Tatsuniyar Juya Ta Sami Gagare

0
7

Ga ta nan, ga ta nanku.

Akwai wata mata da mijinta, ba su taɓa haihuwa ba. Sai ’yan gaza gani a garinsu suka shiga cewa ita juya ce ba mai haihuwa ba. Irin waɗannan maganganu kuwa sukan dame ta. Wata rana tana dawowa daga gona, sai ta ga wani jariri a gindin gamji. Sai ta ɗauke shi, ta goya, ta tafi da shi gida. Da mijin ya shiga gida, sai ta gaya masa ta haihu a gona.

Ya yi murna, amma fa da ’yar shakka. Bayan mako guda aka raɗa wa jariri suna Tabi. Daga nan sai ta shiga zaman jego a gida, ta yi kwana arba’in tana cin kaji. Bayanta cika arba’in, sai ta gaya wa mijinta tana buƙatar yarinyar da za ta taimaka mata wajen renon yaron. Mijin kuma ya nemo mata.

Ashe yaron nan ba mutum ba ne, aljani ne, amma ba su sani ba. Kullum idan mai gidan da matar za su je gona, sai yaron yace: “Iya ki zo mini da ɓera; baba ka zo mini da fara.” Kuma da zarar sun fita daga gidan, sai yaron ya rikiɗa ya zama babban mutum. Tuni kuma ya ja kunnen yarinyar, ya ce mata: “Idan kika gaya wa mutanen nan abin da nakan yi bayan sun tafi gona, to zan kashe ki.”

Shi ke nan, kullum sai ya sa ta shiga rumbu, ta ɗebo hatsi yasa ta shiga niƙawa, yana yi mata kiɗa da gurmi. Ga waƙar da yakan yi airin wannan lokaci: “Kai Ɗan Tabi, Kai Ɗan Tabi, Ɗan mai gajerar fuska, Wagga mata ba ta haifi ɗa ba, Sai ka sa ta sami Tabi. Tabi, Tabi na me ye?” Da zaran ya ƙintaci iyayen sun kusa komowa gida, sai ya rikiɗa ya koma yaro, kamar yadda suka san shi, ya sa yarinyar ta goya shi.

Idan suka dawo sai su ba shi ɓeran da farar da suka kamo masa. Kowacce rana sai sun kawo masa ɓera da fara. Ana nan, a kwana a tashi, sai suka lura yarinyar tana ramewa, amma ba su san abin da ke damun ta ba. To, ashe wata tsohuwa maƙwabciyarsu tana ganin duk abin da yake faruwa tsakanin yarinyar nan da ɗan aljanin nan.

Sai wata rana ta kasa jurewa, ta kira mijin da matar tace da su: “Ku yi kamar za ku gona, sai ku ɓuya a gidana, ku gaabindayaronku yakan yi.” Washe-gari da sassafe suka je gidan tsohuwa, suka sa idonsu a ƙafar danga, suka shiga jira. Jim kaɗan kuwa yaron ya rikiɗa, ya zama babban mutum. Suna gani ya ɗauki yarinya ya jefa ta cikin rumbu. Suna gani ta miƙo masa hatsi, ta fito ta fara niƙa masa.

Sai ya bugi cikinsa, riga ta fito. Da ya sake bugawa, sai ga hula. Da ya buga a karo na uku, sai ga gurmi. Nan take ya fara kaɗa gurmi yashiga yin wannan waƙar: “Kai Tabi, Kai Ɗan Tabi, Ɗan mai gajerar fuska, Ka ga mata ba ta haifi ɗa ba, Sai ta sa ma ɗa suna Tabi, Tabi na meye.” Sai mijin ya tambayi tsohuwar yadda za su yi.

Tsohuwar tace da su: “Yanzu ku koma gida; gobe za mu je gidan mai magani.” Washe-gari suka yi kamar sun je gona, suka nemo ɓera da fara suka kai wa yaron. Sai yaron ya ce: “Mama, yau ba ku je gona ba.” Sai ta ce masa sun je, sun gaji shi ya sa ba su samo masa ɓera da fara masu kyau ba. Sai yaron ya ce ba zai ci ba, amma gobe idan sun je gonar su zo masa da fara da ɓera masu kyau.

Washe-gari suka je wurin tsohuwa ta raka su wurin mai duba. Suka gaya masa duk abin da ake ciki. Ya duba, ya gano cewa yaron nan fa ba mutum ba ne. Da suka tambayi mai duba yadda za su rabu da yaron nan, sai ya ce to su je su sami baƙin rago mai farar ƙafa da gyaɗa da riɗi a soye, da ƙwarya da garin dawa, sai su tafi da su bakin rafi.

Duk wanda aka aika, to idan ya tafi kada ya sake dawowa, ya je ya hau wata bishiya. Sai suka je, suka nemo duk abin da aka ce, suka kai. Ɗan duba mai magani ya ce su je su ɗauko yaron, su je bakin rafi da shi. Suka sa yarinya mai goyonsa ta goya shi suka ce za su je bakin rafi kamun kifi. Sai ta goya shi, suka tafi.

Da suka je bakin rafi, sai ɗan duban ya ce ya kamata a fara dafa abinci kafin a kama kifi. Ashe wai suna yi wa Tabi wayo ne, sai matar ta yi kamar za ta hura wuta sai ta ce: “Af, mun yi mantuwa. Mun manta auduga da dutsen hura wuta.” Sai suka cewa yarinyar ta sauke goyon, ta je ta ɗauko musu dutsen hura wutar.

Sai ta sauke yaron, ta je, ta hau kan bishiya. Da suka ji shiru, sai suka ce tsohuwa ta bi sawun yarinyar ta duba ko lafiya. Ita ma ta je shiru. Sai mijin shi ma ya bi tsohuwa, shi ma shiru. Sai matarsa ta bi sawunsa. Daga ƙarshe dai kowa ya tafi, suka bar yaro da ɗan duba. Shi ma mai duba sai ya yi wa yaro dabara ya tafi ya bar shi. Da yaro ya ji shiru, sai ya yi ta kiran su, amma ina, sai ya ce: “Wato mutanen nan suna so su ci amanata ne.”

Sai ya juye gyaɗa da riɗi a cikin aljihunsa. Idan ya ɗiba sai ya watsa a bakinsa, sai yace wannan ƙafar wane ne, yana ta bin sawunsu, har ya isa gindin bishiyar da suka hau. Yana ɗaga kansa, sai ga su gaba ɗaya kan bishiyar. Dukansu tsoro ya kama su. Sai ya ce: “Yanzu haka za ku yi min? Na kwanta a gindin bishiya ina hutawata kika zo kika ɗauke ni, kuma yanzu za ki ci amanata? Ki sani idan Allah bai ba ki ɗa ba, to ba wanda zai iya baki shi. Ku sauko ku tafi na yafe muku. Amma nan gaba kada ku ƙara tsintar ɗa, ku ce za ku riƙe.” Kurunƙus.

Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

  • Abin da Allah bai ba ka ba, babu wanda ya isa ya ba ka shi.
  • Zaƙin nema ba ya kawo samu.
  • Tsintattar kyanwa ba ta mage.
  • Idan za ka yi fatan samun ɗa, yi fatan samun nagari.

Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceTatsuniyar Ɗankucaka
Labarin na GabaMaƙala Mai Taken: Zamani Abokin Tafiya: Tasirin Kafafen Sada Zumunta ga Tashin Tashinar Zamfara
wikiHausa
wikiHausa kundin ilimi (insakulofidiya) ce da ke ilimantar da jama'a yara da manya da maza da mata wajen samun ilimi a saukake, cikin harshen Hausa.