Tag: tatsuniya

  • Tatsuniyar Cin Amanar Ɗan’uwa

    Tatsuniyar Cin Amanar Ɗan’uwa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum da ‘ya’yansa guda biyu. Suna nan, suna nan, sai wata rana babansu ya tura su neman furannin ƙawa. An ɗauka cewa duk wanda nasa ya fi kyau, to mahaifinsu zai fi nuna masa soyayya a gidan, kuma za a yi masa aure. Shi ke nan, sai suka je. Da suka je, sai ƙaramin ya tsinki fure mai kyau.

    Da yayansa ya gani, sai ya ƙwace, sannan kuma ya kashe shi. Sai ya kai furen nan gida. Sai babansa ya yi masa aure. Daga baya sai babansa ya tambaye shi inda ƙanensa yake, sai ya yi wa uban ƙarya, ya ce masa ya bar shi a baya, kuma zai ƙaraso gida ba da jimawa ba. Ana nan, ana nan, har wuni biyu, yaro bai dawo ba, Mahaifinsu ya jure ya kau da kai.

    Wata rana wani boka ya zo wucewa, sai ya ci karo da ƙashin yaron da aka kashe, ya ɗauka yana hurawa. Sai ƙashin ya fara rera wa bokan nan wannan waƙa: “

    Kai bokan nan kai bokan nan;

    Ƙashina ne kake hurawa.

    Baba ya aike mu daji, Mu samo furannin ƙawa,

    Nawa sun fi na ɗan’uwana kyau,

    Sai ya ƙwace nawan, Ya kashe ni.”

    Da boka ya ji haka, sai ya kai wa Sarki wannan ƙashi. Da Sarki ya hura sai ya ce:“Kai Sarkin nan, kai Sarkin nan, Ƙashina ne kake hurawa. Baba ya aike mu daji, Mu samo furanni, ni da yayana, Nawa sun fi na wana kyau, Sai ya ƙwace nawan, Ya kashe ni.”

    Sai Sarki ya sa a yi shela a sanar da mutanen garin cewa washegari gaba ɗayansu su zo ƙofar fadarsa, domin a tambaye su wanda ya yi wannan ɗanyen aiki. Da suka taru washe-garin, sai kowa ya ce ba shi ba ne. Sai Sarki ya ce, to za a sa duk wanda ke garin ya hura wuta, domin ƙashin zai faɗi wanda ya yi kisan kan.

    Sai aka fara ta kan mahaifin yaron da aka kashe. Da ya hura, sai ƙashi ya ce: “Kai babana, kai babana, Ƙashina ne kake hurawa, Kai ka aike mu daji, Ni da wana, mu samo furanni, Nawa sun fi nasa kyau, Sai ya ɗauke nawan, Ya kashe ni.” Sai Sarki ya ce to ya kira yaron, watau yayan wanda aka kashe.

    Ya zo, aka ba shi ƙashin ƙanensa, da ya fara hurawa, sai ƙashi ya ce: “Kai yayana, kai yayana, Ƙashina ne kake hurawa, Baba ya aike mu daji, Mu samo furanni, Nawa sun fi naka kyau, Sai ka ɗauke nawan, Ka kashe ni.” Sai Sarki ya ce to a kama yaron shi ma a kashe shi. Aka kama shi, aka kashe. Shi ke nan, an yi maganin wanda ya ci amana. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Cin amana kan jawo wulaƙanci.
    • Zafin nema ba shi ke kawo samu ba.
    • Idan Allah ya nufi mutum da arziki ba wanda ya isa ya hana.
    • Alhaki kare ne, mai shi yake bi.
    • Abin da ka shuka, shi za ka girba.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Ya Tsinci Dami A Kala

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Ɗan Agwai Da Kura

    Tatsuniyar Ɗan Agwai Da Kura

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani Ɗan Agwai yana kiwon ɗan akuyarsa, har ya girma ya yi ƙiba. Sai wata rana ya kama shi ya kai shi kasuwa. Namun daji da yawa suka yi ta taya ɗan akuyar, to amma da zarar sun ji tarihinsa, sai su wuce, su ƙi saye. Ana nan, ana nan, har labari ya kai ga kunnuwan Kura, uwar son na banza.

    Sai ta shirya, ta je a yi cinikin ɗan akuya da ita. Kura ta ga ɗan akuya ya yi ƙiba, kuma tana so. Sai ta tambaya: “Nawa kuɗin ɗan akuyan nan?” Sai Ɗan Agwai ya ce wa Kura: “Ni fa kokawa ce za ki yi da ni ta kwana bakwai a jere. Idan kullum kina ka da ni har kwana bakwai ɗin a jere, to ɗan akuya zai zama naki.

    Idan kuma kin kasa, to mun dinga yin kokawar ke nan har sai ranar da kika sami nasara.” Sai Kura ta ce: “To na yarda.” Aka tara ’yan kallo, aka ce da su Kura za ta sayi ɗan akuyar Ɗan Agwai. Kowa ya share wuri ya zauna don kallon ciniki. Can sai Kura ta shirya, ta fito fage suka kama kokawa da Ɗan Agwai.

    Kura ta ka da Ɗan Agwai; ta rinƙa cin nasara har tsawon kwana shida. A kwana na bakwai sai Ɗan Agwai ya ka da Kura, ya yi mata shegen duka, har ta kasa tashi. Da ta murmure, da ƙyar ta kai gida. Sai ta ce: “Yau ban fita da sa’a ba.” Washe-gari ta fita, Ɗan Agwai ya sake tiƙa ta da ƙasa, har ta suma.

    Da ta samu aka kai ta gida, washe-gari sai ta ce da ’ya’yanta su ɓoye ta a cikin rumbu, kuma idan an zo neman ta, su ce ta yi tafiya. Da Ɗan Agwai ya yi jira a fagen kokawa, shiru bai ga Kurar ba kuma babu labarinta, sai ya je gidanta, ya yi sallama, amma sai ’ya’yanta suka ce mahaifiyarsu ta yi tafiya.

    Sai Ɗan Agwai ya ce: “To, amma bari in ɗan buɗe rumbun nan, don in ga hatsin da ke ciki.” Kafin yaran su hana, Ɗan Agwai har ya buɗe rumbun, ya leƙa; sai ga Kura a cikin rumbun. Sai ya ciro ta, ya kai ta fagen kokawa. Suka fafata; ya ɗauke ta sama, ya danƙara ta da ƙasa. Daga ƙarshe dai Kura ta koma gida, da rarrafe.

    Da ’ya’yanta suka ga haka, sai suka ce: “Baba, wannan sai fa mun nemi asirin da za ki sha ki sami nasara, in ba haka ba, wannan Ɗan Agwai zai kashe ki.” Washe-gari tun da sassafe suka shirya, suka tafi gidan wani boka neman asirin samun nasara a kan Ɗan Agwai. Da suka isa, suka yi wa boka bayani, sai ya ce: “Babu magani, amma akwai wata dabara ɗaya da zan taimaka muku da ita.”

    Suka yi shiru, suna ji. Sai ya ce: “Akwai wani mutum mai suna Mai-barci-bana ya tashi-baɗi; yana can a ɗakinsa yana barci. Yadda ake ta da shi shi ne, za a samo garwashin wuta a kai ɗakinsa, sai ku je ku ce da Ɗan Agwai: ‘Ga wani zai yi cinikin ɗan akuyarka da kokawa.

    A guje zai yarda zai bi ku; idan kun isa ɗakin mai barcin, sai ku zuba barkono a wuta, ku fita, ku bar su.’” To, da ma duk wanda ya ta da shi daga barci, sai ya kashe shi, muddin ya je kusa da shi. Sai suka je suka shirya yadda boka ya gaya musu. Kuma suka kawo Ɗan Agwai ɗakin Mai-barci-bana ya tashi-baɗi suka kulle su tare.

    Can sai hayaƙin barkono ya tashi. Da Mai-barci-bana ya-tashi baɗi ya ji zafin hayaƙin barkono, sai ya ce: “Wane ne yake damu na?” Yana tashi sai ya ga Ɗan Agwai a kansa. Sai kawai ya kashe shi, ya fito ƙofar ɗaki. Sai ya hango Kura gefe tana jiran ta ga abin da zai faru, ya ce mata ta raka shi farauta, yana jin yunwa.

    Kura ta yarda. Suka kama hanya. Da suka shiga daji, sai suka tarar da mutane masu yawa suna noma a gonar Sarki. Sai ya ce: “Ga nama, amma ba zai ishe ni ba. Amma bari mu ɗan taɓa.” Nan take ya kama mutanen nan ya murɗe wuyan kowannensu. Ya tara itace zai gasa, amma babu wuta. Daga nan ya hura bakinsa, wuta ta fito, suka gasa mutanen nan.

    Ya yi wa Kura tayi, ta ce tun da shi ne babba, ya fara ci. Yana cin naman mutanen nan, har ya ƙare, Kura ba ta ci ba. Bayan ya gama, sai ya sa Kura ta samo masa tsinken sakatar haƙora. Ta samo, ta ba shi. Duk sanda ya sakato nama daga bakinsa, sai Kura ta amsa, ta cinye.

    Da haka har ta ƙoshi. Daga nan Mai-barci-bana ya-tashi-baɗi ya ce, su je rafi shan ruwa. Da suka je, ya nemi Kura ta fara sha, ta ƙi, saboda shi ne babba, gara ya fara sha. Da ya kafa bakinsa, sai ya shanye duk ruwan rafin da ya taru a cikin shekara ashirin. Da ya fara cire haƙorinsa sai Kura ta razana, sai ta faɗi ta suma. Da Mai-barci-bana ya-tashi-baɗi ya ga haka, sai ya sa hannu ya ɗauki Kura, ya kama hanyar ɗakinsa. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Duk inda ka kai ga zalunci sai ka haɗu da wanda ya fi ka zalunci.
    • Wani lokaci dabara ta fi ƙarfi tasiri.
    • Kaddara ta riga fata.
    • Kura da shan bugu, gardi da amsar kuɗi.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsunyar Ɗan Buwaila Da Ɓangorinsa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsunyar Ɗan Buwaila Da Ɓangorinsa

    Tatsunyar Ɗan Buwaila Da Ɓangorinsa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani ƙauye wai shi Wake-Wake, kusa da Dajin Aljanu, inda aka yi wata mata mai ’ya’ya biyu, mace da namiji. Wata rana sai mahara suka kai wa ƙauyen Wake-Wake hari. Maharan kuma suna da yawan gaske kuma sun fi zaratan Wake-Wake yawa da tarin makamai.

    Faɗa ya ƙaure, aka yi musu kaca-kaca, ko’ina sai gawarwakin mutanen Wake-Wake ake gani a yashe. Mata da tsofaffi da ƙananan yara suka ruɗe, hankalinsu ya tashi, gigita ta yawaita. Da uwar yaran nan ta ga maharan sun hallaka jama’ar garin masu yawa, sai ta suri ’yarta domin ta kare ta daga ’yan harin.

    Da namijin ya ga haka sai ya ce: “Iya ni ba za ki kare ni ba? Ni ne fa idan na girma zan kula da gonarki, in gina miki gida kuma in tara miki shanu da sauran dukiya.” Sai uwar ta saki ’yar, ta ɗauki namijin. Da budurwar ta ga haka sai ta ce: “Haba Iya, ki kula da ni domin ni ce mai yi miki wanke-wanke da ɗaukar ruwa da shara, in taya ki girki da dai sauran ayyukan gida.

    Idan ba ki kula da ni ba, mahara suka kashe ni, wa zai taimake ki?” Da mahaifiyarta ta ji haka, sai ta ajiye namijin, ta ɗauki yarinyar suka ɓuya inda mahara ba za su gan su ba. Da namijin ya ga haka, sai ya shige cikin ganyen kabewar da ta yi yaɗo, ya ɓuya, ko motsi ba ya yi.

    Numfashinsa ma ba ya ɗaga cikinsa domin gudun kada a ga alamun mai rai a mafakarsa. Can sai ga maharan sun zo wucewa ta kusa da inda ya ɓuya, sai ɗaya daga cikinsu ya ce da sauran: “Kai baraden fama mu duba cikin ciyawar nan, na ji ƙanshin mutum.”Sai Jarmai, watau jagoransu ya ce: “Kai dai wawa ne, yaya mutum zai ɓuya a nan?

    Mu yi gaba mazajen fama.” Sai maganar Jarmai ta janye hankalinsu, ba su duba ba. Yaro dai ya haye hatsarin shan kaifin barandamin barade. Da yaron nan ya tabbatar maharan sun tafi, sai ya fita daga maɓoyarsa. Yana cikin tafiya sai ya ga bishiyar Buwaila. Sai ya faɗa ta da sara.

    Da sara ya fara ratsa bishiya sai ta ce: “Kai yaro, me za ka yi da ni ne idan ka sare ni?” Ko tsorata bai yi ba, sai ya ce: “Zan ci ne idan na sara, yunwa da ƙishirwa sun dameni.” Da bishiya ta ji haka, sai tausayi ya kama ta ta ce: “Zaga ta hannun dama za ka ga tukwane biyar, ɗaya ta abinci, ɗaya ta ruwan sha, ɗaya ta ruwan wanka, ɗaya ta wurin bayan gida, ɗayar kuma ta wurin barci.”

    Murna ta kama yaro ya ce da bishiya: “To, na gode.” Bayan ya ci ya ƙoshi, ya sha ruwa, ya yi wanka, sai ya zauna ya huta. Bishiya dai ta yaba da hankalinsa har dai suka saba. Yau da gobe dai har mutanen gari suka gane dangantakar yaro da bishiyar, sai suka yi masa laƙabi da Ɗan Buwaila.

    Ana nan, ana nan, sai wata rana bishiyar ta ce da Ɗan Buwaila: “Ya kamata ka mallaki dukiyar kanka saboda halin yau da gobe.” Sai ya ce: “Gaskiyarki, duk abin da kika yi mini na gode.” Can sai wata saniya da ke kiwo ta biyo ta kusa da bishiyar, sai bishiyar ta ce da Ɗan Buwaila, “Bugi cikin saniyar nan ka ga abin mamaki.”

    Da ya bugi cikin saniya sai ga shanu masu yawan da ba zai misaltu ba, garke-garke suna tuɗadowa, sai ta ce: “Duk waɗannan shanu fa naka ne.” Bayan wani lokaci, wasu mutanen garin su Ɗan Buwaila suka fara zunɗe suna cewa: “Ta yaya wannan yaro zai fi Sarki dukiya?” Wasu daga cikinsu suka ce: “A sare bishiyar kowa ma ya huta.”

    Kamar da wasa, sai aka yi gayya, aka sare bishiyar. Ɗan Buwaila ya zamanto maraya ba inda zai je neman shawara. A nan ne fa ya kama kuka. Can sai wata jijiyar bishiyar ta ce da shi: “Daina kuka Ɗan Buwaila, ɗauke ni ka ɗasa.” Da ya ɗasa jijiyar sai ko bishiyar Buwaila ta tsiro ta girma, wanda bai sani ba ma ba zai ce an taɓa sare wata bishiya a wurin ba.

    Da mutanen garin suka ga haka, sai suka sare wannan sabuwar bishiyar, suka shiga gari da ita. Sai wani ɓangore na jikin bishiyar ya ƙubuta ya je ya sami Ɗan Buwaila ya ce da shi: “Yanzu dai mutanen garin nan sun gama da ni, gara ka bar garin nan, in ba haka ba kuwa za su kashe ka.”

    Sai Ɗan Buwaila ya ce: “To.” Sai ɓangorin bishiyar ya ce da shi: “Ka ɗauki wannan ɓangori nawa ka tafi da shi duk inda za ka, kuma ka tafi da shanunka sun ishe ka zaman duniya. Kuma ka buga wannan ɓangorin a tsakiyar shanun, za su cure su zama ɗaya. Idan ka je garin da za ka zauna sai ka bugi saniyar da ɓangorin yawansu zai komo.”

    Shi ke nan, Ɗan Buwaila ya shiga tsakiyar shanu ya yi abin da ɓangorin bishiyar ya umarce shi sai shanun suka ɓata, sai saniya ɗaya tak, ya kama hanya. Yana cikin tafiya da saniyarsa ɗaya, har ya kai wani gari ya yi tambaya, aka nuna masa gidan Sarki, ya kuma isa ya yi gaisuwa a fada, sai ya sanar da Sarki buƙatarsa ta neman izinin zama a garinsa.

    Sarki ya yi murna, ya ce da shi: “Ai mu haka muke so jama’armu ta ƙaru.” Ya sa aka gina wa Dan Buwaila gida. Bayan ’yan kwanaki Ɗan Buwaila ya zama ɗan gari, sai ya bugi saniyar da ɓangoren bishiyar nan, sai yawan shanunsa ya komo. Nan da nan kuwa ’yan tsegumi suka ce da Sarki: “Bai dace a ce wani a garin nan ya fi ka dukiya ba.”

    Hassada da sara da suka da haɗa rigingimu dai suka yi yawa, har ta kai fadawa suka ba Sarki shawarar cewa: “Lallai Sarki ka yi wani abu don a ƙure ƙaryar yaron nan domin ya bar garin nan.” Sai Sarki ya yarda, amma fa ba domin ransa yana so ba. Sai ya ba da irin ƙwarya ya ce: “Ku ba shi a ce ya shuka yau kuma ta fito ta girma, ta yi ’ya’ya, ya fafai, a kawo mini duka a yau.”

    Da Ɗan Buwaila ya gaya wa ɓangorin bishiyar Buwaila sai ya ce da shi: “Ba komai, totse ni a ƙasa.” Da ya totse shi, sai ya ga idanu da baki sun fito masa, sai ya ce: “Idan ka je gaban Sarki ka tambaye shi wai ban da shi akwai wani Sarki a garin nan ne? Idan an ce babu, sai ka ce, to saboda me za a ce a kai wa Sarki mai daraja ruwa a cikin ƙwarya mai ɗaci?”

    Ɗan Buwaila ya je fada, a gaban Sarki ya yi yadda ɓangorin ya gaya masa. Sai Sarki ya ce: “Kana da gaskiya, yi tafiyarka.” Amma duk da haka masu suka ba su daina ba.Sai wasu kuma suka zuga Sarki wai a kai wa Ɗan Buwaila rago a ce ya sa shi ya haihu. Idan ya kasa, an ƙure shi ke nan, daga nan sai a kore shi daga garin.

    Sai Ɗan Buwaila ya gaya wa ɓangorin bishiyar; sai ya ce masa: “Ka je fada gaban Sarki kana kuka. Idan ya ce me ya sa kake kuka, ka ce masa an aiko maka cewa babanka yana naƙuda zai haihu. Idan suka ce ba su taɓa jin namiji da haihuwa ba, sai ka ce da su: ‘Ashe kun san ragon nan ma ba zai haihu ba ke nan.”

    Da safe ya ja rago har ƙofar fada ya ɗaure shi, ya shiga sai gaban Sarki, ya faɗi ya yi gaisuwa, yana kuka. Da Sarki ya ga hawaye a fuskarsa, sai ya ce: “Lafiya Ɗan Buwaila?” Sai ya ce da Sarki: “Ka daɗe mai duniya, adali, an aiko mini ne cewa mahaifina yana can yana naƙuda zai haihu.”

    Da fadawa suka ji haka, musamman ma masu yi masa hassada a gaban Sarki sai suka ce: “Ƙarya yake yi, yaya namiji zai yi naƙuda? Ai maza ba sa haihuwa.” Sarki dai bai ce komai ba, amma sai Ɗan Buwaila ya yi farat ya dubi Sarki yace: “To, Mai martaba sun ce maza ba sa haihuwa, amma an aiko mini rago an ce lallai in sa shi ya haihu.

    Ta yaya zan sa rago ya haihu?” Da Sarki ya ji haka sai ransa ya ɓaci, domin fadawansa sun sa ya yi kuskure. Sai Sarkin ya ce: “To, idan haka ne kuwa ina so wane da wane daga cikin fadawana su bar mini ƙasata. Suna nema su haɗa ni rigima da jama’a.” Nan take aka yi waje da su aka kai su can iyaka da ƙasar Wake-Wake.

    Kan tilas suka bi hanyar shiga Dajin Aljanu da ke kusa da Wake-Wake. Bayan kamar wata biyar da yin haka, sai Ɗan Buwaila ya nemi yardar Sarki domin ya je Wake-Wake ya zo da mahaifiyarsa da ’yar’uwarsa, su zauna tare. Sai Sarki ya ce da shi: “An ba ka izinin, idan ka dawo kuma zan aura maka ɗaya daga cikin ’ya’yana.”

    Sai ya yi godiya, ya koma gidansa, ya shirya, ya kama hanyar garinsu Wake-Wake. Ɗan Buwaila ya je ya kawo mahaifiyarsa da ’yar’uwarsa, Sarki kuma ya cika alƙawarin da ya yi masa na aurar masa da ’yarsa, suka zauna cikin farin ciki da jin daɗi, domin ya zama surukin Sarki, babu wani algungumi da zai sake sukar sa a gare shi. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Haƙƙin iyaye ne su kula da ’ya’yansu maza ne ko mata.
    • Hassada ga mai rabo taki.
    • Mahaƙurci mawadaci.
    • Nuna jarunta da gwagwarmaya don neman kyakkyawar makoma.
    • Rabon kwaɗo ba ya hawa sama.
    • Mai arziki ko a ƙwara ya sayar da ruwa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Darajar Neman Sani

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Darajar Neman Sani

    Tatsuniyar Darajar Neman Sani

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wani mutum mai suna Duna wanda yake zaune da matarsa Delu a wani ɗan ƙauye da ke kusa da garin su Koƙi matar Gizo, sun jima da yin aure ba tare da Delu ta yi ko da ɓatan wata ba. Mijin dai bai damu ba, ita kuma ta dangana komai ga Mai sama.

    Ana nan sai wata rana Delu ta yi ɓatan wata. Ita da mai gidanta Duna suka yi murna. Bayan wata tara kuma ta sauka lafiya, ta haifi ɗa namiji. Bayan sati guda aka raɗa masa suna Maishuni. Da ya ɗan data, sai Duna ya ce da Delu: “Kin ga dai ga shi mu mun rayu cikin duhun jahilci, ya kamata mu tura Maishuni makaranta.”

    Ta ce: “Haka ne, amma fa ina tsoron kada ya galabaita a can.” Mai gidanta ya rarrashe ta, ta fahimci darajar sani, ta yarda a kai yaro wurin neman sani. Bayan mahaifin ya shirya sai ya ɗauki Maishuni suka tafi ya kai shi wani gari a wata tsangaya, ya haɗa shi da wani babban masani; ya kuma shiga cikin ƙolaye.

    Da Duna zai tafi sai ya ce da ɗan: “Ko da bayan na rasu, idan ka dawo gida kana so ka gane mahaifiyarka, sai ka yi cigiya. Duk wadda ta ce ita ce sai ta gaya maka a inda ta haife ka.” Yaro ya yi shiru yana saurare. Da uban ya gama sai ya ce: “To, me za ta faɗa in gane ita ce?” Sai mahaifinsa ya ce: “Idan ta ce a tsakar ɗaki ta haife ka, to ita ce mahaifiyarka.”

    Ya yi ban kwana da Maishuni ya koma garinsu. Uban bai fi wata tara da komawa ba sai ya rasu. Delu ta yi baƙin ciki matuƙa, domin ba ta san garin da mai gidanta ya kai ɗansu karatu ba. Ta cigaba da zama cikin haƙuri. Ana nan bayan kamar shekara ashirin da bakwai, sai Maishuni wanda tuni ya zama babban malami, kuma mai dukiya, ya ji yana son zuwa ganin mahaifarsa.

    Amma fa bai san sunan garinsu ba. Ya yi ta bincike, har a ƙarshe ya sami waɗanda suka yi masa kwatancen garin. Bayan ya shirya sosai, sai ya kama hanyar garinsu. Da ya shiga garin sai ya kama wannan waƙa ta cigiyar mahaifiyarsa: “Wace ce mahaifiyata? Wace cemahaifiyata?”

    Sai wata mata wadda ba ta wuce sa’arsa ba ta ce: “Ni ce mahaifiyarka, Samari ai ni ce mahaifiyarka.” Da ya dube ta sai shakka ta kama shi. Da gani ya san ba ta yi shekarun da za a ce ta haifi kamarsa ba, amma dai saboda halaye irin na masu sani da kuma bin umarnin mahaifinsa sai ya ce: “A ina kika haife ni? Faɗi inda kika haife ni.”

    To da yake ta ga alamun sukuni tare da Maishuni, sai ta ƙirƙiro zancen da take ganin ya dace da matsayinsa ta ce: “A kan gadon ƙarfe, A kan gadon ƙarfe.” Sai da ya bari ta gama hauragiyarta, sai kawai ya mayar mata da wannan jawabi inda ya ce:“Ba ke ce mahaifiyata ba, Ba ke ce mahaifiyata ba.”

    Sai ya kama hanya tare da masu raka shi, suna ta tafiya dai a cikin gari. Da suka kai tsakiyar gari sai ya fara rera waƙarsa. Mata suka fito, wata ta ce a kan gado, wata kuma ta ce kan tabarma, wata ma cewa ta yi a kan gadon zinariya. Haka dai, ba wadda ta faɗi gaskiyar magana.

    Har sai da shi da abokan tafiyarsa suka fara gajiya, sai can ya ga wata mata a zaune ta kasa rogo. Da gani ka san ta jigata, ko da yake ba ta karaya da rayuwa ba sai ya dube ta ya ce: “Wace ce mahaifiyata?, Wace cemahaifiyata?” Wannan waƙar ta sa Delu yin murmushi da tunanin baya.

    Ta so ta gane muryar Maishuni, to amma sai ta yi shakka irin ta natsuwa, sai kawai ta mayar masa da waƙa: “Ni ce mahaifiyarka, Ni ce mahaifiyarka.” Sai Maishuni ya ji kamar ya gamsu da maganarta, saboda muryarta ta yi kama da wata murya da ke tsakiyar birnin zuciyarsa, sai ya ce: “Ina kika haife ni?, Ina kika haife ni?”

    Wannan tambayar da ya yi ta sa ta tunanin cewa lallai ga alama Maishuni ne Allah ya dawo mata da shi gida. Ga bayanin da ta yi: “Na haife ka a tsakar ɗaki, Nahaife ka a tsakar ɗaki.” Da jin jawabin da ta mayar masa, sai farin ciki ya cika masa zuciya. Nan take idanunsa suka cika da ƙwalla, amma ya yi ta maza ya kanne.

    Ya je gabanta ya durƙusa, ya gaishe ta yana mai cewa: “Lallai ke ce mahaifiyata, Lallai ke ce mahaifiyata.” Ta tashi suka shiga cikin gida. Bayan shi da abokan tafiyarsa sun huta, sai ta shiga ba shi labarin rayuwarta da rasuwar mahaifinsa da yadda jikinta yake gaya mata cewa za su gana.

    Shi kuma ya ba ta labarin baiwar da ya samu daga Allah, ta ilimi da dukiya mai amfani, kuma ga shi tana da rai za ta more shi. Suka yi koke-koke na jin daɗi. Bayan Maishuni ya huta, sai ya nemi izinin mahaifiyarsa a kan ya gina mata kataferen gida. Aka gina ya kawo kuɗi ya cika mata tukwane da wani ɗan ƙaramin rumbu.

    Kafin ya koma kwaso iyalinsa kuma, ya yi magana da dattijan gari da sauran shugabanni don a nuna inda za a gina makaranta. Ya kawo kuɗin aikin kuma ya bayar. Bayan ’yan kwanaki ya koma garin da ya yi karatu da nufin ya kawo iyalinsa mahaifarsa. Aka gama ginin makaranta, shi kuma ya kwaso iyalinsa da dukiyarsa ya dawo garinsu ya zauna shi ne babban malami a garin inda ake zuwa ɗaukan karatu daga ko’ina a wannan yanki nasu. Kurunkus.

    Abubuwan DaLabarin Yake Koyarwa 

    • Ilimi shi ne gishirin rayuwar duniya. Ilimi shi ne tushen duk wani alheri da ake samu.
    • Maƙurci, mawadaci.
    • Ƙaddara ta riga fata.
    • Arziki a ƙasa yake, tako shi ake.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Ladi Da Dodo

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Ladi Da Dodo

    Tatsuniyar Ladi Da Dodo

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wata yarinya kyakkyawa tana tare da iyayenta waɗanda suke maƙwabtaka da surukan Gizo a wani ƙauye wai shi Yana. Sunan yarinyar Ladi. Wata rana sai ƙawayenta suka biya mata domin su tafi bayan gari cin kaɗanya. Da yayyenta suka ji inda za su, sai suka ce kada ta je saboda akwai wani mugun Dodo da yake kashe mazauna Yana in sun fita bayan gari.

    Ladi ta ƙeƙasa ƙasa, ta kafe ita sai ta je. Sai ta sha ɗamara, ta ɗauki sanhon zuba kaɗanya, ta bi ƙawayenta, suka fita bayan gari. Ba su tsaya ba sai gindin wata babbar kaɗanya da ta yi ’ya’ya birjik, abin ban sha’awa da sa marmari. Sai ɗaya daga cikin ’yan matan nan ta ce: “Kowacce ta hau kaɗanya ta ɗebi rabonta.”

    Kowacce ta hau, suna cikin kaɗar kaɗanya, sai Dodon nan ya zo gindin bishiyar ya tsuguna, ya ce: “Ku ’yan mata, ku sauko in cinye ku.” Sai ko suka fashe da kuka saboda tsoro, idanu suka raina fata, ciki ya ɗuri ruwa, kowacce sai kyarma take yi, duk sun ɗimauta. Can sai wata mai wayo daga cikinsu ta kama waƙa tana cewa:

    “Dodo, Dodo,

    ba ni ce Ladi ba,

    Ladi fara ce, kyakkyawa,

    In ta yi dariya, nono ne ke zuba,

    In ta yi murmushi, madara ce ke zuba.”

    Da Dodon ya ji wannan waƙa, sai ya yi wani irin gunji, ya yi miƙa da gyatsa ya ce: “Sauko ’yata ba da ke nake ba, Da Ladi nake, Zan kakkarya ta, In sha madararta da ke zuba.” Da ƙawayen Ladi suka ga yadda ɗayarsu ta ceci kanta daga sharrin Dodo da wannan waƙa, sai wata daban kuma ta ɗauka:

    “Dodo, Dodo, ba ni ce Ladi ba,

    Ladi fara ce, kyakkyawa.

    In ta yi dariya, nono ne ke zuba,

    In ta yi murmushi, madara ce ke zuba.”

    Da ya ji wannan waƙar ma, sai ya mayar mata da cewa:“Sauko ’yata ba da ke nake ba, Da Ladi nake, Zan kakkarya ta, In sha madararta da ke zuba.” Sai ta sauko, ita ma ta kama hanya, ta gudu gida. Da haka da haka duk ’yan matan nan suka sauko, saura Ladi ita kaɗai ta rage a kan kaɗanya, ƙasa kuma ga Dodo yana jira ta sauko ya halaka ta.

    Kamar dai dabara za ta ɓace mata, amma dai ita ma ta kama waƙa irin wadda sauran suka rera: “Dodo, Dodo, ba ni ce Ladi ba, Ladi fara ce, kyakkyawa, In ta yi dariya, nono ne yake zuba. In ta yi murmushi, madara ce ke zuba.” Sai Dodo ya ce: “Na ji ba ke ce Ladi ba, amma sauko in cinye ki, yunwa nake ji.”

    Da Ladi ta ji lafazin Dodon, sai ta fashe da kuka. Tana cikin kuka sai wani tsuntsu ya sauka a kan kaɗanyar kusa da ita ya ce: “Me ya sa kike kuka?” Sai ta ba shi labarin yadda ƙawayenta suka yi suka gudu, amma Dodo ya ce sai ya cinye ta. Da tsuntsu ya ji halin da Ladi take ciki sai ya ce: “To, ina dabara?”

    Sai Ladi ta yi masa kwatancen gidansu domin ya je ya gaya wa mahaifanta. Tsuntsu ko ya je ya gaya musu. Iyayen ko ba su ɓata lokaci ba, suka yi gayyar jama’a don a je a ceto ta. Da yake suna da farin jini a garin, nan da nan majiya ƙarfi suka ɗebo makamansu, aka zo inda Dodo yake aka yi sukuwar salla a kansa aka yi kaca-kaca da shi.

    Ladi ta sauko, sai gida tare da jama’ar gari. Daga wannan rana Ladi ta daina zuwa ko da ƙofar gida, sai da yardar iyayenta ko yayyenta. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Rashin bin maganar magabata yana sa a faɗa cikin hatsari.
    • Zaman lafiya da jama’a yana kawo samun taimakon gaggawa a lokacin da buƙatar hakan ta taso.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Talume

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Talume

    Tatsuniyar Talume

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana wata yarinya wai ita Talume sun je daji cin ɓaure ita da kawayenta da sauran ’yan matan garinsu, tare kuma da yayyensu mata. Bayan sun gama shan ɓaure, sai yayyen yaran nan suka ce da su: “Kowacce ta share hannunta, ta goge bakinta, kuma kada a ce za a ɓoye a kai gida.”

    Ashe Talume ta ɓoye wani ɓauren domin ta kai wa mahaifiyarta, ga kuma danƙonsa da ta bari a hannunta ba ta share ba domin ta riƙa lasa a hanya. Suna cikin tafiya sai ta riƙa tanɗar hannunta, tana jin zaƙin ɓaure, har suka isa gida. Da ta kawo ɓauren ta ba mahaifiyarta, sai ta tambaye ta da cewa:

    “Kai wannan ɓaure da zaƙi yake, a ina kika samo shi?” Sai ta ce da ita: “Ni da su yaya muka samo shi a daji.” Ana nan, ana nan, rannan Talume da ƙawayenta sun shirya za su je biki, sai ta roƙi mahaifiyarta ta ba ta aron zannuwanta ta ɗaura. Da uwar ta ji haka, sai ta ce mata: “Zan ba ki, to amma sai kin kawo mini irin ɓauren nan na kwanakin baya.”

    Sai Talume ta ce: “To bari in je daji ko zan samo shi.” Ta kama hanya tana tafiya har ta kai gindin ɓaure, ta rasa yadda za ta yi. Sai ta kama waƙa, tana yi ɓaure yana mayar mata suna cewa:

    Talume: “ɓaure, ɓaure ka ba ni ɓaure.”

    Baure: “Yarinya, in ba ki Baure? In ba ki Baure ki kai wa wa?”

    Talume: “In kai wa babata.”

    Baure: “Ta ba ki me?”

    Talume: “Ta ba ni kaya.”

    Baure: “Ki je ina?”

    Talume: “In je biki, ’Yan mata duk sun tafi, Samari duk sun tafi.”

    Sai Baure ya ce mata ta iya waƙa, kuma ta je ta nemo kashin shanu ta kawo masa kafin ya ba ta ’ya’yansa. Ta kama hanya ta sami shanu suna kiwo. Kamar yadda suka yi da ɓaure, ga waƙar da ta fara suka amsa mata:

    Talume: “Shanu, shanu ku ba ni kashi.”

    Shanu: “Mu ba ki kashi, ki kai ina?”

    Talume: “In kai wa ɓaure.”

    Shanu: “Ki kai wa Baure ya ba ki me?”

    Talume: “Ya ba ni ’ya’ya.”

    Shanu: “Ya ba ki ’ya’ya ki kai ina?”

    Talume: “In kai wa babata.”

    Shanu: “Ki kai wa inna ta ba ki me?”

    Talume: “Ta ba ni kaya.”

    Shanu: “Ta ba ni kaya, ki je ina?”

    Talume: “Ta ba ni kaya in je biki, ’Yan mata duk sun tafi, Samari duk sun tafi.”

    Sai ɗaya daga cikin shanun ta ce: “Ki je ki kawo mana ciyawa mu ci, sai mu yi kashi ki kwasa.” Sai ta ce: “To.” Ta doshi inda ciyawa ta fito ta yi lif-lif, koriya shar gwanin ban sha’awa ta ce:

    “Ciyawa, Ciyawa ki ba ni ciyawa.”

    Ciyawa: “In ba ki ciyawa ki kai ina?”

    Talume: “In kai wa shanu.”

    Ciyawa: “Ki kai wa shanu su ba ki me?”

    Talume: “Su ba ni kashi.”

    Ciyawa: “Ki kai wa wa?”

    Talume: “In kai wa Baure.”

    Ciyawa: “Ki kai wa Baure ya ba ki me?”

    Talume: “Ya ba ni ’ya’ya.”

    Ciyawa: “Ya ba ki ’ya’ya ki kai wa wa?”

    Talume: “In kai wa babata.”

    Ciyawa: “Ta ba ki me?”

    Talume: “Ta ba ni kaya in je biki, ’Yan mata duk sun tafi, Samari duk sun tafi.”

    Sai Ciyawa ta ce: “Hanzarta ki ɗebo ruwa ki kawo. Ki zuba mini, in ya so ki yanke ni ki kai wa shanun.” Yarinya ta ce: “To, ciyawa, na gode.” Da ta isa bakin wani babban gulbi mai ruwa garai-garai, sai ta ce: “

    Gulbi, Gulbi, ka ba ni ruwa.”

    Gulbi: “In ba ki ruwa ki kai wa wa?”

    Talume: “Ka ba ni ruwa in kai wa ciyawa.”

    Gulbi: “Ta ba ki me?”

    Talume: “Ta ba ni ciyawa.”

    Gulbi: “Ki kai wa wa?”

    Talume: “In kai wa shanu.”

    Gulbi: “Su ba ki me?”

    Talume: “Su ba ni kashi.”

    Gulbi: “Ki kai wa wa?”

    Talume: “In kai wa Baure.”

    Gulbi: “Ya ba ki me?”

    Talume: “Ya ba ni ’ya’ya.”

    Gulbi: “Ki kai wa wa?”

    Talume: “In kai wa babata.”

    Gulbi: “Ta ba ki me?”

    Talume: “Ta ba ni kaya.”

    Gulbi: “Ki je ina?”

    Talume: “In je biki, ’Yan mata duk sun tafi, Samari duk sun tafi.”

    Sai Gulbi ya ce: “Kai wannan yarinya da ƙoƙari kike, zo ki ɗebi ruwan da zai kashe wa Ciyawa ƙishirwarta domin ta yarda ki yanke ta.” Yarinyar ta ɗebi ruwa mai yawa salka-salka ta je ta zuba wa Ciyawa. Ciyawa ta ƙara kyau, abin sai wanda ya gani, sai ta ce da Talume:

    “Yanki yadda za ta ƙosar da shanun nan domin su yi kashi da yawa.” Sai ta yanka ta kai wa shanu, suka ci suka yi kashi mai yawa, kuma subul-subul mai kyau. Nan da nan Talume ta lafci kashin nan ta kai wa ɓaure ya yi murna da wannan kashin shanu da bai taɓa cin mai daɗi irinsa ba.

    Sai shi kuma ya zubo mata da ’ya’ya masu yawa, waɗanda suka nuna lugub ta ɗiba ta kai wa mahaifiyarta,ita kuma ta yi godiya, ta kawo kayan da ta nema ta ba ta. Talume ta sa kaya, ta je wurin biki ta tarar an gama biki, amma Kuraye suna yin nasu. Da Kurayen nan suka ga Talume, sai suka yi kanta za su cinye ta, sai ta gudu, suka bi ta, har gida.

    A gidansu kuma, sai ta tarar an rufe ƙofar kowane ɗaki. Sai ta doshi ƙofar ɗakin mahaifiyarta ta ce: “Iya buɗe mini ɗaki.” Sai mahaifiyarta ta ce: “Abin da ya biyo ki, ya cinye ki.” Haka ta yi ta bi ɗaki-ɗaki, ba wanda ya buɗe mata. Amma da ta je ɗakin kakarta ta buga, sai ta buɗe mata.

    Da Kuraye suka ga Talume ta shiga ɗaki, sai suka haƙura saboda tsoron ko tarko aka yi musu suka gudu, ita kuma ta tsira. Washe-gari bayan kowa ya tafi gona sai Talume ta tattara kayanta, ta bar garinsu; ta je wani gari ta sami miji ta yi aure, ta ƙi zuwa ko da ganin gida shekara da shekaru. Mahaifanta sun so ganin ta, amma ta ƙi zuwa gida.

    Ana nan sai mahaifan Talume suka ji labarin garin da ta yi aure, sai mahaifinta ya ce a je a gaya mata mahaifiyarta ta rasu. Aka kuwa same ta, aka gaya mata, amma ta ƙi zuwa. Bayan wasu watanni kuma ya ce a je a ce mata mahaifinta ya rasu. Aka je, aka gaya mata, amma ta ƙi zuwa.

    Daga ƙarshe dai sai aka tashi wani tsuntsu Goraje aka aike shi don ya gaya mata yayyenta da ƙannenta duk sun mutu. Goraje ya tashi fir, bai tsaya ba sai a ƙofar ɗakinta ya ce:

    Goraje: “Salamu alaikum Talume.”

    Talume: “Wa alekumus-salam Goraje.”

    Goraje: “Mahaifiyarki ta mutu Talume. Bariki ba gida ba.”

    Talume: “Bariki ba gida ba, Goraje, Uwata ƙi ni, Goraje, Baba ya ƙi ni, Goraje, Yaya ta ƙi ni, Goraje, Kaka ta so ni, Bariki ba gida ba, Goraje, Ku je ku binne, Goraje.”

    Sai tsuntsun ya koma ya shaida wa waɗanda suka aike shi, cewa Talume ta ƙi zuwa. Can sai wani maƙwabcin babanta da ya san tarihin abin da ya faru ranar da Kuraye suka bi ta za su kashe ta ya ce: “Idan kuna so ta zo, ku aika mata cewa kakarta ta rasu.” Jin haka ke da wuya sai aka sa tsuntsu Goraje ya je ya gaya mata kakarta ta rasu, ana can za a rufe ta.

    Sai ta ce da tsuntsu: “Ga ni nan, kada a rufe ta sai na gan ta.” Talume ta shirya kayanta ta je garinsu, ta isa har gida. Sai ta tarar duk mutanen gidan ba wanda ya mutu, amma duk sun tafi gonakinsu aiki, in ban da kakar nan tata. Ta gayar da ita, suka yi hira. Jim kaɗan ta ce za ta komagarin mijinta.

    Sai kakar ta ce da ita: “Kina da gaskiya, kama hanya, aure ba abin wasa ba ne.” Talume ta shirya ta ɗauki kayanta, ta kama hanya. Da iyayenta da yayyenta da ƙannenta suka dawo suka ji ta zo, amma ta ƙi jiran su, sai suka ce: “Kai wani hali sai su Talume.” Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Wanda bai ji bari ba ya ji hoho.
    • Shan wahala a rayuwa ba ya hana a ƙarshe a sami kyautatawar hali.
    • Motsi ya fi zama
    • Mai nema yana tare da samu
    • Mahaƙurci, mawadaci.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Sarki, Gizo Da Kwarkwata

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Sarki, Gizo Da Kwarkwata

    Tatsuniyar Sarki, Gizo Da Kwarkwata

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana a can kusa da garin da Gizo ke sarauta, wani tsoho yana cikin gonarsa yana kashe kwarkwata, sai ya ga wata ƙatuwar kwarkwata, har ya haɗa manyan yatsunsa zai murtsuke ta, sai ta ce da shi: “Kada ka kashe ni, zan yi maka tsaro a gonarka, kada ka kashe ni.”

    Sai ya tambaye ta: “Idan na bar ki, me za ki yi mini?” Sai Kwarkwata ta ce: “Kai dai ka sake ni a cikin gonarka ka gani.” Mamaki ya kamaTsoho, sai ya sake ta a cikin gonarsa. Ya yi kamar ya tafi gida, amma sai ya sami wuri ya ɓuya. Yana maƙe, sai ga wasu fadawan Sarki Gizo sun zo gonar sata.

    Da suka je za su yanki harawar wake sai Kwarkwata ta fara waƙa tana cewa:

    “Caca bille, caca bille,

    Burabusko bille,

    Fadawan Sarki Gizo,

    Sun zo satar harawar wake,

    Su kai wa dokin Sarki.”

    Waƙar Kwarkwata da ta ratsa fadawan Sarki sai suka fara rawa. Da Sarki Gizo ya ga shiru, sai ya tura dogarawansa, watau su Kiyashi da Kyankyaso da Fara su kamo fadawan da ya tura don su yanko harawar wake. Dogarawa na zuwa suka ce da fadawa: “Yaya Sarki ya tura ku ciyawa kuka yi zamanku?

    To, an ce mu kama ku.” Sai fadawan nan suka ce da dogaran Sarki: “Ku taɓa waken ku ma ku gani.” Da dogaran suka taɓa waken kamar za su yanki harawar, sai Kwarkwata ta shiga abin da ta saba:

    “Caca bille, Caca bille,

    Burabusko bille,

    Fadawa sun zo,

    Dogarawa sun zo,

    Satar harawar wake,

    Su kai wa dawakin Sarki.”

    Su ma dogarawa suka kama rawa. Ba damar komawa fada, balle Sarki Gizo ya san me ake ciki. Da daɗewar ta yi yawa, sai Sarki Gizo ya taso baradensa, wato manyan mayaƙansa, irin su Kudan zuma da Kunama da Sari-kutuf da Macizai da Rina da Kwarkwasa domin su kamo masa fadawa da dogarawa saboda sun yi wa Sarki ƙyuya.

    Suna isa suka fara daka wa fadawa da dogarawa tsawa, suna cewa: “Sarki ya aiko ku yankan harawar dawakinsa, ba ku koma ba. Kun raina Sarki ke nan ko?” Fadawa da dogarawa ba su tsaya wani wuni-wuni ba, suka ce da sojojin nan: “Ku taɓa waken nan kamar za ku yanki harawar ku ga abin da zai faru.”

    Sai suka taɓa; sai Kwarkwata ta rera waƙarta:

    “Caca bille, Caca bille,

    Burabusko bille,

    Fadawa sun zo,

    Dogarawa sun zo,

    Sojoji sun zo,

    Garin satar harawar wake,

    Su kai wa dawakin Sarki.”

    Sai su ma suka kama rawa. Da Sarki ya ji shiru, sai ya je gonar shi da kansa a fusace. Yana isa sai ya ga baradensa da dogarawansa da fadawansa suna ta dirkar rawa ba ƙaƙƙautawa a wannan gonar. Sai ya faɗa su da faɗa. Da suka ga ran Sarki Gizo ya ɓaci, sai wasu daga cikinsu suka ce: “Ranka ya daɗe, taɓa waken nan kamar za ka yanki harawar ka gani.”

    Gaya wa Sarki haka ke da wuya, sai ya ƙara harzuƙa, sai ya ce: “Zan sa a fille muku kawuna.” Baki ɗayansu sai suka ce: “Don girman ikon da ke hannunka ka taɓa waken ka ga abin damaki.” Sai Sarki ya taɓa wake, hannunsa na sauka a kan waken nan sai Kwarkwata ta shiga aikinta:

    “Caca bille, Caca bille,

    Burabusko bille,

    Fadawa sun zo,

    Dogarawa sun zo,

    Barade sun zo,

    Sarki ya zo satar wake,

    Ya kai wa dawakinsa.”

    To, Sarki Gizo bai yi rawar ba, saboda shirinsa ya fi na Kwarkwatar. Wato hatsabibancin Sarki ya fi na Kwarkwata ƙarfi. Sai ya ce da fadawansa: “Kai wannan gonar ta wace ce?” Tsoho da ke maƙe bai mabari fadawa sun yi wa Sarki jawabi ba sai furut ya fito ya faɗi a gaban Gizo ya ce: “Mai duniya ka daɗe, ni ne mai gonar nan.”

    Sai Sarki Gizo ya ce: “Wane aiki ka yi wa gonarka take yin haka?” Sai Tsohon nan ya ba Sarki labarin yadda suka yi da Kwarkwata. Sai Sarki Gizo ya ce: “Tana ina?” Nan da nan ya ɗauko ta ya je gaban Sarki ya miƙa masa ita. Sai Sarki ya ce da Tsoho yana son ya bar masa Kwarkwatar nan, kuma ya sa ta saki fadawansa da dogarawansa da baradensa da ta sa su rawa.

    Da ya roƙe ta sai ta sake su, suka daina rawar, kuma ya mallaka wa Sarki Kwarkwata. Sarki Gizo saboda jin daɗi ya kawo kuɗi masu yawa ya ba Tsoho, shi kuma ya tafi fada da wannan Kwarkwatar. Duk sanda yake cikin nishaɗi sai ya sa ta zo ta rera masa waƙoki iri daban-daban.

    Duk sanda yake cikin raha kuma sai ya tsokani dogarawansa da fadawansa da sojojinsa ya ce: “Na gaban Sarki waɗanda Kwarkwata ta ci ku da yaƙi.” Sai duk a fashe da dariya. Haka dai Sarki Gizo ya ci gaba da tafiyar da mulkinsa tare da fadawansa da dogarawansa cikin jin daɗi. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Tausaya wa halittar Ubangiji yakan yi sanadin samun nasara.
    • Adalci shi ne sinadarin samun nasarar kowane shugabanci; azzalumin shugaba kuma ƙarshensa nadama.
    • Kula da kaya, ya fi ban cigiya.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Kogi Mai Cinye Maƙaryata

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kogi Mai Cinye Maƙaryata

    Tatsuniyar Kogi Mai Cinye Maƙaryata

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum da ’ya’yansa su goma sha biyu. Wata rana sai ya samo ’ya’yan kaɗanya ya kai gidansa. Da ɗaya daga cikin ’ya’yansa ya ga kaɗanya nunanniya, sai ya ɗauka ya shanye. Mahaifinsu ya tambaye su wanda ya shanye masa kaɗanya, kowanne daga cikinsu ya ce ba shi ba ne.

    Ya sake tambayar su, kowa ya ce ba shi ba ne. Suka yi ta yin haka, shi kuma wanda ya shanye kaɗanya bai bayyana kansa ba. Can dai sai mahaifin nasu ya ce da su: “To, tun da kun kasa fitar da wanda ya shanye kaɗanyar nan, za mu je da ku kogin da ke cinye maƙaryata.

    Duk wanda ya shanye mini kaɗanya, to ko ruwa zai cinye shi.” Mahaifinsu ya shige gaba, suka bi shi duu, ba su tsaya ba sai a bakin kogin da kowa ya san yakan cinye marasa gaskiya. Zuwansu ke da wuya, sai babban cikinsu ya shiga kogi, ya fara wannan waƙa:

    “Kogi, kogi maganin maƙaryata,

    In ni ne na shanye kaɗanyar baba,

    Alkawari mai dare da rana,

    Cinye ni kogi,

    Tafi da ni kogi.”

    Da ya gama waƙar sai ya tsunduma cikin kogi, ya haye ɗaya gaɓar lafiya ya tsaya. Sai mai bi masa shi ma ya yi waƙa, ya faɗa kogin nan ruwan bai cinye shi ba. Haka dai suka yi ta shiga. Goma sha ɗaya suka haye ruwanlafiya. Da na ƙarshe ya zo ya shiga, sai shi ma ya sa waƙa:

    “Kogi, kogi maganin maƙaryata,

    In ni ne na shanye kaɗanyar baba,

    Alkawari mai dare da rana,

    Cinye ni, Cinye ni kogi, Janye ni kogi.”

    Tun bai gama waƙar ba ruwan kogin ya fara shan kansa. Kafin ’yan’uwan su farga, kogi ya fara janye shi. Sai ya fashe da kukan baƙin ciki da nadama; ’yan’uwan su ma suka fashe da kukan rashin ɗan’uwansu. Shi yana kuka, su ma suna yi, har ya nutse a ruwan nan, suka daina ganinsa.

    Da suka koma gida sai babansu ya ce da su: “To kun ga sakamakon taɓa kayan wani ba da yardarsa ba ko?” Suka ce: “Mun gani Baba, daga yau ba za mu sake taɓa kayanka ba sai ka ba mu.” Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Yin cikakken bincike yayin da za a yi wani hukunci yana haifar da sakamako mai kyau.
    • Kwaɗayai mabuɗin wahala
    • Son zuciya ɓacin zuciya.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Kurege Da Biri

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kurege Da Biri

    Tatsuniyar Kurege Da Biri

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Kurege da Biri suka ga wata yarinya, kowannensu ya nuna yana son ta da aure. Sai kowannensu ya aika a tambayo masa izinin nemanta da aure. Iyayen yarinya suka ce duk wanda yake son ‘yarsu da aure sai ya kawo musu fatun namun daji. Da Kurege ya ji haka, sai ya je wurin Kaza ya ce da ita: “Ina gayyatar ki aiki a gonata gobe.”

    Kaza na jin haka ta ce: “To, zan zo amma fa kada ka gaya wa Kyanwa.” Sai ya ce: “Haba me zai sa in gaya mata kuwa?” Daga gidan Kaza Kurege bai zame ko’ina ba sai gidan Mage, ya ce da ita: “Ina son za ki taya ni aiki a gona gobe.” Mage na ji sai ta yi farat ta ce: “To, amma fa kada ka gaya wa Kare, ka san idan ya gan ni a wurin zai cinye ni.”

    Kurege ya ce da ita: “Haba, ai na san haka, wa zai gayyaci wannan a gonarsa?” Yana fita sai ya nufi gidan Kare, ya same shi ya ce da shi: “Ina so ka taya ni aiki a gona gobe.” Da gari ya waye, tun da sassafe Kurege da Kaza suka isa gona, suna cikin aiki sai ga Mage. Sai Kurege ya ce da Kaza: “Maza ki ɓuya a cikin ciyawa.”

    Da Magenta isa kusa da Kurege sai ta ce: “Na ji kana magana kai da wane ne?” Sai Kurege ya ce: “Ni da Kaza ne, ga ta can a cikin ciyawa. Idan kin cinye namanta, ni ne da fata.” Nan da nan Kyanwa ta gano inda Kaza ta ɓuya. Tana ganin ta sai ta auka mata, ta murƙushe ta, ta kashe, ta cinye nama, ta ce da Kurege: “Ga fatar da ka ce kana so.”

    Kurege da Mage suka ci gaba da aiki a gona. Jim kaɗan sai ga Kare, ya zo yana haki bayan ya yi gudun ceton rai, saboda yara sun bi shi za su kashe a hanya. Bayan Kurege ya yi wa Kare barka da zuwa, sai Kare ya ce: “Kurege kai da wane ne a gonar nan?” Sai Kurege ya matsa kusa da shi ya kashe murya ya ce: “Ni da Mage ne, tana can tana aiki.

    Idan ka kashe ta, ka cinye naman, ka bar mini fatarta.” Kare ya yi godiya ya je ya shammaci Kyanwa ya turmushe ta, ya shaƙe wuyanta. Da ta mutu ya cinye naman, ya bar wa Kurege fatar. Sai Kare ya dubi Kurege ya ce da shi: “To amma fa ka san idan ka gaya wa Kura ba zan zo ba.” Kurege ya ce da shi, “Wa zai gaya wa Kura?

    Me za a yi da wannan sarauniyar kwaɗayi?” Da Kurege ya fita bai tsaya ba sai a ƙofar ramin Kura. Bayan sun gaisa sai ya ce da ita: “Na zo gayyatar ki aiki ne a gonata gobe da safe.” Yana rufe baki sai Kura ta ce: “Kai ni gobe ba zan sami dama ba, zan je cin wani mushe da na gani jiya.”

    Da Kurege ya ji haka sai ya ce da Kura: “Haba Kura, idan aka yi aikin gonata ba ki je ba, ai za a ce ni da ke mun ɓata. Kin san ke ce babbar ƙawata. Ki tuna fa mun sha yin abubuwa da yawa tare.” Wannan maganata Kurege ta yi wa Kura daɗi, sai ta dube shi ta ce: “To zan zo, amma fa kada ka gaya wa Damisa, ka san ta da nuna fin ƙarfi.”

    Sai Kurege ya ce da Kura: “Me ya gama ni da Damisa kuma? Ban san inda take ba ma yanzu.” Da Kurege ya fita sai ya nufi dutsen da Damisa take tare da ‘ya’yanta. Bayan ya gayar da ita, sai ya ce mata: “Ranƙi ya daɗe, ina roƙon ki zo aiki a gonata gobe da safe, idan da hali. Kin san ku manya sai kun sami hali.”

    Sai Damisa ta yi miƙa, ta buɗe bakinta, Kurege ya ga haƙoranta masu kaifi da tsini sai ta ce: “Kai Kurege wa ka gayyata bayan ni?” Sai Kurege ya yi durƙuson ban girma ya ce: “Kura dai tana ciki.” Da Damisa ta ji haka, sai ta ce: “Yawwa, ka kyauta yaron kirki, lallai zan zo.”

    Kare da Kurege suka kama aiki, amma saboda Kare ya ƙoshi da naman Kyanwa sai ya kwanta a gindin wani ƙargo ya fara barci. Can sai ga Kura ta iso ta dubi Kurege ta ce: “Abokina yanzu ba wanda ya zo aikin nan sai ni?” Sai Kurege ya ce: “Ai ke ƙawata ce, kuma kina da kirki, amma Kare ya riga ki zuwa, ga shi can ma yana barci.

    Idan kin cinye shi, ki bar mini fatar.” Da man Kura tana jin yunwa saboda Kurege ya sa ta haƙura da zuwa wurin mushen da ta gaya masa ta gani, sai ta ce: “Amma kuwa na gode.” Sai ta je ta kashe Kare a cikin ruwan sanyi saboda yana barci, ta cinye namansa ƙafaf saboda haɗama har ma ta fara cin fatar Kurege ya je ya fisge.

    Daga nan Kura da Kurege suka kama aiki a gonar. Can sai ga Damisa ta tunkaro gonar. Shi Kurege da ma ya san haka, amma Kura ba ta sani ba. Da ya fara hango Damisa tana zuwa, sai ya ce da Kura: “Babbar ƙawata, ai ya kamata ki ɓuya ina gani kamar za mu yi manyan baƙi.”

    A tsorace Kura ta sami gindin wata kuka ta raɓe. Da Damisa ta isa gonar sai Kurege ya ce: “Kai madalla, sannu da zuwa manyanmu.” Sai ta harare shi ta ce: “Ka ce Kura za ta zo, ko tana ina ne?” Sai Kurege ya nuna mata maɓoyar Kura sai ya ce da ita: “To, amma idan kin kashe ta, ina roƙo ki ba ni fatar.” Ta ce: “To na ji.”

    Damisa na faɗin haka sai ta nufi inda Kura ta ɓuya. Kafin Kura ta san abin da ake ciki, tuni Damisa ta sa haƙoranta masu kaifi da tsini ta tsinke jijiyoyin wuyan Kura ko shurawa ba ta yi ba. Kafin wani lokaci Damisa ta yi kaca-kaca da ita, ta cinye ta. Sai fatar kawai ta bari da ƙoƙon kanta. Da ta gama, sai ta je wurin Kurege ta ce: “Ga fatar can.

    Ka kuma gayyatar wata Kurar aiki a gonarka zan zo.” Kurege yana ƙyarma, ya ce da Damisa: “To, na gode, zan sanar da ke idan za a sake yin irin wannan aiki.” Cikin murna Kurege ya shiga tara fatun nan. A zuci ma ya riƙa cewa: “Yawwa, ni ne zan sami mata. Biri kam sai haƙuri.”

    Da Biri ya ji labarin abin da Kurege ya aikata, kuma ya ji yana cewa shi ne zai auri yarinyar nan sai a zuciyarsa ya ce: “Haba Kurege, za ka ga tsiyata kuwa.” Biri kuwa ya je ya samo gyaɗa mai yawa, ya bi hanyar gidan iyayen yarinyar yana zubarwa, wato inda Kurege zai bi don ya kai musu fatun da suka nema.

    Da Kurege ya kama hanya ya ga gyaɗa a warwatse sai ya fara tsinta yana cewa: “Yau daɗi goma, ga shi na samo fatu zan kai a ba ni mata, kuma ga ƙauyawa sun sayo gyaɗa daga kasuwa sun ajiye mini domin in ci in more.” Kurege na matsawa gaba, gyaɗar tana ƙara yawa, har dai ta kai shi bakin wani ƙasko wanda yake cike da gyaɗa.

    Sai kawai ya tsuguna a kusa da ƙaskon, ya zubar da fatu gefe, ya duƙufa a kan cin gyaɗa. Shi kuma Biri sarkin wayo sai ya bi ta bayan Kurege yana sanɗa, ya kwashe fatun nan Kurege bai sani ba. Biri ya tafi da fatu ya kai wa iyayen yarinyar nan, suka amsa, aka ɗaura masa aure da ita.

    Bayan Kurege ya ci gyaɗa ta yi masa karo, sai ya waiwaya zai ɗauki fatunsa, sai ya ga wayam, ba komai a wurin, sai ya ce: “Na tabbata Biri ne ya yi mini wannan aikin. Amma bari in kai musu ragowar gyaɗar wataƙila su yarda su ɗaura auren da ni.” Kurege na isa iyayen yarinya suka ce ai tuni Biri ya kawo fatu, har ma an ɗaura masa aure da yarinyar.

    Da Kurege ya ji haka, sai ya ba su gyaɗar da ya je da ita, tare da igiyar da ya tanada wai ta ɗaurin aurensa da yarinya, ya ce: “Ga wannan igiya za ta yi muku amfani, gyaɗar kuma ku soya ku ci.” Suka karɓa ya tafi. Kurege bai tsaya ba sai a gidan Biri, sai ya tarar da wani tsohon Biri, watau kawun ango, ya ce da shi: “Ni abokin ango ne.”

    Jin haka sai tsohon Birin ya ƙyale Kurege ya shiga inda ango ke barci. Da shigarsa sai ya sa wa Biri dafi a baki, wanda a ƙarshe ya kasa tashi daga wannan barcin, ya mutu. Sai nan da nan Kurege ya nemo garin dawa a gidan, ya cusa a bakin Biri, don a ce garin ne ya ci ya yi masa karo ya kashe shi.

    Can sai amaryar Biri ta shigo ɗakin ta ce: “Yaya na ga ango yana barci, amma kuma ga shi kamar yana cin wani abu?” Da ta ɗan taɓa shi, sai ta gane dai ya mutu, sai ta fara kuka, shi ma Kurege ya shiga kuka. Da ya yi shiru, sai ya ce da matar Biri: “Akwai wani Dodo a daji, ya kamata mu je ya gaya mana abin da ya kashe miki miji.”

    Da suka shiga dajin nan, sai Kurege ya ce ta jira shi yana zuwa. Nan da nan ya je ya zane jikinsa da gawayi, ya canza kamanninsa ya sha gabanta, ya tsaya kamar shi ne Dodon, sai ya ce: “Ke baƙuwata, ni ne Dodon baƙin daji, me ya kawo ki?” Ita kuma ba ta gane Kurege ba ne sai ta ce da shi: “Mijina ne ya mutu, ina son sanin wanda ya kashe shi.

    Kuma ina son sanin wanda zan aura.” Sai Dodo ya ce: “Ai Kurege abokin Biri ne, kuma ƙanensa ne saboda Biri ya girme shi ko?” Sai matar Biri ta ce: “Ba shakka haka ne, ko shi zan aura?” Sai Dodo ya kaɗa kai domin nuna amincewa. Ta ƙara tambayar sa, har dai ta tambaya sau uku, duk yana nuna cewa ta auri Kurege.

    Daga nan ya sallame ta, ta koma gidan Biri. Shi kuma Kurege ya je wani tafki ya yi wanka ya kama hanyar gidan Biri, ya tafi yana kuka. Da amaryar marigayi Biri ta ga Kurege yana kuka sai ta ce: “Mene ne kuma ya faru?” Sai Kurege ya ce: “Na tuna ɗan’uwana, kuma abokina ne.”

    Da ta ji haka, sai ta dubi Kurege a cikin tausayi ta ce da shi: “Ai Dodo ya ce kai zan aura saboda haka ka daina kuka, ka zo mu je a ɗaura mana aure.” Sai Kurege ya daina kuka, suka kama hanyar gidan iyayenta inda za a ɗaura musu aure. Aka ɗaura musu aure suka zauna cikin jin daɗi lokaci mai tsawo. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Zamba da cin amana mai yin sa ba ya kai wa ga nasara.
    • Komai za a yi ya kamata a yi shi cikin hikima da ƙwarewa, yin haka shi yake kawo samun biyan buƙata.
    • Ƙarya fure take, ba ta ‘ya’ya.
    • Matar mutum kabarinsa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar ‘Yar ‘auta Da Kogin Rantsuwa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ‘Yar ‘auta Da Kogin Rantsuwa

    Tatsuniyar ‘Yar ‘auta Da Kogin Rantsuwa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum mai mata ɗaya da ‘ya’yansu tara maza da mata, waɗanda yake ƙaunar su ƙwarai. Kullum idan ya je kasuwa, sai ya sayo kifaye tara saboda yaran nan. Suna nan haka cikin annashuwa, sai wata rana da ya kai kifayen nan tara, ‘yar autar gidan ta ɗauki ɗaya ta cinye ba tare da ta tambaya ba.

    Ta yi haka ne kuwa saboda wautar ƙuruciya. Da ya duba ya ga kifaye ba su cika ba, sai ya ce a tafi rafin Tantafane domin ‘yan ruwa su yi maganin wanda ya cinye kifin nan. Shi ke nan, da suka je sai babbar cikinsu ta fara waƙa tana cewa:

    “Kogi, kogin Tantafane,

    In ni na cinye kifin baba,

    Ruwa ka tafi da ni,

    Kar ka dawo da ni.”

    Da haka ɗaya bayan ɗaya har takwas daga cikin yaran suka yi waƙa, amma ruwan bai cinye su ba, ya rage ‘Yar auta. Ita kuma tana can gefe tana shirme irin na yarinta, sai suka ce: “Saura ke, ‘Yar’autar iya da baba.” A nan dai ‘yan’uwan suka matsa sai ta yi, har ma suka ce idan ba ta yi ba za su kashe ta.

    ‘Yar’auta ta sa ƙafafunta a cikin ruwa, ta yi waƙa ƙafin ma ta gama waƙar ‘yan ruwa sun janye ta, wato ruwa ya tafi da ita. To, akwai wata tsohuwa da ta saba da ‘yan ruwan da suka kama ‘Yar’auta. Sun saba da ita ne kuwa saboda ta fi shekara sha uku tana zuwa rafin nan kamun kifi.

    Saboda haka ba su cinye ‘Yar’auta ba domin sun ga kyakkyawa ce, sai suka ba tsohuwar nan ita riƙo. Yarinya ta bi tsohuwa kamar ita ce ta haife ta, ita kuma ta riƙe ta kamar ‘yarta. Ana nan, ‘Yar’auta ta girma, har masu neman aurenta suka fara fitowa, har mata fitar da ɗaya daga cikin manemanta, tsohuwa ta amince da zaɓen da ta yi.

    To, amma sai ta ce da manemin yarinyar: “Ka je ka kawo buhun kwarkwata, wannan ne abin da za a ba ‘yan ruwa.” Nan da nan yaron ya je ya gaya wa mahaifiyarsa ita da danginta suka haɗa ƙarfi; washe-gari suka kai wa tsohuwa buhun kwarkwata cikakke har da toliya.

    Ba tare da wani ɓata lokaci ba aka ɗaura musu aure, ‘Yar’auta ta tare a gidan miji. Ashe angon nan yayan ‘Yar’auta ne bai sani ba, amma ita ta gane, sai dai ta yi shiru ba ta faɗa ba. Duk sanda mazan gidan suka tafi gona, da ta fara dakan garin abincin da za ta yi musu, sai ta fara waƙa tana cewa:

    “In daki turmin gidanmu,

    In daki turmin gidanmu,

    Tim, ƙwal, ƙwal.

    A yau uwata,

    Ta zama surukata.

    Ubana ya zama surukina,

    Ƙannena ne abokan wasana.

    In daki turmin gidanmu,

    In daki turmin gidanmu,

    Tim, ƙwal, ƙwal.”

    To akwai wata tsohuwa da takan zauna a zaure duk sanda mutanen gidan suka bar amaryar nan a gida, takan ji abin da amaryar kan faɗa. Rannan sai tsohuwa ta ce da mutan gidan: “Idan kun shirya tafiya gona, ku laɓe ku ji abin da amaryar nan za ta faɗa.” Suka kuwa karɓi shawararta, suka kuma aikata abin da ta ce su yi.

    Ɗaya daga cikinsu ma ta koma cikin gidan, da amaryar ta gan ta sai ta ce da ita: “Me kike yi a gida?” Sai ta ce: “Na mance fartanyata ne na zo ɗauka, zan koma gona.” Da ta ɗauki fartanya, sai ta yi kamar ta kama hanyar gonar ne, jim kaɗan sai amaryar ta ɗauki turmi, ta hau daka tana yin waƙar da ta saba yi.

    Sai ko gaba ɗayansu suka fito daga maɓoyarsu suka ce: “Ashe ‘Yar’auta ce?” Ita kuwa sai dariya take yi tana cewa: “E, ni ce.” Nan take suka rungume juna, kowa sai kukan murna yake yi. Daga nan kuma sai aka manta da zancen aure ta ci gaba da zama a cikin danginta. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Shugabannin ƙwarai su suke ƙoƙarin hukunta marasa gaskiya ko da a cikin iyalinsu suka fito.
    • Hukunta marar gaskiya ba zai hana shi zama mutumin kirki ba.
    • Aukawa cikin wata hulɗa ba tare da yin bincike ba yakan haifar da matsala.
    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Kushewar baɗi sai baɗi.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Gwaidayara

    Edita@rumasau-kallamu