Category: Tarihi

Mun samar da wannan ɓangaren ne domin samar da dukkanin Tarihi a cikin harshen Hausa a sauƙaƙe.

wikiHausa ta kowa ce. Kowa zai iya taimakawa da ilimi ko gyara. Bugu da ƙari, kowa na iya amfani da wannan kafa wajan ɗora Tarihi ko saukewa

  • Yanayin Duniya Kafin Aiko Da Manzon Allah

    Yanayin Duniya Kafin Aiko Da Manzon Allah

    Duniya Ta Kasance A Cikin Baƙin Duhu, Kafin Aiko Manzon Allah (SAW), Komai A Rikice Yake Sai Abin Da Ba A Rasa Ba Kuma Ko’ina Da Irin Abin Da Suke Fama Da Shi Na Irin Matsalar Su, Da Zalunci Da Jahilci.

    Manyan Dauloli Kamar Roma Da Farisa, Babu Abin Da Yake Gabansu Sai Yaƙe-Yaƙe Da Hankoron Faɗaɗa Da’irar Mulkinsu, Talakawan Da Suke A Ƙarƙashin Su Sun Shiga Uku Saboda Zalunci Da Danniya, Da Baƙin Mulki Da Gallazawa Da Ake Yi Musu.

    Ƙasar Larabawa Kuwa Musamman Garin Makka Tana Cikin Duhun Jahilci, Da Ɓatan Hankali, Saboda Rashin Shiriya Ta Addini, Ga Kuma Yawan Shan Giya Da Suke Yi, Don Haka Suka Yi Rayuwa Ta Tsaurin Rai Da Bushewar Zuciya, Har Su Ka Dinga Binne Ƴaƴa Mata Da Ransu, Wai Don Gudun Kar Su Girma Wata Rana A Kame Su A Matsayin Ribar Yaƙi, Ko Kuma Gudun Talauci.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Dabarun Zaman Lafiya Da Mutane danna nan.

    Shugabannin Addinai Kuma Kamar Yahudawa Da Nasara Mafi Yawansu Sun Shagala, Domin Sun Kaucewa Sahihiyar Koyarwar Da Allah Ya Saukar Ga Annabawansu.

    Yahudawa Sun Sauka Daga Hanyar Annabi Ibrahim, Kuma Sun Jirkita Koyarwar Annabi Musa, Sun Ce, “Ubangijin Nasu Ne Su Kaɗai Wanda Ya Halitta Musu Duk Abin Da Suke So Na Son Kai Da Zaluncin Mutane” .

    Nasara Kuma Sun Buge Da Zancen Kasa Ubangiji Guda Uku, Ga Shi Kuma Ba Su Da Cikakkiyar Shari’a (Dokoki) Wadda Za Ta Tsara Zamantakewar Ɗan Adam A Rayuwarsa.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Abubuwan Da Suke Hana Karɓar Gaskiya danna nan.

    Masu Addinin Gargajiya Kuma (Kamar Farisawa) Sun Nutse A Rayuwar Dabbanci Da

    Almubazarranci .

    A Cikin Wannan Yanayi Allah Ya Aiko Da Manzon Allah (SAW) Shi Ne Annabi Kuma Manzo Na Ƙarshe A Cikin Annabawa Da Manzannin Allah, Kuma Allah Ya Aiko Shi Da Saƙonsa Zuwa Ga Talikai Baki Ɗaya Na Gabas Da Yamma Kudu Da Arewa Tun Daga Lokacin Da Aka Aiko Shi Har Zuwa Ƙarshen Duniya.

    Wannan bayanin anciro shi ne daga littafin “Bita A Cikin Tarihin Shugaban Halitta” Domin karanta cikakken littafin ko daukoshi  danna nan

  • Haihuwar Manzon Allah (Saw)

    Haihuwar Manzon Allah (Saw)

    An haifi Manzon Allah (SAW) ranar Litinin 12 ga watan Rabi’u Auwal. Mahaifinsa shi ne Sayyidina Abdullahi ɗan Abdulmutallib, nahaifiyarsa kuma Nana Amina yar Wahab.

    Ana kiran shekarar da aka haife shi (SAW) shekarar giwa, saboda a wannan shekarar ne Abrahata ya zo daga “Yaman” da rundunarsa tare da giwa don ya rushe Ka’aba, amma Allah ya halaka su ta hanyar aiko da tsuntsaye suka dinga jifan su da tsakuwa daga wutar “Jahimu” har sai da suka halaka baki ɗaya.

    Domin karanta cikakken bayani akan Mafifitan Aiyukan Mai Azumi danna nan.

    Annabi (saw) ya girma a cikin maraici, dama mahaifinsa Abdullahi ya rasu tun kafin a haife shi, sannan kuma mahaifiyarsa Amina ita ma ta rasu a lokacin da yake ɗan shekara shida a duniya! Bayan rasuwar mahaifiyarsa, sai kakansa Abdulmutallib ya karɓi rainonsa, shi ma Abdulmutallib ɗin sai ya rasu a lokacin Manzon Allah (SAW) yana ɗan shekara takwas a duniya! (wato bayan shekara biyu da rasuwar mahaifiyarsa) daga nan sai baffansa Abu Ɗalib ya karɓi rainonsa.

    Da akwai abin lura a cikin wannan lamari, kasancewar Annabi (SAW) an haife shi maraya, kuma Allah Maɗaukakin Sarki ya ɗauke rayuwar magabatansa amma kuma duk da haka ya sami kulawa ta musamman daga Allah Maɗaukakin Sarki, maraya ne shi amma ya fi kowa tarbiyya, da nutsuwa da halaye nagari, wannan bayanin ya fito a cikin Alkur’ani inda Allah yake bayyana wa Manzon (SAW) cewa (ألم يجدك يتيما فاوى ) wato:

    Allah ya samar da Manzon Allah kuma ya ƙaddara masa tasowa a cikin maraici, sai Allah Ta’ala ya jiɓinci kulawa da shi, dama an ce Manzon Allah ya ce: “Ubangijina ne ya ladabtar da ni kyakkyawar ladabtarwa”

    Domin karanta Halayen Da Ya Kamata Mai Azumi Ya Siffantu Da Su Danna nan 

    Haƙiƙa irin waɗannan abubuwan lura suna daga alamun Annabta ga masu tsinkaye, kuma irin su suna da yawa a rayuwar Annabi Muhammad kamar abin da ya faru a lokacin da kakansa ya bayar da shi raino da shayarwa ga Nana Halimatus Sa’diyya wadda kafin ta karbi rainonsa (SAW) tana cikin ƙuncin rayuwa da rashin ƙosassun dabbobi, amma tana karɓar Annabi ta kai shi gidanta sai albarkatu suka dunga ɓarkowa  ta ko’ina.

    Kuma Annabi (saw) ya bambanta daga da dukkan sa’aninsa wajen nutsuwa da nagarta har sai da aka yi masa laƙabi da sunan “Amintacce” shi suke kaiwa ajiyar kayansu masu tsada, kuma shi su mke gayyata ya raba gardama a tsakaninsu idan jayayya ta tufke!

    Bugu da ƙari, a lokacin da Manzon Allah (SAW) ya bi baffansa Abu Ɗalib zuwa ƙasar Sham don yin kasuwanci Wani Malami “Buhaira” ya ga alamomin Annabin ƙarshen a tare da Manzon Allah, waɗanda ya san su daga bayanan masana littafan da suka gabata. Nan take Buhaira ya tambayi Abu Ɗalib cewa: “Yaya kuke da wannan yaron?” (a lokacin shekarun Manzon Allah SAW goma sha biyu) sai Abu Ɗalib ya ce da shi, “Ɗana ne”. Ta ke Buhaira ya ce, “Bai kamata a ce mahaifinsa yana raye ba, sannan ne Abu Ɗalib ya ce “Ɗan ƙanina ne, wanda ya rasu kafin a haife shi….”

    Haka ma a lokacin da Manzon Allah (SAW) ya cika shekara ashirin da biyar

    Labarin kirkinsa da amanarsa ya yaɗu a garin Makka, wannan ne ma abin da ya ja hankalin Nana Khadija har ta nemi ya amince ya karɓi dukiyarta don kasuwanci, kamar yadda takan ba wa wasu mutane.

    Manzon Alllah SAW ya amince ya tafi ƙasar Sham tare da yaronta Maisara, wannan tafiya ta kasance mai cike da albarka da kuma ɗumbin nasarori,

    Domin karanta bayani Yadda Ake Buɗe Karatun Alƙur’ani Da BismillAh A Cikin Sallah Danna nan 

    Bayan sun dawo Makka, sai Maisara ya kwashe duk labarin abin mamakin da ya dinga gani a wajen Manzon Allah (saw) ya gaya wa Nana Khadija ya faɗa mata kirkinsa, da nagartarsa da kuma amanarsa…. saboda haka ne Nana Khadija ta nemi Annabi ya amince ya aure ta.

    Bayan Manzon Allah (SAW) ya auri Nana Khadija ta ruɓanya ƙaunarta da kuma biyaryarta gare shi, tare da ba shi goyon baya da sadaukarwa a kan duk abin da ya damu da shi.

    Tun kafin Allah ya aiko Manzon Allah da saƙon Manzonci, ayoyi da alamomi sun nuna cewa yana da wata baiwa ta musamman wadda ta wuce irin baiwar da aka saba gani a wajen haziƙai da jarumai na tarihi. Shi tasa baiwar tanadi ce daga Allah, don ya zamar da shi Annabi kuma Manzon na ƙarshe, wanda saƙonsa zai zama gamamme mai shiryarwa izuwa tafarkin tsira har zuwa ƙarshen rayuwar duniya.

    Wannan bayanin anciro shi ne daga littafin “Bita A Cikin Tarihin Shugaban Halitta” Domin karanta cikakken littafin ko daukoshi  danna nan

  • Kakannin Manzon Allah (Saw)

    Kakannin Manzon Allah (Saw)

    Nasabar manzon Allah sallahu Alaihi wa sallama tana tiƙewa har zuwa ga Annabi Ibrahim Hikimar Ubangiji ta ƙaddara cewa shi Annabi Ibrahim wanda  shi ne kakan Annabawan Bani Isra’ila, kuma shi ne dai zai zama kakan Annabi Muhammadu Balarabe daga tsatson Annabi Isma’il.

    Haka kuma duk da cewa Annabi Ibrahim ya girma ya tashi a Lardin Iraqi amma sai bisa hikimarsa ya kimsa wa Annabi Ibrahim ɗin ya yi ƙaura zuwa Falasɗin a can ya ajiye matarsa Sara sannan kuma ya tafi da Hajara tare da jaririnta Isma’il zuwa gurin da a yau ake cewa da shi garin Makkah.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Yin Ruku’u danna nan.

    A lokacin da Annabi Ibrahim ya ke tafiya da su (Hajara da jaririnta) bai san takamaimai inda zai zaunar da su ba, tafiya kawai yake yi a bisa umarnin Allah, har sai da ya zo bigire wanda babu ruwa, babu tsiro a nan Allah ya yi wa Annabi Ibrahim wahayi cewa a nan ne inda zai ajiye matarsa da jaririnta.

    Babu shakka a nan akwai jarrabawa ta ubangiji ga Annabi Ibrahim wadda ta nuna mana juriya da haƙuri da kuma biyyaya na Annabi Ibrahim ga Mahaliccinsa Allah (swt) saboda ya sami haihuwa a lokacin da ya girma don haka ya yi matuƙar murna da samun wannna haihuwa amma a lokacin kuma aka umarce shi da ɗauke su (iyalansa) ya kai su can wani guri mai nisa ya ajiye a gurin da babu kowa ya koma Falasɗinu ya bar su a nan!

    Ita ma Hajara ta nuna biyayya ga mijinta kuma ta miƙa wuya ga umarnin Allah mahiliccinta, saboda a lokacin da Annabi Ibrahim ya ajiye ta tare da jaririnta ya juya zai bar su sai Nana Hajara ta ce da shi, “Yaya za ka bar mu a nan wajen mu mu kadai kuma ka tafi kabar mu? Shin ubangiji ne ya umarce ka da aikata haka?” Sai Annabi Ibrahim ya ce,  “Haka ne”.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Tahiyya danna nan.

    Sai Nana Hajara ta ce, “To je ka, tunda Allah ne ya umarce ka, haƙiƙa ba zai taɓar da mu ba”. Nana Hajara a nan ta nuna tsantsar biyayya da miƙa wuya.

    Annabi Ibrahim bai bar su haka ba sai ya yi addu’a ta musamman:-

    ربنا إنى أسكنت من ذريتى بواد غير ذى زرع عند بيتك المحرم، ربنا ليقيموا الصلاة فاجعل أفئدة من الناس تهوي إليهم وارزقهم من الثمرات لعلهم يشكرون

    “Ya Ubangijinmu ga shi na ajiye zuri’ata a wani kwari wanda babu wata shuka a cikinsa a inda ɗakinka mai alfarma yake, (nayi haka ne) ya Allah domin su tsayar da sallah, to (ina roƙon ka) ka karkato da zukatan mutane i zuwa gare su, kuma ka arzurta su da kayan abinci (ɗiyan itatuwa) domin su zama masu yin godiya”. Daga nan ne asalin samuwar garin Makka ya faro.

    Larabawan Yaman sun yi hijira daga lardinsu sai suka zo inda Nana Hajara take a tare da jaririnta Annabi Isma’il sai suka nemi izininta domin su maƙotance ta saboda sun ga akwai ruwa (zam-zam) a inda take. Waɗannan Larabawa na Yaman, ana cewa da su ƙabilar Jurhum, su ne suka assasa garin makkah, kuma a cikinsu Annabi Isma’il ya tashi har daga bisani ya auri ɗaya daga cikin ƴaƴansu kuma daga gare su ne, aka haifar da kakannin Manzon Allah (SAW)

    Dukkanin kakannin Manzon Allah (SAW) inganttun mutane ne masu martaba da karamci da yin alheri ga mutane.

    Wani muhimmin abin lura game da nagarta da Allah ya dasa a tsatson Manzon Allah, shi ne kakansa Annabi Ibrahim wanda ya tabbata mai nagarta, da ƙarfin Imani, tare da saurin miƙa wuya, ga umarnin Allah, haka shima ɗansa Annabi Isama’il wanda ya ci jarabawa a lokacin da mahaifinsa Annabi Ibrahim ya yi mafarki yana yanka shi, nan take Annabi Isma’il ya miƙa wuya ga umarnin Allah, ya yi biyayya ga mahaifinsa, ya ce, “Ya yarda a yanka shi”. A lokacin ne kuma Allah ya kuɓutar da shi daga yanka, to, haka kuma sauran kakannin Manzon Allah har zuwa mahaifinsa Abdullahi dukkansu Allah ya sanya su managarta ne su.

    Wani abin lura kuma game da hikimar Ubangiji a tarihin Annabi Ibrahim shi ne, yadda Allah ya kimsa masa ɗauke Hajara da jaririnta zuwa yankin Makka, sai gashi wannan ne sanadin a haifi Manzon Allah a cikin Larabawa, daga jinin Annabi Ibrahim wanda sauran ƴaƴansu kuma su ne Annabawan Bani Isra’ila.

    Haka kuma ya faru ne saboda matar Annabi Ibrahim ta farko Nana Sara ita a yankin Falasɗinu ta zauna, kuma ita ce ta haifi Annabi Ishaq shi kuma ya haifi Yakubu, wanda shi ne kakan Banu Israila saboda haka Annabi Ibrahim ya zama shi ne kakan Annabawan Bani isra’ila kuma shi ne kakan Annabi Muhammad wanda shi kuma Balarabe ne (saw).

    Wannan bayanin anciro shi ne daga littafin “Bita A Cikin Tarihin Shugaban Halitta” Domin karanta cikakken littafin ko daukoshi  danna nan.

  • Tarihin Kano

    Idan ana so a nakalci Tarihin Kano sosai, dole ne sai an tabo tarihin kasar Hausa. Shi kuma tarihin kasar Hausa sai an leka cikin tarihin Sudan. Shi kuma tarihin kasar Sudan sai an lelleka cikin tarihin daular Larabawa ta Banu Ummayyata da ta Banu Abbasi. Har ila yau kuma da binciken labarin wani tunzuri da ya sa jama’a suka rika kauratowa daga tsakiyar kasar Asiya suka yi wo yamma.

    Kasar Sudan itace yankin kasar Afrika na wajen tsakiya, daga gabas ta iyaka da kasar Habasha (watau Ethiopia), daga arewa ta yi iyaka da Sahara daga kudu ta yi iya da yankin gabar Tekun Atlantic da ake kira ‘Gulf of Guniea’ — da kuma kasashen sunkurun kurmin nan na tsakiyar Afrika. Kalmar nan ‘Sudan’ ma’anarta baki, saboda galibin al’ummar da ke zaune a cikin yankin Sudan masu bakar fata ne. An ce zafin rana shi ke sa su baki (kunne ya girmi kaka), gama dukkan kasar Sudan tana daf da wurin da ake kira ‘Haddul Etidali’ watau ‘Equator’. Kasar Hausa ita ce yankin nan na kasar Sudan wanda ke wajen tsakiya-tsakiya. Daga gabas da ita ga kasar Borno; daga Yamma ga kasar Dahomey (wacce yanzu ake kira Jamhuriyar Benin); daga arewa ga Hamadar Sahara; daga kudu kuma ga kasashen Nupe da kasahen da ake kira ‘Middle Belt’. Kasar Kano tana daga yankin tsakiya na arewacin kasar Hausa. Daga gabas ta iyaka da kasashen Borno da Bauchi; daga yamma ta yi iyaka da Katsina; daga kudu ta yi iyaka da Zariya; daga arewa kuma tayi iyaka da kasar Neja. Tun daga yanzu za a fara fahimtar lalle Kano wajibi ne ta zama babbar alkarya saboda ita ce kamar tsakiyar kasar Sudan duka.


    Taswirar birnin Kano

    Tun da dadewa kasar Hausa da kuma sauran kasashen Sudan sun sami adabunsu na zaman duniya daga fuska biyu mabambanta —- watau Gabas da Yamma. Sa’adda sabawa ta sa jama’ar kasar Mangoliya ta Asiya suka rika fuskantowa yamma-yamma, a hankali sai masarauta ta rika kafuwa, in wannan ta fadi, wata kuma ta tashi a can gabas. Shi ne daga bisani mulkin Farisa, (watau persia), ya kafu, ya mallake kasashen gaba duka.

    Mazaunan Farko

    A kasashen Karni na Tara (9th Century) na Masihiyya wadansu maharba, wadanda babu hakikar daga inda suka zo suka zauna kan duwatsun da ke kewaye da sararin da ake kira Kano yanzu. Irin duwatsun nan sune irinsu Dala. Gwauran Dutse, Magwan da Dutsen Fanisau.
    Su maharban nan suka rika yin farauta a wani kurmi wanda ya ke shine tushen rafin Jakara, inda kasuwar Kurmi ta Kano ta samo suna. dan wadannan maharba suka jarraba dan koma suka ga wurin yana da albarka, sai suka ci gaba suna kara saran dajin suna yin gonaki. Albarkar wurin nan mai ban mamaki sai ta jawo wadansu mutane daga wadansu wurare suna zuwa. Da taron mutanen wannan lokaci mai nisa, ya kan zama mutum ne da ke da fifikon karni game da tsafi.

    Babu tahakikanin akan irin tsarin mulkin da wadannan al’umma su ka gina shugabacinsu, amma duk da haka ana iya cewa aikin shugaba a wannan lokaci bai wuce tsare dokokin farauta da kuma kusaci da tsafin da mutanen ke bautawa

    An bayar da bayanan nan a karkashin littafin ‘Kano Ta Dabo Cigari’ wallafar Alhaji Abubakar Wazirin Kano.
    ISBN: 978-140-501-2218

  • Yaƙe-yaƙen Annabi S.A.W A Watan Ramadan?

    Yaƙe-yaƙen Annabi S.A.W A Watan Ramadan?

    Yaƙi biyu ne kawai ya yi cikin Ramadan, Yaƙin Badar babba da Fatahu Makka.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Shin Shugaban Halitta Yana Karatun Alƙur’ani Na Musamman Cikin Watan Ramadan? danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Karatun Manzon Allah (Sallallahu alaihi wassallam) danna nan.

    Danna link ɗinnan; https://chat.whatsapp.com/JtD82AjZZmo3AtSTaKP05r domin shiga WhatsApp group namu na Ramadan.

  • Tarihin Dutsen Dala Da Rayuwa A Kewayensa

    Tarihin Dutsen Dala Da Rayuwa A Kewayensa

    Dala

    An fara ambatar Kano da sunan Jihar Kano daga lokacin da sojoji suka karɓi mulkin ƙasar nan, kuma suka yayyanka ƙasar zuwa jihohi, kafin wannan lokaci, cewa ake da ita lardin Kano, ko kuma a ce Kano da maƙwabtanta.

    Shi wannan birnin na Kano, ya kafu ne tun lokacin da ba a sani ba, wanda hakan yasa aka samu mabambantan ra’ayoyi dangane da lokacin da Kano ta kafu, wasu suna cewa, “Kano ta kafu ne tun lokacin da ba a sani ba”. Yayin da wasu suke cewa, “Ta kafu ne tun lokacin jahiliya, kafin zuwan Musulunci”. Wasu ɓangaren suna cewa, “Ta kafu ne tun shekara ta 208 A.H (bayan Hijira), wasu sun ce a shekara ta 303 A.H. ko shekara ta 444 A.H. ko kuwa 906 A.D.

    Kamar yadda aka yi saɓani a kan mazaunan ta na farko, inda wasu suka ce mutanen Gaya ne, waɗanda suke zuwa daga alkaryar Gaya, don ɗibar tama; a yayin da damuna ta sauka, sai suka zauna daga yammacin Dala; da wasu manyan rahoniyoyinsu masu kama da tsawon mutum, suna dafa tama a ciki bayan sun yi tsafe-tsafensu, idan ta haɗu, sai su yi ƙarfe da ita, ƙarfen shi ne suke ƙera kayen noma da yaƙi da kuma farauta, sai su bayar a musanya musu, a ba su abinci da sauran kayan buƙatu, waɗannan makera har yanzu akwai zuriyarsu suna yin ƙira.

    Kuma, wasu ko sun ce ‘yan farauta ne, waɗanda suka haɗu da mutunen da suka tarar, suka yi ‘yar alkarya ƙarama, waɗannan su ne iyalan ƙasaitaccen mutumin nan da ake kira da ‘Dala’, wanda Dutsen Dala ya samo sunansa daga gare shi, don ya zauna a kan saman ‘Dala’ shi da iyalansa.

    Bayan da Kanoki ya dawo Dala ya zauna, sai kasuwa ta buɗe masa. Mutane daga ko’ina suka riƙa zuwa wajensa, suna sayen kayan noma da na farauta da na aikin gidaje.

    Wannan kasuwa sai ta jawo masa ƙabilu iri daban-daban, waɗanda suka yiwo ƙaura, suka zo wajensa don su zauna tare da shi. To da yake kowace ƙabila takan zo da abin da Allah ya hore mata na sana’a, sai  masana’antu suka tashi a gurin. Masakar tufafi da marina da majema duk suka yawaita.

    Wannan ƙaramin buɗi na arzikin ƙasa, shi ne ya kawo kafa birnin Kano a gindin Dala, wanda ya ƙunshi dangin ƙabilu sha ɗaya. Kuma kowace ƙabila tana da sana’ar da ta kware a kai. Saboda sunan wannan makeri Kanoki da ya farazama a gurin ake kiran gurin Kano, kuma ƙabilarsa aka dinga kiranta Abagayawa.

    Wannan ƙaramin juyi, ana zaton ya faru ne a tsakanin ƙarni na 5-6 daga haihuwar Annabi Isa (A.S) kuma su waɗannan ƙabilu guda goma sha ɗaya da suka kafa wannan birni a gindin Dala, za ka karanta su a nan gaba kaɗan, kamar yadda tarihin Kano ya ambace su.

    Wani abin sha’awa cikin rayuwar waɗannan ƙabilu   shi   ne,  zaman   lafiya   da   haɗin kai na taimakon   juna.   Tun da dabarar yin sarki, a matsayin shugaban kowa da kowa, ba ta zo ba, to limamin addininsu shi ne shugabansu. A lokacin ruwan Jakara suke bautawa kuma Mazauda shi ne limanin bautar  Jakara,  saboda haka, ya zama shugaba.

    To cikin waɗannan mutane ne, Dala ya zo ya zauna tare da su a kan dutsen Dala. An ce Dala ya zo wannan wuri tare da ‘ya’yansa guda bakwai, huɗu maza uku mata. Sunan babban su Gargaji, shi ne kakan Buzami uban   Barbushe, kuma Barbushe shi ne ya gaje shi daga baya.

    Daga Ina Dala Ya Zo?

    Malaman tarihin Kano irin su Alkali Zangi Waziri Abubakar ba su yi nishaɗi mai yawa ba, tare da labarin Dala da iyalinsa, balle a san daga ina ya zo, kuma shi wane ne kafin ya zo ɗin. Idan ban da  littafin  Tarihin  Kano  na  Muhammadu Bello (Sarkin Kano  1883-1892) ba wanda ya faɗi labarin Dala. Ko shi ma wannan littafin, bai faɗi wani abu mai tsawo ba a kan zuwan Dala nan ƙasar . Abin da littafin kawai ya faɗa shi ne:

    “Shi Dala mutum ne baƙi kuma ƙaƙƙarfa, kuma mafarauci kwarai. Domin shi yakan kashe giwa da sandarsa, ya dauko ta a kansa, ya yi tafiya da ita kamar mil tara. Ya zo garin nan ba a san asalinsa ba. Da ya zo ya gina gidansa a Dutsen Dala, ya zauna a kanta shi kaɗai tare da matansa da ‘ya’yansa bakwai, huɗu maza, uku mata. Sunan babbansu Gargaji, shi ne kakan Buzami uban Barbushe. Barbushe ne ya gaji halayen Dala daga sanin dukkan dangogin tsafi da al’ajubansa da sihirinsa da rinjaye ga ‘yan uwansa, domin haka, ya zama shugabansu!”

    To wannan abin da aka kawo maka cikin littafin Tarihin Kano game da Dala, shi ne kawai abin da za ka ji game da shi, ba daɗi ba ragi, Wannan kuwa ɗan bayani na Dala, ba zai ƙosar da duk wani almajirin Tarihin Kano ba. Kuma tun da yake babu   littattafai a ƙasar  Hausa a  yanzu, waɗanda za su taimake mu, su ba mu haske don mu san daga ina Dala ya fito, kuma da inda ya koyi sihirinsa da dabarar sarrafa su, don neman mu san daga inda ya fito.

    To dole ne mu yi namu ƙoƙarin, Idan ka yi tsokaci mai nisa cikin abin nan da littafin Tarihin Kano ya faɗa game da Dala, za ka ga shi wannan mutum, ya zo da abubuwa uku waɗanda ba a san su a nan ƙasar ba, kafin zuwansa, kuma su waɗannan abubuwa da ya zo da su, su suka sa ya sami shugabancin matsafan wannan guri, har ya bar wa jikansa Barbushe wannan shugabanci.

    Su waɗannan sababbin abubuwan dai da Dala ya kawo su ne:

    1. Dabarun gina wa gunki ɗaki na musamman, da sa masa ranar bauta, da sallar idi biyu; ƙaramar salla da babbar salla, kamar yadda ake bauta a Ka’aba a ƙasar Larabawa a zamanin jahiliyya.
    2. Dabarar sihirce-sihirce da tsafe-tsafe wanda ta burge mazauna wannan wuri, har suka yi wa Dala mubaya’a suka bi jikansa Barbushe da gunkinsa Tsumburbura bi na haƙiƙa.
    3. Dabarar sarrafa giwa wadda ta nuna cewa dama can kafin Dala ya zo nan kasar, ya san giwa da yadda ake sarrafa ta. Tun da yake waɗannan abubuwa da muka lissafa haka suke ga Dala, to shi Dalan daga ina ya fito? Kuma a ina ya sami sanin waɗannan dabaru nasa da aka ambata a sama?

    Shehu Nasiru Kabara ya gaya min cewa, Dala ya zo ne daga tsibirin Dahlak na Rasar Habasha. Wannan tsibiri a bakin kogin Maliya yake, kuma a yanzu yana cikin Kasar Eritrea ne. To ka ga ashe Dala ya fito ne daga cikin ƙasashen gabas, waɗanda suka sami ci gaba wajen ilmin sihiri da tsafi da bautar gumaka da farauta irin ta wancan lokaci fiye da na mazaunan Kano na farko.

    Don haka suka bi shi dole, ba don ra’ayi ba.

    Amma a nazarin da Lugard  ya yi a kan tarihin Hausawa a cikin littafinsa mai suna Tropical Dependence ya ce, “Masu irin wannan addini na gunkin tsumburbura watakila Kibdawan Misira ne na ƙabilar Phonecian, wato Banu Kan’ana kamar yadda aka san su a ƙasar Hausa. Sabooda haka, Dala da jikansa Barbushe ana zaton kibɗawan Misira ne suka yiwo ƙaura daga tsibirin Dahlak na kogin Baharul Maliya, wanda a wannan lokacin a ƙarƙashin mulkin Fir’aun bin Inf yake. Da suka zo nan, suka mallake mutanen wannan   ƙasa na   farko;   ƙabilun  Kwararrafa saboda ci gabansu da ƙwarewarsu wajen tsafi da farautar giwa.

    Zuwan Dala Da Aikin Hajji A Kano

    Zuwan Dala wannan garin tare da iyalinsa da sauran jama’a da ya zo da su, ya kawo ci gaban mazauna wannan wuri na asali. Da farko dai, an samu auratayya tsakanin iyalinsa da mutanen wannan guri, wanda daga ƙarshe ta haɗe mutanen, har aka san su da ƙabilar Dala. Na biyu kuma Dala ya zo da sabuwar bautar gunki irin wadda ake yi a Makka ta su Lata da Uzza kafin Musulunci ya bayyana”.

    Haka kuma, shi ne ya fara gina wa gunki ɗakin bauta mai kusurwa guda huɗu wanda ba mai shiga sai shi kaɗai, ya kirawo wannan gunki nasa Tsumburbura, (watakila wannan ya yi  kama da Kulaista Abraha Sarkin Yaman).

    Bayan wannan, Dala ya sa wa wannan gunki nasa bikin idi a kowacce shekara wanda ake yi a daidai da lokacin da ake hawan Arfa da Babbar salla a Makka. Waɗannan sababbin  abubuwa  sun  bai  wa  Dala ƙarfin ɗaukaka   daga   mabiyansa   na   ko’ina   na ƙasar Kano. Wannan ɗaukaka ta Dala, ita ce ta haɓaka, har ta zama gadon gargajiya da ɗan jikansa, Barbushe ya gaji duk sihirinsa da tsafinsa, bayan shi ya mutu.

    Game kuma da irin addinin da Dala ya zo da shi wanda ya sha bamban da bautar Jakara, ga abin da Malam Adamu naMa’aji ya fada a kai:

    “Ana yin  bikin  Idi sau  ɗaya  a shekara, a (Dala), daidai da lokacin da ake yin Sallar Id-el- Adha a watan Zul Hajj a Makka. A ranar sallar Idi Barbushe, wanda shi ne babban Limami, shi yake jan duk mahajjata zuwa ɗakin gunkinsu, yana rike da baƙin bunsuru na layya. Idan an yanka wannan bunsuru, sai a zuba jininsa a cikin wata gidauniya, wadda aka ajiye a gaban gunkin.

    To, a nan ne Barbushe zai saurari abin da gidauniyar za ta yi. Idan jinin ya yi sanyi a cikin gidauniyar to, alama ce ta komai zai daidaita a sami zaman lafiya da arziki a wannan shekara. Idan kuma jinin ya yi zafi to alama ce ta abin da zai faru a wannan shekara na dangin masifu. Yawan zafin jinin yawan abin da zai faru kenan ko, yaƙi ko annoba ko yunwa. Daga nan sai Barbushe ya shaida wa maƙarrabansa abin da ya gani na masifar da za ta afku, da kuma lokacin da za ta afku din.

    Sannan kuma sai ya ba da umarnin kowane mahajjaci ya yi layya da abin da ya zo da shi don a roki gumaka su kare masifar da za ta zo, ko su rage ta, ta yi wa mutane sauƙi yadda za su iya jure ta”. Wani abin sha’awa a nan shi ne, irin wannan bauta da ake yi a Kano, ita Larabawa suke yi wa Lata da Uzza a Ka’aba a Makka, kafin bayyanar addinin Musulunci.

    A cikin littafinsa mai suna Nuril Yakeen Fi Sirat Sayyadil-Mursalin, Sheikh Muhammad al-Hadhari ya bayyana irin gidauniyar da ake zuba jinin bautar gunki a Makka ta waccan lokacin, ya ce sunan gidauniyar “al-Nasab”, kuma dutse ne aka fafe shi ya zama gurin zuba jinin bauta. Koda yake a nan Malam Adamu na Ma’aji, bai faɗi sunan gidauniyar tsafi ta Barbushe ba, bai kuma faɗi siffarta ba, wataƙila gidauniyar tsafin Barbushe ta ƙarfe ce, wadda mutanen Kano suka ƙera masa, don irin wannan ibada ta gumaka.

    Wannan siffar bautar gunkin Tsumburbura da Malam Adamu na Ma’aji ya bayyana, ta yi daidai da abin da littafin Tarihin Kano ya bayyana game da Idin da ake yi a Dala a wancan lokaci, kuma ga abin da littafin ya ce: Ya fara da nahiyoyin da ake tahowa Dala domin bikin Idi biyu; sallah karama da Sallah babba.“Tun daga Tudu zuwa Danbakoshi, daga Duji zuwa Dankwai, dukkansu suna taruwa wurin Barbushe daren sallah biyu, domin shi ne babbansu cikin tsafi.

    Sunan wurin da gunkinsa yake “Kakuwa”, sunansa kuwa “Tsumburbura domin itaciya ce da ake ambaton ta “Shamus”, sunan mutumin da yake a zaune a karkashinta dare da rana “Mai Tsumburbura”. An kewaye itaciyar da gini, babu mai shiga cikin ginin sai Barbushe, dukkan wanda ya shiga sai ya mutu nan da nan.

    Barbushe kuma ba ya saukowa daga dutsen Dala sai idan ranakun Idi biyu sun kusato. Sa’an nan mutane su zo masa daga gabas da yamma, kudu da arewa, maza da mata. Daga cikinsu wadansu su zo da bakin kare, wadansu da bakar kaza, wadansu da bakiin bunsuru“.

    Wannan ita ce siffar gunkin Barbushe da masu bauta masa da kuma lokacin da suke yin wannan bauta, wato Salla babba da Salla ƙarama ko Kuma mu ce Hajji da Umra, kamar yadda ake yin su a Makka ta lokacin Jahiliyya.

    Ban da wannan kuma ga yadda suke yin hawan arfa  da Ɗawafi i na jahiliyya, bayan su kuma su yi layya “Idan sun taru a ƙarƙashin dutsen Dala ranar jajibri (ranar Arfa) bayan la’asar, sa’an nan Barbushe ya fito daga gidansa da Isha tare da makaɗansa (na Kuru da Gunduwa da Tsintsima). Ya riƙa kururuwa da ƙarfi yana cewa; “Babban Jimina akasa mun gama karaga ga laya Tsumburbura”.

    Mutane kuma su ce, ga Tsumbirbirar Kanawa, ga wajen Dala”. Bayan wannan ya sauko su tafi tare da shi zuwa wurin gunki. Da isa wurin gunkin, kowa ya yanka abin da ya zo da shi, sannan Barbushe ya shiga cikin ginin shi kaɗai yana cewa, Magajin Dala, da kun ƙi da kun so ku bi, ni ba ra’ayi ba‘. Su kuma su ce,

    “Maigida bisa kan dutse, ubangijin Mama, bi mun bi ka, ba a ra ‘ayi ba”. Suna faɗar wannan suna kewaye ginin (suna dawafi) har hudowar alfijir, sa ‘an nan su tsaya tsirara su ci abinci.

    Ya fito, ya ba su labarin dukkan abin da zai faru cikin dukkan wannan shekara, har da bakon da zai fuskanto zuwa wannan gari, ko na alheri ne ko na sharri ne. Shi ne ma ya ba su labarin gushewar mulkinsu da sarewar itaciyarsu da Konewarta da ginin wannan masallaci.

    Kuma ya ce musu wani mutum zai zo wannan gari tare da rundunarsa, ya mallake mu”. Suka ce masa “don me ka fadi wannan? Wannan magana ce mummuna, ya yi shiru. Sa’an nan ya ce da sannu ku gan shi da alfarmar Tsumbirbura! Idan bai zo a zamaninku ba, ya zo a zamanin ‘ya’yanku, ya mallaki dukkan wanda ya samu a cikin wannan ƙasa dukkanta, ya sa a manta da ku duk da jama’arku, ya kuma bayyana da ƙabilar tasa zamani mai tsawo.”

    Wannan duba na Barbushe bai yi wa mabiyansa daɗi ba, don haka suka yi bakin ciki kwarai suka ce masa, “Yaya za mu yi mu kawar da wannan al’amari? Ya ba su amsa da cewa ba yadda za ku yi, sai hakuri. Watakila Barbushe ya hango wani gagarumin juyi, wanda ƙabilar Madatai za ta zo da shi wanda zai haɗiye ƙabila tasa da sannu, shi ya sa ya yi wannan duba cikin tsafinsa, ya ga abin da ya gani na wannan juyi, ya gaya wa mabiyansa.

    Kogin Jakara

    Koda yake waɗannan ƙabilu ba lokaci ɗaya suka zo Kano ba, kuma ba gaba ɗaya suka zo ba, a’a kaɗan-kaɗan suka dinga zuwa, har suka taru suka yi ƙungiya iri biyu, kungiyar Dala ta masu bautar gunki, wato Tsumburbura da kungiyar ‘Yan farauta. Lokacin da wadannan kungiyoyi suke zaune a Kano suna zaune kusa da juna, amma kogin Jakara da manya-manyan itatuwan da suke kewaye da kogin su ne suka raba su, ƙabilar Dala tana arewa da ita, ƙabilar Madatai tana kudu da ita.

    Ita dai Jakara wata ƙorama ce wadda ta faro daga wani guri, yammacin birni, wanda ake kira Bulbula, a Aisami, gabas da Gwauron Dutse. Ta keta ta Dausayi ta Karofin Wanka-da-Shuni, ta cikin Kasuwar kurmi, ta yi gabas har ta je Wasai ta garin Minjibir, ta miƙe da tafiya har ta kai Duku, ta ƙasar Garkin Dirani, inda ta ƙare , ba ta sake tafiya ko’ina ba.

    Wannan ƙorama da duhuwarta, su ne suka raba waɗannan ƙabilu gudu biyu, kamar yadda muka faɗa a baya. To su waɗannan ƙabilu tun zuwan su, sun tarar da mazauna wannan guri na asali, suka zauna tare da su, suka koya musu irin sababbin dabarun zaman duniya da suka zo da su inda suka yiwo ƙaura, waɗanda mazauna wannan guri na asali ba su san su ba.

    Kafin Dala, kakan Barbushe ubangijin Tsumburbura, ya zo wannan gari, akwai mutane da suke zaune a nan suna rayuwa irin tasu.

    Mutanen da suke zaune a wannan guri, kafin zuwan Dala Kabilu ne iri daban-daban, kuma suna zaune ne zama irin na rinji. Zaman rinji shi ne zaman da kowane maigida yake zaune da ƙungiyarsa, a waje ɗaya, wadda ta haɗa gidansa da gidan ‘ya’yansa da na ƙannensa da kuma na barorinsa, ko kuma na waɗansu mutane daban da suka kawo caffa gurinsa don ya riƙe su, kamar ‘ya’yansa.

    Kowane rinji akwai sana’ar da aka san shi da ita, kuma mutanen da suke zaune cikin rinjin an san iyakar wuraren da suka mallaka don noma da waɗansu ayyuka na sana’a.

    Kamar yadda littafin Tarihin Kano ya fada, wasu daga cikin mutanen da Dala ya samu a nan, suna zaune ne kusa da kan Dutsen Dala, inda shi kansa ya hau ya gina nasa gidan. Waɗannan mutane kamar yadda Tarihin Kano ya bayyana, su ne: Gunzago mai gida a ƙarƙashin Goron-Dutse a Ga-giwa, wanda yake kama giwa da igiya don ƙarfinsa da Gubanasu da Ibrahim da Bardoje da Nisau da Kamfatsu da  Duje da Janberi da Gamakora da Gaftaro da Hangugu da Kar-dangi.

    Waɗannan mutane su ne littafin Tarihin Kano ya bayyana su da cewa su ne muƙarraban Barbushe, jikan Dala. Wataƙila ma auratayya ce ta haɗa kakanninsu da ƙabilar Dala; wadda ya zo da ita, har wannan dangantaka ta shiga tsakaninsu.

    Har ila yau; akwai wasu Rinjinan (Rijau) da shugabanninsu suka yi caffa ga Dala da gunkinsa; koda yake su ma zaman kansu suke yi, kuma nesa da Dala suke. Waɗannan kabilu su ne:
    1. Ƙabilar Danburu wanda yake zauna a Jigirya, wajen mil goma gabas da Dala.
    2. Ƙabilar Jandamisa wanda ake kira Ruma. Shi kuwa a kan Dutsen Magwam yake, wato Nassarawa ta yanzu; kuma ƙabilar wannan mutum wato Rumawa sun fi kowace ƙabila yawa a Kano a wancan lokacin. Domin su ne suka yaɗu tun daga inda suke, har zuwa Salanta wato kudu da Dala kamar mil goma.
    3. Ƙabilar Hambarau waɗanda suke zaune a kan Dutsen Tanagar.
    4. Ƙabilar Nisau wadanda suka zauna a kan Dutsen Fanisau. Shi Nisau shi ne uban Gumban ɗaya daga cikin manyan da suke bin Tsumburbura da Barbushe.

    Domin karanta cikakken bayani akan Taƙaitaccen Tarihin Kano Kashi Na Ɗaya(1) danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Taƙaitaccen Tarihin Ƙasar Hausa danna nan.

  • Zuwan Tajwidi Da Musabaƙa Da Tasirinsa Cikin Tsarin Tsangaya

    Zuwan Tajwidi Da Musabaƙa Da Tasirinsa Cikin Tsarin Tsangaya

    Tajwidi dai ba sabon al’amari ba ne wajen ma’abota tsangaya, domin kuwa, makaranta da yawa a Maiduguri da Kano sun karɓe shi, kuma sun koye shi tun farko-farkon ƙarni na goma sha tara.

    Misali a nan shi ne, Malam Rabi’u Ɗantinki da Malam Ɗankwandarai, waɗanda duka alamajirai ne wajen mashahurin masanin ilmin Tajwidi da ƙira’o’in nan, watau Gwani Hamad.

    Hakan kuwa ya yi tasiri da gaske wajen kyautata karatun Alƙur’ani a Kano. A Maiduguri kuwa za mu ga cewa, al’amarin Tajwidi da ilmin ƙira’o’i ya ƙara bunƙasa ne bayan zuwan wasu malamai daga ƙasar Chadi, waɗanda suka yi karatu a wurin Shehun Azahar da ke ƙasar Masar. Waɗannan sun haɗa da Sheikh Daha da kuma Sheikh Hassan bn Umar Almuƙuri.

    Duk da wannan alaƙa tsakanin ma’abota tsangaya da Tajwidi tun kimanin shekaru tamanin baya; Tajwidi da ilmin ƙira’a bai yaɗu ya yi tasiri ba, sai bayan zuwan Musabaƙa. A nan ne makaranta masu tilawa mai ƙarfi daga tsangaya; suka riƙa koyon Tajwidi suna yin fice a musabaƙar cikin gida da ma duniya baki ɗaya.

    Babu shakka, hakan ya zama sababin tsundumar makaranta fagen neman ilmin fannin Musulunci; wasu ma suka fara danganawa da jami’o’in gida da ma wajen Najeriya, Fitaccen kwatance a nan shi ne Sheikh Ja’afar Mahmud Adam; wanda asalin karatunsa tsangaya ce.

    Daga bisani kuma, har ya dangana da Jami’o’in Musulunci da ke Madina da Sudan; don samun digiri na farko da na biyu wato Majistera. A halin yanzu kuma yana ƙoƙarin yin digiri na uku (Doctorate).

    Malam Ja’afar a yau ɗaya ne daga fitattun malamai, ba a Kano kawai ba, har ma Najeriya gaba ɗayanta. Baya ga ɗaiɗaikun makarantan da suka faɗa wasu fannoni a sababin Tajwidi da Musabaƙa; da yawan tsangayu a Maiduguri da Kano da kewayensu, sun buɗe ɓangaren Tajwidi wanda aka fi sani da ɓangaren Tahfeez. Babban misali a nan shi ne, Gwani Saleh Ɗanzarga Tahfeez da ke Kano; da kuma Tahfeez ta Sheikh Ghibirima; wadda ake kira Institute for the Memorisation of the Holy Qur’an Nguru.

    Duk da irin wannan tasiri da Tajwidi da Musabaƙa suka yi ga tsarin tsangaya a Arewacin Najeriya; har yanzu mafi yawan tsangayu da makaranta suna kan tsohon tsarin karatu bisa ƙarin harshenmu na gargajiya.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ma’anar Tsangaya danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ma’anar Waƙafi danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Misalan Waƙafi Ababen Koyi A Tarihin Musulunci

    Misalan Waƙafi Ababen Koyi A Tarihin Musulunci

    1. Zamanin Halifofi Shiryayyu ba shakka an samiu nau’o’i daban-daban a wannan lokaci, kaɗan daga cikin misalan su sun haɗa da:

    Waƙafin da sayyidina Umar ya yi da kasonsa guda ɗari dake Khaibar, wanda ya rubuta wasiyya da kansa da cewa:- “Da sunan Allah Mai rahama Mai jinƙai, wannan takarda sheda ce ta wasiyyar da bawan Allah Umar shugaban muminai ya yi ko wani abu zai faru da shi (yana wasiyya da cewa) Samgah da Sirmata bn Al-Akwa (gonaki biyu) da dukkan bayin da suke cikinsu da kasona guda ɗari dake Khaibara da dukkan bayin da suke cikinsu”..

    Waƙafin da Sayyidina Ali Bn Abi-Ɗalib Allah Ya yarda da shi ya yi, wanda ya rubuta shi kamar haka:- “Wannan takardar sheda ce bisa abin da Ali bn Abi-Ɗalib ya yi, ya kuma hukunta da dukiyarsa cewa; na sadaukar da (amfanin gonakinsa) na Yanbu da Wadil-Kura da Azinah da Ra’ah a cikin hanyar Allah; kuma ga ‘yan uwa na kusa da na nesa, kamar yadda ba za a yi kyauta da su ba, kuma ba za a gaje su ba, a lokacin rayuwa ko bayan raina”.

    Ba shakka wannan kaɗan ne daga cikin misalai da yawa na waƙafi; a lokacin halifofi shiryayyu, Allah ya yarda da su.

    2. Zamanin Mulkin Banu Umayya

    Ba shakka akwai misalai masu ƙayatarwa matuƙa na irin nau’o’i daban-daban na waƙafi da aka yi a wancan lokaci. Ga kaɗan daga cikinsu:-

    Gina babban masallacin nan na birnin Dimashk wanda har zuwa wannan zamani namu yana nan daram, wanda kuma muka ambata a baya cewa an gina shi a zamanin Halifa Walid ɗan Abdul – Malik wanda aka ruwaito cewa; a lokacin da zai gina wannan masallaci, sai da ya sa aka kawo masa ƙwararru daga ko’ina; waɗanda yawan su da sauran ma’aikatansu ya kai kimanin mutum dubu goma sha biyu.

    Ya kuma kashe kuɗi kimanin akwati ɗari huɗu; kowane akwati yana ɗauke da kwabbunan tataccen zinare guda dubu ashirin da takwas. Sai da ya shafe tsawon shekaru ashirin yana ginin wannan masallaci.

    Gina Asibitoci Da Hanyoyi Da Rijiyoyi

    Haka nan kuma shi dai wannan bawan Allah; shi ne mutum na farko da ya gina asibitoci na musamman don amfanin mutane.

    Haka kuma ya gina waɗansu na musamman da ya keɓance su ga masu ciwon kuturta; waɗanda a lokacinsa ya killace su, ya hana su bara; ya kuma ware maƙudan kuɗaɗe don yi musu magani da ba su cikakkiyar kulawa. Haka kuma, ya bayar da umarni ga gwamnansa mai kula da Madinah a wancan lokaci Umar ɗan Abdul-Aziz cewa ya gyara unguwanninta ya kuma gina rijiyoyi, ya kuma ɗauki ma’aikatan da za su rinƙa janyo ruwa don amfanin jama’a.

    Haka nan, ya aikawa dukkan jami’ansa a ko’ina kuɗaɗena suke cewa; su ware musamman ga mabuƙata tare da shimfiɗa hanyoyi da gidaje domin saukar baƙi kyauta. Bugu da ƙari kuma, wani kyakkyawan misali na waƙafi don amfanin al’umma shi ne ; yadda halifofin Banu Umayyah na wancan zamani suka bayar da muhimmanci matuƙa wajen gina madatsan ruwa, alal misali, a lokacin halifancin Umar ɗan Abdul- Aziz haka madatsan ruwa a wurare masu ɗumbin yawa kamar su Basra, da Arnmenia, da Dimashk da sauransu.

    3. Zamanin mulkin Abbasiyyawa

    Ba shakka halifofin zamanin Abbasiyya sun bayar da muhimmanci ga waƙafi a fannin gina asibitoci; da samar da littattafai don horar da ƙananan likitoci, tare da hayar ƙwararru da za su koyar da su duk ta hanyar waƙafi. Kaɗan daga cikin misalan asibitoci da aka gina a wancan lokaci; sun haɗa da asibitocin nan da ake kira Almustashfà Al-adudiy (wanda muka ambata a baya) wanda Haifa Adudud – Daulah al-Buwaihiy ya gina a birnin Bagdad a shekara ta (366 Hijiriyyah /976 Miladiyya) ya kuma ɗauki ƙwararrun likitoci a fannoni daban-daban waɗanda kimanin yawansu ya kai 24.

    Komai na asibitin kyauta ne, ga kulawa da marasa lafiya wajen abinci; da abin sha; da ɗinka musu sababbin tufafi, baya ga tsarin bayar da guzurin komawa gida ga duk wani marasa lafiya da aka sallama. Kamar yadda kuma ya zo a littattafan tarihi cewa, waɗansu daga cikin gwamnoni na wannan daula, sukan kashe kuɗaɗe maƙudai wajen yin irin waɗannan nau’o’i na waƙafi kamar yadda aka samu cewa, Ahmad ɗan Dolon gwamnan Masar a wancan lokaci, ya gina asibiti a lokacin da ya kammala, sai ya sadaukar masa da kuɗaɗen shigar da ake samu daga dar addiwan da kasuwar bayi da waɗansu gidaje nasa.

    Haka kuma ya kafa ƙa’idar cewa; a cikin waɗanda za su amfana da wannan asibiti ban da manyan hafsoshinsa da fadawansa da ‘ya’yan sarauta; haka kuma duk wanda za a kwantar a asibitin, sai an ba shi sababbin kaya ya sa, tsofaffin kuma za a adana masa su ne har zuwa lokacin da Allah ya ba shi sauƙi sai a damƙa masa kayansa.

    Haka kuma akan yi masa sabuwar shimfiɗa a kula da cin sa da shan sa, da yi masa magani, kuma ba za a sallame shi ba, har sai ya warke sarai; ya dawo yana cin duk wani abinci da ya saba ci kafin rashin lafiyarsa.

    Haka kuma a waɗansu lokuta akan gayyato likitoci daga wurare daban-daban don bayar da kulawa ga marasa lafiya, wato kamar dai abin nan da muka sani a wannan zamani da ake kira “medical tour”; (wato likitoci ‘yan sha-ka- tafi tare da biyansu haƙƙoƙinsu da ɗaukar ɗawainiyar duk wata buƙata ta su).

    Misalai na waƙafi da aka yi wancan zamani ba wai ya tsaya ne kawai ga gina asibitoci ba; haka kuma bai tsaya ga ɓangaren hukuma kawai ba. Wani ɗan ƙaramin misali da zai tabbatar mana da hakan shi ne, wani waƙafi da wani attajiri ya yi mai suna Fakhruddaula bn Almuddalib a birnin Bagdad (ya rasu a shekara ta 578 bayan Hijira ); ya gina wata katafariyar makaranta mai suna Dar Adhdhahab, ya damƙa ta a hannun wani mashahurin malami mai suna Jamaluddin bn Fadlan Ash- Shafi’i ya kuma sadaukar mata da wata dukiya tasa da abin da take samarwa kowace shekara, ya kai kimanin dinare dubu ɗaya da ɗari biyar.

    Bugu da ƙari, su kansu mata ba a bar su a baya ba; wajen wannan ayyuka na alheri, domin kuwa ya zo a littattafan tarıhi cewa Sayyida Zubaidah bnt Ja’afar bn Mansur; matar Halifa Harun Ar-Rashid ta haƙa rijiya da ake kira da “ainul mashash a Hijaz” ta kuma sa aka yi wa ruwanta hanya a tudu da gangare; har tsawon tafiyar mil goma sha biyu zuwa garin Makkah; wanda wannan aiki ya lashe kuɗi kimanin dinare miliyan ɗaya da dubu ɗari bakwai; (wanda ƙiyasin kowanne dinare ɗaya a zamaninmu shi ne nauyin giram 4.25 na tataccen zinare).

    A ɓangare na makarantu kuwa, tarihi ba zai taɓa mantawa da jerin gwanon makarantun nan da ake yiwa laƙabi da makarantun Nizamiyya ba; waɗanda waziri Nizamul Mulk Addardusi (ya rasu shekara ta 485 Hijiriyya) ya kafa, waɗanda da yawa daga cikinsu suka zamo a sahun farko a tarihin jami’o’i a duniya baki ɗaya. Haka nan ya ci gaba da gina irin waɗannan makarantu a ko’ina a cikin daular Musulunci, kamar yadda aka sami mashahuran malamai da suka koyar a waɗannan makarantu. Alal misali, a daidai lokacin da Imam Al-Ghazali yake koyarwa a reshenta na Bagdad, shi kuwa shahararren malamin nan mai suna Imam Al-Haramain Abu Al-Ma’ali Al-Juwaini yana koyarwa a reshenta na Naisabur.

    4. Daular Musulunci Ta Andalus

    A haƙiƙanin gaskiya ana iya cewa waƙafi na ɗaya daga cikin alamomin wuraren da daulolin Musulunci; suka kafu a ko’ina a faɗin duniya; domin kuwa shi ne kamar wata alama da ta zama ruwan dare a waɗannan dauloli a tsawon tarihinsu; duk da kasancewar sun kafu ne a wurare daban-daban kuma a lokuta mabambanta. Dalilin faɗin hakan kuwa shi ne, duk da cewa daular Musulunci da ta kafu a Andalus(Spain) ta yi nisa matuƙa; daga ƙasashen Larabawa waɗanda suke gabashin duniya.

    Domin kuwa Andalus tana cikin nahiyar Turai ne, to amma duk da haka, nau’o’i daban-daban na waƙafi da aka yi a cikinta, ko kaɗan bai gaza ga waɗanda aka yi a ƙasasshen gabas ɗin ba, a Alal misali, an samu Waƙafi a fannoni da dama a zamanin sarakuna irin su sarki Alhakam ɗan Abdur-Rahman An-Nasir wanda a lokacinsa ne wannan al’amari ya kai ƙololuwar bunƙasarsa, domin kuwa a zamaninsa ne ya sa aka jawo ruwa daga wurare masu matuƙar nisa zuwa ga wuraren buƙatar jama’a, waɗanda suka haɗa da masallacin Ƙurdubah.

    Kamar yadda ya yi waƙafi a fannin bunƙasa ilmi tun daga matakin koyon karatu da rubutu; har zuwa ga matakin ƙwarewa a fannonin haddar Alƙur’ani da Hadisi da Fiƙhu da sauransu.

    Hakazalika, an sami malamai da yawa waɗanda suka yi waƙafin litattafansu ga manyan cibiyoyin ilmi mai zurfi, kaɗan daga cikinsu sun haɗa da; Al Imam Abul-Ƙasim Abdul-Khaliƙ bn Abdil- Warith as-Sayuri (ya rasu a shekara ta 462 Hijiriyya) da al-Imam Kasim bn Isa bn Naji (ya rasu a shekara ta 839 Hijiriyya).

    Wani abin al’ajabi shi ne, ganin cewa yankin Andalus yanki ne mai yawan rafuka; wanda hakan yakan daƙile walwalar mutane matuƙa, sai musulmai na wancan lokaci suka yawaita yin waƙafi wajen gina gadoji. Littattafan tarihi sun ruwaito cewa gadar da ta fi kowacce girma da shahara a wancan lokaci ita ce gadar da sarki Hisham ɗan Abdur-Rahman ɗan Mu’awiya (ya rasu a shekara ta 180 hijiriyya) ya gina wacce ya kashe kuɗi matuƙa wajen gina ta.

    Kamar yadda ya ɗauki nauyin sa ido a kan aikin gina ta shi da kansa, wanda saboda da ganin haka har sai da waɗansu mutane suka fara gunagunin cewa; ya gina ta ne don amfanin kansa, a lokacin da labari ya kai gare shi, sai ya yi rantsuwa da cewa, “Ba zai yi taɓa bi ta kan wannan katafariyar gada ba, har sai idan tafiya yaƙi ko wani dalili ne ya tilasta masa yin hakan”.

    Kamar yadda kuma waɗansu daga cikin irin waɗannan gadoji sun yi ƙarƙo matuƙa; har zuwa wannan zamani namu, misali gadar da Mansur ɗan Abi Amir ya gina a shekara ta 389 Hijiriyya; wacce ya kashe mata kimanin kuɗi dinare dubu ɗari da arba’in.

    Wani abin mamaki dangane da yawaitar nau’o’in waƙafi a daular Musulunci ta Andalus; shi ne wani waƙafi da aka yi na musamman don sayen wani irin nau’i na kifi wanda ake kawowa a wani lokaci na shekara don raba shi ga matalauta; waɗanda ‘ya’yansu ƙanana na iya shiga cikin damuwa ganin yadda ‘ya’yan attajirai suke wadata da shi.

    5. Daular Uthmaniyyah

    Daular Musulunci ta Usmaniyya wacce Turkawa suka kafa, ita ce daula ta ƙarshe da ta faɗi. Ba shakka tarihin wannan daula cike yake da nau’o’i daban-daban na waƙafi; waɗanda lokaci ba zai ba mu dama mu yi bayanin su a wannnan ɗan ƙaramin littafi ba, to amma a taƙaice duk wani nau’i na waƙafi da muka ambata a baya, to su ma Turkawa ba a bar su a baya ba.

    Sannan kuma bugu da ƙari, muhimmancin da suka ba al’amarin waƙafi kai an samu cewa; akwai nau’o’i’ da dama a waƙafi da aka yi a lokacin mulkin wannan daula, kula da dabbobi marasa lafiya.

    6. Daulolin Musulunci na Nahiyar Afirka

    A haƙiƙanin gaskiya, abu ne mai matuƙar wahala a ce za a ƙididdige irin rawar da daulolin Musulunci na nahiyar Afirka; suka taka wajen bunƙasar al’ummarsu ta hanyar waƙafi. To amma hakan ba zai hana mu ɗan bayar da misalai na kaɗan daga cikinsu ba. Daga cikin mafiya muhimmancin irin waɗannan nau’o’i daban-daban na waƙafi sun haɗa da:

    Daular Musulunci ta Songhai

    An yi wani shahararren sarki na wannan daula mai suna Mansa Musa wanda ya yi gine-gine masu yawa da suka shafi na makarantu; domin bunƙasa harkar ilmi, ya gayyato tawaga ta musamman ta manyan masana a lokacin da ya je aikin Hajji da kuma gina masallatai guda biyu; na Gao da na Tumbuktu bisa taswirar da ɗaya daga cikin ƙwararru da ya zo da su a fannin gini mai suna Ishak el-Teudjin ya zana masa. Wannan masallaci ne daga baya ya zama shahararriyar jami’ar nan ta Sankore, duk a zamanin wannan sarki, a farkon ƙarni na goma sha huɗu na Miladiyya.

    Kamar yadda kuma an samo a tarihi cewa; a shekara ta 988 Miladiyya, an sami wani malami mai suna Al-Kadi Aƙib ɗan Mahmud ɗan Umar; wanda ya lashi takobin cewa; sai wannan gari na Tumbuktu ya tafi kafaɗa da kafaɗa da sauran manyan garuruwa na duniya a fagen bunƙasar ilmi mai zurfi. Domin aiwatar da wannan aniya tasa, sai ya nemi masu hannu da shuni da su taimaka da kuɗaɗe; don katafaren aikin faɗaɗa masallacin Tumbuktu da muka ambata a baya, ta yadda zai ɗauki malamai da almajirai masu yawa.

    Wani abin mamaki da ban sha’awa shi ne, sai aka sami wata mata mai dukiya; ta ɗauki nauyin gudanar da aikin ita kaɗai, a cikin dukiyarta a matsayin waƙafi.

    Daga baya wannan jami’a ta yi matuƙar shahara; har sai da ta zamo ɗaya daga cikin manyan jami’o’i na duniya a wancan lokaci; wanda har sai da yawan ɗalibanta ya kai kimanin dubu ashirin da biyar (25,000); haka nan katafaren ɗakin karatu da wannan jami’a take da shi daga littattafan da suka kama daga; dubu ɗari huɗu zuwa dubu ɗari bakwai (400,000 – 700,000). Nagartar karatunta ya zarce da yawa daga cikin manyan jami’o’in duniya na wancan lokaci.

    Dangane da al’amarin bunƙasa rayuwar al’umma kuwa, wannan daula ta bar wannan abin alfahari da dama; domin kuwa an samo cewa a lokacin wani sarki mai suna Muhammad Askiya, ya yi abubuwa a fannoni daban-daban da suka haɗa da kulawa; da jin daɗin matafiya masu keta hanyoyin sahara da suka gifta ta waccan ƙasa.

    7. Tsohuwar Daular Ghana

    Wani abin ban sha’awa dangane da ayyukan waƙafi a wannan daula shi ne; bayan Musulunci ya shiga wannan daula ba da daɗewa ba, al’umomin wannnan yanki suka fara aiwatar da abubuwa daban-daban da suka shafi; jin daɗin al’umma ta hanyar waƙafi.

    Alal misali addinin Musulunci ya shiga wannan daula ne a kashi na farko na ƙarni na ɗaya bayan Hijira; to amma sai ga shi a cikin shekaru goma da shigarsa; wato a shekara ta 60 bayan Hijira an samu cewa; yawan masallatai dake babban birnin wannan daula; waɗanda aka gina a ɓangarorin da musulmai suke; sun kai kimanin masallatai goma sha biyu; kowannen su cike yake da manyan malamai da ɗalībai a fannonin ilmi da dama.

    8. Zamanin Da Muke Ciki

    Kamar yadda muka ambata a baya cewa waƙafi wata babbar alama ce ta samuwar al’ummar musulmai a duk inda suke; ba shakka za mu iya ganin hakan har a wannan zamani da muke ciki; domin kuwa an sami mutane masu son aikin alheri da ƙungiyoyi waɗanda suka bayar da misalai ababan koyi na waƙafi. Ƙadan daga cikin waɗannnan misalai sun haɗa da:

    Tsarin Hannun Jarin Waƙafi Na Annur

    Wannan wani tsari ne da waɗansu bayin Allah suka yi. Reshen wannan gidauniya yana ƙasar Malaysia, to amma tana aiwatar da ayyukan waƙafinta a ko’ina a faɗin duniya. Ta hanyar da wannan gidauniya kuwa take gudanar da ayyukanta shi ne, ta tsattsara ayyukan da take son aiwatarwa; sannan sai ta rarraba shi a sigar hannun jari kowanne da farashinsa; wato abin nufi, iyaka yawan hannayen jarin da mutum ya saya, su ne gudunmawar da ya bayar wajen aiwatar da waɗannan ayyuka; waɗanda ake fatan ladansu zai ɗore har bayan rayuwar wanda ya bayar da taimakon.

    Wani misali na irin waɗannan ayyuka shi ne, wani tsari na juya kuɗaɗen taimakon da aka tara a cikin gidauniyar, ta hanyoyi masu sauƙin asara; idan ƙarshen shekara ta yi, sai a buga Alƙur’anai a raba da sunan wanda ya zuba jarin don yin haka kowacce shekara.

    Gidauniyar mai Martaba Muhammad Rashid Al Makhtum.

    Wanda ya kafa wannan cibiya shi ne sarkin Dubai wanda sunansa ne take ɗauke da shi. Manufar wannan cibiya shi ne, bunƙasa fannonin ilmi na Musulunci da fannonin ilmin kimiyya da fasaha; ta hanyar bayar da tallafi ga ‘ya’yan talakawa ‘yan baiwa, don su sami ilmi da horo a waɗannan fannoni. Wani abu da zai ba mai karatu sha’awa dangane da wannan gidauniya shi ne, irin maƙudan kuɗaɗe da ake ware mata; waɗanda sun kai dubunnan miliyoyi a kowacce shekara.

    Hubusin al Rajhi ɗan ƙasar Saudıyya, a inda kafin rasuwarsa ya yi wasicin dukkan dukiyarsa, a matsayin waƙafi ga talakawa da ayyukan alheri, bayan fitar da haƙƙin magada. Ubangiji Maɗaukaki kaɗai ne Ya san adadin talakawan dake rayuwa da iyalinsu cikin wannan dukiya mai albarka.

    Waƙaful Umm:

    Wannan wani sabon tsarin waƙafi ne na zamani kamar Annur na Malaysia. Da farko akan shata wata kadara mai nauyi, sannan a kasa ƙimarta zuwa ƙananan kaso na mai ƙaramin ƙarfi; don ‘ya’ya masu albarka su saya wa mahaifansu rayayyu ko marigaya. Jimillar kuɗin ita ce za a sai waccan kadara a bayar da hayar ta ga kamfanonin kasuwanci. Ribar ita za ake aiwatar da ayyukan alheri da ita. A halin yanzu wannan tsari na gudana a wasu daga ƙasashen Larabawa; Don ƙarin haske sai a duba littafinmu Jagorar ayyukan Cigaban Al’umma Mai Ɗorewa.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Nau’o’in Masu Amfani Da Waƙafi Ko Hubusi danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Gudunmowar Waƙafi/Hubusi Da Tasirinsa Wajen Gina Tattalin Arzikin Al’umma; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Taƙaitaccen Tarihin Waƙafi A Musulunci

    Taƙaitaccen Tarihin Waƙafi A Musulunci

    Ba shakka addinin Musulunci ya kwaɗaitar da mabiyansa dangane da waƙafi a matsayinsa na sadaka; wacce ladan ta yake ɗorewa har bayan rayuwar wanda ya yi ta. Kamar yadda ya zo a cikin faɗin Allah Maɗaukakin Sarki; “Kuma ku tsayar da sallah kuma ku bayar da zakka kuma abin da kuka gabatar; domin kanku daga alheri za ku same shi a wurin Allah, lalle ne Allah ga abin da kuke aikatawa mai gani ne”. (Baƙara aya ta 110).

    Haka kuma ya zo a hadisin Ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana cewa; a lokacin da ɗan Adam ya rasu dukkan ayyukansa sun tsaya in ban da abubuwa guda uku; sadaka mai gudana (waƙafi), ko wani ilmi da ake amfana da shi; ko ɗa nagari da yake yi masa addu’a.

    Haka nan fassarar abin da ake nufi da sadaka mai gudana ta zo a wani hadisi da Ibn Majah ya ruwaito; wanda a cikinsa ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yake cewa; “Lalle abin da kawai zai cigaba da iske mumuni na kyawawan ayyukansa bayan mutuwarsa. Shi ne wani ilimi da ya yaɗa ko ɗa na ƙwarai da ya bari ko wani Alƙur’ani da ya bar gadonsa; ko wani masallaci da ya gina ko kuma gida da ya gina don (amfani) matafiya.

    Ko wata ƙorama da ya tona take gudana ko kuma wata sadaka da ya fitar daga cikin dukiyarsa; a lokacin da yake da lafiya sanda yake raye wacce ladanta zai ci gaba da riskarsa har bayan rayuwarsa”.

    Haka nan kuma ya zo a cikin littattafan sirah cewa; a lokacin da Ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi Hijira daga Makka ya sauka birnin Madina. A duk faɗin birnin, babu wata hanya ta samun ruwan sha mai daɗi, sai wata rijiya da ake kira rijiyar Rumah, wacce a wancan lokaci mallakar wani marowacin mutum ce; wanda yake tsawwalawa mutane wajen sayen ruwanta.

    Ganin haka sai Ma’aiki Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kwaɗaitar da sahabbansa da cewa; “Wane ne zai sayi rijiyar Rumah (ya sadaukar da ita) Allah ya biya shi da mafiticinta a gidan Aljannah wanda nan take kuwa Sayyidina Uthman ya saye ta dirhami dubu talatin da biyar, kuma Ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce da shi “Ka sadaukar da ita ga musulmai, Allah zai ba ka lada, shi kuwa bai yi wata-wata ba ya aikata hakan.

    Haka nan Bukhari da Muslim sun ruwaito daga sayyidina Umar ɗan Khaɗɗab (Radiyallahu Anhu) cewa; ya ce da ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi na sami wata gona a Khaibara; wacce ban taɓa samun wata dukiya da ta kai darajarta a tsawon rayuwata ba”.

    Sai Ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce; “Idan ka ga dama kana iya riƙe asalinta ka sadaukar da amfaninta da Sayyidina Umar. Ya ji haka sai ya sadaukar da ita bisa sharaɗin cewa, ba za a sayar da ita kanta gonar ko a kyautar da ita ko a ci gadonta ba; tare da sadaukar da duk wani amfani nata ga talakawa, da ‘yan uwa, da bayi; da hanyoyin ɗaukaka addinin Allah, da baƙi, da kuma matafiya.

    Babu laifi ga masu kula da ita su ci ‘ya’yan itatuwanta; su kuma yi kyauta ga abokansu gwargwadon yadda aka sani a al’adance ba da sayarwa ba.

    Wannan al’amari na waƙafi ya watsu matuƙa a cikin sahabban Ma’aikin Allah; tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, bayan kwaɗaitarwar da ya yi da aikata hakan. Domin kuwa sun yi waƙafi na abubuwa daban-daban da suka haɗa da masallatai da gonaki; da rijiyoyi da kayan jihadi don ɗaukaka kalmar Allah.

    Ya tabbata cewa adadi mai yawa na sahabban Ma’aikin Allah; tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi sun yi waƙafi. Kaɗan daga cikinsu sun haɗa da Khalid ɗan Walid, da Jabir ɗan Abdullah, da Sa’ad ɗan Ubadah; da Ukbat Abdullahi ɗan Zubair, da Sa’ad ɗan Abi Waƙƙas, da uwar muminai Sayyidatina A’isha; da kuma Asma’u yar Abubakar – Allah ya yarda da su gaba ɗayansu.

    Babu wani mai hali daga cikin sahabban Ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi; wanda bai yi waƙafi ba, Haka kuma an rawaito daga Imam ash-Shafi’iya na cewa; “Labari ya ishe ni cewa mutum tamanin daga cikin sahabban ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi; ‘yan Madinah kowanne a cikin su ya yi waƙafi” .

    Domin karanta cikakken bayani a kan Manufofin Waƙafi danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Nau’o’in Masu Amfani Da Waƙafi Ko Hubusi danna nan

    Wannan baya nin an ciro shi ne daga Littafin Gudunmowar Waƙafi/Hubusi Da Tasirinsa Wajen Gina Tattalin Arzikin Al’umma. Wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tarihin Magabata da Haihuwar Ɗanƙwairo

    Tarihin Magabata da Haihuwar Ɗanƙwairo

    Magabatan Musa Ɗanwaƙiro Maradun su ne; kakanninsa da mahaifinsa da mahaifiyarsa da yayansa da ‘ya’yansa da kuma sauran ‘yan’uwa na jininsa.

    Musa Ɗanƙwairo da magabatansa sun fito ne daga garin Ɗankadu ta cikin Gundumar Bakura ta jihar Zamfara ta yanzu.

    2.1 Usman Ɗankwanagga: Mahaifin Ɗanƙwairo

    Usman Ɗankwanagga shi ne ɗan Kaka Maiganga, kuma shi ne ya haifi Musa Ɗanƙwairo. Usman Ɗankwanagga da zuriyyarsa mutanen Ɗankadu ne da ke cikin Gundumar Bakura, kamar yadda bayanai suka gabata.

    Usmaan Ɗankwanagga manoni ne, mai jajircewa a ayyukan gona. Haka kuma makaɗi na noma ne wanda ya shahara sosai. Sannan ya gaji kiɗan noma daga mahaifinsa, Makaɗa Kaka Maiganga. Har wa yau kuma Usman Ɗankwanagga ya gwama kiɗan fada da kiɗan noma. A kiɗan fada ya kaɗa abin kiɗa na kotso ne.

    A wani ƙauli an nun a wajejen 1914 Usman Ɗankwanagga ya bar garinsa na asali; ya fita neman wani wuri da zai yi noma shi da iyalinsa. A wannan tafiya ce ya haɗu da Sarkin Maradun, Alhaji Ibrahim I (1903-1923) a wata gonarsa ta Bazamawa. A wannan haɗuwa ce Sarkin Maradun ya amince ya ɗauki nauyin Usman Ɗankwanagga da dukkan jama’arsa; shi kuma ya zama makaɗinsa. Daga nan ne Usman Ɗankwanagga ya zaɓi ya zauna Birnin Ƙaya gari mai dausayi da ƙasar noma mai albarka. Iyalin Usman Ɗankwanagga sun zauna a ƙasar Ƙaya a wani wuri da ake kira Tunga, mai yalwar ƙasar noma7.

    Bayan da Usman Ɗankwanagga ya tsufa, sai ya yi murabus; aka naɗa babban ɗansa Abdu Kurna Sarkin Kiɗan Sarkin Maradun, mai amfani da kotso.

    2.2 ‘Yarnunu: Mahaifiyar Ɗanƙwairo

    ‘Yarnunu ita ce mahaifiyar Alhaji Musa Ɗanƙwairo. Ita kuma ‘yar asalin Goran Namaye ce, Bazamfariya ce gaba da baya.

    2.3 Makaɗa Abdu kurna

    Shi makaɗa Abdu Kurna an haife shi ne a garin Ɗankadu, a cikin Gundumar Bakura; Ƙaramar Hukumar Bakura, Jihar Zamfara a yau a daidai shekara ta 1899 bisa ƙiyasi. Tare da Abdu Kurna ne Usman Ɗankwanagga ya baro Ɗankadu zuwa Tunga ta Birnin Ƙaya, Maradun. Makaɗa Abdu Kurna ya yi kiɗan noma da na masu Sarauta . Makaɗa Abdu Kurna ne ya gaji Halifar Mahaifinsa Usman Ɗankwanagga ta Sarkin Kiɗan Sarkin Muradun. An naɗa Abdu Kurna a matsayin makaɗa na Sarkin Maradun a yayin da mahaifin nasu Usman Ɗankwanagga ya tsufa; kuma ya roƙi a maye gurbinsa na sarautar kiɗa da babban ɗansa Abdu Kurna.

    2.4 Yanayin Haihuwar Musa Ɗanƙwairo (1909)

    Yanayin haihuwar Musa Ɗanƙwairo ya riski wani hali na ɓurɓushin tasirin da zai zo wa Hausawa da al’ummar Arewa na shigowar Turawan Mulkin Mallaka a ƙarƙashin jagorancin Sarauniyar Ingila. Duk da saɓanin tarihin haihuwa; an ɗauka an haifi Musa Ɗanƙwairo a 1909, jim kaɗan da tsayar da mulkin mallaka na Turawa a 1902.

    Haihuwar Musa Ɗanƙwairo ta wakana a garin Ɗankadu na gundumar Bakura a yau ta Jihar Zamfara; kafin iyayensa su koma Tunga, Birnin Ƙaya ta gundumar Maradun. An raɗa wa Ɗanƙwairo sunan yanka na Musa.

    Shi kuwa Ɗanƙwairo wata alkunya ce ake gaya wa Musa bayan da ya kai shekaru bakwai da haihuwa; kuma ya fara sa hannu a harka ta kiɗa da waƙa a ƙarƙashin mahaifinsa Makaɗa Usman Ɗankwanagga. A cikin mataimakan kiɗa na Usman Ɗankwanagga akwai wani baransa, wani mutum mai murya wasai; mai zaƙi da shiga jiki wanda ake yi wa laƙabi da Ƙwairo. To sai Musa ya gaji irin wannan murya, shi ne mahaifinsa Usman Ɗankwanagga yake faɗin; ‘Ga Ɗanƙwairo an mayas (Gusau, 1996: sh. 104). Bishiyar Nasabar Kaka da Iyayen Musa Ɗankwairo.

    Makaɗa Kaka Maiganga

    Binta Amina Usman na Ɗankwanagga
    Sa’idu Shayi
    Mairana Naruwa Ɗantomi16
    Ali Sabon Kiɗi
    Abubakar Muh Maigayya Amadu Zuwaira Lawali Umaru17
    Lawali Shamsiyya Aliyu Musa Ibrahim Nasfatu
    (a) (b) (c)

    = Karima = Yarnunu = Ba’u (Mora)
    Abdullahi
    (Yawale) Ya Rasu a Ilorin
    Abdu Kurna Hauwa Musa Ɗanƙwairo Binta (Maryam)
    Galadima Maituwo Amina “Yardaudu Ƙauna
    (Indo A’isha)
    Ambaye Amina ‘Yaddaudu (Dosara)
    Garba Sambo Mani Ige Ibrahim
    (Ɗandarali) (Zuma) Usman (Kahiyo)
    Tamaidaji20 Umaru Karɓa Iro Abdu
    (Tsahara) ɗankutuɓe Maikano
    Tashayi (Inno) Safiya (‘Yarkwando)

    15 Makaɗa Usman Ɗankwanagga ya koma sabon mazauninsa na Tunga, Birnin Ƙaya; a Gundumar Maradun tare da dukkan wannan zuriyya ta mahaifinsa Makaɗa Kaka Maiganga.

    16 Sauran ‘ya’yan Amina su ne: Mustafa da Ibrahim da Mukhtari da Talatu da Rabi da kuma Saratu.

    17 Saruan ‘ya’yan Ali Sabon Kiɗi su ne: Abubakar da Zuwaira da Rumasa’u da Lawali.

    18 Sauran ‘ya’yan Muhammadu Maigayya su ne: Amadu da Ladidi da Hamida da Nomau Libiris (Namagarya).

    19 A dubi ‘ya’yan Musa Ɗanƙwairo a 3.3.2.

    20 ‘Ya’yan Tamaidaji (Tsahara) su ne: Ta’inna (A’isha) da Muhammadu Magaji (Sarkin Gida) da Sale da Hassi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Iyalin Musa Ɗanƙwairo danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Taƙaitaccen Tarihin Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.