Tatsuniyar Rimi Da ‘Yar Amana

0
10

Ga ta nan, ga ta nanku.

An yi wani gari mai yawan jama’a da Sarkinsu mutumin kirki. Shi ke nan akwai wani mutum mazaunin wannan gari shi da matarsa da’yarsu ɗaya. Suna nan sai wata rana ciwon ajali ya kama matar wannan mutum. Kafin ta rasu sai ta kira shi ta ce: “Mai gida, ni fa ina jin ba zan tashi daga ciwon nan ba, amma ga amanar ‘yarmu nan ka kula da ita sosai.

Kada ka bari wani mugun abu ya same ta.” Mijin ya amsa. Da matar ta rasu sai shi kuma uban yarinyar ya ci gaba da renon ‘yarsa har ta yi wayo. Sai wata rana shi ma ciwon ajali ya kama shi, sai ya rasa yadda zai yi da ‘yarsa, kuma ba shi da kowa a garin.

To amma akwai wata tsohuwar bishiyar rimi a kofar gidansa, sai ya fito ya ɗauko yarinyar ya kawo ta gindin rimin. Sai ya dubi rimin nan ya ce ya ba shi amanar ‘yarsa domin yana jin wa’adinsa ya kusa cika. Daga nan ya koma gida, bai sake fitowa ba, har ya rasu.

Bayan rasuwarsa da ‘yan kwanaki, duk sanda yarinya ta ji yunwa sai ta je wurin rimin ta kama waƙa tana cewa: “Rimi, rimi uwata, Rimi ubana ya ba ka amanar Allah, Uwata ta ba ka amanar Allah.” Da ta yi wannan waka sai rimi ya ba ta abin da take so. Kullum haka sai wata rana Gizo ya fita yawo sai ya ga ‘yar budurwa tana wanki a gindin rimi.

To da ma sunanta Jummai. Da Gizo ya ga kyaunta sai ya garzaya gidan Sarki. Ya sami Sarki a fada tare da fadawansa, ya faɗi ya yi gaisuwa yace da Sarki: “Sarki, Sarki kunnenka nawa?” Sai Sarki ya ce da Gizo: “Biyu.” Shi kuma Gizo ya ce: “Ƙara biyu ka sha labari.”

Sai Sarki ya yi murmushi ya dubi Gizo ya ce: “Na ƙara.” Da Gizo ya sami yadda yake so, sai ya kwashe labarin Jummai ya gayawa Sarki. Da Sarki ya ji haka sai ya tura fadawansa su ɗauko yarinya. Da suka isa wurin rimi sai yarinyar ta gan su, kuma ta razana ta je ta rungumi rimi ta fara waka tana cewa:

“Rimi, rimi uwata, rimi ubana, Uwata ta ba ka amanar Allah, Ubana ya ba ka amanar Allah.” Sai rimi ya ce: “Yi wankinki, Yi wankinki, Yi wankinki Jummai, Cikin ɗari da goma, Ɗaya ya koma, Cikin ɗari da goma, Ɗaya ya koma.” Da dogarai suka matsa sai duk suka mutu.

Da Sarki ya ji labari sai yasa a je a sare wannan rimi. Da aka taru za a sare, idan aka sara jikin sai ya sake tohowa. Idan an sake sara ma haka, har dai masu saran suka gaji, suka haƙura. Har yanzu wannan rimi da ya riƙe amana yana can a garin, mutane suna zuwa kallon sa. Kurunkus.

Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

  • Rikon amana garkuwa ne ga kowane mahaluki.
  • Azzalumi ba shi da riba a harkokinsa na zalunci

Danna nan don karanta Tatsuniyar Gizo Da Damon Sarki

Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceTatsuniyar Gizo Da Damon Sarki
Labarin na GabaTatsuniyar ‘Yar Sarkin Da Ta Saci Ɗinya
wikiHausa
wikiHausa kundin ilimi (insakulofidiya) ce da ke ilimantar da jama'a yara da manya da maza da mata wajen samun ilimi a saukake, cikin harshen Hausa.