Category: WikiHausa

Yadda ake amfani da WikiHausa

  • Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 15th August 2025

    Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 15th August 2025

    Huɗubar Juma’a daga Masallaci mai alfarma:21 Safar 1447
    15 August 2025
    Mai huɗuba: Sheikh Dr. Bandar bin Abdul-Aziz Badila
    Mai fassara: Dr. Usman Muhammad Ahmad
    Shugaban sashi: Dr. Abdulkarim Tahir Abdullahi

    Huɗuba ta farko:
    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Ya halicci halittu kuma Ya ƙaddara ƙaddarori, Ya rarraba arziki kuma Ya rubuta ajali, muna yaba masa tsarki ya tabbata a gare Shi kuma muna gode masa, Ya fari halittar rayuwa kuma Ya gudanar da ƙoramu, Ya shimfiɗa ƙasa kuma Ya tsaga tekuna.

    Kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, Ya hore rana da wata, da dare da yini. Kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa, kuma zaɓaɓɓen Annabinsa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da alayensa tsarkaka, da sahabbansa nagartattu, da waɗanda suka biyo su da kyautatawa a dukkan darare da yini.

    Bayan haka:
    Ya ku mutane! Ina muku wasici da ni kaina da tsoron Allah, ku ji tsoron Allah, Allah Ya muku rahama, kuma ku sani cewa babu abin da ke faruwa a cikin wannan rayuwa face sai da ƙaddarar Allah da kuma nufinsa, da hikimarsa da iradarsa; na dare da yini, da iska da ruwan sama, da sanyi mai tsanani da zafi, da sauye-sauyen yanayi da maimaituwarsa, abin da zai sa mumini ya tabbatar da cewa wannan duniya ba gidan dawwama ba ce.

    Kuma wannan gaba ɗayansa yana daga cikin ayoyin Allah na halitta masu nuna girman ƙarfinsa da ikonsa, da yalwar iliminsa da hikimarsa, da zurfin nufinsa da rahamarsa, da kuma cewa kowane abu a wurinsa tsarki ya tabbata a gare Shi yana da iyaka.
    ((Lallai a cikin halittar sammai da ƙasa da sassaɓawar dare da rana, tabbas akwai ayoyi ga ma’abota hankula Su ne waɗanda suke ambaton Allah a tsaye da kuma zaune da kuma kishingiɗe, suna kuma tunani a kan halittar sammai da ƙasa (suna cewa: “Ya Ubangijinmu, ba Ka halicci wannan a banza ba, tsarki ya tabbata gare Ka, Ka tsare mu daga azabar wuta)).

    Ya ku bayin Allah!
    Waye a cikinmu da zafin rani bai taɓa cutar da shi ba? Kuma waye a cikinmu da ƙunar rana ba ta taɓa ƙona fuskarsa ba? Dukanmu mun samu rabonmu daga wannan, ko dai kaɗan ko ko dayawa, lallai wannan shi ne zafin rani, mai wa’azin nan da Allah Yake tunatar da bayinsa zafin taron alƙiyama da azabar wuta da shi.

    An rawaito daga Miƙdad ɗan Aswad Allah ya ƙara masa yarda ya ce: Na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa: (Za a kusanto da rana ga halittu a ranar alƙiyama har ta kasance kamar tazarar mil daga gare su). Sulaim ɗan ‘Amir ya ce: Na rantse da Allah ban san me yake nufi da mil ba, yana nufin na tazarar ƙasa, ko ko mil da ake amfani da shi wajen sanya kwalli a ido? Ya ce: (Sai mutane su kasance cikin zufa gwargwadon ayyukansu; daga cikinsu akwai wanda zufa za ta kai masa idanuwan sawu, akwai kuma wanda za ta kai masa gwiwoyi, akwai wanda za ta kai masa zuwa ga kwuiɓinsa, akwai kuma wanda zufa za ta yi wa bakinsa linzami sosai). Sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi nuni zuwa ga bakinsa da hannunsa. Muslim ne ya rawaito shi.

    Ya ku musulmi!
    Lallai tsananin zafi yana daga cikin ayoyin da Allah yake aiko wa bayinsa don tsoratarwa da tunatarwa, da zama wa’azi da ɗaukan izina, kamar yadda Allah Ya ce: ((Kuma ba Ma aiko da ayoyi sai don tsoratarwa)).

    An rawaito aga Abu Huraira Allah ya ƙara masa yarda ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Wuta ta kai kokenta ga Ubangijinta, ta ce: Ya Ubangiji, sashina na cin sashi, sai Ya ba ta izinin numfasawa sau biyu; numfasawa a lokacin sanyi, da numfasawa a lokacin zafi, to wannan shi ne mafi tsananin zafin da kuke ji a lokacin rani, da kuma mafi tsananin sanyi da kuke ji a lokacin hunturu). Bukhari da Muslim ne suka rawaito.

    To, ya ku muminai! Mai rabo, shi ne wanda ya yi guzuri daga zafin duniya domin kuɓuta daga zafin lahira, da kuma wanda ya yi haƙuri da ibada a lokacin tsananin zafi, domin ya more ni’imar da ba ta ƙarewa a ranar da za a tona ɓoyayyun sirrikan zukata.
    ((Ya ku waɗanda kuka yi imani, ku kare kanku da iyalanku daga wuta, wacce makamashinta mutane ne da duwatsu, masu kula da ita mala’iku ne masu kaushin hali, masu tsananin gaske, ba sa saɓa wa Allah abin da Ya umarce su, kuma suna aikata abin da aka umarce su da aikata shi)).

    An rawaito daga Abu Sa’id Alkhudri Allah ya ƙara masa yarda ya ce: Na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa: (Duk wanda ya yi azumin yini ɗaya saboda Allah, Allah zai nesanta fuskarsa daga wuta na tsawon shekara saba’in). Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi.

    Kuma Abu Darda Allah ya ƙara masa yarda ya kasance yana cewa: “Ku azumci yini mai tsananin zafin rana saboda kuɓuta daga zafin ranar tashin alƙiyama, kuma ku yi raka’a biyu cikin duhun dare saboda ku kuɓuta daga duhun ƙaburbura”. Abu Nu’aim ne ya rawaito shi a Hilya.

    Kuma ku sani Allah Ya jiƙan ku cewa dukkan abin da zai samu mumini a cikin zafi na tsanani da wahala, da gajiya da ƙosawa, to, dukkansu za a rubuta su, za a kiyaye su kuma za a ƙididdige su, a wajen Wanda ayyukan ƙwarai ba sa tozarta a wajensa, kuma ba a rasa ayyukan ɗa’a a wajensa, da su za a kankare zunubai, kuma a ninka kyawawa, kuma a ɗaga darajoji.

    An rawaito daga Abu Sa’id da Abu Huraira Allah Ya ƙara musu yarda, sun ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Babu wani abu da zai samu musulmi, na ciwo, ko wahala, ko jinya, ko bakin ciki, har ma da damuwa da za ta sauko masa, face sai an kankare masa zunubansa da shi). Muslim ne ya rawaito shi.

    Kuma lallai ayyuka ana ninninka ladansu, kuma ana ƙara sakamakonsu, kuma ma’auninsu na nauyaya, da gwargwadon abin da ya tabbata na niyya da ikhlasi da juriya da haƙuri a zukatan ma’abotansu. Ibnul Asir Allah Ya yi masa rahama ya ce: “Kuma neman lada a cikin ayyuka nagartattu da kuma lokacin da ake ƙi, shi ne gaugawa zuwa ga neman lada da kuma samun sa ta hanyar miƙa wuya da haƙuri”. Ƙarshen maganarsa kenan.

    Kuma yana daga cikin rahamar Allah ga bayinsa shar’anta musu abin da za su iya yi na ayyuka da ya yi, kuma bai ɗaura musu abin da zai wahalar da su ba, an rawaito daga Abu Huraira Allah Ya ƙara masa yarda, daga Annabi tsirda da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Idan zafi ya tsananta, to ku sanyaya sallarku, saboda tsananin zafi daga hucin Jahannama yake). Bukhari da Muslim ne suka rawaito. Abin da ake nufi da sanyaya salla, shi ne jinkirta ta zuwa ƙarshen lokacinta, lokacin da zafin garji zai yi sauƙi, kafin shigar lokacin sallar da za ta biyo bayanta.

    Kuma za a gwama dukkan wata ibada da ke cikin jinsinta da ita, cikin abin da ya halatta a jinkirta shi, don haka, duk wanda ake bin shi azumi na watan Ramadan, ko kuma kaffara ta azumi ko makamancin haka, to, ya halatta a gare shi ya jinkirta shi zuwa ga lokutan sanyi, idan biyansa a lokacin zafi zai ba shi wahala, akwai hadisin A’isha Allah Ya ƙara mata yarda da yake nuni a kan haka, ta ce: “a kan samu wani lokaci da ake bi na azumi da na sha tun a watan Ramadan, amma na kasa samun daman biya sai a watan Sha’aban”. Bukhari da Muslim ne suka rawaito. Amma gaggauta biya shi ya fi,

    Don haka, ya ku bayin Allah!
    Ku gode wa Allah a bisa dukkan hali da yanayi, kuma ku gade masa a kan abin da Ya tanada muku na hanyoyi da sabuba, waɗanda Ya sauƙaƙe muku wahalar zafi da tsananinsa da su, da ƙunarsa da hucinsa, da na’urorin sanyayawa da wuraren hutu a lokacin zafin rani, kuma ku riƙa bincikan halin ‘yan uwanku talakawa da marasa abin hannu, kuma ku sauƙaƙa musu abin da suke fama da shi na tsananin zafi da ƙunar rana, kowa ya yi dai dai ƙarfinsa da ikonsa, kuma daga cikin haka akwai shayar da ruwa mai sanyi a waɗannan lokuta na zafi, saboda hakan yana daga cikin sadokoki mafiya falala, kamar yadda Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ba mu labarin hakan.

    Kuma ku riƙa tunawa da wasu ‘yan’uwanku a Addini, waɗanda raɗaɗin rashi da tawaya ta dukiya da rayuka da ‘ya’yan itacuwa suka ƙaru a gare su a kan abin da suke fama da shi na tsananin zafi, ya Allah Ka yaye musu abin da ya sauko musu, ya Allah Ka sauya tsoronsu da aminci, biƙin cikinsu da farin ciki, yunwarsu da ƙoshi, kuma Ka taimake su a kan maƙiyanka kuma maƙiyansu ya Mai ƙarfi ya Mabuwayi.

    Ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina nema wa kaina gafarar Allah, da ku da sauran musulmi, daga kowane zunubi, don haka ku nemi gafararsa, lallai Shi Mai yawan gafara ne kuma Mai jinƙai.

    Huɗuba ta biyu:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Wanda dukkan al’amura suke samuwa daga aikinsa da nufinsa, muna yaba masa tsarki ya tabbata a gare Shi kuma muna gode masa a bisa falalarsa mai yalwa da ni’imominsa, da kyakkyawar afuwarsa da gafararsa, tsira da amincin Allah su ƙara tabbata ga mafificin Manzanninsa kuma zaɓɓaɓensa, da alayensa, da sahabbansa da tabi’ai, da waɗanda suka biyo su da kyautatawa har zuwa ranar rarrabewa da tashin alƙiyama.

    Bayan haka: Ku sani, Allah Ya muku rahama, cewa lallai bayyana fushi da raki don tsananin zafi yana daga cikin suka ga hukuncin Allah da ƙaddararsa, da nufinsa da ganin damansa, da kuma cewa lallai babu abin da zai auku a wannan duniya face sai da wata hikima da maslaha da fa’ida da amfani, daga cikin haka akwai yadda muke ganin dayawa daga cikin shukoki da ‘ya’yan itatuwa ba sa yin daɗi kuma ba sa daidaituwa har sai lokacin da rani ya kai maƙurarsa, haka kuma dayawa daga cikin cututtuka da annoba ba sa ɓacewa har sai lokacin da zafi ya kai ƙololuwar matakinsa, Ibnul Ƙayyim Allah Ya masa rahama ya ce:

    “A lokacin rani, iska na rikiɗewa ta yi zafi sosai, sai ‘ya’yan itatuwa su nuna, kuma sauran ababe marasa amfani da ababen da suka cakuɗu da jiki su gushe a lokacin hunturu, kuma sai sanyi ya kutsa ya shiga cikkuna, don haka ne ma maramaren ruwa da rijiyoyi suke yin sanyi”. Ƙarshen maganarsa kenan.

    Saboda haka, ku ji tsoron Allah, ya ku bayin Allah, kuma ku kiyaye zukatanku da harsunanku daga dukkan abin da zai rage imaninku, ya lalata tauhidinku, domin yana daga cikin cikar tauhidi yarda da kuma miƙa wuya ga dokokin Allah na shari’a da tsarinsa na gudanar da duniya.

    Sannan ku yi salati da sallama ga mafi alherin halittun Allah, Muhammadu bin Abdullahi, domin Ubangijinku Ya umarce ku da hakan, sai Ya ce: ((Lallai Allah da mala’ikunsa suna salati ga Annabi; ya ku waɗanda kuka yi imani, ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa)).

    Ya Allah, Ka yi salati da sallama, da ƙarin daraja da albarka ga bawanka kuma ManzonKa, Annabinmu Muhammadu, kuma ka ƙara yarda da sahabbai baki ɗaya, da tabi’ai, da waɗanda suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.
    Ya Allah, ka ɗaukaka Musulunci da Musulmai, Ka kiyaye shingen addini, Ka taimaki bayinka muminai masu tauhidi.

    Ya Allah, ka yaye damuwar masu damuwa daga cikin musulmai, ka kwaranye baƙin cikin masu baƙin ciki, Ka biya bashin wadanda ake bi bashi, Ka warkar da marasa lafiya daga cikinmu da na sauran musulmai.

    Ya Allah Ka amintar da mu a ƙasashenmu, Ka shiryar da shugabanninmu kuma jagororinmu, Ka ƙarfafi Shugabanmu kuma jagoranmu Hadimin Masallatai Biyu Masu alfarma da gaskiya da dace da gamonkatar, Ya Allah, ka tsawaita rayuwarsa cikin waraka da ƙoshin lafiya, da ni’ima mai yalwa kuma cikakkiya, kuma Ka datar da shi da magajinsa amintacce ga abin da alheri ne ga ƙasa da mutane, da ɗaukaka ga Musulunci da musulmi ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah Ka kasance Mai ƙarfafawa da kawo ɗauki da agazawa da taimako ga ’yan’uwanmu masu rauni, ya Allah, Ka taimake su a ƙasar Falasɗinu a kan yahudawa ‘yan ƙwace, ya Allah, Ka ƙididdige adadin yahudawa, Ka halaka su ɗaya bayan ɗaya, kuma kada Ka bar ko ɗaya daga cikinsu.

    Ya Allah Ka kiyaye dakarunmu masu dako a kan iyakoki da fagage, Ya Allah, Ka kiyaye su da idonka da ba ya barci, Ka tsare su da ƙarfinka da ba a iya rinjayarsa ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah Ka azurta mu da haƙuri akan jarrabawa, da yarda da ƙaddara, da godiya a lokacin yalwa, kada Ka ɗora mana abin da ya fi ƙarfinmu, domin aminci daga gare Ka shi ya fi yalwa a gare mu ya Mafi tausayin masu tausayi.

    Ya Allah Ka tsare mu daga azabarka a ranar da Za Ka tashi bayinka, ya Allah Ka tsare mu daga azabarka a ranar da Za Ka tashi bayinka.
    ((Ubangijinmu, Ka ba mu alheri a duniya, da alheri a lahira, kuma Ka tsare mu daga azabar wuta))
    ((Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin buya daga abin da suke sifantaShi da shi () Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni () Kuma dukkan yabo ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai)).

    Karanta Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya 1st August 2025

    Edita@rumasau-kallamu

  • Dalilan Mace-macen Aure Daga Bakin Mawaƙan Situdiyo

    Dalilan Mace-macen Aure Daga Bakin Mawaƙan Situdiyo

    Ko shakka babu, mawaƙa sun kasance wasu rukunai masu wayar da kan al’umma; imma ta hanyar yin hannunka mai sanda ne ko kuma ta hanyar fitowa ƙarara su bayyana wata matsala ce; sannan su yi ƙoƙarin kawo mafita daga matsalar a irin tunaninsu. Bisa haka, a nan za mu yi ƙoƙarin hakaito wasu ɗiyoyi daga wasu waƙoƙin baka na Situdiyo tare da ƙoƙarin fashin baƙi kan saƙon da suke ƙunshe ciki; ta hanyar kawo matsalolin da kuma hanyoyin magance su.

    Dalilan Mace-macen Aure su ne:

    1. Rashin Bincike Kafin Aure.

    Bincike kafin aure abu ne mai asali kuma mai muhimmanci, domin da bincike ne za a gano irin tarbiyyar gidan su mace ko miji.

    Wannan ya sanya da zarar yaro ko yarinya ta bayyana wanda take so ko yake so a gaban iyaye; to abin da za su fara yi shi ne binciken gidan su.

    Idan aka yi rashin sa’a, yaro ko yarinya ɗaya ba tarbiyya; to an karya babbar gwafar da za ta riƙe auren.

    Wannan ya sanya a nan, Zabiya Lawisa a waƙarta ta Sakin Aure ta bayyana cewa, abu na farko da yake kawo mutuwar aure a yau, shi ne rashin bincike, wanda da rashin binciken ake aurar maras tarbiyya ko maras kunya ko kuma wanda bai dace a bai wa mata ba.

    Ga abin da ta ce:

    Jagora: Abin da yake ta kawo saki; na aure kun ji ya ‘yan’uwa,
    Da farko dai rashin bincike; yana haifar da duk damuwa,
    Domin kwa rashin sanin tarbiyyar; miji na sa rashin jituwa,
    Bayan auren rashin nuttsuwa,
    Mata da mijin cikin damuwa,
    Wannan sakacin iyaye suke; a auren sai ya yo mutuwa,

    Bayan an yi aure ba tare da an yi bincike ba, wanda hakan zai sa a yi ta samun saɓani, to dole saki ya iya biyo baya. A nan, sai ta ɗora sakacin hakan a kan iyayen ma’aurata, domin su ne suke da haƙƙin yin wannan binciken.

    A waƙarta ta Sakin Aure; Fatima Jalo, ita ma ta bayyana laifin iyaye a matsayin abin da yake kawo mutuwar aure, domin hasashenta ya nuna muddin aka sami mai tarbiyya, to zai yi wuya a rinƙa samun matsala. Don haka idan iyaye za su yi bincike, to za su aurar wa mai tarbiyya ko su auro wa ɗansu mai tarbiyya.

    Ga abin da ta ce:

    Jagora: Wataran laifin iyaye ne suka bar auren ya ɓalɓalce,
    Ka ga ‘ya’ya babu tarbiyya, dole auren za ya lalace,
    Matsayin ke ce uwa tarbiyya ke ce za ki jajirce,
    Sai Allah ya taya ki daga nan kuma ke ce za ki jajirce,
    Ba su san darajar mazaje ba ta ya aurensu zai zarce,
    Ki gyara halinki mamata sai tarbiyya ta zam fata.

    Abin dai da take son ta ce a nan shi ne, duk lokacin da aka sami maras tarbiyya, to dole aure ya shiga garari, shi kuwa gane mai tarbiyya mace ko namiji yana hannun iyayen ma’aurata ta la’akari da gidan da za su aura ko aurarwa.

    2. Auren Dole

    Auren dole shi ne auren da ake tursasa ɗaya ya amince ya auri ɗaya da so ko babu so. To a nan, idan an yi auren dole, za a iya riskar saki kamar yadda Zabiya Lawisa ta bayyana

    Jagora: A sannan kana aure na do; leshi ma na saka ai saki,
    Iyaye za su tursasa ‘yar; su koda ba ta so ai biki,
    To tunda akwai ƙiyayya a ran; ta sai ta ƙi yi abin arziki,
    Komai ya saka ta tai sai ta ƙi,
    Silar haka sai mijin yai saki,
    To kun ga akwai fa illa fa bab; ba auren dole ba arziki.

    A irin wannan zamantakewar aure ce muddin macen ta ga an takura mata, za ta yarda a yi auren, amma fa za ta iya yin dukkanin wulaƙanci da ƙin kyautata wa miji, kamar yadda shi ma miji kan iya yin hakan ga matar da aka tursasa masa ya aure tab a da son ransa ba. Irin wannan abin da ke kawo ƙarshen sa, shi ne saki.

    3. Rashin Sana’ar Miji

    Sana’a muhimmiyar aba ce wadda dukkanin ɗawainiyar rayuwar ɗan’adam ke ɗoruwa a kanta kacokan. Bahaushen mutum ya yarda da sana’a, saboda muhimmancin ta ne ya sanya har sarautu ake yi wa sana’o’i a gargajiyance, sannan idan mutum bai da ita, ake masa kallon mutumin banza. A harkar auratayya, idan mutum bai da sana’a ma ba a ba shi, domin ba shi da abin da zai riƙe matar.

    Zabiya Lawisa a nan ma, ta bayyana rashin sana’a ga miji na kawo mutuwar aure.

    Jagora: Rashin sana’ar miji ma yakan; kashe aure a ɗan lokaci,
    Domin kwa idan ya auro mace; ya kawo babu mai za ta ci,
    A kwana a tashi yau da gobe; ta fara yi mar baƙin furuci,
    Ta je ta gidansu sannan ta ci,
    Domin kuwa shi ya yo sakkaci,
    To kun ga hakan yakan sa ashe; aure ya mace rashin shad a ci.

    Sanin kowane da sana’a ake gudanar da dukkanin wasu ɗawainiya na rayuwa, da ita ake sarrafa al’amuran buƙatun gida. A lokacin da miji ba shi da aikin yi to zai fuskanci matsala a gidansa, domin ba zai iya sauƙe haƙƙinsa na ciyarwa da sayar da matarsa ba, ƙarshe nan ma saki ya iya biyo baya.

    4. Matsalar Dangin Miji

    Dangin miji sun haɗa da iyayensa, yayunsa, ƙannensa da dukkanin wani ɗan’uwansa ko ƙannen iyaye da yayu. Sau da dama dangin miji kan taka rawa wajen mutuwar aure kamar yadda dangin mata ma kan taka rawar afkuwar hakan. Wannan batu kuwa ya tabbata daga Zabiya Lawisa, a inda ta ce:

    Jagora: Sannan matsala ta danjin miji; tana sa ai saki kunjiya,
    Da ƙanne ne da yayye da ma; uwa sirika gaba ki ɗaya,
    Waɗansu idan ka auro mace; da itta kuna zaman lafiya,
    Su sa zargi cikin zuciya,
    Su fara yi matta halin tsiya,
    Sannan ce ta mallake ɗan’uwan; su sai a sake ta domin wuya.

    Mallakewa a nan, shi ne idan suka ga ana zaman lafiya, ƙila ma idan suka ga yana yawan ambaton ta da alheri. To a nan, dangin miji za su yi duk yadda za su yi domin su ga sun rusa auren.

    Zabiya Fatima Jalo ma, ta kawo wannan a matsayin dalilan da ke sabbaba mutuwar aure.

    Jagora: Wani auren ba ya tasiri saboda uwar miji ta ƙi,
    Duk abin da ya yo na alkairi uwar nan sai ta ce ta qi,
    Kuma za ka ga ta turo ‘ya’yanta su bincike ɗaki,
    In matar ta hana su za su yi mata dukan ba da mamaki,
    In ya dawo gida ta faɗa masa zancen ba da mamaki,
    Ka ga ɗan aikin nan Hajiya ta saka ta ta ce da mu ta ƙi,
    Ai dole ka zaɓa ka sake kawai shi ne buƙata ta.

    Mafi yawa iyaye kan tilalas ‘ya’yansu su saki matansu saboda wani abu da ke tsakaninsu na rashin fahimta ko kuma son zuciya, shi ne abin da ake son bayyana mana a nan

    5. Zugar Ƙawaye/Abokai

    Ƙawaye ko abokai su ne waɗanda ke kusa da ma’aurata, kusanci na zahiri ko na baɗini. A nan, aure kan iya samun tangal-tangal a dalilin tasirinsu wanda har saki ya biyo baya. Zabiya Lawisa ta tabbatar da wannan a ɗiyar da ke biye.

    Ƙawaye ko abokai su ne waɗanda ke kusa da ma’aurata, kusanci na zahiri ko na baɗini. A nan, aure kan iya samun tangal-tangal a dalilin tasirinsu wanda har saki ya biyo baya. Zabiya Lawisa ta tabbatar da wannan a ɗiyar da ke biye.

    Jagora: Sannan kuma kana har ma zugar; abokai na saka ai saki,
    Domin ko wani idan ya ga kai; da mata taka kun arziki,
    Ya sa kishi cikin ransa sai; ya tunzura zuciyarka ka ƙi,
    Kuma ya ce matarka har tai jiki,
    Sakin fuska ka bar yi ka ƙi,
    A sannan sai ka daina ka can; ja hali gun ta har kai saki.

    Abin da take son tabbatarwa a nan shi ne, a duk lokacin da ƙawaye ko abokai suka ga yadda ma’aurata ke cikin jin daɗi da nutsuwa, kuma hakan ya ba su haushi da taƙaici, sai su shigo da batun zuga ta yadda har za su yi tasirin rusa wannan aure.

    Fatima Jalo ma ta yarda da wannan ra’ayi na matsalar ƙawaye, domin suna tasirin wajen mutuwar aure.

    Ga abin da ta ce:

    Jagora: Wataran laifin ƙawaye ne masu sa aure ya bar ƙarko,
    Za ka gan su suna ta kai-kawo lokacin da ake bikin baiko,
    Su haɗa ka da saurayi sabo dole soyayya ta yo narko,
    A gidansu ake ta soyayya a gabansu ake ta kai saƙo,
    Auren nan baya tasiri darajar aurenki ta saƙƙo,
    Renon Haisal masoyi ce Jalo sunana cikin mata

    Ita kuma a nan ta nuna wani auren kan ƙulluwa ne yayin da ƙawayen suka rusa wata soyayyar da ke tsakanin wata da wani, sai su ƙulla wani, to wanda suka ƙulla ɗin sun san komai a kai, ƙarshe sai saki ya biyo baya sakamakon tasirin su da kuma sanin sirrin komai a auren.

    6. Rashin Haƙuri

    Haƙuri ja-gaba ne wajen tafiyar da al’amuran duniya babba daga ciki aure, domin sai da haƙuri ake cin nasarar gudanar da shi. A ra’ayin Lawisa, idan aka rasa haƙuri to dole a sami matsalar da za ta iya haifar da mutuwar aure.

    Jagora: Rashin haƙuri a aure ƙwarai; yana jawo saki kun jiya,
    Idan da akwai a zauna idan; kwa babu a kasa yin juriya,
    Miji ya sake ta dan yanzu ya; ga ba shi da shi yana shan wuya,
    To ko ita taƙ ƙi yin juriya,
    Da rashin haƙuri cikin zuciya,
    Gajen haƙuri akwai ko ko ba; bu na sa ai saki kun jiya

    A nan ta danganta rashin haƙurin da yake kawo saki, shi ne idan ya kasance miji ba shi da kuɗi, wanda da shi zai yi amfani wajen sayo dukkanin abin da zai gudanar da rayuwarsu.

    7. Rashin Adalci

    Adalci a aure shi ne yi wa kowacce mace kwatankwacin abin da aka yi wa ‘yar’uwarta bisa daidaito da tsari da buƙatuwarta. A tsarin rayuwa, ba lalle ne yawan abincin da wannan za ta ci, shi wannan za ta ci. Don haka ba a ce dole a ba su daidai wa daida ba, wato idan wannan ta ci ya ishe ta, wannan kuma sai ishe ta ta yadda za ma ya mata yawan da zai kai ga yin almubazzaranci 

    A nan, bayar da komai bisa buƙatar kowa shi ne adalci. Zabiya Lawisa ta bayyana rashin adalci kan kawo mutuwar aure, kamar yadda ta ce:

    Jagora: Sannan matsalar rashin yi da nu; na adalci a gun maigida,
    Domin wani in yana da mata; guda biyu dole ne in faɗa,
    Ya rinƙa ta nuna halin rashi; na adalci a cikkin gida,
    Ya bambanta ya ware guda,
    Guda ya mayar ta ɓawon gyaɗa,
    A sannu a hankali sai ta ka; sa jurewa ta bar mai gida.

    Rashin adalci kan sanya mace ta nemi saki, ko kuma ma ta kama kaban ta ta bar gidan kamar yadda wannan ɗiya ta nuna.

    8. Kishi

    Zabiya Lawisa, ta bayyana kishi na kawo mutuwar aure. Ga abin da ta ce:

    Jagora: Sannan kishi yakan sa saki; a gun wata dan gudun kishiya,
    Da zarar za a auro wata; ta canja hali ta hau yin tsiya,
    A koyaushe tana hauhawa; tana bin ra’ayin zuciya,
    Rashin haƙuri cikin zuciya,
    Tana halin rashin tarbiyya,
    Silar haka sai ya sa ai saki; domin kuwa ba zaman lafiya.

    A nan, tana nufin yayin da miji ya yi yunƙurin ƙara aure, to sai matar da yake aure ta hau wani hali na rashin kyautatawa da bala’I, wanda ƙarshe zai iya sanya mijin ma ya sake ta saboda irin abin da take masa na rashin kyautatawa.

    9. Ƙarya

    Zabiya Lawisa ta bayyana ƙarya a matsayin abin da ke sabbaba mutuwar aure, ga abin da ta ce:

    Jagora: Sannan kala ƙarya tana; kashe aure na ɗan saurayi,
    Ya ce mata in ya aure ta ko; me ye ta biɗa ƙwarai za ya yi,
    Da zarar an yi aurensu sai; ya canjo dukkanin ra’ayi,
    Komai ta biɗa ya ce ya ƙi yi,
    Ya ce mata bai da shi ba ya yi,
    A sannan sai rashin jituwa; saki ya biyo su ce tsautsayi.

    A nan, tana nufin saurayi kafin ya auri mace, yakan hure mata kunne da ƙarerayin cewa duk abin da ta nema zai yi mata, duk abin da take so zai sayo mata, amma da zarar an yi auren; sai a sami akasin haka, wato abin da ya faɗa ba shi da shi ma. Don haka, wannan sauyin da ta gani, sai ya haifar musu da tashin-tashina, ƙarshe saki ya biyo baya.

    10. Cin Amana da Zargi

    Cin amana da zargi munanan abubuwa ne, domin cin amana shi ne ɗaya ya rinƙa ha’intar ɗaya cikin mutuncinsa. Zargi kuwa ɗaya ya rinƙa zargin ɗaya, ko kowannensu ya rinƙa zargin juna. A nan, wannan ma na kawo saki kamar yadda Lawisa ta bayyana.

    Jagora: Sannan kuma cin amana irin; ta aure ‘yan’uwa kunjiya,
    Tana janyo saki nan da nan; a take a yi shi ba shan wuya,
    Idan ɗai ac cikinsu ya ga; guda ɗaya na ta yin bibiya,
    Da alfasha cikin zuciya,
    A take a nan a hau yin tsiya,
    A kwana a tashi har zuciya; ta tunzura ai saki ba wuya.
    Jagora: Sannan zargi yakan sa saki; a aure kun ji ya ‘yan’uwa,
    Gurin mace ko gurin maigida; tsakaninsu suna tsarguwa,
    Kowanne ba shi yarda da ɗan’uwansa me ye yake faruwa,
    Junansu suna ta yin tsarguwa,
    Koyaushe suna rashin jituwa,
    A koyaushe kawai sai faɗa; tsakanin nasu ba jituwa.

    A nan tana nufin idan ɗaya na zargin ɗaya, ko kuma suna zargin junansu, to fa dole aure zai sami matsala, domin dukkanin wani aminci ya kau, daga lokacin da aminci ya kau, yarda ta kubce, to aure ya sami matsala.

    11. Matsalar Miji

    A nan, Fatima Jalo na son nuna cewa, miji ma na haifar da wata matsala wadda take sabbaba mutuwar aure, ga abin da ta ce:

    Jagora: Wataran laifin masoyi ne mafarin dukkanin ɓarna,
    In ta zo ta tana amarya ba ka hana ta idan tana ɓarna,
    Ta riga ta horu kan haka kai ka ɓata rawar ka yayana,
    Yanzu ba damar hana ta kai ka ɓata rawar ka yayana,
    In ka taso za ka yo gyara ai dole a kai ruwa rana,
    Roƙon da nake Ilahu ka gyara dukkanin halinmu nai fata.

    Irin horo ko riƙo da miji zai yi wa matarsa na daga cikin abin da zai gyara aure ko lalata shi. A nan, idan mace tana amarya kuma tana da wasu ɗabi’u ko tana aikata wasu abubuwa, sai mijin ya kasance ba ya kwaɓarta domin kasancewarta amarya ko don zurfin son da yake yi mata. 

    To lokacin da ta kai shi maƙura ko kuma ya so sanya ta a layi, ba lalle hakan ta faru ba; sakamakon yadda abin ya zame mata jiki. Don haka, daga wannan lokacin aure ne zai fara tangal-tangal, ƙarshe saki ya biyo baya.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Nazarin Matsalolin Aure A Ƙasar Hausa Daga Mahangar Zabiya Lawisa da Fatima Jalo wanda Ibrahin Baba (Nayaya) ya wallafa shi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Abin da Bincike Ya Gano Game Da Matsalolin Aure a Ƙasar Hausa danna nan

    Domin karanta bayani a kan Kula da Miji: Yadda Za Ki Nuna Wa Mijinki Tsantsar Kula danna nan

  • Sauya Akalar Kiɗan Gado Zuwa Na Fada Da Na Game-Gari

    Sauya Akalar Kiɗan Gado Zuwa Na Fada Da Na Game-Gari

    Makaɗa Musa Ɗanƙwairo Maradun tun yana cikin aiwatar da kiɗa na Gayauna; wato tun kafin a naɗa shi Sarautar Sarkin Kiɗan Sarkin Maradun yake shigowa da wasu halaye masu jan hankali; da buɗa ido a yanayin kiɗan da ya taras iyaye da kakanni suna yi a gidansu.

    Domin haka tun a aiwatar da waƙoƙin baka na Gayauna Musa Ɗanƙwairo yake shiryawa da sadar da:

    i) Waƙoƙin Noma

    A waƙoƙin noma, Makaɗa Musa Ɗanƙwairo, ya yi farin jini sosai, jama’a sun so waƙoƙinsa, musamman waƙoƙi na noma; waƙoƙi ne da suke ƙunshe da lugga da zaɓaɓɓun kalmomi. Ga kuma zayyana faruwar abubuwa da adonta harshen waƙa tun ma ba a turken yabo; da ɗiya na zambo da ba’a da sauransu ba. Sannan ga Ɗanƙwairo da murya mai zaƙi da kaurara zance kuma mai jan hankali mai sauraro.

    ii) Waƙoƙin Fada

    Waƙoƙin fada, waƙoƙi ne waɗanda Ɗanƙwairo ya yi wa ‘ya’yan Sarakuna da Sarakuna kansu da Hakimai; da Dagatai da masu riƙe da muƙaman Sarauta da sauran masu jinin Sarauta da makamantansu.

    iii) Sarkin Kiɗa

    Makaɗa Abdu Kurna Maradun (1899-1962) yayan Ɗanƙwairo, ya lura da irin tumbatsa cikin ƙwarewar da Alhaji Musa Ɗanƙwairo ya samu a kiɗan noma da na fada (Sarauta); inda kuma ya dinga kai gayaunan kiɗa, ya sutta kuma ya jima.

    Abdu Kurna ya dinga jan kunnuwan Musa Ɗanƙwairo, yana yi masa kandarki, har dai wata rana ya gaya wa ubangidansa, Sarkin Ƙayan Maradun da bakin waƙa yana shaida masa:

    Jagora: Sarkin Ƙaya wa Ƙwairo faɗa,
    ‘Y/Amshi: Bai barin halinai,
    Jagora: Daga zuwa Maƙera, ni maikiɗi,
    : Ban ji labarinai ba,
    : Sai can zuwa Ɗanmanau,
    : Na Ruwan Kiɗi sa sirdi,
    ‘Y/Amshi: Hau ko kana gane shi,
    : Na Ruwan kiɗi hau doki,
    : Tahi ko kana iske mai,
    : Shi yay yi damben girma,
    : Jikan Hassan ɗan Iro,
    : Sarkin Ƙaya mai gayya,
    : Na Magaji ba tagewa.

    (Musa Ɗanƙwairo, Waƙar Shi yay yi dambe girma & Gusau, 1988: sh. 224).

    iv) Waƙoƙi Game -Gari

    Kurwar Musa Ɗanƙwairo ta waƙar baka ba ta keɓe shi ya tsaya a rera waƙoƙin noma ko na fada ba. Musa Ɗanƙwairo ya kawo wani yanayin sussuka da daddare; yayin da ya shigo da aiwatarwa da rera waƙoƙin da a yau nake kira da waƙoƙi Game-Gari (Gusau, 2008a, sh. 161-162).

    Waƙoƙi Game-Gari kuwa sun ƙunshi waƙoƙin Malamai da Alƙalai da Lauyoyi da Attajirai; da sauran ‘Yan Kasuwa da Ma’aikata da ‘Yansiyasa da siyasar kanta da Sojoji da Jarumai da Dakaru da sauran Mayaƙa; da Mafarauta da Maharba da masu sana’o’i da Samari da ‘Yanmata da Dabbobi da Tsuntsaye da Ƙwari da Gulabe da Dazuzzuka da sauran madangantan waɗannan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Fitattun Iyayengida Na Ɗanƙwairo a Kiɗan Fada danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Bayanin Manyan Malaman Sunna A Kan Matsayin Sayyidina Husaini (RA) Da Ranar Ashura

    Bayanin Manyan Malaman Sunna A Kan Matsayin Sayyidina Husaini (RA) Da Ranar Ashura

    Haƙiƙa Sayyidina Husaini (Radiyallahu Anhu) yana da maɗaukakiyar daraja da alfarma a zukatan dukkan musulmi na ƙwarai musamman ma malamai.

    Wannan ya sa bakinsu ya zo ɗaya wurin bayyana darajojinsu da falalarsa da nuna alhini da takaicin yadda ƙarshen rayuwarsa ta kasance. Wannan yana tabbatar da ƙaryar masu cewa wai Ahlussunna suna ƙin Ahlulbaiti ko kuma wai suna murna ga abinda ya faru ga Husaini da sauransu na zaluntarsu da aka yi wannan sharri ne ƙage ne.

    Amma a lokaci guda Ahlussunna basa goyon bayan bidi’o’i da fitintinu da ake yi duk shekara idan ranar ashura ta zo har zuwa kwana arba’in, da sunan nuna juyayi da ta’aziyyar Husaini (Radiyallahu Anhu) da ‘yan tawagarsa, saboda babu wani daga cikin shugabannin Ahlul Baitin ko malamai na ƙwarai da suka aikata hakan. Su kuwa sun fi kowa son Ahlul Baiti da goyon bayansu (Radiyallahu Anhuma) da damuwa da halin da suke ciki.

    Maganganun malamai suna da yawa dangane da falalar Husaini (Radiyallahu Anhu) da kuma matsayinsu a kan kashe shi da aka yi a ranar ashura a shekara ta 61 daga hijra, saboda haka zan kawo kaɗan daga cikinsu domin su wakilci sauran.

    1- Ibn Abdulbarri Abu Amr Yusuf (A.H.S368 Y.M.S 495H)

    Ibn Abdulbarri Ibn Abdulbarri haɗaɗɗen malami ne mai tsoron Allah da faɗin gaskiya, masanin hadisi, a cikin littafinsa na tarihin sahabbai mai suna “Al-Isti’ ab yana cewa:

    “Husaini ya kasance mutum ne mai daraja, da tsananin riƙo da addini, da yawan azumi da salla da aikin hajji. Ya yi aikin hajji sau ashirin da biyar a ƙasa, an kashe shi ranar Juma’a goma ga watan Muharram shekara ta 61 daga hijira”.

    2- Ibnul Arabi Al-Maliki (A.H.S. 468 Y.M.S543)

    Shaihin malami Alƙali Abubakar Ibnul Arabi Almaliki bayan ya yi bayanin abinda ya faru a taƙaice na shahadar Husaini (Radiyallahu Anhu) sai ya ce:

    “Ina ma dai a ce mai girma ɗan mai girma, sharifi ɗan sharifiya Alhusaini ya yi zamansa a gidansa, cikin iyalansa, yaƙi sauraran duk wanda ya zo da maganar ya nemi halifanci, koda kuwa irinsu lbn Abbas ne da Ibn Umar, ina ma dai a ce ya tuna abinda kakansa ya faɗa a kan wansa Hassan(ɗan nan nawa shugaba ne Allah zai sasanta rundunoni biyu manya masu yaƙar juna saboda shi).

    Da ya tuna da ɗan uwansa ya rasa halifancin nan alhali yana da goyon bayan dukkanin rundononi kuma duk wasu manya a lokacin Suna tare da shi, sai ya ga to shi yaya za a yi ya samu wannan halifanci ta hanyar goyon bayan tarkacen mutanen Kufa. Ga kuma manyan sahabbai sun hana shi, Suna janye jikinsu daga neman halifancin da yake?

    Kai ni dai na rasa ta cewa sai dai kawai na miƙa wuya ga hukuncin Allah, da kuma alhinin rasuwar jikan Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ba don manyan sahabbai sun san cewa Allah bai ƙaddara halifanci ga iyalan Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ba, kuma bai kamata a shiga cikin fitina ba, ai da ba zasu taɓa ƙyale shi ba.

    3. Shaihul Islam Ibn Taimiyya (A.H.S 660 Y.M.S 728)

    A iya ɗan ƙaramin sani na, a cikin dukkan malamai da suka yi Magana akan abinda ya faru ga Hussaini (Radiyallahu Anhu) da kuma matsayinsu game da Yazidu da mahaifinsa Mu’awiyya, da kuma shi’anci, babu wanda ya fi shan zagi da tsinuwa da tsana har ma da Kafirtawa a wurin ‘yan Shi’a Kamar Ahmad Ibn Abdulhalim Ibn Abdussalam Ibn Taimiyya.

    Ibn Taimiyya ya wallafa wani babban littafi mai mujalladi tara mai suna “Minhajussunnatin Nabawiyya fi naƙdhi kalamis shi’a wal kadariyya” kan bayanin ɓacin aƙidun shi’a, a ciki yayi bayanai kan wannan mas’ala.

    Kuma matsayin da ya ɗauka, ba wani abu da ya keɓanta da shi ba, a’a akwai malamai da suka gabace shi da kuma waɗanda suka zo bayansa da suke akan wannan matsayi, amma shi suka fi jin haushi, har ma da yi masa ƙazafin ƙin Ahlul Baiti da ma Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam), saboda kawai tsanain kiyayya, da kwarewa a cikin karya da karya da kage.

    Wani babban malami wanda ya yi fice kan tattara littatafai da fatawowin Ibn Taimiyya, musamman waɗanda suke a rubutun hannu da buga su, mai suna Muhammad Ibn Ƙasim Rahimahullah, ya tattara maganganun da lbn Taimiyya yayi akan Ahlul Baiti, da sahabbai da matsayin Ahlusunna da ‘yan shi’a akansu, kasancewar masu zargin Ibn Taimiyya da ƙin Annabi (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) da iyalansa suna yawan ƙin maganganunsu daga wannan littafi.

    Amma fa a gaskiyar Magana, basa kula da amanar ilimi a wajen ciro maganganun nasa, saboda suna yanko iya wurin da ya dace da son ransu sai kawai Su gina hukunci a kai, su yanke duk wurin da suka san asirinsu zai tonu in sun kawo shi.

    Domin bayanin gaskiyar lamari kan matsayin Ibn Taimiyya akan wannan mas’ala da ma waɗansu mas’alolin zan kawo gaba ɗayan babin da malamin ya kawo a cikin littafin, sannan kuma in kawo bayanin matsayin wasu daga cikin fitattun almajiransa, domin in tabbatarwa da mai karatu cewa Ibn Taimiyya cikakken masoyin Manzon Allah ne (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) da iyalansa.

    Amma kifin wannan ga abinda yake faɗa a cikin “fatawa” ɗinsa da manyan baƙaƙe: “Tsinuwar Allah da ta Mala’iku da ta mutane gaba ɗaya ta tabbata  akan wanda ya kashe Hussaini, ko ya taimaka aka kashe shi. Kada Allah ya karɓi ibadunsa na farilla da na nafila.

    “Ƙaunar Ahlul Baiti, tilas ne wajibi ne a kanmu, shi ne ya sa kullum muke yi musu salati a cikin sallolinmu Tsinuwar Allah da ta mala iku da mutane baki ɗaya ta tabbata a kan maƙiya Ahlul Baiti.
    To mai karatu mu je zuwa da fatan ba za ka Ƙosa ba. Shaihul Islam Ibn Taimiyya ya ce:

    Domin karanta cikakken bayani a kan Manufar Makokin Husaini Da ‘Yan Shi’A Sukeyi danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Azumin Annabi Dawud (Alaihis salam) domin nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Gaskiyar Magana A kan Ashura wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Sunayen Wasu Kayan Abinci Da Itatuwa Da Turanci

    Sunayen Wasu Kayan Abinci Da Itatuwa Da Turanci

    Mu san sunayen turanci na wasu kayan abinci da itatuwa waɗanda muke yawan mu’amala da su, domin masu binciken amfaninsu ga lafiyar jiki.

    1 – Ɗoɗɗoya (Scent Leaf)

    2 – Ɗinya (Black Plum)

    3 – Ɗorawa (Honey Locust)

    4 – Gujjiya (Bambara Nut)

    5 – Goruba (Doum Palm)

    6 – Kaɗanya (Shea)

    7 – Kabewa (Pumpkin)

    8 – ’Ya’yan Kalaba ko Kuka (Baobab Fruit)

    9 – Kurna (Ziziphus)

    10 – Lansir (Cress)

    11 – Riɗi/Kantu (Sesame Seed)

    12 – Rinji (Senna)

    13 – Aya (Tigernut)

    14 – Zogale (Moringa)

    15 – Magarya (Jujube)

    16 – Tsamiya (Tamarind)

    17 – Aduwa (Balanites)

    18 – Mummuƙi (Bread)

    19 – Kanya (Ebony tree)

    20 – Danya (Sclerocarya Birrea)

    21 – Goro (Kolanut)

    22 – Gwate (Porride)

    23 – Tuwo (Fufu)

    24 – Kunu (Gruel)

    25 – Awara (Tofu)

    26 – Ɗumame (Recheuffe)

    27 – Dambu (Chicoins)

    28 – Fura (Millet Flour Balls)

    29 – Rama (Jute)

    30 – Abarba (Pineapple)

    31 – Kankana (Watermelon)

    32 – Ayaba (Banana)

    33 – Lemun Tsami (Lemon)

    34 – Kanumfari (Cloves)

    35 – Hulba (Fenugreek)

    36 – Kirfa (Cinnamon)

    37 – Kanwa (Potash)

    38 – Shuwaka (Bitter Leaf)

    39 – Albasa Mai Lawashi (Spring Onions)

    40 – Na’a Na’a (Mint Leaf)

    41 – Tafarnuwa (Garlic)

    42 – Shambo (Chilli)

    43 – Alayyahu (Spinach)

    44 – Gauta (Bitter Egg)

    45. – Yalo (Garden Egg)

    46 – Dabino (Date)

    47 – Masoro (Black Pepper)

    48 – Barkono (Birds Eye Chilli)

    49 – Kimba (African Black Pepper)

    50 – Ɓaure (Fig)

    52 – Accha (Fonio)

    53 – Habbatus Sauda (Black Seed)

    54 – Farar Wuta (Sulphur)

    55 – Namijin Goro (Bitterkola)

    Karanta Abubuwan Da Ya Kamata Mu Kiyaye Don Inganta Lafiyarmu
    Edita@rumasau-kallamu

  • Abubuwan Da Ya Kamata Mu Kiyaye Don Inganta Lafiyarmu

    Abubuwan Da Ya Kamata Mu Kiyaye Don Inganta Lafiyarmu

    MU DAINA AIKATA WAƊANNAN HALAYEN

    Aikata waɗannan ɗabi’un marasa kyau ga mutum na iya jawo masa ciwon ƙoda (Nephritis) don haka in ka ji ko kin ji wani abu da kin san halinki ne to ki daina don Allah.

    1. Riƙon fitsari: Jinkiri wajen yin fitsari cutar da kai ne mutum ya kasance yana jin fitsari amma ya ƙi zuwa ya yi yai ta riƙon sa yana takurewa, to ku sani duk sanda ƙoda ta tace fitsari ta turo shi ga mafitsara ba abinda da ake so irin a fitar da shi domin in kana riƙe shi to a hankali wani zai fara komawa ga ƙoda (kidney) wanda daga nan kuma matsala za ta fara afkuwa.

    2. Ƙin shan ruwa: Rashin shan ruwa wadatacce yadda ya kamata nan ma matsala ne, ko mutum yana jin ƙishi sai ya sha kaɗan ko kuwa ma mutum ya gama cin abinci amma ya ƙi shan ruwan kwata-kwata musamman abinci mai nauyi da mai gina jiki irin su (carbohydrate & protein). Mai irin wannan hali ya kuka da kansa shi ruwa ana so ka dinga shan sa ba sai in kana jin ƙishi ba. Sannan in da hali in abinci ka gama ci to ka sha tea ko ruwan ɗumi ba ruwan sanyi ba.

    3. Yawan shan gishiri akwai matsala ga ƙoda ba sai ga mai hawan jini ba, musamman mutanen da ke da irin ɗabi’ar nan ta ƙarawa abinci ko miya ɗanyen gishiri idan bai musu daidai ba, to su ma su kiyaye yana interfering da aikin cortex cikin ƙoda.

    4. Rashin shan magunguna ga ƙananun cututtuka da ake ganin ko ba a sha ba za a warke kamar jin zafi ko murɗawar ciki, zafin fitsari ko ƙaiƙayin maƙogwaro.

    5. Sannan kuma shan magunguna ba bisa ƙa’ida ba kuma ba bisa umarnin likita ba wato (self medication) wannan na cutar da ƙoda ƙwarai da gaske don haka duk mai irin wannan shi ma to ya sani ya miƙawa ciwon ƙoda takardar gayyata.

    6. Yawan cin nama fiye da ƙa’ida: Su ma masu wannan al’adar su sani cewa ba burgewa ba ne a ce ka mayar da cin nama kullum kullum ko kuwa kwana 1 ko 2 kurum kake ɗaga ƙafa, hasali ma ƙila ba ka ko ba ki da ƙoƙarin motsa jiki, Sannan in kuka samu sai kun ji kun ci kun yi hani’an to mutum ya kiyayi kansa.

    6. Rashin cin wadataccen abinci: Mutum ya riƙa ma kansa ƙwauro da gangan saboda tsurfa ko kuwa tunanin kar ya yi ƙiba, to masu irin wannan suma su kula.

    SHAWARA TA A GAREKU

    Shi fa jiki yana son service kamar mota ce in ana mata juye ta fi lafiya. Don haka jiki ma na buƙatar hutu, wanka, sanya tsaftataccen tufafi da kuma abinci mai kyau ba mai tsada ba. Yana da kyau kar ka mayar da cikin ka kodayaushe abinci iri guda, wato ka yi ta cin carbohydrate ko protein, jiki baya son haka shi yasa masu yawan cin carbohydrate kan yi fama da kitse a jika haka su ma masu cin protein kan yi ta fama da nauyin jiki.

    Ki sani in kina cin waɗannan (masara, tuwo, dankali, doya, rogo, garin kwaki, flower,) ko da ba rana ɗaya kike haɗa su ba, abu ɗaya kike ci kullum domin duk carbohydrate ne, don haka ake gaurayawa da vitamins, lipids, water, protein, and minerals a yi tsari me kyau.

    Da an ga alamun cuttukan sanyi wato ƙaiƙayin gaba, ko fitar ruwa a gaba ga mace ko namiji a nemi magani, ku daina yadda da zancen cewa ko ba magani yana tafiya ko ka ji wasu ma ana ce musu wai mataccen maniyyi ne, duk ƙarya ce ba wani mataccen maniyyi a likitan ce.

    Karshe Da An Ji Alamun;

    Yawan ciwon baya daga kasa ko sama wajen kafada, canzawar ɗanɗanon baki zuwa kalar kanwa ko ƙarfen da ya yi tsatsa, canzawar fitsari zuwa duhu-duhu kuma kaɗan-kaɗan in an je yi, yawan ganin jiri da kasa samun nutsuwa, yawan kasala, to a hanzarta zuwa a ga likita domin waɗannan alamun ciwon ne.

    Allah ya kare mu! Ya ƙara mana lafiya da zama lafiya!!!

    Karanta Yadda Ciwon Baki Yake
    Edita@rumasau-kallamu

  • Illolin iPhone Ga Tarbiyyar ‘Ya’yanmu

    Illolin iPhone Ga Tarbiyyar ‘Ya’yanmu

    Galibi mutane suna ɗaukar annobar cututtuka da masifun rashin zaman lafiya su ne kaɗai masifu; ana mantawa da wasi abubuwa da ke yaƙar mu kuma suke yin galaba sau tari ba tare da mai da hankalinmu a kansu ba.

    Musulunci da ya zo ƙasar Hausa ya tarar da Hausawan wancan lokacin a kan ɗabi’u kala-kala, sai ya tsame na gari bai yi hani a kansu ba amma waɗanda suka danganci baɗala, tsafi ko kafirci nan take ya taka musu birki. Alhamduluillahi; Al’ummar Hausawa suka kasance masu ɗa’a da yakana da amana da taimakekeniya da rufin asirin junansu, a ƙolololuwa kuma masu tsoron Allah da gaske, ga shi wasu ba su da tarin ilimin addinin musulunci irin na wannan zamanin.

    An sannu sannu Malam Bahaushe ya yi watsi da waɗannan gwalagwalan ɗabi’u na gari wanda ya sa ko a da a kudancin Najeriya iidan za a yi alƙalanci tsakanin mutane, Bahaushe ake nema kokuma ana son a ba da ajiya ko amana shi ma Bahaushe ake nema. Na san mutanen kudu da dama waɗanda a wancan lokacin manyan abokanensu Hausawa ne har ma su suka kasance musu manyan abokai lokacin aurensu a can ƙasashen nasu na kudu.

    Zuwan Turawa da kuma mutanenmu da suke yawan zuwa Turai sun zo da ɗabi’un Nasara amma a wancan lokacin ƙyamatarsu ake yi, yanzu kuwa rungumarsu ake yi. A sannu-sannu yanzu Yahudanci da Nasaranci ya ratsa Hausawa har wasu na ganin abin kunya ne a ce ‘ya’yansu sun fi iya Hausa a kan Turanci. Bature ya yi tasiri wajen yaɗa manufofinsa da muradansa ta hanyar mutanenmu saboda haka har yanzu wannan igiyar ta “Indirect Rule” ba ta tsinke ba.

    Jama’a ina so ku yi nazari cikin hankali da nutsuwa wajen tantance abubuwan Nasara da suke amfanar mu da waɗanda suke cutar da mu. Da yawa wasu suna ganin in suka ƙyale ‘ya’yansu suna yin abin da suke so shi ne wayewa, ci gaba da kuma zaman lafiyarsu. A da talaka ya tsaya a matsayinsa amma a yau haɗa kansa yake da kowa, wannan shi ne musabbabin jefa al’ummar Hausawa cikin yanayin da suke, kowa ya bar matsayinsa yana kokawar komawa na wani.

    Daga ƙarshe ina so in jawo hankalin iyaye, yayye da duk wanda tarbiyya take hannunsa da ya duba irin barnar da kafofin sadarwa suke yi mana sannan babbar masifar iPhone da take yaɗuwa kamar wutar daji a tsakanin ‘ya’yanmu musamman mata. Kashi sama da casa’in na ‘ya’yan marasa ƙarfi da suka mallaki iPhone sun mallake su ne ba ta hanya mai kyau ba.

    Babu abin da ba a yi da ‘ya’yan Hausawa don kawai a ba su iPhone a nan Kano da kuma wajen Kano. Zina, luwaɗi, maɗigo, shaye-shaye, tsafi, guduwa daga gida da dai sauransu, yin su ake a ‘kulli yaumin’ amma mun yi biris ko kuma mun yi kunnen-uwar-shegu, ba ta wannan muke ba.

    To wallahi wutar dajin nan ta kusa ƙone mu ƙurmus, sai dai tokar mu idan ba mu tashi haiƙan wajen kashe ta ba. Wayar iPhone ba ƙaramar masifa ba ce, kuma ta saka yara da dama yi wa iyayensu maza rashin kunya da rshin yi musu biyayya da tsanar su da kallon su a matsayin waɗanda suka gaza don kawai ba su mallaka musu iPhone ba, duk sun manta da ɗawainiyar da iyayen suka yi da su da iyayensu mata har zuwa girmansu da yanzu suke jin sun kawo ƙarfin su mallaki iPhone.

    Wayar iphone ta kasance hanya da take kangarar da yara take iskantar da yara take sa yara yin shirka da dai sauransu. Ya kamata gwamnati da jama’a su yi wani babban motsi wajen ganin wannan masifa ba ta ƙara gaba ba.

    Ɗan uwanku Taufiq Aminu Yahya, Jami’ar Bayero Ta Kano

    08035972272 taufiqyahya29@gmail.com

    Karanta Zikiri Yayin Shiga Gida

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Sababbin Karin Maganar Hausa

    Sababbin Karin Maganar Hausa

    Sakamakon zagayowar ranar Hausa ta duniya ta shekarar 2025, ga wasu sabbin karin magana:

    1. Abin nema ya samu matar Bakano ta haifi buhun kuɗi.

    2. Abin nema ya samu matar Basakkwace ta haifi buhun taba.

    3. Abin nema ya samu matar Bazazzage ta haifi kunyar doya.

    4. Abin nema ya samu matar Ɗangaruwa da cikin tulu.

    5. Abin nema ya samu matar Marubuci ta haifi biro.

    6. Abin nema ya samu matar Ɗanjarida ta haifi amsa-kuwwa (Speaker)

    7. Abin nema ya samu matar liman ta haifi ladan.

    8. Abin nema ya samu matar Likita ta haifi allura.

    9. Abin nema ya samu matar mai-shayi ta haifi mummuƙi (burodi)

    10. Abin nema ya samu matar malami ta haifi alli.

    11. Abin nema ya samu matar Bafulatani ta haifi saniya.

    12. Abin nema ya samu matar direba ta haifi mota.

    13. Darajar sana’a wanzami yake taɓa gemun sarki.

    14. Ba kuka na ba, ɗan kishiya ya faɗa rijiya ya mutu.

    karanta Isra’i Da Mi’iraji

    Edita@rumasau-kallamu

  • Gudunmawar Sarki Abdulazeez Da Birtaniya Wajen Kafa Ƙasar Saudi Arabia

    Gudunmawar Sarki Abdulazeez Da Birtaniya Wajen Kafa Ƙasar Saudi Arabia

    Abdulaziz Ibn Saud da Kafuwar Ƙasar Saudi Arabia: Binciken Tarihi Kan Rawar Da Birtaniya Ta Taka

    Taƙaitaccen Bayani

    Ƙirƙirar masarautar Saudi Arabia a shekarar 1932 ba ta kasance wani abu da ya zo kwatsam ko kuma sakamakon ƙoƙarin gida kawai ba. A haƙiƙanin gaskiya, ta samo asali ne daga jerin yaƙe-yaƙe da dabarun siyasa da Abdulaziz Ibn Saud (1876–1953) ya gudanar har ya daidaita mulki a yankin Larabawa.

    Nasarorinsa na farko sun samo asali daga jarumta, basira, da kuma aƙidar Wahabiyya, amma daga baya rawar da Birtaniya ta taka ta zama tilas wajen tabbatar da ƙarfinsa. Wannan maƙala ta yi nazari kan yadda aka ci garuruwan Riyadh (1902), Makka (1925), Madina (1929), da Jidda (1932), tare da binciken yadda Birtaniya ta shiga wajen taimakawa kafuwar ƙasar Saudi Arabia.

    Gabatarwa

    Tashin Abdulaziz Ibn Saud, wanda aka fi sani da Ibn Saud, ya zama babbar alama a tarihin zamani na Larabawa. Rushewar ikon daular Usmaniyya bayan yaƙin duniya na ɗaya ya bar giɓi da shugabannin Larabawa daban-daban suka yi ƙoƙarin cikawa. Ibn Saud ya fito fili a matsayin babban mai kafa sabon ƙasa.

    Duk da cewa tarihin ƙasashen Larabawa na nuna cewa nasarorinsa sun fito daga ƙoƙari na cikin gida, shaidu na tarihi sun nuna cewa Birtaniya wadda take son tabbatar da tasirinta a Tekun Fasha da hanyoyin zuwa Indiya, ta taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar masa da iko.

    Yaƙin Ƙwace Riyadh (1902)

    Mataki na farko na kafa Saudi Arabia ya kasance a 15 ga Janairu, 1902, lokacin da Ibn Saud ya sake ɗaukar Riyadh daga gidan Rashid. Da ƙaramar tawaga, ya kai farmaki, ya kashe gwamnan Rashid, sannan ya maido da mulkin dangin Al Saud a Najd. A wannan lokaci, nasarar ta fito ne daga jarumta da ƙoƙarin kansa, ba tare da wani taimako daga ƙasashen waje ba. Birtaniya a lokacin tana fiye da kula da Kuwait da sauran ƙasashen Tekun Fasha, ba ta ba shi goyon baya kai tsaye ba.

    Yaƙin Hijaz da Ƙwace Makka (1925)

    Bayan ya tabbatar da iko a Najd, Ibn Saud ya nufi Hijaz, wanda Sharif Husayn bin Ali ke mulka shugaban juyin Larabawa a lokacin yaƙin duniya na ɗaya. Dangantakar Husayn da Birtaniya ta lalace saboda ya ƙi amincewa da tsarin da Turawa suka shimfiɗa a yankin. A 1924–1925, Ibn Saud ya shiga Hijaz, ya fatattaki sojojin Sharif, ya kuma mamaye Makka.

    Kodayake ba da taimakon kai tsaye Birtaniya ta yi ba, ƙin tallafa wa Sharif Husayn ya zama taimako a gefe ga Ibn Saud. Daga bisani kuma, Birtaniya ta amince da mulkinsa domin samun abokin hulɗa mai sauƙin sarrafawa a Hijaz.

    Ƙwace Madina da Yaƙin Ikhwan (1929)

    Bayan Makka, Ibn Saud ya mamaye Madina a shekarar 1929. Amma wannan nasara ta jawo cece-kuce tsakaninsa da Ikhwan, mayaƙan Wahhabi da suka taimaka masa a yaƙe-yaƙe. Ikhwan sun nuna rashin jituwa saboda tattaunawarsa da Birtaniya da kuma hana su ƙara faɗaɗa mulki zuwa Iraq da Kuwait (masu ƙarƙashin Birtaniya).

    Wannan rikici ya kai ga Yaƙin Sabilla (1929) inda Ibn Saud, da taimakon makamai, harsasai, da har ma jiragen saman yaƙi daga Birtaniya, ya fatattaki Ikhwan. Wannan ya nuna cewa a wannan lokaci, Birtaniya ta taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da nasararsa.

    Ƙwace Jidda da Ayya­na Saudi Arabia (1932)

    Birnin bakin teku na Jidda ya faɗi ƙarƙashin ikon Ibn Saud a 1932 bayan doguwar kakkabo. A wannan lokaci, Birtaniya ta riga ta amince da ikon sa ta fuskar diflomasiyya, ta kuma rattaba hannu kan yarjejeniyoyi da suka tabbatar da shi a matsayin shugaba na Najd da Hijaz. Ranar 23 ga Satumba, 1932, aka ayyana masarautar Saudi Arabia a hukumance. Wannan nasara ta samo asali ne daga haɗin gwiwar yaƙin soja da kuma goyon bayan diflomasiyyar Birtaniya.

    Kammalawa

    Shaidun tarihi sun nuna cewa tashi da nasarar Abdulaziz Ibn Saud ba za a iya raba su da muradun siyasar Birtaniya ba. Duk da cewa nasararsa ta farko a Riyadh ta fito daga ƙarfin kai, mamaye Makka, Madina, da Jidda ya kasance da taimako kai tsaye ko a kaikaice daga Birtaniya. Masarautar Saudi Arabia ta fito ne ba kawai daga jihadi da ƙoƙarin gida ba, amma har da hulɗar siyasar mulkin mallaka. Wannan fahimta ta taimaka wajen gane asalin Saudi Arabia da kuma dangantakarta da siyasar duniya tun asali.

    Ƙafafun Bayani

    1. Madawi al-Rasheed, A History of Saudi Arabia (Cambridge: Cambridge University Press, 2010), 34–36.

    2. Joseph Kostiner, The Making of Saudi Arabia, 1916–1936: From Chieftaincy to Monarchical State (Oxford: Oxford University Press, 1993), 82–85.

    3. John S. Habib, Ibn Sa‘ud’s Warriors of Islam: The Ikhwan of Najd and Their Role in the Creation of the Saudi Kingdom, 1910–1930 (Leiden: Brill, 1978), 205–210.

    Karanta Tarihin Kafuwar Ƙasar Iran

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ciwon Baki Yake (Mouth ulcers)

    Yadda Ciwon Baki Yake (Mouth ulcers)

    “Mouth ulcers” Ɗaya ne daga cikin ciwukan baki da a turance akan kirasa da canker sore (shankaso), Ƙaramin ciwo ne na kwailewar fata dake faruwa a cikin baki musamman a jikin leɓe ta ciki daga sama ko ƙasa, ko gefen leɓen daga hagu ko dama, wani lokacin kuma a ƙasan harshe. Yana da matuƙar zafi, zugi da raɗadi.

    Asali yana farawa ne daga ƙanƙanin kumburi kafin ya kwaile ko a ga yayi ja, inda daga nan sai fari-fari da ja inda nan take yakan iya fara zafi sosai, musamman idan aka ci abinci mai zafi, yaji, zaƙi ko mai ɗaci.

    Galibi girmansa ba ya wuce girman ƙwayar dawa ko ɗan abinda ba-a-rasa ba. Duk da yana hana sukuni amma lokuta da yawa yana warkewa da kansa cikin sati 1 zuwa 2.

    ME KE HADDASA SHI

    Wani lokacin akan rasa dalilinsa kai tsaye, amma a wasu garkuwar jikinsu ce ke cin kanta da kanta wato Autoimmune stomatitis wanda shi ke jawowa,  wanda za a ga har jini yake ya ƙi ya warke, ko ya warke bayan magani sai ya kuma dawowa, a ɗau shekaru ana fama, tunda Autoimmune ba shi da magani zuwa yanzu. Amma masu wancan nau’in ba su da yawa amma suna shan azaba.

    Sai a sauran mutane;

    1. Taune leɓe ko rauni a baki na daga abinda ke jawo shi, wanda wannan kuwa na nufin ko da ta hanyar taune leɓen ko harshe yayin cin abinci ko a mutane masu sanye da Braces na haƙora.

    2. Sannan rayuwa cikin matsatsi, wahala da damuwa wato dai “stress” kowanne iri ciki har da na lokacin Haila a Mata wato “stress during menstruation” na jawo irin wannan sore ɗin saboda motsawar Hormones daga normal zuwa Higher concentrations.

    3. Ƙarancin sinadaran bitamins da minirals musamman nau’in bitamin B12, iron, forlate da zinc, duk suna sanya mutum cikin hatsarin samun canker sore.

    4. Ciye-ciye ko mu’amala da abubuwan da jikin mutum ba ya so wato Allergic wanda wannan hatta a makilin akwai wanda bakinsa baya son wani nau’i na ingredients dinsa, ko abinci irin su; Ayaba, lemon ɓawo, chocolate, coffee, strawberries, gyaɗa, da cheese.

    5. Rashin samun isasshen bacci tare da gajiya wannan ma na ta’azzara matsalar.

    6. Sannan wani lokacin hakan na iya zama dalilin wani ciwo da ake da shi a jika ko dalilin wani magani da mutum ke sha, kamar magungunan chemotherapy a masu cutar Cancer, HIV, Magungunan tarin T.B, magungunan cutar farfaɗiya ko Sara (epilepsy seizures)

    7. Hakazalika shan taba sigari, wiwi ko SHISHA duk kan iya haddasa wannan yanayin, ko shan abu me zafi da ƙarancin tsaftar baki.

    MAGANIN MATSALAR

    1- Kamar yadda nace galibi yana warkewa da kansa, amma za ku iya: Riƙa wanke baki da ruwan gishiri sau 3 ko 4 a yini a riƙa kurkurawa ana wankewa musamman kafin kwanciya bacci.

    2- Shafa maganin rage zugi; irin su benzocaine gel ko alpa-xylocaine gel, ko magungunan shafawa da ke kashe ƙwayoyin cuta irin su BONJELA GEL ko wanke baki da CHLORHEXIDINE MOUTH WASH maimakon ruwan gishirin. Duk ana Saida su a manyan pharmacy store.

    3- Sai kiyaye cin abinci mai yaji, mai zafi ko mai zaƙi sosai.

    4- Sai kuma a riƙa shan ruwa sosai.

    IDAN DUK BAYAN WANNAN AKA GA YA CIGABA:

    Ta hanyar ganin yana ƙara a girma sosai, ko yana ciwo matuƙa wataƙila har da jini, ko bai warke cikin sati biyu ba, ko yana yawan dawowa bayan ya warke. To yana da kyau a zo a ga likita ko likitan haƙori don a duba ko akwai wata matsala ta cikin jiki da ke jawo hakan walau ƙarancin waɗancan vitamins ɗin, Autoimmune ko wasu cuttukan na ciki domin ulcer ma iya jawowa idan duodenal ce tunda jiki ba ya amfana da iron ɗin da ake samu idan akwai ta. Da fatan an ilmantu.

    Karanta Zubar Da Ruwa A Farko Da Kuma Ƙarshen Juna Biyu

    Edita@rumasau-kallamu