Tatsuniyar Yarima Da Labbi

0
7

Ga ta nan, ga ta nanku.

Wani Bafulatani yana yawo a jeji sai ya tarar da wata mata a zaune a gindin wata kuka. Yau da gobe yana zuwa har suka saba. Kullum haka yakan same ta bayan azahar ko kuma dab da azahar. Duk sanda ya je takan ba shi ruwa ko kunu ya sha. Bayan sun yi hira kuma sai ya koma yaci gaba da kiwon dabbobinsa.

Wani lokacin kuma yakan kai mata madarar shanu da dambu. Ashe da man matar nan ba mutum ba ce, kasa ce da ke zaune a cikin kogon wannan kukar take rikiɗa ta zama mace. Sannu a hankali sai ƙauna ta shiga tsakaninta da Bafulanin nan, har dai suka yi aure.

Bayan wasu watanni da aurensu, sai ta ɗauki ciki. Daga ƙarshe ta haifi ’ya. A ranar suna aka taru, aka sa wa jaririyar suna Labbi. Bayan ’yan shekaru, sai kasar nan ta ce da ’yarta: “Ba za ki zauna a wannan jejin ba, ki tafi ko wani gari ki zauna.” Sai ’yar ta tafi Hawul ta sauka a gidan Sarkin garin ta zauna.

To shi Sarkin yana da ɗa mai suna Yarima. Wannan yarinyar kuwa mummuna ce; ba ta da kyau ko kaɗan. Ana nan, sai wata rana yarinyar ta ce za ta je garinsu. Da ta isa garinsu, watau dajin da uwarta kasa take, sai ta gaya wa mahaifiyarta cewar za a yi
wasa a kofar gidan Sarkin Hawul.

To da ma Sarkin yana so ɗansa Yarima ya aure ta, amma Yarima ba ya sonta saboda muninta. Labbi dai duk ta kwashe wannan labari ta gayawa mahaifiyarta kasa Uwar ta ji haka, sai ta ɗauki Labbi ta hadiye, ta amayar da ita sai ta ga ba ta yi mata kyau ba. Sai ta sake haɗiye ta, har dai haɗiya ta kai uku, sai yarinya ta futo kyakkyawa, ba irinta a duk duniya.

Uwar kuma ta kawo kujerar zinare ta ba Labbi. Yarima ya hango wannan yarinya, ya je kusa da ita ya ce: “Ina ne garinku?” Sai ta dube shi ta ce: “Daga nan zuwa garinmu tafiyar wata uku ce.” Yarima ya ba ta wani zobensa na kawa.

Dila ya ga zobensa a cikin gayan furar ne fa ya gane ashe ita ce matarsa. Nan da nan ya ce da ayarinsa kowa ya karya linzami, su koma gida domin matarsa tana gida. Da Yarima ya dawo gida sai ya sa aka kira Labbi yace zai aure ta…

Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa:

  • Alheri danko ne ba ya faduwa kasa banza.
  • Matar mutum kabarinsa.

Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

Danna nan don karanta Tatsuniyar Budurwa Mai Neman Ganyen Miya

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceTatsuniyar Budurwa Mai Neman Ganyen Miya
wikiHausa
wikiHausa kundin ilimi (insakulofidiya) ce da ke ilimantar da jama'a yara da manya da maza da mata wajen samun ilimi a saukake, cikin harshen Hausa.