwa. Sai suka yi shiru. Da dai ya gane munafunci suka yi, sai ya kore su, ya ci gaba da rayuwarsa da ’yarsa Binta. Shi ya sa duk wanda ya je garin zai ji ana cewa: “Binta ’Yar Sarki.” Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Alkawari kaya ne.
    • Kowa ya ci amana sai amana ta ci shi.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar ’Ya’yan Sarki Da Ƙadangare

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ’Ya’yan Sarki Da Ƙadangare

    Tatsuniyar ’Ya’yan Sarki Da Ƙadangare

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani Sarki da ’ya’yansa mata su biyu kyawawa. Amma tun suna ƙanana ya hana su fita waje domin tsaron lafiyarsu. Kullum suna gida har suka girma, suka isa aure. Ganin sun kai munzalin aure, sai ya bari suka ɗan fara fita waje.

    Ana nan, rannan dai Sarki ya ce zai aurar da su. Manema suka fito. Wannan ya zo, a ce a a, bai yi ba. Wancan ya zo, a hana shi. Wata rana dai sai Sarki ya ce a tara mutane, duk wanda ya kira sunan ɗaya daga cikinsu, to shi za a ba wadda ya faɗi sunanta. Shi
    ke nan aka sa ranar tara mutane don a ji wanda zai faɗi sunan.

    Matasa da sauran waɗanda ba su wuce auren budurwa ba, kowa ya shiga neman sunayen ’yan matan; abu dai ya gagara. Sai Biri ya sami labari kuma ya ce ya san dabarar da zai yi. Sai ya je ya samo mangwaro nunannu kyawawa guda biyu. Da ya make mangwaron nan biyu, sai ya garzaya cikin lambun Sarki inda yaran suke hira, ya zauna a kan bishiyar da suke zama a gindinta ya shiga jira.

    Da suka fito, sai ɗaya daga cikin ’yan matan ta je gindin bishiyar da Biri yake kai, sai ya jefa mangwaro ɗaya. Da ta gani sai ta ɗauka tace: “Kirindi zo ki ga wani nunannen mangwaro na samu.”Wannan ya sa Biri murna saboda ya ji sunan ɗaya daga cikinsu. Da ɗayar ta doshi wajen wadda ta kira ta don ta je ta ga mangwaron Kirindi, sai ya jefa ɗaya mangwaron, sai ita ma ta ganshi.

    A cikin murna da ɗoki ta ce: “Ai ni ma na samu Karanda.” Biri na ji sai ya kama murna yana cewa: “Yawwa ai ni zan aure su tun da na ji sunayensu.” Bayan lokacin da Sarki ya yanka wa mutane ya cika, sai aka tara mutane ana tambayar su ko sun sami sunan ’yan matan.

    Wannan ya zo ya ce kaza ne, a ce masa a a, wancan ma ya zo bai canka ba. Haka dai aka yi ta fama har aka zo kan malam Biri. Ana zuwa kansa sai aka ji a cikin raɗa saboda tsoro ya ce: “Kirindi da Karanda.” Sai Ƙadangare da ke gefensa ya ji, sai kawai ya yi farat da ƙarfi ya ce: “Kirindi ce da Karanda.”

    To shi kuma Sarki ya riga ya yi alkawarin duk wanda ya faɗi sunayensu, zai ba shi su aure. Ba tare da ɓata lokaci ba, aka ba Kadangare auren ’ya’yan Sarki. Ashe Biri ya ji haushin ƙwacen da Ƙadangare ya yi masa, kuma ya saɓi laya sai ya ɗauki fansa a kan Ƙadangare.

    Saboda haka bayan an gama bikin amaren Ƙadangare sun tare a gidansa, sai
    rannan Biri ya haura dangar gidan gonar Sarki inda Sarki ke kiwo. A cikin dabbobin da Sarki ke kiwo kuwa, akwai wata babbar kazarsa wadda ya fi so a kan duk sauran abubuwan da yake kiwo a gonar.

    Sai Biri ya kama wannan kaza ya yanka, ya fige, ya dafa ya cinye. Da ya cinye ya sha ruwa, sai ya kwashe duk gashinta da ƙasusuwanta ya je ya haura dangar gidan Kadangare ya zuba. Gari na wayewa, sai labari ya je ga Sarki cewa an sace masa kaza. Sai ya sa fadawa su bi gida-gida su nemo kazar nan kafin a zahar.

    Fadawa na shiga gidan Kadangare, sai suka tarar da gashin kazar Sarki da ƙasusuwa. Suna ganin haka, sai suka kai wa Sarki labari. Saboda kunya da kara irin ta manya, da Sarki ya ji cewa a gidan surukinsa ne aka sami gashi da ƙasusuwan kazarsa, sai ya ce a bar maganar, kuma ya hana a hori Kadangare.

    Biri dai bai ji daɗin haka ba. Duk domin ya yi ramuwar gayya, sai ya yanka akuya ya dafa aka yi romo mai kayan yaji. Ya ɗauka ya kai gidan Kadangare, romo da naman akuya suna tafasa saboda zafi. Da Kadangare ya buɗe mazubin, sai ya ga naman akuya da romo, ga ƙamshinsa ya cika gari.

    Sai kwaɗayinsa ya tashi, bai yi wata- wata ba sai ya kai bakinsa. Yana ɗosana bakinsa kuwa sai yaƙone, ya ja baya. Matansa na fitowa sai hankalinsu ya tafi kan mazubin nan. Da suka buɗa, suka ga naman akuya ne a cikin romon da ya sha kayan yaji, sai su ma suka kwasa, suna kai wa bakunansu sai zafi ya sa kowacce ta ƙwala ihu, ta tofar da wanda ta guntsa.

    Dukkansu uku, watau Kadangare da matansa biyu ba wand abai ƙone ba. Da Biri ya ga haka, sai ya fita daga inda ya maƙe, ya kama hanya ya tafi yana dariyar ƙeta da jin daɗi, ya bar su da jinya. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kowa ya cuci wani zai ga mummunan sakamako.
    • Duk abin da ka samu ta hanyar rashin gaskiya ba za ka moreshi ta hanyar jin daɗi ba.
    • An ɓata goma ɗaya ba ta gyaru ba.
    • Rabon kwaɗo ba ya hawa sama.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Tsurondi

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ƊanAuta Da ’Yar Gwaggo

    Tatsuniyar ƊanAuta Da ’Yar Gwaggo

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum yana da ’ya’ya biyu mace da namiji. Macen ce babba, namijin ne ƙarami. Ita sunanta ’Yar Gwaggo, shi kuma sunansa Ɗan’auta. Da iyayensu za su rasu sai suka kira ’Yar Gwaggon suka ce: “Za mu bar miki ƙaninki Ɗan’auta. Kada ki ba shi wahala, duk abin da yake so ki ba shi; kuma duk abin da ya ce zai yi, kada ki hana shi; ki bar shi ya yi.”

    ’Yar Gwaggo ta ce: “To na ji.” Sai iyayen suka kwanta, suka rasu. To da ma iyayen sun bar musu dukiyar abinci da kadarori. Bayan ’yan kwanaki da rasuwarsu sai Ɗan’auta yace su tattara dukiyar da abincin da gidan baki ɗaya su ƙona. Sai ’Yar Gwaggo ta ce: “Haba Ɗan’auta, idan muka ƙona kuma me za mu ci, kuma a ina za mu zauna?” Sai Ɗan’auta ya ce: “Ba su baba sun ce idan ina son komai ki ba ni ba, kuma duk abin da zan yi kada ki hana ni?”

    Sai ta ce: “To shi ke nan, ka tashi mu tara kayan a ƙona.” Suka tara kayan da abincinsu rumbu-rumbu, suka ƙona. Da yunwa ta fara damun su sai ’Yar Gwaggo ta ce to su tafi bara. Suka kama hanya har gidan Sarki sai suka tarar da ’ya’yan Sarki suna wasan kirbe-kirbe, sai yace shi ma sai ya yi.

    Sai ’Yar Gwaggo ta ce: “Haba Ɗan’auta, wannan fa gidan Sarki ne, kuma ’ya’yan Sarki suna wasa. Idan aka kama mu fa?” Sai ya ce: “Ba su iya da baba sun ce duk abin da na ce zan yi ki ƙyaleni ba?” Sai ta bar shi ya shiga wasan ’ya’yan Sarki. A cikin wasan ya ɗaga ɗaya daga cikinsu, ya ƙwala da kasa sai cinyarsa ta karye.

    Sai Sarki ya sa fadawa su kama shi. Ganin haka sai ’Yar Gwaggo ta kama hannun ƙanenta suka kama gudu, har cikin jeji, dogarai suna bin su. Can sai suka hau kan wata bishiya, suka ɓuya. Da dogarai suka zo sai suka rasa hanyar da suka bi, sai suka ce bari su huta a gindin bishiyar nan. Su Ɗan’auta na kan bishiyar.

    Da ɗaya daga cikin dogaran ya kwance rawaninsa domin ya sha iska, ga shi ya aske kansa ƙwal-ƙwal yana ƙyalli, sai ɗan’auta ya auna kan dogarin sosai, sai kawai yace wa ’Yar Gwaggo: “Zan yi kashi.” Tsoro ya kama ’Yar Gwaggo, domin idan dogaran nan suka ji motsi za su kama su. Sai ta ce: “Haba Ɗan’auta, idan ka yi kashi za su gan mu, su kama mu fa.”

    Sai ya ce: “Ba iya da baba sun ce duk abin da zan yi ki ƙyale ni ba?” Sai ta ce: “To shi ke nan yi kashinka.” Sai ya tuɓe wandonsa ya auna daidai kan dogari sai ya ɓarke da kashi. Da kashi ya zuba kan dogari sai ya ce: “Wannan wane ɗan iskan tsuntsu ne ya yi mini kashi?”

    Da suka ɗaga kai sama sai ga su Ɗan’auta da ’Yar Gwaggo, sai suka fara sarar bishiya, saura kaɗan ta faɗi, sai ga wata ’yar tsuntsuwa za ta wuce, sai ’Yar Gwaggo ta ce: “‘Yar tsuntsuwa ki taimake mu mana.” Sai tsuntsuwar ta ce: “To ku hau bayana.” Suka hau bayan ’yar tsuntsuwa, ta tashi da su sama suka fara tafiya.

    Bayan sun fara nisa a can sama, sai Ɗan’auta ya ga gindin tsuntsuwa na ta motsi, yana budewa ya rufe. Sai kawai ya ce zai tsokale gindin tsuntsuwa. Yayarsa ta ce: “Haba Ɗan’auta, ita da ta taimake mu. Da an kama mu an kashe. Ka yi haƙuri mana.” Sai ya ce: “Ba inna da baba sun ce idan na ce zan yi abu kada ki hana ni ba?”

    Sai ta ce: “To ka yi.” Sai ya sa kara ya tsokale gindin tsuntsuwa. Sai ta juyar da su, suka faɗa cikin wani babban rafi. Suka yi ta iwo har suka kai bakin ruwa. Sai suka fita a daidai wani ɗan ƙauye. Da suka shiga ƙauyen sai suka fara neman masauki. Sai suka haɗu da wata ’yar tsohuwa suka gaya mata su baƙi ne masu neman masauki.

    Sai tace: “To zan ba ku masauki, amma fa a garin nan ba a fita da daddare don akwai wani dodo da yake cin mutane; har sarki ya yi alƙawari zai ba duk wanda ya kashe dodon rabin gari kuma ya aura masa ’yarsa.” Sai suka ce: “To shi ke nan.” Da dare ya yi sai Ɗan’auta ya ce shi fa sai ya ga dodon da yake hana mutane fita.

    Yayarsa ta yi, ta yi da shi kada ya fita waje, ya hura wuta a gefensa. Da wuta ta ruru, sai ya saka duwatsu bakwai a cikinta, har suka yi jawur. Sai ya zauna a tabarmarsa, ’yar tsohuwa kuma don tsoro sai ta shiga randarta ta buya a ciki. Da dodo ya iso gari ya shiga waƙa yana cewa: “Wa ya yi da ni a garin nan, Wa ya yi da ni, ni dodo in cinye shi?”

    Sai Ɗan’auta ya mayar masa yana cewa: “Na yi da kai a garin nan, Na yi da kai ni Ɗan’auta.” Da tsohuwa ta ji sai ta fara zawo a cikin randar don tsoro. Sai dodo ya nufo inda Ɗan’auta yake. Da Ɗan’auta ya ga ya buɗe baki, sai ya ɗauki dutsen nan da ya yi jawur da wuta, ya jefa a cikin bakin dodo.

    Sai dodon nan ya hadiye. Ya ci gaba da matsowa, shi kuma Ɗan’auta ya ci gaba da jefa duwatsun nan, har ya zo kan na ƙarshe. Da ya jefa na bakwai, sai kawai dodon ya faɗi matacce. Da Ɗan’auta ya ga haka, sai kawai ya koma ya kwanciyarsa. Da gari ya waye sai aka aika wa Sarki cewa an kashe dodon da ke damun mutanen gari.

    Sarki kuwa ya ce duk wanda ya kashe dodon za a ba shi rabin gari, kuma a aura masa ’yar Sarki. To da ma shi Ɗan’auta ya manta takalmansa a inda ya yi faɗa da dodo. Da aka tara mutane suka zo suka yi ta gwada takalma amma bai yi ba, sai da suka nemi baƙin da suke garin.

    Da Ɗan’auta ya gwada takalma sai suka yi daidai da shi. Nan take aka ba shi rabin gari, Sarki kuma ya cika alƙawari, wato ya ba shi auren ’yarsa. Ƙurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Wauta ne a sakar wa yaro linzami ya yi abin da ya ga dama.
    • Mai wayo ya fi mai zafin nama cin nasara.
    • Ya kamata a karɓi bako da hannu bibbiyu don ba a san alhairindazai kawo ba.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Gizo Da Sarki

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Gizo Da Sarki

    Tatsuniyar Gizo Da Sarki

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wata tsohuwa a wani ɗan ƙauye; tana da ɗan maraƙinta kyakkyawan gaske; ga shi ƙosasshe. Ana nan wata rana Gizo ya je gidan wannan tsohuwa bara sai ya ga wannan maraƙi. Sai ya fasa bara ya fita daga gidan, ya sheƙa a guje sai gidan Sarki.

    Ya faɗi a gaban Sarki, ya ce: “Ko kunnuwan Sarki nawa ne?” Sarki ya ce: “Biyu.” Sai ya ce wa Sarki: “Ƙara biyu, a kan biyu ka sha labari.” Sarki ya ce: “Na ƙara.” Sai Gizo ya ce: “Akwai wani kyakkyawan sa a gidan wata tsohuwa, in ba gidanka ba, to sai gidana.” Sai Sarki ya ce: “To shi ke nan.”

    Sai Sarki ya tura dogarai don a kamo kuma a kawo masa wannan san. Da dogarai suka kama hanya ba su tsaya a ko ina ba sai a gidan tsohuwa. Suka same ta, suka isar da saƙon Sarki. Da ta ji bayanin dogaran Sarki sai ta ce: “To yaya zan yi yau.” Dalilin tsohuwa na faɗin haka shi ne wannan sa ba ya yin komai sai dai zninta.

    Dogaran Sarki suka yi, suka yi su kwance sa daga turkensa su tafi da shi amma abin ya gagara. Can dai sai tsohuwa ta saka san a gaba tana yi masa waƙa tana cewa:

    “Tafi tafiye tirke,

    Sarakan bana kwaɗayi gare su,

    Abu kadan a kai ka fada,

    Abu kadan a kai ka fada, Har gaban Sarki.”

    Haka ta rinƙa rera wannan waƙa san yana yi mata biyayya har suka isa gidan Sarki. Da suka isa fada Sarki ya ga sa sai ya ce za a yanka shi. Sai ya tambayi tsohuwa abin da take so daga jikin san. Sai ta ce ita abin da take so kawai shi ne kayan ciki. Sarki ya ba da umarni aka yanka sa, aka feɗe aka ɗebi kayan ciki aka ba tsohuwa.

    Da tsohuwa ta koma gidanta sai ta shanya kayan cikin nan, ta mai da hankalinta a kan aikinta na gona. Wata rana ta dawo daga gona sai ta tarar an yi mata shara a gida da sauran aikace-aikacen gida. Sai abin ya ba ta mamaki tana tunanin ba ta da kowa, kuma wanene zai zo ya yi mata wannan aiki.

    Kashe-gari ma aka sake yi mata aikin. Ashe da ma kayan cikin nan da tsohuwa ta shanya su ke rikiɗa su koma ’yan mata kyawawa guda biyar. Kullum idan ta tafi gona, sai su fito daga ƙarƙashin gadonta inda suke kwana su yi mata hidima. Wata rana sai tsohuwa ta ce tun da ba ta san mai taimaka mata ba, za ta shirya kamar za ta gona sai ta ɓuya a bayan danga domin ta ga mai yi mata wannan hidima.

    Haka kuwa aka yi. Ta ɓuya a bayan danga, can sai ga ’yanmata kyawawa sun fito daga ƙarƙashin gadonta. Nan da nan suka fara aikace-aikacen gida, suka buɗe randunanta suka cika da ruwa, suka yi share-share da duk sauran ayyukan da suka kamata. Can sai kwatsam tsohuwa ta faɗo tsakar gida suka gan ta.

    Ta yi musu magana. Daga wannan rana sai ’yan matan nan suka daina ɓuya, suka zauna da tsohuwa suna taya ta aikace-aikacen gida. Bayan wasu ’yan kwanaki sai tasa wa kowacce budurwa suna. Akwai Ta-kitse da Ta-hanji da Ta-tumbi da Ta-hanta da Ta-huhu.
    Ana nan, ana nan wata rana Gizo ya sake komawa bara gidan tsohuwa, sai ya hango waɗannan ’yan mata kyawawa a gidan tsohuwa.

    Ya fita da gudu sai gidan Sarki. Da ya isa sai ya ce: “Sarki, Sarki kunnenka nawa?” Sai Sarki ya ce: “Biyu.” Sai Gizo ya ce: “Ka ƙara biyu ka sha labari.” Sai Sarki ya ce: “Na ƙara.” Daga nan sai Gizo ya kwashe labarin ’yan matan da ya gani ya gayawa Sarki. Nan take sai Sarki ya tura fadawa a kawo masa guda ɗaya daga cikinsu.

    Sai dogarai suka je gidan tsohuwa suka yi sallama da ita. Da ta fito sai ta ga fadawan sarki ne. Sai ta koma gida ta fara waƙa tana cewa: “Ta-hanta, Ta-hanta, Ɗebo ruwa ki kai wa baƙon da ke waje.” Sai Ta-hanta ta ce: “Tabɗi, in ɗebo ruwa Ta-huhu tana nan.”

    Sai tsohuwa ta sake rera waƙa ta ce: “Ta-huhu, Ta-huhu, Ɗebo ruwa ki kai wa baƙon da ke waje.” Sai ta ce: “Tabɗi, in ɗebo ruwa in kai wa baƙon da ke waje, ga Ta-hanji
    tana nan?” Da haka, da haka har tsohuwa ta gama zagaya ’yan matan nan, har ta kai
    kan Ta-kitse. Ita ce ta ƙarshe.

    Sai ta ɗauko ƙoƙo, ta ɗebi ruwa ta kai wa baƙon da ke waje. Tana fita da ruwan nan sai fadawa suka kama ta, sai gaban Sarki. Da Sarki ya gan ta sai ya ce zai aure ta. Nan da nan kuwa ya aure ta ya sa ta cikin matansa. Amma ba ta fita rana, kuma ba ta zuwa kusa da wuta domin ita kitse ce, idan ta sha rana ko zafin wuta ya buge ta sai ta narke.

    Wata rana Sarki ya tafi yaƙi, sai kishiyoyin Ta-kitse suka ce sai ta fito ta yi girki, tun da ita ma auro ta aka yi kamar su. Da suka matsanta sai ta yi girki, sai ta je bakin murhu. Tana zuwa sai ta narke. Da tsuntsun Sarki ya ga abin da ya faru sai ya yi tsalle ya tashi sai filin daga inda su Sarki suke fafatawa da abokan gaba.

    Sai tsuntsun nanyafara waka yana cewa: “Sarki, Sarki, Ka mai da yaƙi baya, Ta-kitse ta narke, Ta narke ta zama ruwa.” Da Sarki ya ji waƙar tsuntsun nan sai ya bar yaƙi ya komo gida. Sai ya tarar har Ta-kitse ta gama narkewa. Saboda laifin da matansa suka yi masa na sa Ta-kitse girki a kan dole, sai ya kore su gaba ɗaya ya yi zamansa shi kaɗai. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Son zuciya ɓacin zuciya.
    • Abin da ka shuka shi za ka girba

    Karanta Tatsuniyar Kura Da Kurege (Na Huɗu)

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kura Da Kurege (Na Huɗu)

    Tatsuniyar Kura Da Kurege (Na Huɗu)

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana Kurege yana farauta a daji sai ya ga mushen Kurciya, sai ya ɗauka ya ajiye a kan itace. Ya ci gaba da tafiya sai kuma ya ga mushen Giwa, ya matsa kusa, ya dubi mushen da kyau, ya yi dariya. Daga nan sai ya kai wa Kura ziyara.

    Ya same ta tana saka zana sai yace: “Ki bari in kwanta a kan zanar nan taki.” Sai Kura ta ce: “To, kwanta mana.” Da Kurege ya kwanta sai ya lumshe idanunsa. Jim kaɗan kuma ya buɗe; sai ya ce da Kura: “Na yi mafarki wai mun je yawo da ke sai muka sami kan Kurciya mai kyau.”

    Kura na jin haka sai ta ce: “Kai-kai, ai gara ka sake kwanciya ko ka ƙara yi mana mafarki mai daɗi fiye da wannan.” Kurege ya rufe ido, ya buɗe sai ya ce: “Kai na sake yin mafarki wai kin sami mushen Giwa ke kaɗai.” Kura na jin haka sai ta ce da Kurege: “To mu tafi mu bi sawu.”

    Da ya ji sai ya ce: “Yanzu dare ya yi, sai dai can idan gari ya kusa wayewa.”Bayan zakara ya yi cara sai Kura ta sake cewa da Kurege su tafi, shi ko yace ta bari sai da hantsi. Kura ta kasa haƙura, sai ta hura wuta a kan ɗakinta wai hantsi kenan. Amma Kurege sai ya gane, ya ce da ita: “Ai wannan wuta ce kika hura a kan ɗakinki.”

    Daga ƙarshe dai da gari ya waye hantsi ya ɗaga, sai suka kama hanyar bin sawun mafarki. Suna cikin tafiya sai Kurege ya tura Kura wajen kan Kurciya. Da ta gani ta kirawo shi suka raba. Suna cikin tafiya sai Kurege ya tura ta wajen mushen Giwa. Da ta gani sai ta je ta yi kashi domin ta kasayar da abin da ke cikinta, domin ta sami damar cin naman mushen Giwa sosai, tun da ga nama kamar ba iyaka.

    Kurege da Kura suka shiga gyara nama. Suna cikin wannan aiki kenan sai ga ‘ya’yan Giwa sun bi sawun uwarsu. Sai tsoro ya kama Kurege da Kura. Sai Kurege ya ce: “Zan shiga cikinta in buya.” Sai Kura ta ce: “Kai yaro ne, ni babba ce zan shiga ciki.” Da Kura ta dage sai ta shiga cikin Giwa, shi sai ya shiga mafitsarar mushen Giwar.

    Da ‘ya’yan Giwa suka je kan mushen uwarsu, sai suka fitar da mafitsarar suka yar da Kurege a ciki. Da Kurege ya fita daga cikin mafitsarar, sai ya ga wata ƙarama daga cikin ‘ya’yan Giwar tana yankan ciyawa sai yace: “Wayyo, wa ye ya zuba mini ruwa?” Sai ‘ya’yan suka ce: “Ayya sannu ba mu san kana nan ba.”

    Sai ya ce: “A a, me ya sami kakata?” Sai baki ɗayansu suka ce: “Ba mu sani ba.” Sai Kurege ya ce: “Ku kawo jar dawa in zuba a ruwa in yi muku duba.” Da suka ba shi jar dawa sai ya ce: “Abin da ya kashe kakar nan tawa yana cikinta. Abin da za ku yi sai ku ɗauko sanduna ku yi ta dukan cikin.” Sai ko ‘ya’yan Giwa suka yi kamar yadda Kurege ya faɗa.

    Da duka ya ishi Kura sai ta ce: “Ba ni kaɗai ba ce, ni da Kurege ne.” Kurege ya ce: “Kada ku saurari maganarta, ku bugi wajen gefen bakinta.” Haka suka yi ta jibgar Kura, ta fito daga cikin Giwa jina-jina, ta gudu ta tsira da ƙyar. Sai ‘ya’yan Giwa suka ɗauki sauran mushen uwarsu suka kai gida domin su binne. Sai Kurege ya roki su ba shi kan kakarsa dominwai yabinne a gidansa. Sai suka yarda suka ba shi.

    Niyyarsa yana so ya dafa ne. Da zuwansa gida sai ya sa a tukunya aka hura wuta, aka sa tukunya akan murhu, kuma ya ce wa ‘yarsa: “In wuta ta mutu sai ki zo ki faɗa mini cewa ciyawa ta kare a gaban doki.” ‘Yar Kurege ta ce: “To baba, na ji.” Shi kuwa Kurege ya sa kai ya koma wurin ‘ya’yan Giwa zaman makoki.

    Da wuta ta cinye icen, sai ‘yar ta je gidan Giwa inda ubanta ke zaman makoki tace masa: “Baba ciyawa ta kare a gaban doki.” Kurege na jin haka ya ɗauki hannu, kuma ya tashi ya bi ‘yarsa suka tafi gida. Ya tarar naman kan Giwa bai gama dahuwa ba, sai ya ƙara ice, ya koma gidan makoki. Bayan wani dan lokaci da kan Giwa ya gama ɓararraka, sai yarinyar ta koma gidan Giwa inda ake zaman makoki ta ce masa: “Baba ai kan kaka kamar ya nuna.”

    Da ‘ya’yan Giwa suka ji haka, sai suka ce: “Ashe ba binne kan ka yi ba, dafawa kake yi? To sai a kama shi a kashe nan take.” Da ya ji haka sai ya falle da gudu tal-tal-tal ana bin sa, sai ya tarar da wani Kurege yana saƙa. Sai Kurege mai saƙa ya ce da Kurege mai gudu: “Me ya koro ka?” Sai Kurege mai gudu ya ce da Kurege mai saka: “Ai Sarki ne ke son wutsiyar Kurege dubu, sai mu gudu.”

    Da jin haka sai Kurege mai saƙa ya falle da gudu shi kuwa Kurege mai laifi
    ya yi zamansa ya kama saƙa. Da ‘ya’yan Giwa da masu taya su bin sawun Kurege mai laifi suka ga wancan Kurege yana gudu, sai suka bi shi, har suka kama shi, suka kashe. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Zafin nema ba ya kawo samu.
    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Dabara ta fi ƙarfi.

    Karanta Tatsuniyar ‘Yar Sarkin Da Ta Saci Ɗinya

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ‘Yar Sarkin Da Ta Saci Ɗinya

    Tatsuniyar ‘Yar Sarkin Da Ta Saci Ɗinya

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani Sarki yana da ‘ya’ya maza da mata da yawa. Wata rana an kawo masa ɗinya sai ya ajiye ta a dakinsa. Rannan sai tafiya ta kama shi. Sai ɗaya daga cikin ‘ya’yansa ta ɗauki dinyar ta cinye. Da Sarki ya dawo sai ya tarar an cinye masa ɗinya. Sai ya tara matansa da ‘ya’yansa ya tambaye su ko waye ya cinye masa ɗinya.

    Sai suka shiga yi masa rantsuwa cewa ba su suka ɗauka ba. Bayan an yi, an yi babu wanda ya amsa cewa shi ne ya ɗauka, sai Sarki ya ce da fadawansa su tara matan da ‘ya’yan a kai su Kogin Rantsuwa su rantse, kuma duk wanda ya ɗauka to ruwa ya cinye shi, ya tafi da shi.

    Suka yarda aka kama hanyar kogi. Da aka isa sai aka fara rantsuwar da matan Sarki. Duk wadda ta shiga cikin ruwan sai ta fara waka tana cewa: “Kogi, kogi, In ni ce na ci ɗinyar Sarki, Ka tafi da ni, Kuma ka dawo da ni. Kada ka hadiye ni.” Matar farko ta fita ruwa bai tafi da ita ba.

    Ta biyu ma ta shiga ruwan bai tafi da ita ba, har matar ƙarshe ta shiga ita ma ruwa bai tafi da ita ba. Daga nan sai aka shiga kan ‘ya’yan Sarki maza. Aka zuba su gaba ɗaya suka rantse, su ma ruwa bai cinye ko ɗaya daga cikinsu ba. Shi ke nan aka zo kan ‘ya’yan matan.

    Su ma aka shigar da su, ba wadda ruwa ya ci har aka zo kan ta ƙarshe wadda ta cinye ɗinyar. Sai ta shiga ta fara waƙa tana cewa: “Kogi, kogi, Idan ni ce na ci ɗinyar baba, Ka tafi da ni, Kuma ka dawo da ni, Kada ka haɗiye ni.” Sai Kogin Rantsuwa ya tafi da ita. Sai matan Sarki da sauran ‘ya’yansa suka juya, suka koma gida, aka je aka gaya wa Sarki abin da ya faru.

    To ashe duk jama’ar gidan Sarki ba su san cewa wannan yarinya da ruwa ya tafi da ita Sarki na matuƙar son ta ba. Dalili kuwa ita ce ‘yar autarsa, sai ya yi ta kuka. Ruwa kuwa da ya tafi da ita sai ya kai ta wani baƙin jeji. Tana nan a rufe, can sai ta ga wata tsohuwa tana kama kwaɗi.

    Da tsohuwa ta ƙyallara ido ta ga yarinya, sai ta ɗauke ta, ta kai ta gidanta. Yarinya ta shari barcin gajiya. Da ta farka sai tsohuwa ta tambaye ta labarin abin daya faru. Sai ta kwashe labari ta gaya wa tsohuwa. Da tsohuwa ta ji labari sai ta ce wa yarinya: “Zan taimake ki, in sauya miki kamanni.

    Amma da sharaɗi, idan kin sami mijin aure zai kawo mini buhunan tsutsa biyu.” ‘Yar Sarki ta yarda. Nan take tsohuwa ta haɗiye ta sau bakwai. Da ta yi amanta ta haɗiye ta sau bakwai sai ga yarinya ta sauya kamanni baki ɗaya, ta zama fara jawur kamar ‘yar Sarkin aljanu.

    Bayan wasu shekaru, wata rana sai yarinya ta je cin kasuwa, sai ta haɗu da wani ɗan Sarki. Shi kuwa ɗan’uwanta ne na jini, to amma ba ta sani ba, don sun girma ba za ta gane shi ba. Shi kuma da ma ba zai gane ta ba saboda tsohuwa ta sauya mata kamanni. Shi ke nan sai ɗan Sarki yace zai aure ta. Sai ta ce sai dai ya je wurin kakarta su yi magana.

    Sai ya amince, suka je wurin tsohuwa. Da tsohuwa ta ji bayanin ɗan Sarki sai ta ce ya je ya kawo mata buhunan tsutsa biyu. Ɗan Sarki ya tashi cikin mamaki. Ya je ya nemo buhunan tsutsa biyu, ya kawo wa tsohuwa. Daga nan sai aka ɗaura masu aure. Ya ɗauki matarsa ya kai ta garinsu.

    Bayan ya kai ta gidansu, sai ta ga ashe gidan babanta ne. Sai kawai ta shiga cikin gida gayar da surukanta. Sai ta ga ai wadda ta haife ta ce surukarta. Shi kuma mijin yayanta ne, ubansu ɗaya. Da ta gane sai hankalinta ya tashi, amma babu yadda za ta bayyana wannan al’amari a gamsu tun da tsohuwa ta sauya mata kamanni.

    Kullum idan za ta yi daka sai ta fitar da turmi a tsakar gida tana daka tana waƙa tana cewa: “Babana da ya haife ni ya zama surukina, Innata da ta haife ni ta zama surukata
    Yayana da nake binsa ya zama mijin aurena, Kannena da suke bi na sun zama abokan wasana, Zan daki turmin gidanmu, Zan daki turmin gidanmu timkwalan-kwalan.

    Ana cikin haka kullum, sai wata tsohuwa ta kasa kunne ta ji abinda amarya take cewa. Rannan dai sai tsohuwar nan ta kira yaron ta gaya masa idan ya fita kamar za shi zaman fadanci, to ya laɓe a cikin gida ya saurari waƙar da matarsa take yi idan tana daka, ya ji abin da take cewa. Rannan sai ɗan Sarki ya fita, kamar ya tafi, sai ya laɓe.

    Jim kaɗan da amarya ta fara daka sai ta kama waƙar tana maimaita abin da take cewa kullum. Da ya ji waƙar matarsa sai ya fahimci abin da take faɗa, kuma ya gane cewa ƙanwarsa ce. Sai ya ruga da gudu, ya kama ta, yana kuka ya ce: “Ashe ke ce ‘yar autar baba, amma kika ki faɗa?”

    Ya ɗauke ta sai wurin babansa. Da ya yi gaisuwa, ita ma ta gai da Sarki, yace ta ba mahaifinta labarin abin da ya faru. Sai ta kwashe labari yadda ta cinye ɗinyar babanta, har ruwa ya tafi da ita. Ta faɗi yadda tsohuwa ta ɗauke ta, da yadda ta haɗiye ta ta sauya mata kamanni.

    Bayan ta kammala ba su labari, sai baki ɗayansu suka yi ta kukan murna, ‘yarsu ta dawo. Daga nan sai aka raba wannan aure, domin mutum ba ya auren ‘yar uwarsa. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Ba a tausaya wa ɓarawon da aka kama.
    • A kowane jinsin mutane auren zumunta yana da ƙa’ida

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Rimi Da ‘Yar Amana

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Gizo Da Damon Sarki

    Tatsuniyar Gizo Da Damon Sarki

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana Sarki ya kawo Damo babba. Sai ya kai shi gonarsa bayan gari. Bayan ‘yan kwanaki kaɗan ya sake kawo wasu don kiwo, kuma yasa aka yi shela a gari cewa kada a taɓa su, tare da bayanin cewa duk wanda ya yanka ya ci zai mutu.

    Ana nan, sai wata rana kwaɗayin nama ya kama Gizo, sai ya zagaya inda Damon Sarki suke. Ba tare da jin wani tsoro ba ya kama ɗaya ya yanka, ya kawo wa matarsa ta dafa masa ya cinye. Da ya ji daɗi sai kullum ya zagaya ya kama ɗaya ya yanke, har sai da ya gama Damon Sarki duka shi kaɗai.

    Da ya ƙarasa cinye naman Damo sarai, rannan sai ciwo ya kwantar da shi. Sai ya aika wa Ƙoƙi domin ta zo ta kai shi wurin magani. Da Ƙoƙi ta ɗauki Gizo suka kama hanya za su neman magani, suna cikin tafiya sai suka haɗu da Kura a cikin jeji. Sai Kura ta ce: “Ke Ƙoƙi ina za ki?” Sai ta ce: “Zan kai Gizo ne gidan magani.”

    Sai Kura ta ce: “In kin je ki gaya masa ba zai yi rai ba don ya ci Damon Sarki.” Sai Ƙoƙi ta ce: “Wai, wai ashe cutar ba ta warkewa ba ce. Gwanin zafi, gwanin zaƙi.” Haka dai suka ci gaba da tafiya. Can kuma sai suka haɗu da Zaki. Sai Zaki manyan dawa ya dubi Ƙoƙi ya ce: “Ke Ƙoƙi ina za ki?” Sai ta ce: “Mai girma Manyan Dawa zan kai Gizo ne gidan magani.”

    Sai Zaki ya ce: “In kun je ku gaya masa Gizo ba zai yi rai ba.” Sai Ƙoƙi ta yi salati, ta ce: “Ashe cutar ta fitar rai ce. Gwanin daɗi, gwanin zafi.” A nan ne fa Ƙoƙi ta sauke Gizo daga bayanta, ta yar da shi ta ce: “Tunda ka ci Damon Sarki, ka ci mutuwarka. Bari in bar ka a nan idan ka mutu kada ka yi musu wari a gari.” Sai Ƙoƙi ta koma gida, ta bar mijinta Gizo a cikin ciwon ajali. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Wanda bai ji bari ba ya ji hoho.
    • Ba a karya dokar Sarki a kwana lafiya.
    • Kowa ya ɗebo da zafi, bakinsa.

    Karanta Tatsuniyar Talipaku Da Kurciya

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Talipaku Da Kurciya

    Tatsuniyar Talipaku Da Kurciya

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana tsuntsuwa Talipaku da Kurciya suka yi sheƙa a bishiya ɗaya. Da lokacin saka ƙwan da suka ɗauka ya zo, sai suka haɗa ƙwansu a wuri ɗaya. Bayan sun gama kwanci, sai suka ƙyanƙyashe ƙwayayensu, suka sami ’ya’yansu guda biyu.

    Suna nan a haka, kullum sai su fita neman abincin’yan tsakinsu. Kansu ya haɗu, komai na tafiya rumui-rumui. To ashe ita Talipaku ba ta jin daɗi da bakin ’yarta ya yi tsawo fiye da na’yar Kurciya, wadda ba wani abu da ya dami ’yarta, kyakkyawar gaske. Duk lokacin da za su fita neman abincin ’ya’yansu, sai a karɓi renon’yar Kurciya, amma a bar ’yar Talipaku a sama cikin sheƙa.

    Shi ke nan sai wata rana Talipaku ta yanke shawarar sace ’yar Kurciya ta gudu da ita. Wata rana suna wurin neman abinci, sai Talipaku ta sulale, ta je ta sace ’yar Kurciya ta gudu da ita. Da Kurciya ta ɗaga kai ba ta ga Talipaku ba, kuma suna daf da tafiya gida, kuma ta nemi ƙawarta har ta gaji, sai ta dawo gida ita kaɗai.

    Da ta shiga sheƙa, sai ta ga ba ’yarta, sai ɗiyar Talipaku. Sai ta fita ta kama cigiya. Sai
    aka ce mata ai an ga Talipaku ta ɗauki ’yar Kurciya sun yi yamma. Da jin haka sai Kurciya ta koma sheƙarsu ta ɗauki ’yar Talipaku ta fito fur ta kama waƙa tana cewa:

    “Talipaku, Talipaku,

    Don bambancin ’ya’ya,

    Nawa a gabanki,

    Naki a bayana,

    Kika ɗauki mai kyau,

    Kika bar mummuna.

    Garinmu, garinmu,

    Garinmu da Sarki,

    Mai yawa in kin je,

    Sai idonki ya ɓata,

    Mu je mu, mu je mu.”

    Haka dai ta dinga yin wannan waƙa, tana tafiya tana ci gaba da bincike har ta haɗu da wasu manoma. Sai ta gaishe su, suka amsa, sai ta tambaye su ko sun ga Talipaku ta wuce? Sai suka ce: “E, tun ɗazu ta wuce.” Kurciya ta ɗauki ’yar Talipaku tana waƙa ta ci gaba da tafiya ta je wajen masu kiwo, sai ta tambaye su ko sun ga Talipaku? Sai suka ce: “E, ba ta daɗe da barin wurin nan ba.”

    Haka dai Kurciya ta ci gaba da tafiya tana waƙa, tana tambaya. Ita kuwa Talipaku tuni har ta isa garin Sarkin tsuntsaye ta tambayi hanyar gidan Sarkin. Aka kai ta gidan Sarkin tsuntsaye. Sunan Sarkin Miki. Da ta je gaban Sarkin, sai Sarkin ya tambayi Talipaku ko me ke tafe da ita?

    Sai tace ta zo ne ita da ’yarta a ba su wuri a garin domin ta zauna. Da Miki ya ji haka, sai ya ce: “To ai ’yar da kika zo da ita ba ta yi kama da ke ba. Ba ’yarki ba ce. Ina kika samo ta?” Ita kuwa Kurciya tuni ta haɗu da wasu mutane a jeji ta tambaye su ko sun ga Talipaku?

    Sai suka gaya mata cewa yanzu ta tambaye su hanyar gidan Sarkin tsuntsaye. Sai suka nuna wa Kurciya hanyar, suka ce ta yi sauri ko ta same ta a gidan Sarkin tsuntsaye. Nan take ta kama hanyar zuwa gidan Sarkin tsuntsaye. Tana zuwa gidan, sai ta tarar ana tambayar Talipaku a inda ta samo’yar da ba ita ta haifa ba.

    Sai Kurciya ta fara rera waƙa ta faɗi a gaban Sarkin tsuntsaye ta yi gaisuwa, ta kuma yi wa Sarki bayani a kan yadda suka yi da Talipaku. Sai Sarkin ya sa aka ƙwace ’yar Kurciya, aka ba ta ’yarta. Ita ma Talipaku aka ba ta ’yarta. Sarkin tsuntsaye ya ja kunnen Talipaku da kada ta kuskura ta sake satar ’yar wani tsuntsu.

    Idan kuma aka sake kawo ƙararta, to za a kashe ta. Sai aka sallame su. Kurciya ta ɗauki ’yarta. Ta yi godiya ta tafi. Ita kumaTalipaku ta tafi da ’yarta. Ƙurunƙus.

     Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Maciyi amana ba shi da mabuya a duniya.
    • Baƙin ciki da abin da Allah ya yi wa wani ba zai ƙara komai ba sai faɗawa cikin wahala.
    • Maci amana yana tare da jin kunya.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Yarima Da Labbi

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Yarima Da Labbi

    Tatsuniyar Yarima Da Labbi

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wani Bafulatani yana yawo a jeji sai ya tarar da wata mata a zaune a gindin wata kuka. Yau da gobe yana zuwa har suka saba. Kullum haka yakan same ta bayan azahar ko kuma dab da azahar. Duk sanda ya je takan ba shi ruwa ko kunu ya sha. Bayan sun yi hira kuma sai ya koma yaci gaba da kiwon dabbobinsa.

    Wani lokacin kuma yakan kai mata madarar shanu da dambu. Ashe da man matar nan ba mutum ba ce, kasa ce da ke zaune a cikin kogon wannan kukar take rikiɗa ta zama mace. Sannu a hankali sai ƙauna ta shiga tsakaninta da Bafulanin nan, har dai suka yi aure.

    Bayan wasu watanni da aurensu, sai ta ɗauki ciki. Daga ƙarshe ta haifi ’ya. A ranar suna aka taru, aka sa wa jaririyar suna Labbi. Bayan ’yan shekaru, sai kasar nan ta ce da ’yarta: “Ba za ki zauna a wannan jejin ba, ki tafi ko wani gari ki zauna.” Sai ’yar ta tafi Hawul ta sauka a gidan Sarkin garin ta zauna.

    To shi Sarkin yana da ɗa mai suna Yarima. Wannan yarinyar kuwa mummuna ce; ba ta da kyau ko kaɗan. Ana nan, sai wata rana yarinyar ta ce za ta je garinsu. Da ta isa garinsu, watau dajin da uwarta kasa take, sai ta gaya wa mahaifiyarta cewar za a yi
    wasa a kofar gidan Sarkin Hawul.

    To da ma Sarkin yana so ɗansa Yarima ya aure ta, amma Yarima ba ya sonta saboda muninta. Labbi dai duk ta kwashe wannan labari ta gayawa mahaifiyarta kasa Uwar ta ji haka, sai ta ɗauki Labbi ta hadiye, ta amayar da ita sai ta ga ba ta yi mata kyau ba. Sai ta sake haɗiye ta, har dai haɗiya ta kai uku, sai yarinya ta futo kyakkyawa, ba irinta a duk duniya.

    Uwar kuma ta kawo kujerar zinare ta ba Labbi. Yarima ya hango wannan yarinya, ya je kusa da ita ya ce: “Ina ne garinku?” Sai ta dube shi ta ce: “Daga nan zuwa garinmu tafiyar wata uku ce.” Yarima ya ba ta wani zobensa na kawa.

    Dila ya ga zobensa a cikin gayan furar ne fa ya gane ashe ita ce matarsa. Nan da nan ya ce da ayarinsa kowa ya karya linzami, su koma gida domin matarsa tana gida. Da Yarima ya dawo gida sai ya sa aka kira Labbi yace zai aure ta…

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa:

    • Alheri danko ne ba ya faduwa kasa banza.
    • Matar mutum kabarinsa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Budurwa Mai Neman Ganyen Miya

    Edita@rumasau-kallamu