Tarihin Magabata da Haihuwar Ɗanƙwairo

0
567

Magabatan Musa Ɗanwaƙiro Maradun su ne; kakanninsa da mahaifinsa da mahaifiyarsa da yayansa da ‘ya’yansa da kuma sauran ‘yan’uwa na jininsa.

Musa Ɗanƙwairo da magabatansa sun fito ne daga garin Ɗankadu ta cikin Gundumar Bakura ta jihar Zamfara ta yanzu.

2.1 Usman Ɗankwanagga: Mahaifin Ɗanƙwairo

Usman Ɗankwanagga shi ne ɗan Kaka Maiganga, kuma shi ne ya haifi Musa Ɗanƙwairo. Usman Ɗankwanagga da zuriyyarsa mutanen Ɗankadu ne da ke cikin Gundumar Bakura, kamar yadda bayanai suka gabata.

Usmaan Ɗankwanagga manoni ne, mai jajircewa a ayyukan gona. Haka kuma makaɗi na noma ne wanda ya shahara sosai. Sannan ya gaji kiɗan noma daga mahaifinsa, Makaɗa Kaka Maiganga. Har wa yau kuma Usman Ɗankwanagga ya gwama kiɗan fada da kiɗan noma. A kiɗan fada ya kaɗa abin kiɗa na kotso ne.

A wani ƙauli an nun a wajejen 1914 Usman Ɗankwanagga ya bar garinsa na asali; ya fita neman wani wuri da zai yi noma shi da iyalinsa. A wannan tafiya ce ya haɗu da Sarkin Maradun, Alhaji Ibrahim I (1903-1923) a wata gonarsa ta Bazamawa. A wannan haɗuwa ce Sarkin Maradun ya amince ya ɗauki nauyin Usman Ɗankwanagga da dukkan jama’arsa; shi kuma ya zama makaɗinsa. Daga nan ne Usman Ɗankwanagga ya zaɓi ya zauna Birnin Ƙaya gari mai dausayi da ƙasar noma mai albarka. Iyalin Usman Ɗankwanagga sun zauna a ƙasar Ƙaya a wani wuri da ake kira Tunga, mai yalwar ƙasar noma7.

Bayan da Usman Ɗankwanagga ya tsufa, sai ya yi murabus; aka naɗa babban ɗansa Abdu Kurna Sarkin Kiɗan Sarkin Maradun, mai amfani da kotso.

2.2 ‘Yarnunu: Mahaifiyar Ɗanƙwairo

‘Yarnunu ita ce mahaifiyar Alhaji Musa Ɗanƙwairo. Ita kuma ‘yar asalin Goran Namaye ce, Bazamfariya ce gaba da baya.

2.3 Makaɗa Abdu kurna

Shi makaɗa Abdu Kurna an haife shi ne a garin Ɗankadu, a cikin Gundumar Bakura; Ƙaramar Hukumar Bakura, Jihar Zamfara a yau a daidai shekara ta 1899 bisa ƙiyasi. Tare da Abdu Kurna ne Usman Ɗankwanagga ya baro Ɗankadu zuwa Tunga ta Birnin Ƙaya, Maradun. Makaɗa Abdu Kurna ya yi kiɗan noma da na masu Sarauta . Makaɗa Abdu Kurna ne ya gaji Halifar Mahaifinsa Usman Ɗankwanagga ta Sarkin Kiɗan Sarkin Muradun. An naɗa Abdu Kurna a matsayin makaɗa na Sarkin Maradun a yayin da mahaifin nasu Usman Ɗankwanagga ya tsufa; kuma ya roƙi a maye gurbinsa na sarautar kiɗa da babban ɗansa Abdu Kurna.

2.4 Yanayin Haihuwar Musa Ɗanƙwairo (1909)

Yanayin haihuwar Musa Ɗanƙwairo ya riski wani hali na ɓurɓushin tasirin da zai zo wa Hausawa da al’ummar Arewa na shigowar Turawan Mulkin Mallaka a ƙarƙashin jagorancin Sarauniyar Ingila. Duk da saɓanin tarihin haihuwa; an ɗauka an haifi Musa Ɗanƙwairo a 1909, jim kaɗan da tsayar da mulkin mallaka na Turawa a 1902.

Haihuwar Musa Ɗanƙwairo ta wakana a garin Ɗankadu na gundumar Bakura a yau ta Jihar Zamfara; kafin iyayensa su koma Tunga, Birnin Ƙaya ta gundumar Maradun. An raɗa wa Ɗanƙwairo sunan yanka na Musa.

Shi kuwa Ɗanƙwairo wata alkunya ce ake gaya wa Musa bayan da ya kai shekaru bakwai da haihuwa; kuma ya fara sa hannu a harka ta kiɗa da waƙa a ƙarƙashin mahaifinsa Makaɗa Usman Ɗankwanagga. A cikin mataimakan kiɗa na Usman Ɗankwanagga akwai wani baransa, wani mutum mai murya wasai; mai zaƙi da shiga jiki wanda ake yi wa laƙabi da Ƙwairo. To sai Musa ya gaji irin wannan murya, shi ne mahaifinsa Usman Ɗankwanagga yake faɗin; ‘Ga Ɗanƙwairo an mayas (Gusau, 1996: sh. 104). Bishiyar Nasabar Kaka da Iyayen Musa Ɗankwairo.

Makaɗa Kaka Maiganga

Binta Amina Usman na Ɗankwanagga
Sa’idu Shayi
Mairana Naruwa Ɗantomi16
Ali Sabon Kiɗi
Abubakar Muh Maigayya Amadu Zuwaira Lawali Umaru17
Lawali Shamsiyya Aliyu Musa Ibrahim Nasfatu
(a) (b) (c)

= Karima = Yarnunu = Ba’u (Mora)
Abdullahi
(Yawale) Ya Rasu a Ilorin
Abdu Kurna Hauwa Musa Ɗanƙwairo Binta (Maryam)
Galadima Maituwo Amina “Yardaudu Ƙauna
(Indo A’isha)
Ambaye Amina ‘Yaddaudu (Dosara)
Garba Sambo Mani Ige Ibrahim
(Ɗandarali) (Zuma) Usman (Kahiyo)
Tamaidaji20 Umaru Karɓa Iro Abdu
(Tsahara) ɗankutuɓe Maikano
Tashayi (Inno) Safiya (‘Yarkwando)

15 Makaɗa Usman Ɗankwanagga ya koma sabon mazauninsa na Tunga, Birnin Ƙaya; a Gundumar Maradun tare da dukkan wannan zuriyya ta mahaifinsa Makaɗa Kaka Maiganga.

16 Sauran ‘ya’yan Amina su ne: Mustafa da Ibrahim da Mukhtari da Talatu da Rabi da kuma Saratu.

17 Saruan ‘ya’yan Ali Sabon Kiɗi su ne: Abubakar da Zuwaira da Rumasa’u da Lawali.

18 Sauran ‘ya’yan Muhammadu Maigayya su ne: Amadu da Ladidi da Hamida da Nomau Libiris (Namagarya).

19 A dubi ‘ya’yan Musa Ɗanƙwairo a 3.3.2.

20 ‘Ya’yan Tamaidaji (Tsahara) su ne: Ta’inna (A’isha) da Muhammadu Magaji (Sarkin Gida) da Sale da Hassi.

Domin karanta cikakken bayani a kan Iyalin Musa Ɗanƙwairo danna nan.

Domin karanta cikakken bayani a kan Taƙaitaccen Tarihin Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau danna nan.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

labarin da ya wuceYanayin Harshen Waƙar Baka
Labarin na GabaSadarwa A Waƙar Baka
Prof. Sa’idu Muhammad Gusau
FARFESA SA'IDU MUHAMMAD GUSAU, An haife shi a Gusau jihar Sakkwato, (Maris 24, 1952). Ya yi karatun firamare na Islamiyya daga 1965-1969, ya je kwalejin sarkin Musulmi Abubakar daga Junairu 1970 zuwa Yuni 1973. Ya yi Diploma, Digiri Na farko (B.A), na biyu (M.A) da Digiri na uku (Ph.D) duk a jami'ar Bayero, Kano.