Tag: tatsuniya

  • Tatsuniyar Auren Kaza Da Muzuru

    Tatsuniyar Auren Kaza Da Muzuru

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wata kaza da ta ce za ta yi aure, sai zakaru suka yi ta zuwa neman aurenta. Duk zakaran da ya zo, sai Kaza ta ce ba ta son sa. Wani tace ya yi gajarta; wani ta ce ba shi da gashi; wani ta ce bai iya cara ba. Wani kuma idan ta raina shi, sai ta ce ba shi da sirdi, ko kuma ya yi tsawo, ko ba shi da kyaun fuska.

    Haka dai ta rinƙa korar su. Sai wata rana Muzuru ya sami labarin halin Kaza, da kuma buƙatar iyayenta na su aurar da ita. Shi ke nan, sai Muzuru ya yi shigar manyan mutane, watau ya sanya babbar riga da hula, ya kuma kawo rawani ya naɗa. Bai tsaya ko’ina ba sai gidan su Kaza. Ya kira Kaza, ta fito tana wani yauƙi.

    Da ta gan shi da shiga irin ta kamala, sai ta sanar da iyayenta cewa yanzu ta sami mijin aure. Iyayenta suka yi ƙoƙarin hana ta, amma ba ta ji maganarsu ba. Daga ƙarshe dai aka ɗaura musu aure da Muzuru. Ranar da za a kai amarya gidan mijinta, sai abokan Muzuru suka rinƙa yin wata waƙa suna cewa:

    “Kaka ga abinci ya shigo mai daɗi, Kayau-kayau.”

    Shi kuma ango yana cewa: “Ku kawo mini abincin nan in ci, In yi maganin kwaɗayi.” Sai Muzuru ya ɗauki allo, wai zai yi karatu, amma sai ya rinƙa cewa: “In jingina allona, In ci Kaza.” Da kowa ya watse, sai ko Muzuru ya cabke Kaza. Tun tana kuka, Kwayat!, Kwayat!!, har aka ji shiru ya gama murɗe wuyanta, ta mutu. Saboda tun fari ba ta ji maganar mahaifanta ba, ba wanda ya yi ƙoƙarin ceton ta daga damƙar da mijinta ya yi mata. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Wanda bai ji bari ba ya ji hoho.
    • Girman kai rawanin tsiya.
    • Kowa ya ɗebo da zafi, bakinsa.
    • Mai rabon shan duka, ba ya jin kwaɓa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Kyawawa Matuƙa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kyawawa Matuƙa

    Tatsuniyar Kyawawa Matuƙa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can ƙasar Turu, an yi wani mutum mai ’ya’ya mata biyu. Allah ya yi su kyawawa. Ga haske, in ka gan su kamar taurari. Ɗaya daga cikin ’yammatan ba ta fita ko da ƙofar gida. Amma ɗayar takan zauna a ƙofar gida, kuma duk wani saurayi da ya zo, sai ta ce za ta kira masa ’yar’ uwarta.

    Ana nan, ana nan, sai wata rana wani dodo ya rikiɗa ya koma saurayi, ya je gidansu. Sai ya tarar da yarinyar nan da kan zauna a ƙofar gida, ya yi mata sannu; ita kuma ta mayar masa. Sai ya ce: “Kai amma yarinyar nan na yaba da kyaunki.” Sai ita ko ta ce masa: “Ai da ka ga ’yar’uwata da ba za ka yi mini magana ba, balle ma ka ce ina da kyau.”

    Dodo ya sami gangara, sai ya ce: “To, ko za ki kira mini ita?” Sai yarinyar ta shiga ta yi wa ’yar uwarta magana. Ita kuma ta tambaye ta: “Da wa ya yi kama?” Sai ta ce: “Ya yi kama da mahaifiyarmu.” Da ta ji haka sai ta ce: “A a, ai babu wani saurayi da ya isa ya gwada kansa da mahaifiyata. Ba zan je ba.”

    Daga nan mai zama a bakin ƙofa ta je ta ba mutumin haƙuri. Ba tare da ya nuna fushi ba, ya kama hanya ya yi tafiyarsa. Amma saboda nacinsa, kullum sai ya je gidan, yana ƙoƙarin ganin yarinyar. Sannu a hankali har yarinyar nan mai tsayawa a waje ta gayawa mahaifinsu halin da mutumin nan yake ciki na tsananin ƙaunar da yake yi wa ‘yaruwarta.

    Da mahaifinsu ya ji bayaninta, sai yace: “Duk sanda ya zo ki shigo ki gaya mini. Can kuwa sai ga mutumin. Nan da nan ta yi masa bayani cewa: “ka jira in yi wa sanar da mahaifinmu cewa ka iso. Mahaifin yaran ya fito, suka gaisa da baƙon, ya kuma sanar da shi cewa yana so ne ya auri ɗaya daga cikin ‘ya’yansa, wato wadda take cikin gida.

    Sai baban yaran yace masa ya jira yana zuwa. Ya shiga gida. Da shigarsa, sai ya ɗauki yarinya ya sa ta a cikin rumbu. Sai ya kira mutumin yace: Ga wannan rumbu ka kai wa kakannin yarinyar a garinsu. mutumin nan ya ɗauki rumbu, ya kama hanya. Yana cikin tafiya sai ya yi tun tuntuɓe ya faɗi; yarinyar da ke cikin rumbun ma ta faɗo.

    Da yarinyar ta ga mutumin sai tace: “sannu kawu” Sai mutumin ya ce: “Ashe ke ce a ciki?” Da ta lura a daji suke, sai ta gudu ta tasamma gida. Washe-gari sai mutumin ya koma gidansu yarinyar, ya tambayi labarinta, to amma kafin ya je, mahaifinta ya tambaye ta abin da ya farutsakaninta da mutumin, ta kuma gaya masa yadda mutumin ya yi tuntuɓe ya faɗi, da yadda ta yi masa sannu bayan ta faɗo daga rumbu.

    Da mahaifinta ya ji haka sai ya ce: “Ai ko nai kamata ki yi masa sannu ba da ya faɗi. “Sai ya sake sa ta a cikin rumbu, ya sake ɗora wa mutumin. Mutumin ya kama hanya, sai ya sake yin tuntuɓe a cikin daji, ya faɗi. Yarinya ta mance da abin da mahaifinta ya gaya mata, sai ta yi masa sannu.

    Shi kuwa ya kama ta, ya fyaɗa da ƙasa, ya mueɗe mata wuya, nan take ko haurawa ba ta yi ba. Daga nan sai ya ɗauki gawar ya jefa a cikin jakarsa. Ya ajiye jakar a gindin wata bishiya, ya tafi neman itacen da zai yi tsire da gawar, ya gasa. Ashe duk abin da suke yi wata tsohuwa tana ganinsu, sai ta yi sauri ta cire gawar yarinyar ta jidi duwatsu ta zuba masa a cikin jakar, ta gudu da gawar, ba ta tsaya ko ina ba sai gidan mahaifin yarinyar nan.

    Ta kai masa gawar ‘yarsa. Da dodo ya samo itacen, ya ɗauki jakarsa ya je inda zai gasa yarinyar nan ya ci nama, sai ya juye duwatsu a tukunya ya hura wuta, ba tare da ya san duwatsu yake dafawa ba. Can da ya ji dutse ya fashe sai ya ce: “Yawwa wannan ƙwaƙwalwarta ce ta fashe. Sai ya ɗebi fasasshen dutse ya cinye.

    Da tsohuwa ta kai gawar sai ta ce da iyayenta: Ku duba abinda kuka sa aka yi wa ‘yarku.

    Mahaifin yarinyar ya yi wa tsohuwa godiya, suka yi sallama ta tafi. Tsohuwa na tafiya, sai uban ya ƙone gawar yarinyar, ya zuba tokarta a cikin mararaki, ya zuba ruwa, sai ya rataye mararakin nan; sannu a hankali ruwan tokar ya fara ɗigowa daga mararaki. Da ya ɗigo, sai yace: “Wannan hannun Sirandi ne.” Can kuma idan ruwa ya sake ɗiga sai yace: “Wannan kuma ƙafarta ce.”

    Da haka dai, kafin wani lokaci yarinyar nan ta haɗu tsaf ta miƙe. Washe-gari kuma sai Dodon nan ya sake zuwa ƙofar gidansu yarinyar. Da mai zama a ƙofar gida ta gan shi, sai ta shiga gida da gudu ta gaya wa mahaifinta cewa ga fa mutumin nan ya sake zuwa. Sai mai gidan ya fito. Da suka gaisa sai ya tambayi baƙon wa kuma ya zo nema.

    Shi kuwa ya ce ya zo ne yana neman wannan yarinyar da ta gudu ta shiga gida, wai ya aura. Sai mahaifinta ya gaya wa baƙon nan cewa ai yarinyar ta yi miji tuntuni. Sai bai komai ba ya tafi abinsa. Bayan ’yan kwanaki aka ɗaura wa yarinyar aure ta tare. Da mutumin ya sake dawowa sai aka ce masa yarinyar ta bar gidan.

    A nan take sai ya kife. Can cikin dare kuma sai ya rikiɗa, ya je inda yarinyar take ya ce zai kashe ta. Sai yarinyar ta nemi mijinta da ya kuɓutar da ita daga hannun wannan azzalumi. Amma sai mijinta yace ai shi ba ya ganin komai. Washe-gari sai ya je ya sami mahaifin yarinyar nan ya ce masa ya lura dai matarsa tana ganin aljanu, saboda haka ya dawo da ita, ba ya auren, ya sake ta.

    Da uban ya ji haka, sai ya tambaye ta abin da ta gani. Ta gaya masa duk yadda suka yi da Dodo. Sai baban yarinyar ya ba ta wata kyanwa, ya ce: “Idan har mutumin nan ya sake zuwa zan ce masa zan haɗa shi da ke ku je gidansa. Idan har ya rikiɗa ya zama wani abu, sai ki ce masa idan da gaske yake to ya rikiɗa ya koma wani ƙaramin abu, kamar ɓera.

    Idan ya zama ɓera, sai kawai ki cinna masa kyanwar nan ta cinye shi. ”Rannan da mutumin ya dawo, sai uban yarinyar nan yace: “Zan ba ka ɗiyata, amma sai ta je da kai ta ga gidanka.” Sai mutumin ya ce: “Ta fito mu tafi.” Nan da nan yarinya ta naɗe tabarmarta, ta saka kyanwa a ciki yadda ba zai gan ta ba, ta fito suka tafi.

    Suna isa kusa da gidansa, sai ya zama Giwa, sai ya ɗauki yarinyar ya kawo ta kusa da tukunya, amma ba ta tsorata ba, sai yarinyar ta ce: “In da gaske kake kana rikiɗa, to ka rikiɗa ka koma wani abu ƙaramin gani.” Nan da nan ya zama bushiya. Da ta ga haka sai ta yi tsaki ta ce: “Wannan ai ka yi rikiɗar kaya ce kurum. Ina so ka rikiɗa ka zama abin da ba shi da kaya.”

    Yana jin abin da ta faɗa, sai ya rikiɗa ya zama ɓera. Kamar walkiya, sai yarinyar nan ta saki kyanwa. Nan take kuma kyanwa ta kama ɓerar nan ta lanƙwame. Jim kaɗan sai kawai dawaki da jakuna da raƙuma da sauran kayayyakin alatu masu ɗimbin yawa suka bayyana.

    Nan da nan ta kwashe su ta ɗora wa raƙuman nan da shanu da jakuna da ta mallaka, ta zaɓi wata taguwa ta haɗa mata sirdi, ta hau, ta kora sauran dabbobin da ta yi wa laftun dukiya, ba ta tsaya ko’ina ba sai a gidansu. Da babanta ya gan ta da wannan dukiya mai tarin yawa, ga shi ta durƙusa ta gaishe shi, ta kuma yi godiya ga Allah saboda ya raba ta da wannan bala’i, sai ya yi matuƙar murna. Ita da mahaifanta da ’yan’uwanta suka ci gaba da morar wannan dukiyar hankali kwance. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Girman kai rawanin tsiya.
    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Abin da babba ya hango yaro ko ya hau rimi ba zai iya hango shi ba.
    • Karen bana, maganin zomon bana

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Kare Da Kura

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kare Da Kura

    Tatsuniyar Kare Da Kura

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani Kare da wata Kura a Dajin Saidawa. Suna ganin juna amma daga nesa, har dai yau da gobe suka saba, sai suka ƙulla abota. Kare yana da ’ya’ya bakwai, Kura kuma tana da’ya’ya biyar. Sai wata rana suka ce za su je daji dakan wake. Sai suka shirya suka fita.

    Suka yi ta tafiya har suka isa wurin dakan wake, suka kama aiki. Can sai Kare ya ce wa Kura: “Gara ki jeki ɗora mana sanwar kalaci. Ina ganin wake da shinkafa ya kamata ki
    dafa. ”Kura na jin haka ta ce: “Gaskiyarka, Kare.” Kura ta je ta kama ’ya’yan Kare, ta zuba su a tukunya, ta ɗora sanwa.

    Daga nan ta koma wurin aiki. Da Kare ya ga ta koma, sai ya tambaye ta: “Kin ɗora sanwa ne?” Kura ta ce masa: “E, na ɗora. Ai yau fa za mu ci daɗi.” Daga nan sai
    Kura ta kama waƙa tana cewa:

    “Mu yi daka da wuri mu tafi,

    ’Ya’yan Kare suna shan wuta,

    Hum tiri hum.”

    Da Kare ya ji abin da take cewa, sai ya ce: “Kura bari inje in duba mana sanwa ko wuta tana ci.” Kura kuma ta ce wa Kare: “Idan ka je kar ka buɗe tukunyar; ka iza wutar kawai ka dawo.” Sai Kare ya ce: “To, na ji.” Kare na isa murhu ya tarar wutar ta mutu; ko zafi ma sanwar ba ta fara yi ba.

    Sai ya buɗe tukunyar domin ya ga abin da Kura take dafa musu. Kare na buɗewa sai ya ga ’ya’yansa suna mutsulniya a cikin ruwa. Bai yi wani ɓata lokaci ba, sai ya fitar da su. Nan da nan ya kamo ’ya’yan Kura ya sa a cikin tukunyar nan, ya nemo guma-guman itace ya haɗa wuta; ya ɗora tukunya a kan murhu.

    Sai ya kai ’ya’yansa ya ɓoye a kan wata bishiya. Da ya koma wurin aiki inda Kura ke jiransa, sai ta tambaye shi: “Ka gyara itacen dai ko?” Ba tare da ya nuna mata abin da ya yi ba, sai kawai ya ce da ita: “E, na gyara, ƙanwar Zaki, surukar Damisa, kanwar Giwa!” A cikin murnar kirarin da Kare ya yi wa Kura da kuma zaton za ta ci naman ’ya’yansa, sai ta ci gaba da rera wannan wakar:

    “Mu yi daka da wuri,

    Kafin rana ta kai tsakiya,

    ’Ya’yan Kare sun sha wuta,

    Sun kusa nuna.

    Hum tiri hum.”

    Sai Kare ya fara tasa waƙar yana cewa:

    “Ka juye nawa ’ya’yan

    Ka bar na an’uwana.”

    Sai Kura ta ce: “Wace irin waƙa ce haka Kare?” Sai Kare ya ce: “Sanda kike yin taki waƙar, na yi magana ne?” Da jin wannan tambaya tasa sai ta yi shiru. Suka ci gaba da gyaran wake, har suka gama. Bayan sun gama aiki, sai Kura ta ce wa Kare: “Je ka ka ɗebo wake da shinkafa daga cikin tukunya mu ci.”

    Sai Kare ya je ya ɗebo musu; ita tana zaton naman ’ya’yan Kare ne. Kura ta ci nama, ci irin na ƙeta da haɗama, har ta rage da nufin za ta kai wa ’ya’yanta. Sai Kare shi ma ya ce zai kai wa ’ya’yansa abin da ya rage. Da ta ji maganar Kare, sai ta fashe da dariya, amma ba ta yi wa Kare bayanin dalilin dariyarta ba.

    Shi kuma bai tambaya ba. Suka tafi, kowa da nufin ya kai wa ’ya’yansa nama. Lokacin da Kura ta isa raminta, sai ta tarar saura ɗanta ɗaya. Sai ta koma da gudu ta tambayi Kare, “Ina ’ya’yana?” Sai Kare ya ce: “Da kika ɗora ’ya’yana a kan wuta za ki dafa, na tambaye ki ne?”

    Sai Kura ta bi Kare da gudu za ta kashe. Da Kare ya ga haka sai ya ce da ’ya’yansa: “Ku miƙo mini igiya.”Suka jeho masa, ya kama, ya haye bishiyar. Da Kura ta kasa hawa bishiyar, sai ta ce wa Kare: “Za mu haɗu da kai.” Sai Kare ya ce: “Gobe ma zan je ɗaukar itace.” Sai Kura ta tafi abinta.

    Washe-gari sai Kare ya ɗauki damin itace. Yana cikin tafiya sai ya hangi Kura tana zuwa. Sai ya shiga cikin itacen, yana mirginawa. Da Kura ta je kusa da itacen sai ta ce:

    “Itace mai mirginawa!

    Itace mai mirginawa!!

    Ba ni hanya, ina neman Kare.”

    Sai itace ya mirgina ya kauce, Kura ta wuce. Da Kura ta yi nisa, sai Kare ya fito ya ɗauki itace ya tafi zarafinsa. Da Kura ta komo sai ta sami Kare a kan bishiya, sai tace: “Kare jiya ka yi mini ƙarya, ka ce min za ka je ɗaukar itace, amma ban gan ka ba.” Sai Kare ya ce: “Jiya ba ki haɗu da wani itace yana murginawa ba?

    ”Kura ta ce: “Na haɗu da shi mana.” Sai Kare ya ce: “A garinku kin taba jin an ga itace yana murginawa shi kaɗai?” Sai Kura ta ce: “To, gobe ina za ka?” Sai Kare ya ce: “Gobe zan je in ɗebo ruwa.” Kura ta tafi, tana tunanin yadda za ta gama da Kare idan gari ya waye. Washe-gari sai Kare ya ɗauki tulunsa, ya je ɗaukar ruwa.

    Sai ya hango Kura ta doshi rafin da yake. Sai ya shiga cikin tulunsa yana murginawa. Da Kura ta je kusa da tulun sai ta ce:

    “Tulu mai mirginawa,

    Tulu mai mirginawa.

    Matsa mini in wuce, Domin ina neman Kare.”

    Sai Tulun ya mirgina, Kura ta wuce. Da Kare ya auna, ya san Kura ta yi nisa, sai ya fito ya ɗauki ruwansa ya tafi. Daga baya kuma Kare da Kura suka haɗu, yana baya-baya da ita. Sai Kura ta ce: “Kare, ka yi min ƙarya.” Shi kuwa sai ya mayar mata da jawabi cewa, “Ba ki haɗu da wani tulu mai mirginawa ba?

    Ai ni ne a cikin tulun.” Kura ta ce ta gamu da shi, ta sake tambayar sa cewa: “To gaya mini inda za ka gobe domin in sami damar gamawa da kai kowa ya huta.” Sai Kare ya harari Kura, ya yi mata kallon raini, ya ce: “Zan je su, watau kamun kifi a gulbin yamma da Dajin Saidawa.”

    Washe-gari Kare da ’ya’yansa suka je su. Can sai suka ga Kura ta tunkari inda suke. Sai Kare ya ce wa ’ya’yansa duk su faɗa ruwa su buɗe haƙoransu. Har shi ma suka faɗa suka buɗe haƙoransu. Kura tana isa a gaɓar gulbi, sai ta ga haƙoran Kare da ’ya’yansa, sai tsoro ya kama ta. Sai ta ce wa ’yarta:

    “Kilatanda! kilatanda!!

    Baya baya ba ta.” Duk ta yi ’yan dube-dubenta ba ta ga Kare ba. Haka Kura ta gaji ta tafi. Da Kare ya ga lallai Kura ta tafi ba ta da nufin komawa bakin gulbi nemansa, sai ya fito da ’ya’yansa. Daga nan suka bar dajin nan domin kada wata rana tsautsayi ya sa Kura ta halaka shi da ’ya’yansa. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • In za ka gina ramin mugunta ka gina gajere, ba ka sani ba ko kai ne za ka faɗa.
    • Rama cuta ga macuci ibada ce.
    • Duk inda ka kai da wayo wani ya fi ka.
    • Cin dare ɗaya kumburin ciki.
    • Wankan wuta sau ɗaya a kan yafa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Naƙuda A Daji

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Naƙuda A Daji

    Tatsuniyar Naƙuda A Daji

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wata mata mai ciki. Sai wata rana ta shirya za ta yi balaguro. Tana tafiya a cikin daji, sai naƙuda ta kama ta. Sai ta raɓa a ɗan wani wuri ta haihu. Ta ɗauki jinjirin ta kama hanya tana tafiya, ko za ta tarar da wani gida ta huta. Sai ko ta tarar da wani gida a tsakar dokar daji ta shiga.

    Ashe gidan nan na Dodo ne. Sai ko mai jegon nan ta ga ruwa a gidan, ta ɗiba ta yi wanka da shi, ta wanke ɗanta, ta dafa abinci. Sai ta hau kan ɗakin Dodon, ta zauna ta ci abincin da ta dafa. Sai ta ga wata wuƙa a gidan Dodo, ta kuwa ɗauke ta, ta hau kan ɗakinsa ta zauna.

    Can Dodo ya dawo daga farauta, sai ko tsoro ya kama ta, sai ta tsunkuni jaririnta, har ya saki zawayi saboda jin zafi. Zawayin kuwa ya zubo a tafin hannun Dodo yayin da yake zaune a gindin ɗakin yana hutawa, sai ya lashe, ya ko yaba da daɗin abin da ya lasa, sai
    ya ce: “Wannan ai miya ce da gauta.”

    Da ya ɗaga kansa domin ganin daga inda wannan abin daɗi yake zo masa, sai ko suka yi arba da matar nan. Sai ta sake tsunkunin ɗanta, ya yi wata irin ƙara. Da Dodo ya ji, sai ya tsorata, ya shiga daji a guje, ya kira sauran dabbobin dawa domin su zo su ga wata irin halitta da bai saba ganin irinta ba, wai yana so su kore ta daga gidansa.

    Dabbobin suka cika gidan Dodo, to amma ba wanda ya shiga saboda tsoro. Suka ce Giwa ta shiga, ta ƙi; aka ce Raƙumin Dawa, ya ko yarda ya shiga. Da ya kunna kansa ya shiga sai ko matar ta riƙe kan. Da sauran dabbobin suka ga ya jima bai fito ba, sai suka tambaye shi abin da ya riƙe shi. Sai ya ce: “Dodo ne ya riƙe mini wuya.”

    Ita kuwa matar sai ta sa wuƙar ta fara yankan wuyan Raƙumi. Tun suna tambayar Raƙumin Dawa yana magana, har ya kasa magana. Jim kaɗan sai suka ga ya faɗi matacce, ba kai a jikinsa. Ganin haka fa duk suka tarwatse da gudu; Dodo mai gidan ne kuwa a kan gaba. Duk bishiyar da ya ci karo da ita sai ya tuge ta don gudu.

    Da matar ta ji ba sauran motsin dabbobin nan, sai ta sauƙo goye da ɗanta ta kama hanya, ba ta tsaya ko’ina ba sai gidan mijinta. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Banza ta kori wofi.
    • Taron tsintsiya ba shara.
    • Dabara ta fi ƙarfi.
    • Yuyu banza, ƙwaƙƙwara ɗaya ya fi amfani.
    • Dabara ɗaukar ɗaki.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Kunkuru Da Matarsa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Juya Ta Sami Gagare

    Tatsuniyar Juya Ta Sami Gagare

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wata mata da mijinta, ba su taɓa haihuwa ba. Sai ’yan gaza gani a garinsu suka shiga cewa ita juya ce ba mai haihuwa ba. Irin waɗannan maganganu kuwa sukan dame ta. Wata rana tana dawowa daga gona, sai ta ga wani jariri a gindin gamji. Sai ta ɗauke shi, ta goya, ta tafi da shi gida. Da mijin ya shiga gida, sai ta gaya masa ta haihu a gona.

    Ya yi murna, amma fa da ’yar shakka. Bayan mako guda aka raɗa wa jariri suna Tabi. Daga nan sai ta shiga zaman jego a gida, ta yi kwana arba’in tana cin kaji. Bayanta cika arba’in, sai ta gaya wa mijinta tana buƙatar yarinyar da za ta taimaka mata wajen renon yaron. Mijin kuma ya nemo mata.

    Ashe yaron nan ba mutum ba ne, aljani ne, amma ba su sani ba. Kullum idan mai gidan da matar za su je gona, sai yaron yace: “Iya ki zo mini da ɓera; baba ka zo mini da fara.” Kuma da zarar sun fita daga gidan, sai yaron ya rikiɗa ya zama babban mutum. Tuni kuma ya ja kunnen yarinyar, ya ce mata: “Idan kika gaya wa mutanen nan abin da nakan yi bayan sun tafi gona, to zan kashe ki.”

    Shi ke nan, kullum sai ya sa ta shiga rumbu, ta ɗebo hatsi yasa ta shiga niƙawa, yana yi mata kiɗa da gurmi. Ga waƙar da yakan yi airin wannan lokaci: “Kai Ɗan Tabi, Kai Ɗan Tabi, Ɗan mai gajerar fuska, Wagga mata ba ta haifi ɗa ba, Sai ka sa ta sami Tabi. Tabi, Tabi na me ye?” Da zaran ya ƙintaci iyayen sun kusa komowa gida, sai ya rikiɗa ya koma yaro, kamar yadda suka san shi, ya sa yarinyar ta goya shi.

    Idan suka dawo sai su ba shi ɓeran da farar da suka kamo masa. Kowacce rana sai sun kawo masa ɓera da fara. Ana nan, a kwana a tashi, sai suka lura yarinyar tana ramewa, amma ba su san abin da ke damun ta ba. To, ashe wata tsohuwa maƙwabciyarsu tana ganin duk abin da yake faruwa tsakanin yarinyar nan da ɗan aljanin nan.

    Sai wata rana ta kasa jurewa, ta kira mijin da matar tace da su: “Ku yi kamar za ku gona, sai ku ɓuya a gidana, ku gaabindayaronku yakan yi.” Washe-gari da sassafe suka je gidan tsohuwa, suka sa idonsu a ƙafar danga, suka shiga jira. Jim kaɗan kuwa yaron ya rikiɗa, ya zama babban mutum. Suna gani ya ɗauki yarinya ya jefa ta cikin rumbu. Suna gani ta miƙo masa hatsi, ta fito ta fara niƙa masa.

    Sai ya bugi cikinsa, riga ta fito. Da ya sake bugawa, sai ga hula. Da ya buga a karo na uku, sai ga gurmi. Nan take ya fara kaɗa gurmi yashiga yin wannan waƙar: “Kai Tabi, Kai Ɗan Tabi, Ɗan mai gajerar fuska, Ka ga mata ba ta haifi ɗa ba, Sai ta sa ma ɗa suna Tabi, Tabi na meye.” Sai mijin ya tambayi tsohuwar yadda za su yi.

    Tsohuwar tace da su: “Yanzu ku koma gida; gobe za mu je gidan mai magani.” Washe-gari suka yi kamar sun je gona, suka nemo ɓera da fara suka kai wa yaron. Sai yaron ya ce: “Mama, yau ba ku je gona ba.” Sai ta ce masa sun je, sun gaji shi ya sa ba su samo masa ɓera da fara masu kyau ba. Sai yaron ya ce ba zai ci ba, amma gobe idan sun je gonar su zo masa da fara da ɓera masu kyau.

    Washe-gari suka je wurin tsohuwa ta raka su wurin mai duba. Suka gaya masa duk abin da ake ciki. Ya duba, ya gano cewa yaron nan fa ba mutum ba ne. Da suka tambayi mai duba yadda za su rabu da yaron nan, sai ya ce to su je su sami baƙin rago mai farar ƙafa da gyaɗa da riɗi a soye, da ƙwarya da garin dawa, sai su tafi da su bakin rafi.

    Duk wanda aka aika, to idan ya tafi kada ya sake dawowa, ya je ya hau wata bishiya. Sai suka je, suka nemo duk abin da aka ce, suka kai. Ɗan duba mai magani ya ce su je su ɗauko yaron, su je bakin rafi da shi. Suka sa yarinya mai goyonsa ta goya shi suka ce za su je bakin rafi kamun kifi. Sai ta goya shi, suka tafi.

    Da suka je bakin rafi, sai ɗan duban ya ce ya kamata a fara dafa abinci kafin a kama kifi. Ashe wai suna yi wa Tabi wayo ne, sai matar ta yi kamar za ta hura wuta sai ta ce: “Af, mun yi mantuwa. Mun manta auduga da dutsen hura wuta.” Sai suka cewa yarinyar ta sauke goyon, ta je ta ɗauko musu dutsen hura wutar.

    Sai ta sauke yaron, ta je, ta hau kan bishiya. Da suka ji shiru, sai suka ce tsohuwa ta bi sawun yarinyar ta duba ko lafiya. Ita ma ta je shiru. Sai mijin shi ma ya bi tsohuwa, shi ma shiru. Sai matarsa ta bi sawunsa. Daga ƙarshe dai kowa ya tafi, suka bar yaro da ɗan duba. Shi ma mai duba sai ya yi wa yaro dabara ya tafi ya bar shi. Da yaro ya ji shiru, sai ya yi ta kiran su, amma ina, sai ya ce: “Wato mutanen nan suna so su ci amanata ne.”

    Sai ya juye gyaɗa da riɗi a cikin aljihunsa. Idan ya ɗiba sai ya watsa a bakinsa, sai yace wannan ƙafar wane ne, yana ta bin sawunsu, har ya isa gindin bishiyar da suka hau. Yana ɗaga kansa, sai ga su gaba ɗaya kan bishiyar. Dukansu tsoro ya kama su. Sai ya ce: “Yanzu haka za ku yi min? Na kwanta a gindin bishiya ina hutawata kika zo kika ɗauke ni, kuma yanzu za ki ci amanata? Ki sani idan Allah bai ba ki ɗa ba, to ba wanda zai iya baki shi. Ku sauko ku tafi na yafe muku. Amma nan gaba kada ku ƙara tsintar ɗa, ku ce za ku riƙe.” Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Abin da Allah bai ba ka ba, babu wanda ya isa ya ba ka shi.
    • Zaƙin nema ba ya kawo samu.
    • Tsintattar kyanwa ba ta mage.
    • Idan za ka yi fatan samun ɗa, yi fatan samun nagari.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Zinari A Bakin Kwano

    Tatsuniyar Zinari A Bakin Kwano

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wani mutum ne yana zaune da matarsa a cikin talauci a wani ɗan ƙauye, babu cin yau balle na gobe. Wata rana sai ya je gona ya ga wata busasshiyar bishiya, ya hau ya fara sara da gatarinsa domin neman abin zaman gari. To akwai wani dutse mai kogo kusa da gonar.

    Sai kwatsam, ga wasu mutane su goma sha biyu riƙe da kwari da baka sun fito daga ciki. Da fitowarsu sai suka zauna suka ci abinci, suka tafi. Amma kafin su bar wurin sai da suka faɗi wani abu kamar haka: “Kalja sum sum, Kalja sum sum, Kalja sum sum.” Da faɗin haka sai mutumin ya ga ƙofar kogon dutsen ta rufe.

    Sai dai ya ga kamar ɗaya daga cikinsu ya manta da wani abu sai yace: “Buɗe sum sum, Buɗe sum sum, Buɗe sum sum.” Sai ƙofar kogon ta buɗe, ya shiga ya ɗauko wata batta daga ciki; ya fita, suka kama hanyarsu. Bayan sun tafi, sai mutumin ya matsa kusa da dutsen domin ya kashe kwarkwatar idonsa.

    To, tun da ya ji abin da suka faɗa, sai shi ma ya faɗa, ƙofar kogon kuma ta buɗe, sai ga ruwa. Ya sake cewa: “Kalja sum sum,” wata ƙofar ta buɗe, sai ga wuta. Bai fasa ba dai, ya sake faɗa, wata ƙofar ta buɗe, amma a wannan wuri sai kawai ya ga ƙyalƙyali irin na zinariya. Ga kuma tarin zinariyar mai ɗinbin yawa, abin gwanin ban mamaki, har ma da tsoro.

    Can gefe kuma tarin azurfa ne kamar ba iyaka, ga kuma kuɗi a wani ɓangaren kamar duk kuɗin duniya baki ɗaya aka tara a can saboda yawansu. Mutumin nan ya shiga ya ɗebi dukiya iya yadda zai iya ɗauka, ya ɗora a ka, yana riƙe da gatarinsa ya kama hanyar gida, amma fa duk sai da ya tabbata ya rufe duk ƙofofin kogon nan da ya buɗe.

    Yana isa gida matarsa ta tarye shi da murna kamar dai yadda takan yi kullum idan ya je neman abinci ya dawo. Mutumin da gaggawa kuma a cikin murna ya nuna wa matarsa zinare da kuɗi da azurfar da ya samo. Matar kuma a guje ta je ta aro ma’auni a wajen maƙwabta suka auna zinaren.

    Ba da saninsu ba ashe akwai ɗan guntun zinaren ya maƙale a ma’aunin da suka mayar masu. Masu ma’auni suka ajiye, har dare ya yi. Sai ga wani abu ya haske musu ɗaki, suka yi ta mamaki. Da gari ya waye suka shiga bincike, suka gano ashe zinare ne a jikin ma’auni da maƙwabta suka ara da maraice.

    Daga nan suka aiki ɗayansu ya je ya tambayi mutumin inda ya samo zinariya. Ya dai matsawa mutumin sai ya nuna masa inda ya samo domin shi ma ya je ya ɗebo. A kan tilas mutumin nan ya tasa ƙeyarsa suka tafi. Da suka isa, sai mutumin ya gaya wa maƙwabcinsa abinda ake cewa ƙofofin kogon dutsen nan su buɗe.

    Daga nan fa sai ya tafi gida abinsa. Maƙwabci ya faɗi abin da mutumin ya gaya masa, sai nan da nan ƙofofin suka buɗe. Sai ga dukiya, kamar ta fi wadda mutumin farko ya fara gani jiya. Maƙwabci ya lafci dukiya iyakar son ransa, to amma da ya zo fita sai ya rikice, ya rasa abinda zai faɗa ƙofar kogo ta buɗe.

    Jim kaɗan sai mutanen nan goma sha biyu suka dawo daga inda suka je. Suka shiga kogon, sai kawai suka tarar da maƙwabci. Ganin ya kwashi dukiya ba tare da izininsu ba, sai suka kama shi suka yanka, suka ajiye gawarsa a gefe. Washe-gari da mutumin ya ji ana cewa maƙwabcinsa bai dawo gida ba, sai ya koma dajin nan, ya jira sai da mutanen nan suka fito suka tafi, ya je ya buɗe kogo, ya shiga.

    Da shigarsa sai ya tarar da gawar maƙwabcinsa a gefe, mutanen nan sun yanka ta gunduwa-gunduwa. Ya tattara gaɓobin, ya zuba a mangala, ya kama hanyar gida. Sai ya ɗebi zinariya, ya je wurin shugaban dogarai ya ce da shi ɓarayi sun tare su, har suka kashe mishi ɗan’uwa, saboda haka ya ce masa: “Don Allah ga ladan zinariya nan ka sake haɗe min shi, domin a rufe shi a haɗe.”

    Sarkin Dogarai ya haɗa mutum, amma tun kafin a ɗauke shi a tafi da shi wurin binnewa ra, sai mutanen kogo suka je gidan Mai Gari suka ce wani mutum ya sayi saniyarsu bai biya ba, amma ya mutu an kawo gawarsa gidan Sarkin Dogarai. Sarki ya bincika aka tabbatar da haka; aka kawo gawar, suka ce a ba su.

    To, dama suna so a ba su gawar ne domin su cinye, Sarki ya hana. Yasa Sarkin Dogarai ya ba mutumin nan gawar maƙwabcinsa, aka binne ta bisa al’adar garinsu. Mutanen kogo suka haƙura, shi kuwa matalaucin nan da ya sami dukiya a dare ɗaya, ya yi ta cin
    duniyarsa shi da matarsa. Amma kuma duk sanda ya ga matalauta yakan taimake su da kuɗi da abinci da jari domin su yi sana’a. Sai mutan ƙauyen suka sa masa suna Mai sa’a. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Mahaƙurci mawadaci.
    • Wanda ya daka rawar wani zai rasa turmin daka tasa.
    • Kuɗi masu gidan rana.
    • Duk wanda ya haƙura da kaɗan Allah zai wadata shi.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Jika Da Kaka

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Jika Da Kaka

    Tatsuniyar Jika Da Kaka

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can wani ɗan ƙauye da ke kusa da Gulbin Tattabaru, an yi wata yarinya da ke zaune tare da kakarta. Rannan yarinyar tana shara sai ta tsinci kurkunu ta bai wa kakarta ta ajiye mata. Da ta gama sharar sai ta je wurin kakar ta tambaye ta: “Kaka, ina kurkununa?” Kakar ta dubi jikarta ta mayar da jawabi: “Ai na cinye, jikalle.”

    Da jin wannan amsa sai yarinya ta fusata; ta ƙura wa kakar ido tace: “A gaskiya kaka ban yarda ba.” Daga nan ta ɗauki buta, ta cika ta da ruwa; ta kama wata kuka ta haye; ta yi zamanta ba niyyar saukowa. Da kakarta ta ga ya kamata ta sauko ta ci abinci, sai ta je kiran ta.

    Yarinya abu kamar da wasa, sai ta ƙi saukowa kakar ta kira maƙwabta da ƙawayen jikarta domin su sa ta ta sauko, ammaina, abu ya faskara. Sai ta ce da wasu samari: “Don Allah ku taimaka ku sare mini kukar nan tun da jikata ta ƙi saukowa.” Samari suka yarda suka debo gatura daga gidajensu.

    Kowa ya yi ɗamara suka fara saran kuka. Suna waƙar gayya, wannan ya sara idan ya gaji wannan ya karɓa, da haka da haka har suka ci ƙarfin kaurin bishiyar. Can da kuka ta nuna layin faɗuwa, sai kawai aka ga yarinyar ta fara rikiɗa, har ta zama kurkunu. A halin haka sai ta haifi ’ya’ya da yawa.

    Kuma nan take ta sake rikiɗa, ta koma mutum a kan bishiyar. Kowa ya buɗe baki sai kallon abin al’ajabi yake yi. Sai ta ce da kakarta da sauran mutanen: “Ga kurkunu nan da yawa ku ci ku ƙoshi, amma ki rage mini guda ɗaya kawai; daga nan sai ki koma gida, zan sauko.”

    Da kowa ya bar wurin, sai yarinya ta sauko ta kama hanyar gida. Tana isa gida sai ta yi wa kakarta bayani cewa: “Ai aljanun da ke zaune a kukar nan ne suka hana a sare ta, saboda haka ne ma suka rikiɗar da ni har na haifi kurkunu domin ki dawo min da shi a ƙyale musu gidansu.

    Kuma sun ce in gaya miki ki gaya wa Mai Gari kada a sake ƙoƙarin sare wannan kukar.” Kakar yarinya ta yi mamakin wannan bayani, kuma ba ta yi nawa ba ta je ta sanar da Mai Gari saƙon da aljanu suka aiko ta hannun jikarta. Shi kuma Mai Gari ya sa aka sanar da jama’arsa cewa kada wani ya kuskura ya sare kukar nan domin gidan mutanen ɓoye ne, abokan zaman lafiyarsu. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Wasa tsakanin jika da kaka ba abu ne mai kawo ɓacin rai ba.
    • Wasu mutan ɓoye abokan zama ne ba abokan faɗa ba.
    • Komai za ka yi ka yi tunani kafin ka aikata shi.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar ’Yan Matan Fangama

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Garin Da Ba Maza Sai Mata

    Tatsuniyar Garin Da Ba Maza Sai Mata

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wani gari da duk mazaunansa mata ne zalla, watau ba wani namiji ko ɗaya a cikinsu. Su matan a kullum sukan tafi rafi su yi wanka, su kuma ɗauko ruwa. Sai wani mutum daga wani gari mai nisa ya ji labarin wannan ƙauye. Ya ɗaura ɗamara, ya kama hanya da nufin sai ya je wannan gari mai ban mamaki.

    Ya yi tafiya mai nisa a cikin ƙungurmin daji kafin ya isa. Da zuwansa sai ya hangi wasu mata kyawawa suna wanka a rafi. Ya matsa har ya isa kusa da su, ya gama kallon su sarai, ba tare da sun sani ba. Da ya ga ba su gan shi ba, sai ya kwashe tufafinsu da ke dab da bakin kogin nan; ya hau bishiya, ya ɓuya.

    Can da matan suka gama wanka suka fito sai suka ga ba suturarsu. Suka duba nan suka duba can ba su ga kowa ba, suna ta mamakin abin da ya faru. Wasu suna ce ko aikin aljanu ne. Can sai wata daga cikinsu ta leƙa saman wata bishiya sai ta ga mutumin. Ita ce kuma ta fi duk sauran kyau.

    Shi kuma mutumin ɗan saurayi ne mai kyan gaske. Daga nan sai matan suka kama waƙa, suna cewa:

    “Kai saurayin nan, Kai saurayin nan,

    Don Allah ka maido mana da kayanmu nan.

    Kai saurayin nan, Kai saurayin nan,

    Ka ji kunyar mu, Ka dawo mana da kayanmu.”

    Nan da nan ya mayar musu da kayansu, amma banda na waccan mata da ta fi sauran kyau. Ya ce zai ba ta kayanta ne kurum idan ta yi masa waƙa mai daɗi, kuma ta ambaci sunansa. Sai ta yarda. Ta rera waƙar mai daɗi, sai dai ba ta ambaci sunansa ba, saboda ba ta sani ba.

    Shi kuwa ya ƙi ba ta kayan. Yana ta ja mata rai, har rana ta kusa faɗuwa. Da mahaifiyarta ta ga shiru ba ta koma gida ba, sai ta aiki ƙanwarta nemanta. Kanwar na zuwa bakin ruwa sai ta tarar da yayarta zindir, haihuwar uwarta. Tana ganin ƙanwar sai ta ce:

    “Akwai wani kyakkyawan saurayi a wurin nan wanda ya riƙe kayana; ya ce ba zai
    ba ni ba sai na ambaci sunansa.” To da man kanwar hatsabibiyace, sai ta yi wani siddabaru irin nata, ta ji kurum kamar daga sama an gaya mata sunan saurayin nan. Nan take ta sanar da yayarta, tace kuma ta yi wakar ta faɗi sunan ta ga abin mamaki.

    Da ta yi haka sai saurayi ya mayar mata da kayanta; ya sauko daga kan bishiyar;
    ya ɗora ta tare da ƙanwar a kan doki; ya karya linzami, ba su zame ko’ina ba sai a ƙofar gidan su yarinyar. Gyatumarsu da maƙwabta suka yi ta mamakin ganin namiji a garin saboda duk tsawon rayuwarsu ba wadda ta taɓa ganin namiji.

    Ba tare da ɓata lokaci ba mutumin ya nemi yarinyar da aure, aka ba shi. Aka yi aure da babban biki mai ƙayatarwa. Bayan can ya sami wuri ya gina gida mai ƙayatarwa a garin, shi da matarsa suka zama abin kallo, ba a zancen komai sai nasu. Bayan ’yan shekaru suka haifi ’ya’ya maza biyu.

    Wata rana mutumin ya ce zai je ganin gida, amma tare da ɗaya daga cikin ’ya’yan. Uwar ta ce su dawo lafiya. Suka je, suka komo. Bayan an kwana biyu mutumin ya ce zai sake ziyartar garinsu, amma a wannan karo yana so ya je tare da ’ya’yan duka, domin ya nuna wa danginsa su baki ɗaya.

    Wannan buƙata ta mutumin ta tayar da hankalin duk matan garin. Amma mahaifiyarsu, ta dage a kan cewa a bar mijin ya yi haka. Da mutumin ya je garinsu, sai ya yi zamansa, bai koma ba. Matar ta yi ta kuka saboda rashin ganin ’ya’yanta. Bugu da ƙari mutumin ya aiko da saƙo cewa ya saki matar.

    Bayan wani lokaci Ubangiji ya share mata hawaye. Wani ɗan Sarki daga wata ƙasa ya je garin, ya neme ta da aure, ta yarda aka ɗaura musu aure aka yi babban biki. Suna nan zaune, har ɗan Sarki ya gaji sarautar gidansu. Ba a jima ba shi ma ya rasu, ɗan da suka haifa da matar ya gaje shi.

    Ita kuma Allah ya ba ta tsawon rai, ta zauna tare da ɗanta cikin ni’ima. Waɗancan ’ya’yan nata na farko su ma sun zo sun girma suka matsa wa mahaifinsu ya bar su suna zuwa a kai a kai suna gaishe su ana musu alfarma. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Wani hani ga Allah baiwa ne.
    • Soyayya gamon jini.
    • Mai haƙuri yakan dafa dutse.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Kanta Da Mugayen Abokananta

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kanta Da Mugayen Abokananta

    Tatsuniyar Kanta Da Mugayen Abokananta

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wasu ’yan mata su goma sha biyu ƙawaye. A cikinsu har da wata ’yar Sarki mai suna Kanta. Ita kaɗai ce a wurin mahaifiyarta. Ita ce kuma ta fi kyau a tsakanin duk ’yan matan garin. Kowane saurayi a garin yana so ya aure ta, amma ta ƙi. A cikin waɗanda suke son ta har da wani maciji wanda ke zaune a cikin kogin da ke kusa da ƙauyen.

    Sauran ’yan matan suna kishin Kanta saboda farin jininta da kyauta. Saboda haka suka haɗa baki cewa za su ja ta zuwa kogin nan domin su kashe ta. Mahaifiyar Kanta ta gane duk ƙulle-ƙullen da ’yan matan suke yi game da ’yarta, saboda haka ta yi ta ƙoƙari ta kare ta.

    Duk lokacin da ’yan matan suka zo neman Kanta, sai ta ce da su ba ta nan. Wata rana sai uwar Kanta ta tafi wata unguwa ziyara. Ganin haka ’yan matan nan suka je har cikin gidan Sarki suka ja hankalin Kanta har ta amince za ta bi su kogin nan. Ta bi su da sunan kamun kifi za su.

    Da suka isa kogin, sai suka ga wani mangwaro mai ’ya’ya, kuma suka yanke shawara za su hau domin su tsinki na sha. Kanta ta ƙi hawa, amma suka matsa mata, har dai ta hau. Kowaccensu ta roƙi Kanta da ta tsinko mata mangwaro. Macijin da ke kogin nan ya ji hayaniya ta yi yawa, sai ya fito.

    Ya nufi inda ’yan matan nan suke. Da suka gan shi suka gudu, suka bar Kanta a sama. Macijin ya hau itacen ya same ta. Can daga baya ’yan matan suka koma wajenta, suka ga halin da take ciki. Da suka iso sai suka kama waƙa, suna cewa:

    “Kai macijin nan don Allah,

    Ka sassauta wa Kanta ta sauko,

    Kai macijin nan don Allah,

    Ka sassauta wa ƙawarmu Kanta ta sauko.”

    Kanta kuwa sai hankalinta ya tashi. Da mahaifiyarta ta dawo ba ta gan ta a gida ba, sai ta shiga nemanta. Ta shiga nan ta shiga can har dare ya yi ba ta gan ta ba. Ƙawayen Kanta kuwa suka koma gida dab da almuru, suka baro ta a kan mangwaron nan na bakin kogi.

    Allah da ikonsa sai ga wani ɗan tsuntsu fari ya zo ya sauka kusa da Kanta; sai ta roƙe shi, ta ce: “Kai ɗan farin tsuntsun nan, don Allah ka taimake ni ka kai saƙona ga iyayena. Babana shi ne Sarkin garin. Ka gaya musu cewa ina cikin matsala. Ƙawayena duk sun gudu sun bar ni da wani maciji wanda yake so ya haɗiye ni.

    Ina nema su kawo mini gudunmawa da wuri don su kuɓutar da ni daga wannan matsala.” Ɗan tsuntsu ya yarda; ya tashi sai fadar Sarki. Da ya isa gaban Sarki sai ya ce: “Mai martaba, na zo ne in ba ka saƙo daga ’yarka.” Da jin haka sai mamaki ya kama Sarki da matarsa.

    A gigice Sarki ya ce da ɗan tsuntsu: “Yi maza ka gaya mana saƙon.” Ɗan tsuntsu ya ce: “Mai martaba, ’yarka ce tana can dogon daji; tana kan wata babbar bishiyar mangwaro, kuma wani babban maciji ya kusa ya haɗiye ta.” Da jin haka, ba tare da ɓata lokaci ba Sarki ya tattara dogarawansa suka tafi ɗan tsuntsu na nuna musu hanya.

    Da suka isa sai suka tarar macijin ya fara barci. Ba tare da yin wani motsi da zai farkar da maciji ba, suka ce ɗan tsuntsu ya yi ƙoƙari ya goyo Kanta, ya sauko da ita. Ɗantsuntsu ya je wajen Kanta ya gaya mata zai goye ta. Ya juya baya ta ɗare, ya tashi fir, yana nishi, da ƙyar ya kai ta fada.

    Dogarai suka sulale, suka bar maciji na barci, suka isa fada lafiya. Washe-gari Sarki ya sa a kirawo duk ƙawayen ’yarsa. Suka zo fada. Da aka bayyana duk abubuwan da suka faru, sai ƙawayen Kanta suka tuba, tare da yin alƙawari ba za su sake yin irin wannan abu ba har abada.

    Suka roƙi Sarki ya yafe musu. Sarki ya yarda, ya yi musu afuwa. Ya kuma sa wasu samari su auri ’yan matan. Aka yi babban biki a fadar Sarki. Har yanzu waɗanda suka san an yi wannan biki sukan ce ba su taɓa ganin biki mai armashi da ƙayatarwa kamarsa ba.

    Amma fa wani abu shi ne, duk da shagalin da aka yi lokacin bikin nan cikin farin ciki, Sarki bai huce baƙi ɗaya ba; sai da yasa aka je aka kashe macijin nan. Zaratan da suka kashe macijin suka ɗauko mushensa suka kai fada. Maciji ne mai tsawon gaske, kuma ba wanda ya taɓa ganin irinsa a ƙauyen.

    An ce ya halaka wasu daga cikin zaratan da Sarki ya tura suka kashe shi. Sarki ya yi wa waɗanda suka mutu wajen kashe macijin alheri, wanda aka ba iyalansu, kuma waɗanda suka dawo lafiya daga cikinsu ya yi wa kowannensu aure. Mutanen garin kan yi bikin tunawa da waɗanda suka rasu saboda bajintar da suka yi. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Ba a rama kirki da mugunta.
    • Kowa ya ci amana sai amana ta ci shi.
    • Wayo ya kada sarkinsa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta tatsuniyar Tatsuniyar Dila Da Zomo

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Dila Da Zomo

    Tatsuniyar Dila Da Zomo

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana Dila ya haɗu da Akuya. Bayan sun gaisa sai Dila ya tambayi Akuya ko za ta ba shi ɗaya daga cikin ’ya’yanta su je bakin kogi shan ruwa? Akuya ta amince amma fa da sharaɗi. Sharaɗin shi ne tana so Dila ya lura da ’yarta sosai kar wani mugun abu ya same ta. Shi kuma Dila ya amince da haka.

    Da Dila da ’yar Akuya suka isa bakin rafi sai suka tarar wuta na ci a wani rami da ke kusa da kogin. Tun da ’yar Akuya ba ta da cikakken wayo, sai Dila ya ce mata shi zai shiga ruwan, ita kuma ’yar Akuya ta shiga ramin da wuta take ci. ’Yar Akuya ta bi
    maganar Dila, ta shiga ramin, wuta ta cinye ta.

    Bayan Dila ya gama kiwo sai ya zaro naman ’yar Akuyar daga ramin, ya cinye. Ya kama hanya, bai tsaya ba sai gidan Akuya, ya fashe da kuka ya ce mata ruwa ya cinye ’yarta. Akuya ta haƙura, amma abin ya yi mata ciwo. Daga nan Dila ya tafi wurin Zomo, ya nemi a ba shi ɗaya dagacikin ’ya’yansu domin su je rafi.

    Aka amince, amma da sharaɗin cewa idan ɗan Zomo zai kai kifi da yawa gida. Dila da ɗan Zomo suka je bakin ruwa, suka shiga. Dila ya yi ta iyo, amma ɗan Zomo da bai iya ruwa ba, ya tsuguna yana kallo. Jim kaɗan Dila ya sa shi ya shiga ramin da ke can gefen rafin wuta na ci a ciki. Sai dai a wannan karon wayon Dila bai yi aiki ba.

    Ɗan Zomo ya ƙi shiga ramin. Maimakon ya shiga, sai ya tuɓe takalmansa, ya jefa su a ciki, ya koma gefe ya ɓuya. Dila kuwa sai ya shiga murna, yana zaton ɗan Zomo ma ya yi irin ta ’yar Akuya. Da Dila ya gama iyo sai ya zaro takalmin ɗan Zomo da ya sha wuta, ya cinye. Ya sha ruwa, ya kama hanya ya tafi gida.

    Tsammani yake naman ɗan Zomo ya cinye. Dila bai sani ba ɗan Zomo na ɓoye a cikin jakarsa. Saboda haka a lokacin da Dila ke kan hanyar komawa gida, sai ɗan Zomo ya kama waƙa yana cewa:

    “Dila ashe kai wawa ne,

    Dila ashe kai wawa ne,

    Ka cinye takalmina,

    Tsammani kake ni ka cinye.”

    Da Dila ya ji waƙa sai ya ce:

    “Ke jakata, ashe kin iya waƙa haka?”

    Bai tsaya ba, har sai da ya isa gidan Zomo. Ya je yana kuka sharaf- sharaf, hawaye sun cika masa fuska, kamar abin tausayi. Amma tun kafin ya yi wa iyayen ɗan Zomo ƙaryar kogi ya cinye musu ɗa, sai ɗan Zomo ya yi farat ya fito daga cikin jakar Dila. Tun kafin Dila ya ce da uwar Zomo ɗanta ya mutu a ruwa, sai ɗan Zomo yace:

    “Ƙarya yake cewa kogi ya tafi da ni. Abin da ya gaya mini shi ne in faɗa cikin wuta don wutar ta ƙone ni, wai shi zai yi iyo. Dabara na yi na tsira daga sharrinsa, domin da na shiga ramin, to da wuta ta cinye ni, ya sami nama ke nan. Maimakon in faɗa wutar ne na jefa takalmana.

    Shi kuwa Dila da ya fito daga iyo ya cinye takalman da suka sha wuta. To bai yi sa’a ba, mugun nufinsa ya ci tura.” Nan take sai ɗan Zomon ya kawo shawara cewa, lalle ne su shaidawa Sarkinsu saboda abin da ya faru da ’yar Akuya haka ya kusa faruwa da shi. Da suka kai ƙara, Sarki ya ba da umurni dogarawansa su kama Dila su je su fille masa kai a bayan gari. Haka kuwa aka yi. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Ba a rama kirki da mugunta.
    • Kowa ya ci amana sai amana ta ci shi.
    • Wayo ya kada sarkinsa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Gizo Da Kura

    Edita@rumasau-kallamu