Category: WikiHausa

Yadda ake amfani da WikiHausa

  • Nauye-nauyen Rayuwar Aure

    Nauye-nauyen Rayuwar Aure

    A Musulunci, rayuwar aure ba ta kyautatuwa ta zama nagartacciya, har sai idan an aiwatar da ita ta salon da Musulunci ya tsara, ta hanyar ɗora wa ma’aurata wasu nauye-nauye da ake buƙatar  da su sauke su kamar haka:

    1. Haƙƙoƙin mace a kan mijinta.
    2. Haƙƙoƙin miji a kan matarsa.
    3. Haƙƙoƙin da miji da mata suke tarayya a kansu.
    4. Haƙƙin wanda mutuwa ta raba shi da abokin zamansa daga cikin ma’aurata.

    1. Haƙƙoƙin Mace a Kan Mijinta:

    (a) Sadaki: Wanda bayaninsa ya riga ya gabata.
    (b) Ɗora iyali a kan bin Allah tare da rainonta da kyawawan ɗabi’u.
    Shi wannan haƙƙi na biyu da samuwarsa da kuma ɗorewarsa ne mace za ta kyautata tsakaninta da ubangijinta, da kuma tsakaninta da bayinsa.

    Da farko Allah Mai girma da Buwaya ya ce:
    “Ka ambaci (labarin) Isma’il cikin wannan littafi (Alƙur’ani), haƙiƙa shi mai cika alƙawari ne, kuma Annabi ne Manzo. Ya zamanto yana umartar iyalinsa da (tsaida sallah da kuma ba da zakka, sannan kuma shi yardajje ne a wajen ubangijinsa ).

    Abin nufi a nan, Annabi Isma’il yardajjen Allah, a zamansa da iyalinsa yana umartar su ne da su riƙa tsayar da sallah, kuma su riƙa bayar da zakka, domin alaƙarsu da Ubangiji ta kyautata.

    Sannan kuma mun ji cewa shi mutum ne mai cika alƙawari, sanin kowa ne kuma duk wanda yake haka za ka tarar yana ƙoƙarin rainon iyalinsa da yin haka. Sannan kuma Allah ya ce da Annabi Muhammad (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi):

    “Ka umarci iyalinka da tsaida Sallah kai ma kuma ka yi haƙurin dawwama a kan tsaida ita, ba za mu tambaye ka dukiya ba, mu ne ma za mu azurta ka, kuma kyakkyawan ƙarshe (duniya da lahira ) ga masu tsoron Allah yake”.

    Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ) ya aiwatar da wannan umarni da Allah yayi masa kamar yadda Imamut- Tirmizi ya rawaito hadisi cewa, an karɓo daga Ummu-salama Allah ya yarda da ita ta ce:

    “Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya kasance idan watan Ramadan ya rage kwana goma ya ƙare, ba ya barin ko da mutum ɗaya daga cikin mutanen  gidansa matukar dai zai iya yin sallar dare face sai ya tashe shi (domin ya yi)”.

    To, ‘yan uwa, idan Annabi bai bar sallar nafila ta wuce mutanen gidansa ba; ina kuma ga sallar farilla. Sannan kuma Allah Maɗaukaki ya ce:

    “Ya ku waɗanda kuka ba da gaskiya, ku tserar da kanku da kuma iyalanku (daga shiga ) wuta (wadda ) mutane da duwatsu ne makamashinta, kuma akwai wasu ƙarfafan mala’iku masu kauri da suke tsaron ta, waɗanda ba sa saɓa wa Allah abin da ya umarce su da shi, kuma suna aikata duk abin da aka umarce su da shi”.

    A wannan ayar kuma kiran muminai gaba ɗaya Allah ya yi, sannan ya umarce su da su dage su bi irin turbar da Annabawa suka bi, wajen ɗora kansu da iyalansu akan hanyar bin Allah da nisantar saɓa masa, domin su gudu tare su kuma tsira tare. Har wa yau, Bukhari ya rawaito hadisi da aka karɓo shi daga Malik ɗan Huwairis Allah ya yarda da shi yace: Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce da (ayarin) jama’ar Abdul- Kais da suka zo wajen

    “Su kiyaye imaninsu da kuma ilmin da ya sanar da su shi, sannan kuma ya ce da su, “Ku koma wajen iyalanku ku sanar da su”.

    Saboda waɗannan dalilan da muka ji ya zama lallai akan miji ya sanar da matarsa ilmin yadda za ta bauta wa ubangijinta, ko kuma ya tura ta inda za ta je ta koya, kamar yadda matan sahabbai suke zuwa wajen Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ) su koyo addini.

    Bayan haka, an karɓo daga Amru ɗan Ahwas Allah ya yarda da shi ya ce, ya ji Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) a hajjinsa na bankwana yana cewa: “Ku saurara, ku yi wa mata wasici da alheri”. ( Tirmizi ne ya rawaito shi ). Haka kuma an karɓo daga A’isha (Allah ya yarda ita ) ta ce: ” (wata rana ) Yahudawa sun zo wajen Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) sai suka ce da shi: “Assamu alaikum” wato halaka ta tabbata a kanku, a maimakon su ce: “Assalamu alaikum” wato amincin ya tabbata a gare ku, jin haka, sai A’isha ta ce: Halaka a kanku, Allah kuma ya tsine muku; ya yi fushi da ku. Sai Annabi ya ce da ita:

    A a A’isha, yi a hankali, ina umartar ki da yin sauƙi, kuma ki kiyayi kausasawa da munanan maganganu. Sai kuwa ta ce da Annabi ba ka ji abin da suka ce ba ne? Annabi ya ce: To ke ba ki ji abin da na ce da su ba? Ai na mayar musu da martani da cewa a kansu dai. Sai Allah ya amsa mini addu’ar da na yi musu, su kuma ba zai amsa musu wadda suka yi mini ba. (Bukhari ya rawaito shi).

    A nan idan muka lura da kyau, za mu fahimci cewa, waɗannan hadisai suna ɗora magidanta ne a kan hanyar da ya kamata su ɗora matansu a kai, ta nusar da su yadda ya kamata su zauna da mutane a cuɗanyarsu da su. Allah dai ya ba mu ikon kulawa da kuma aiki da wannan koyarwar ta Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), amin.

    (c) Samar wa Mace Mazauni (Gida ko ɗaki):

    Shi kuma wannan nauyi ya hau kan miji ne a sakamakon faɗar Allah Madaukaki da ya ce:
    “Ku zaunar da su (mata) a inda kuke zaune daidai halinku, kar ku cuce su don ko ƙuntata musu”. Da kuma faɗar Allah Maɗaukaki cewa: “Ku ji tsoron Allah Ubangijinku kada ku fitar da su daga ɗakunansu, suma kada su fita, sai dai idan sun zo da mummunan aiki mabayyani, waɗancan iyakokin Allah ne, to haƙiƙa ya cuci kansa”.

    Saboda haka, haramun ne mai gida ya ce da matarsa ta fice ta bar masa gidansa, ko ɗakinta don ya sake ta, matuƙar dai ba ta gama idda ba. Haka kuma ita ma mace bai halatta ta bar gidan mijinta ba don ya sake ta har sai bayan ta gama idda. Wannan sai ya tabbatar mana da cewa alhakin miji ne ya tanadar wa matarsa mazauni.

    (d) Ciyarwa da Tufatarwa:

    Haka ma ciyarwa da tufatarwa, haƙƙƙi ne da mace take da shi a kan mijinta. Saboda faɗar Allah Maɗaukaki ya ce: “Ciyar da mata da tufatar da su gwargwadon iko, wajibi ne a kan wanda aka haifawa ɗa, ba a ɗora wa (kowanne) rai sai gwargwadon ikonsa”.

    A wata ayar kuma Allah Maɗaukaki ya ce: “Mai yalwa ya ciyar daga yalwarsa, wanda kuma aka ƙuntata arzikinsa, (wato talaka), to, ya ciyar daga ɗan abin da Allah ya ba shi, Allah ba ya ɗorawa kowacce rai sai abin da ya ba ta, da sannu Allah zai sanya sauƙi bayan matsi (tsanani)”.

    A hadisance kuwa, an karɓo daga Hakim ɗan Mu’awiya daga mahaifinsa (Allah ya yarda da shi) ya ce: “Na tambayi Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) cewa, menene haƙƙin matar kowannenmu a kansa? Sai ya ce: “Ka ciyar da ita idan ka ci, ka kuma tufatar da ita idan ka tufata…”. ( Ahmad da Abu Dawud da wasunsu ne suka rawaito shi).

    Sannan kuma sahabin Annabi Amru ɗan Ahwas ( Allah ya yarda da shi ) ya ce: Haƙiƙa ya ji Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) a hajjinsa na bankwana yana cewa: “Ku saurara, haƙiƙa matanku na da haƙƙi a kanku, haƙƙinsu a kanku, ku kyautata tufatar da su, da ciyar da su”.( Tirmizi ne ya rawaito).

    Bisa dogaro da waɗannan dalilai, ya zama tilas a kan miji ya ciyar da matarsa, ya tufatar ita gwargwadon irin halin da yake da shi. Sannan kuma amana ce a wuyan miji ya ciyar da matarsa da halal ba da haramun ba.

    Haɗarin Ƙuntata wa iyali wajen ciyarwa

    Musulmin da Allah ya yi masa yalwar abin da zai ciyar da iyalinsa, da abin da zai tufatar da su, amma sai ya zama yana ƙuntata musu, ta hanyar ƙin wadata su da abin da zai ishe su, to, a zahirin gaskiya babu wanda yake cuta sai kansa, domin kuwa Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce: “Ya isa mutum laifi, ya riƙa tozarta wanda yake ci a ƙarƙashinsa”. (Abu Dawuda ne ya rawaito shi).

    Kuma an karɓo daga Abu Huraira (Allah ya yarda da shi) yace: Haƙiƙa, Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) Ya ce: “Babu ranar da bayi za su wayi gari a cikin ta, face sai wasu mala’iku biyu sun sauko, sai ɗaya daga cikinsu ya kama cewa: “Ya Allah ka bai wa mai ciyarwa”. Sai shi kuma ɗayan ya ce: “Ya Allah ka haɗa matsolo da asara”. (Bukhari da Muslimu ne suka rawaito shi). Don haka, ‘yan uwa sai a yi hattara.

    Bayan haka, da Allah zai datar da iyalan malam matsolo da samun wata kafa da za su riƙa ɗiban abin da zai ishe su daga cikin dukiyarsa, a shari’ance, ba su yi laifi ba, in sun ɗebi abin da zai ishe su, matuƙar dai ba za su yi ɓarna ba.

    An karbo daga A’isha (Allah ya yarda da ita) ta ce: “Hindu ‘yar Utba matar Abi Sufyanu ta shiga wajen Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) sai ta ce: “Ya Manzon Allah, mijina Abu Sufyan matsolon mutum ne, ba ya ba ni abin ciyarwa da zai ishe ni, kuma ya ishi ‘ya’yana, sai in na ɗebi wani abu daga cikin kudinsa ba da saninsa ba, shin ko ina da laifi game da hakan da nake yi? Sai Annabi ya ce: “Ki ci gaba da ɗaukar abin da zai ishe ki ya ishi ‘ya’yanku daga kuɗinsa”. Wato yin hakan ba laifi ba ne. (Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi).

    Sannan dai ita wannan ta’ada ta matsolanci, haɗarin ta yana da yawan gaske, domin kuwa tana sa mai yin ta ya rasa samun alherin da masu ɗaukar abin hannunsu su bayar suke samu:
    Na Farko: zai rasa samun addu’ar alherin da mala’ika yake yi wa masu ɗaukar abin hannunsu su bayar duk wayewar garin Allah, kamar yadda muka ji.
    Na Biyu: Ya rasa kwarjinin da masu bayar da abin hannunsu suke samu a wajen waɗanda suke agazawa.
    Na Uku: An karɓo daga Abu Huraira (Allah ya yarda da shi) ya ce, Manzon Allah (tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce: “Hannun da yake bayarwa ya fi hannun da yake karɓa. (In za ka bayar) ka fara da wanda nauyinsa ke kanka, ka ba wa babarka, da babanka, da ‘yan uwanka, sannan wanda ya fi kusa da kai, sai wanda yake da kusanci da kai”. (Nasa’i da Darakudni ne suka rawaito shi, kuma Darakudni da ibn Hibban suka inganta shi).

    Domin karanta cikakken bayani a kan Dokokin Suturar Musulma danna nan

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Nagartacciyar Rayuwar Aure wanda Abubakar Abbas ya wallafa shi Domin karanta cikakken littafin danna nan.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Siffofin Masu Ba Da Tarbiya Suke

    Yadda Siffofin Masu Ba Da Tarbiya Suke

    Masu hikima suna cewa: In mutum ya ce zai ba ka riga to ka dubi ta jikinsa kuma “wanda ba shi da abu ba zai iya bayar da shi ba.”

    A kan haka ya wajaba a kan duk wani wanda nauyin tarbiyya ya hau kansa iyaye, malamai da shugabanni ya kasance mai tarbiyya ne shi a kan kansa.

    Wani mutum ya tambayi malamansa cewa ya koya masa yadda ake yin tarbiyyar ‘ya’ya a lokacin ‘yarsa ta fari tana wata ɗaya da haihuwa, sai malamin ya ce da shi ai kuwa ka makara. Saboda ita tarbiyya tun kafin a yi aure ake fara yin ta ba sai an haifi ɗan ba.

    Malamai sun yi bayanin siffofin da ya wajaba mai ba da tarbiyya ya siftantu da su in dai yana son ya sami nasarar aikin tarbiyya kuma ya yi tasiri.

    A Taƙaice Ga Waɗannan Siffofin

    Ya kasance mai haƙuri da juriya da naci, kada ya ɗauka cewa tarbiyya aiki ne na sha yanzu magani yanzu.

    1. Ya yarda cewa haƙƙi ne wajibi a kansa. Ya rinƙa jin haka a ransa a kowane lokaci. wannan zai hana shi yin watsi da tarbiyyar iyalinsa.
    2. Ya rinƙa sa ido da lura da bibiya, saboda tarbiyya kamar dashe ne in ba a bibiyarsa da kula da shi sai ya bushe ya lalace ko dabbobi da ƙwari su kashe shi.
    3. Yi dan Allah (Ikhlasi) kada mutum ya nemi wani lada ko yabo a kan tarbiyyar ‘ya’yansa da iyalınsa sai a wurin Allah kawai. Saboda haka ban da alfahari ban da fariya ban da gorantawa ‘ya’ya da iyali ban da raina ‘ya’yan wasu.
    4. Tarbiyya tana buƙatar tausasawa da bin al amura sannu-sannu daki- daki, tsanani da gallazawa kawai ba sa kawo gyara, dole sai ana cizawa ana hurawa.
    5. Mai ba da tarbiyya shugaba ne, saboda haka ya kamata ya siffantu da siffofi na shugabanci ya kasance jarumi, mai adalci, mai kwarjini, mai iya ɗaukar nauyin waɗanda yake jagoranta, mai kyauta, sauƙin kai da saussauci a inda ya dace, mai tsanani a inda ya dace, da dai sauran siftofi na jagora ko shugaba na gari.
    6. Harkar tarbiyya ba abu ne da ake yinsa da ka ba, lallai sai an yi karatun tarbiyyar saboda tana farowa, tun kafin a auri uwar da har ta haife shi ya balaga, za a yi masa tarbiyyar jiki, Imani, halaye, ladabai, haƙƙoƙi, siyasa da sha’awa. To in ba ilimi ta yaya wannan aiki zai yiwu.
    7. Wajibi ne mai tarbiyya ya kasance mai adalci.
    8. Ya kasance yana ɗaukar matakai na gasakiya a komai ya daidai ta tsakanin tsanani da sassauci da sakin hannu da rowa, ya kasance tsaka-tsaki a komai.

    9 Wanda yake da tsananin rowa da ƙanƙamo da masifar son abin duniya ba zai iya tarbiyya ba. Dole ya kasance mai sakin hannu da sakin fuska. Kada ya ɗauka asarar kuɗi yake yi in ya biya kuɗin makaranta ko ya sai abinci da sauran buƙatun ‘ya yansa.

    10 Ya kasance mai nuna ƙauna ta gaskiya ga’ ya’yansa maza da mata ‘ya’yan uwar gida da na amarya.

    11 Dole ne mai tarbiyya ya kasance nutsattse mai hankali da tsari a rayuwarsa.

    12 Wajibi ne mai tarbiyya ya kasance ya siffantu da kyawawan halayen da yake umarni da a aikata su, yana nisantar munanan ayyukan da yake hanawa. Kada ya zama fitina ga waɗanda suke a ƙarkashinsa.

    13 Ya kasance mai kyakkyawan fata da sakakkiyar zuciya kada ya rinƙa camfa abubuwa ko saurin siƙewa da fidda rai kan samun nasara.

    14 Ya kasance mai jin ƙai da tausayi.

    15 Ya kasance mai tsoron Allah (Taƙawa) wannan sharuɗɗa muhimmancinsa ya gawurta.

    Karanta Masu Rera Waƙa

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Yadda Ake Wuturi

    Yadda Ake Wuturi

    Hadisai da dama sun zo kan bayanin siffofin wutiri kamar haka

    1-  Wutiri da Raka’a Ɗaya:

    Manzon Allah (S. A. W.) ya ce:  “Sallar dare raka’a biyu- biyu ce, idan ɗayanku ya ji tsoron fitowar alfiji, ya sallaci raka’a ɗaya ta zama wutiri ga abin da ya sallata” kuma ya ce ” wutiri raka’a ɗaya ne a ƙarshen dare” (Muslim 752).

    2- Wutiri  da Raka’a Uku:

    A yi raka’a biyu a yi sallama, sannan a yi wutiri a yi sallama. Wannan ya inganta a hadisan Sayyada Aisha, Ibn Abbas, da Ubayyu Ibn Ka’ab (RA) kuma ya inganta cewa Manzon Allah (S.A.W.) yana karanta sabbi isma Rabbikal A’ala raka’ar farko, ƙulyaa ayyuhal kafirun a raka’a ta biyu sannan ƙulhuwallahu a raka’ar wutiri. (Bukhari 991, Malik 1/125) Tahawi  1/285). Amma karanta ƙulhuwallahu da falaƙi da Nasi wannan ya zo a Hadisi mai rauni.

    A yi raka’a ukun a jere  ba tare da an yi zaman tahiya ba sai a raka’a ta uku. (Bukhari 1147, Muslim 783)

    3- Wutiri da Raka’a Biyar:

    Ana so ga wanda zai yi wutiri da raka’a biyar ya yi su a jare kada ya yi zaman tahiya sai a raka’a ta biyar. Wannan ya inganta a Hadisin Aisha (RA) wanda Muslim ya ruwoito.

    4- Wutiri da Raka’a bakwai ko Raka’a tara:

    Ana so ga wanda zai yi irin wannan wutiri, ya yi su a jere kada ya zauna sai a raka’a ta shida ko ta takwas, sannan ya tashi ya kawo raka’a ta bakwai ko ta tara sannan ya yi sallama. Wannan ya zo a Hadisin. (Muslim 746, Abu Dawud 1328 da Nasa’I  2/199).

    Danna nan don karanata Rafkanuwa a Sallar nafila

    Edita:@rumasau-kallamu

     

  • Yadda Za Mu Yi Koyi Da Annabi (S.A.W.)

    Yadda Za Mu Yi Koyi Da Annabi (S.A.W.)

    Duk Wanda ya ce shi Musulmi ne, to lallai ne abin koyinsa ya zamo Manzon Allah (S.A.W), a dukkanin tsare-tsare na rayuwarsa.

    Misali: Tsarin Ilimi, tsarin zamantakewa, tsarin Tattalin arziƙi, tsarin siyasa (shugabanci) da tsarin shari’ah. Abin nufi a nan shi ne, duk waɗannan tsare-tsare na rayuwa su zamo a kan tsarin alƙurani da sunnah, bisa fahimtar magabata na ƙwarai.

    Kada mutum ya zama sai a sallah, Azumi, aikin Haji kaɗai, yake Musulmi. Watau ya zama yana bin tsarin da ya saɓa wa na Allah. Allah (SWT) Yana cewa:

     Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku shiga Musulunci gaba ɗaya (watau ku miƙa wuya gaba ɗaya). Kada ku bi takun sheɗan, ba na Allah ba). Shi abokin gaba ne a gare ku, bayyananne” (suratul BAƙarah, Aya ta: 208).

    Abin takaici shi ne, a halin da muke ciki a yanzu, za mu ga cewa a dukkanin tsare-tsare nan na rayuwa babu wanda muke tafiyar da shi a kan tsarin da Annabi Muhammad (S.A.W) ya zo da shi. Misali: Tsarin Iliminmu ba ya koya mana tauhid da tsoron Allah da ranar lahira da Tarbiyyar Musulunci. A tsarin zamantakewa. Idan muka ɗauki zamantakewarmu ta aure da zaman iyali, ba a kan alƙur’ani da sunnah take ba.
    Tsarin tattalin arzikinmu cike yake da cin hanci da rashawa, cin Riba, gululu’ (Watau satar dukiyar jama’a) da sauransu. Tsarin siyasarmu (shugabanci) tsari ne na Damakwaraɗiiyya, wanda babu Allah a  cikinsa. Shi kuwa tsarinmu na shari’ah kowa ya san dokokin ‘yan Adam muke fifitawa a kan dokokin Allah (SWT). Abin nufi a nan shi ne, son Annabinmu  na baka ne kawai. Ba a aikace yake ba. Gashhi kuwa Allah (SWT) yana cewa:

    Gaya musu, idan kun kasance kuna son Allah, to ku bi ni, sai Allah ya so ku, ya gafarta muku zunubanku. Allah mai gafara ne, mai rahama” (Suratu Ali Imrana, Aya ta:31)

    Allah (SWT) yana cewa: Ka ce musu Idan iyayenku da ‘ya’yanku da ‘yan’uwanku  da matanku, da danginku da dukiyoyinku da kuka nema da hanyar samunku da kuke gudun kada ta yi tasgaro da gidajen da kuke jin daɗinsu, su suka fi soyuwa a  gare ku, maimakon Allah da Manzonsa, da  ƙoƙarin tabbatar da tsarinsa, to ku zauna, har sai Allah ya zo da lamarinsa (Mutuwa ko halakarwa). Allah ba ya shiryar da mutane fasiƙai” (suratul Taubah, Aya ta:24).

    Wannan duka yana nuna cewa ba za mu zama Musulmi ba sai mun gudanar da kowane ɓangare na rayuwarmu bisa tsarin Allah. Wannan kuma ba zai samu ba sai ta hanyar koyi da Annabi Muhammad (S.A.W), watau ta hanyar ruƙo da alƙur’ani da Sunnah. Annabi(S.A.W) ya ce:

    “Na bar muku nauyaya guda biyu, ba za ku ɓata ba, matuƙar kun yi ruƙo da su: Littafin Allah da sunna ta”

    DOMIN SANIN YADDA ZA KA YI KOYI DA ANNABI (S.A.W) DANNA KOREN RUBUTU

  • Yanda Ake Gurasar Tanderu

    Yanda Ake Gurasar Tanderu

    Abubuwan da ake buƙata

    • Fulawa
    • Yis
    • Kantu/riɗi
    • Sikari
    • Gishiri

    Yadda ake haɗawa

    1. A sami fulawa a tankaɗe a zuba mata yis, sai a zuba ruwa a kwaɓa,
    2. Kada a kwaɓa ta yi ruwa, a kwaɓa ta da ɗan tauri.
    3. Idan ana son Gurasa mai sikari, sai a zuba sikari a cikin kwaɓin , idan kuma mai gishiri ce, sai a zuba gishiri a cikin kwaɓin.
    4. Idan lokacin zafi ne za ta yi saurin tashi saboda dama yis zafi yake so, awa uku zuwa huɗu ya ishe shi ya tashi.
    5. Amma idan lokacin sanyi ne yakan daɗe bai tashi ba. Idan ana so a yi gurasa da safe, to sai a kwaɓa fulawar tun da daddare,
    6. Idan an tabbatar kwaɓin ya tashi , sai a zuba karare a cikin tanderu, a kunna wuta domin tanderun ya yi zafi.
    7. Idan an tabbatar tanderun ya yi zafi sosai kuma karan ya cinye sai a yayyafa ruwan kanwa a ciki.
    8. A saka tsintsiya a share toka-tokar da ta maƙale a cikin tanderun.
    9. Sai a kawo kwaɓin a cura shi ya yi faɗi, a faɗaɗa da hannu, yadda dai a ke son faɗinta ya kasance.
    10. Idan kina son kantu/riɗi sai a zuba ɗan kaɗan a kan gurasar a tsakiya, idan kuma ba a so shi kenan sai kawai a saka curin da a ka yi a cikin tanderun.
    11. Idan an gama sakawa sai a kawo tire a rufe tanderun, takan ɗau kamar minti ashirin zuwa minti ashirn da biyar kafin ta yi.
    12. Ba ma sai an kalli agogo ba, da ta yi za a ji ƙamshi ya turare ko ina a gidan.
    13. Sai a kawo wuƙa da tire, a ringa saka wuƙa ana ɓamɓaro ta tana faɗawa kan tiren. Amma sai an yi a hankali saboda zafi kada a ƙone domin tanderu yana da zafi sosai.

    Domin karanta Yadda Ake Faten Wake Da Doya danna nan

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Wanene Ɗan Auta A ‘Ya’yan Abdulmutallib (Kakan Manzon Allah S.A.W)

    Wanene Ɗan Auta A ‘Ya’yan Abdulmutallib (Kakan Manzon Allah S.A.W)

    Wanene ɗan auta a yayan Abdulmutallib Kakan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama:

    Ɗan autan ‘ya’yan Abdulmuttallib kakan annabi Muhammad (s.a.w) shi ne

    1.Hamza(r.a) kawun manzon Allah (s.a.w).

    Domin sanin A ina mahaifiyar annabi Muhammad (s.a.w) ta rasu danna nan

  • Menene Cutar Suga (Diabetes)?

    Menene Cutar Suga (Diabetes)?

    Jikin ɗan Adam na buƙatar wani irin nau’in sinadarin suga (glucose) da ke cikin jini domin aiwatar da wasu daga cikin manya-manyan ayyukan da suka shafi lafiyar jikin.

    Suga (glucose) na bayar da kuzari (energy) ga jikin ɗan Adam wanda ake buƙata wajen narkar da abinci da kuma rayuwar ƙananan halittun da suka tattaru (yawa) suka yi ginin jikin ɗan Adam ko halittarsa tamkar bululluka [tubali] (cells).
    Wannan sugan ‘glucose’ shi ne makamashin da ke ba wa jikin ɗan Adam kuzari domin rayuwa. Kuma ana samun sa ne daga abincin da muke ci, wato nau’in abinci mai samar da kuzari (carbohydrate), kamar irinsu gero, dawa, masara ,shinkafa da sauransu. kwakwalwa (brain), ko hanyoyin sadarwar ƙwaƙwalwa a jiki (nerves) da kuma wasu jajayen halittun jini ( developing red blood cells) , duk kaninsu suna amfani da wannan makamashi (glucose) domin samun rayuwa.
    Ciwon-suga (diabetes) cuta ce wadda suga (glucose) da ke cikin jini yake haurawa sama wato suga ya yi yawa a cikin jini. Yawansa na da illa ga lafiya. Dalilin yawansa na faruwa ne sabili da jikin mutum ba ya samar da da wani sinadarin kemical mai suna ‘insulin’
    ( type 1 diabetes) , ko jikin ne ba ya amfani da ‘insulin’ yadda ake so, ko kuma ma jikin ba ya samar da ‘insulin’ da kyau [wato isasshe]
    ( type 2 diabetes). Idan har babu ‘insulin’ to fa sugan ‘glucose’ zai cigaba da taruwa da yawa cikin jini har ya yi illa ga lafiya.
    Sinadarin ‘insulin’ (a hormone), wata tsoka ce a jikin ɗan Adam take samar da shi (pancreas).
    Amfanin sinadarin ‘insulin’ shi ne ɗaukar sugan ‘glucose’ da ke cikin jinin zuwa cikin ƙananan halittun da suka gina jikin ɗan Adam (cells) domin samun kuzari gare su da cigaban rayuwa.
    Idan babu ‘insulin’ ko ba ya aiki yanda ake buƙata to suga fa zai cigaba da taruwa cikin jini ya yi yawa har ya haddasa munanan matsaloli ga lafiya. Sugan zai iya yin illa ga idanu, ƙoda, wasu jijiyoyin jini da kuma wayoyi/hanyoyin sadarwar ƙwaƙwalwa a jiki.
    Ciwon-suga zai iya haddasa cutar zuciya, mutuwar sashen jiki koma ya jaza yanke ƙafar marar-lafiyar. Idan ciwon ya yi ƙarami zai iya haddasa matsalar ƙashi da gaɓoɓi, matsalar fata, matsalar narkewar abinci, rashin ƙarfin mazakuta, matsalar haƙora da dasashi.
    ‘Type 2 diabetes’ ,wato nau’in ciwon-suga na 2 da muka yi bayani (wanda jiki ba ya amfani da ‘insulin’ yadda ya dace) shi ne nau’in ciwon-suga da ya fi yawa ga mutane da dama fiye da nau’in ciwon-suga na 1: ‘type 1 diabetes’ (wanda mu kace jiki ba ya samar da da sinadarin ‘insulin’).

    Alamomin Ciwon Alamomin Ciwon-suga Nau’i na (type 1 diabetes symptoms):
    • Yawan jin ƙishirwa sosai
    • Yawan yin fitsari
    • Yawan jin yunwa ko gajiya
    • Raguwar nauyin mutum ba tare da mutum ya yi ƙoƙarin rage nauyin ba
    • Daɗewar ciwo/gwambo bai warke ba/warkewa a hankali
    • Rashin gani da kyau. Awon jini zai iya nuna idan akwai ciwon ko saɓanin haka.

    Idan akwai irin nau’in ciwon , toh mutum zai cigaba da amfani da sinadarin ‘insulin’ da aka samar a asibiti, za a ba shi sinadarin a asibiti akan ƙa’ida da umarnin ƙwararren likita. An fi yawan samun ƙananan yara da matasa da irin wannan nau’in ciwon-suga (Juvenile diabetes/Insulin-dependent diabetes) duk da dai cewa zai iya shafar mutane a kowane shekarun su na rayuwa.

    Alamomin Ciwon-suga Nau’i na 2 (type 2 diabetes symptoms):
    • Yawan jin ƙishirwa sosai
    • Yawan yin fitsari
    • Yawan jin yunwa ko gajiya
    • Raguwar nauyin mutum ba tare da mutum yayi kokarin rage nauyin ba
    • Bushewar fata, ƙaiƙayin fata
    • Mutum ya ji kamar ba ƙafarsa ba ko jin tsira a ƙafafu

    Yin awon jini a asibiti ko wata ingantacciyar cibiyar lafiya zai iya nuna maka ko kana da ciwon suga ko kuma akasin haka. Motsa-jiki (exercise), rage nauyin jiki yanda ya dace da koyarwar kiwon lafiya, da kuma kula da tsarin cin abinci da ya dace da ciwon lafiya, ko shakka babu , za su taimaka sosai wajen shawo matsalolin lafiya na ciwon-suga.

    Cututtukan saifa, magunguna, kemikals, kamuwa da wasu cututtukan da gado daga mahaifan mutum na daga cikin dalilin da ake alaƙantawa da suke haddasa ciwon-suga. Allah ya ba mu lafiya AMEEN.

    Danna nan don karanta Sinadarin Ka-Fi Suga

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu