Tag: ilimin tarihi

  • Rasuwar Makaɗa, Sarkin Kiɗan Maradun Alhaji Musa (Ɗanƙwairo)

    Rasuwar Makaɗa, Sarkin Kiɗan Maradun Alhaji Musa (Ɗanƙwairo)

    Rasuwar Makaɗa, Sarkin Kiɗan Maradun Alhaji Musa (Ɗanƙwairo) Usman Ɗankwanagga a 1991.

    Sarkin Kiɗan Maradun, Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun, bayan wata gajeruwar rashin lafiya; Allahu cikin ikonsa ya karɓi rayinsa a ranar Juma’a 13 ga watan Satumba, 1991. Ya rasu a gidansa a Gidan Kano, Ƙaramar Hukumar Maradun, Jihar Zamfara.

    Allahu, karimun rahimun, ya daɗa haskaka makwancinsa, ya hore masa ni’imomi na Raudhatun min Riyadhil Jannah.

    Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo bawanka ne, ya sami shekaru talatin (30) izuwa ga jinƙanka; Allahu ka daɗa yafe kurakuransa, ka yi masa afuwa, ka kwantar da shi cikin Rahamarka, madauwamiya.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Takaiceccen Tarihin Rayuwar Dr. Yahaya Tanko danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatar Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tarihin Garin Gurin Gawa

    Tarihin Garin Gurin Gawa

    Kamar yadda marubutan littafin ‘Urban Society ‘ Gist da Halbert suka faɗa, kuma kamar yadda yake game da asalin ita kanta wayewar, tushen kowanne birni kusan ya samo asali ne daga hijirar mutanen ƙauyuka.

    Birane su ne cibiyar hadar-hadar kasuwanci, tsaro, al’adu, ilimi da bincike. Don haka ya sanya mutanen karkara na kusa da na nesa, da ma wasu mutanen da ke wasu biranen da dama kan ziyarci birane domin samun mafakar tsaro, ko kasuwanci, ko samun ilimi ko cimma wani dalili na al’ada da ma sauran muradai walau ziyarar ta kasance ta wucin gadi ko kuma ta-din-din-din.

    Akwai ilimin tarihi mai yawa da mukan rasa yayin kawar da kawunan mu ga tafarkan da suke sadar da mutane zuwa waɗancan birane. Wannan kuwa ya haɗar da tarihin wasu muhimman abubuwa da aka taɓa yi ko kuma muhimman wurare masu dangantaka da biranen kansu.

    Sau tari a ƙasar Hausa mutane kan niƙi gari domin ziyartar wani birni amma sai su shantake a wasu wurare na kusa ko na nesa da biranen bisa wasu dalilai. Haka kuma a wasu lokutan, sauyawar yanayai kan tursasa mutanen cikin birane komawa makusanta ko manesantan garuruwa ko birane da zama.

    Garin Gurin Gawa na ɗaya daga cikin ƙauyukan da suka kafu a turbar kano. Hasashe ya nuna cewar mabanbantan mutane da akasarin su ƴan tafarki ne suka kafa garin tsawon lokaci da ya shuɗe. Garin yana kudu da garin kano, akan turbar da za ta shigar da mutum birnin kano ta ƙofar Ɗan Agundi (wadda aka sara a wajajen shekarar 1499AD). Don haka duk mutanen da suke son shiga kano daga yankunan Rano, Jos, sassan ƙasar Bauchi da makamantan su sai sun bi ta wannan turba.

    ASALIN SUNAN GURIN GAWA

    Akwai mabanbantan zantuka game da asalin sunan Gurin Gawa.

    1. Na ɗaya: Gurin Gawa daga Gurin Gawarwaki. An ce an samo sunan ne daga kasancewar wurin filin daga. Watau a zamanin yaƙi, da zarar kano ta samu labarin an tunkaro ta da yaƙi ta wannan shiyya, sai ta turo dakarunta ta jibge su a wannan wuri. Don haka a nan za a fafata yaƙi, anan kuma za a samu tulin gawarwaki bayan ƙarewar yaƙi.

    2. Na biyu: Gurin Gawa daga ‘Gurin-Ge‘: Wannan ra’ayin yana cewa an samu sunan ne daga wani Bafillatani mai suna Gurin-ge, wanda kiwo ya biyo da shi ta wajen har kuma dabbobin sa suka gano masa wani kwarmin ruwa, don haka ya mayar da wajen mazaunin sa, daga bisani ƴanuwansa fulani suka riƙa riskar sa da zama.

    3. Na uku: Gurin gawa daga Gurin da aka samu  gawar Kuyangar Sarkin Rano: An ce akwai wani rafi tsakanin Medile da Gurin Gawa wanda ake kira ‘Ci-kuyangi’, saboda yadda ya yi silar mutuwar kuyangi da dama a ciki har da wata amintacciyar kuyangar Sarkin Rano wadda ta rasu a wurin a kan hanyarta ta shiga Kano, an ce daga nan aka samo sunan na Gurin Gawa.

    Zuwa yanzu, garin ya kasu kashi biyu, akwai Ruga inda fulani masu sarautar garin suke, da kuma ɓangaren Hausawa inda ake kira Dausayi. A nan ne mahaifiyar shahararren masani marigayi Sheikh Nasir Kabara ta ke.

    TASIRIN SHAHARAR KANO GA SAURAN MAKUSANTAN GARURUWA

    Kasancewar birnin Kano birnin kasuwanci ne ba birnin Siyasa ba, ya samu ɗaukaka tsawon lokaci saboda yadda fatake ke tururuwar zuwa gare shi bisa dalilan kasuwanci. Wannan ya taimakawa birnin wajen zamowa shahararre, shahararsa kuwa ta yi tasiri ga makusantan ƙauyuka wajen karɓar baƙi a ko-da-yaushe, da kuma hada-hadar kasuwanci.

    Kamar yadda aka sani, a baya babu tsarikan otal ko masaukai a ƙasar Hausa, sannan akan rufe ƙofofin shiga birane idan dare ya yi. Saboda haka, matafiya a zamanin baya sukan samu waje da suka aminta da amincin sa su ya-da zango idan dare ya yi kafin su ƙarasa cikin birni. Don haka kafuwar ƙauyuka a kusa da birane kan zamo masaukai ga baƙin da suke haramar shiga kano yayin da dare ya yi musu.

    A irin haka ne aka samu wani mutumi daga ƙasar Bade ta cikin jihar Yobe a yanzu haka ya ya-da zango a Gurin Gawa tare da soma sana’ar Kwarami (awo), inda ya samu shahara a wannan sana’ar, ya rinƙa sauƙaƙawa fatake masu zuwa kano da jakuna siyan hatsi da kuma masu fitowa daga Kano neman haja ba tare da sun yi dogon zango ba. (Har yanzu ana yi wa mazaunin wancan babarbare laƙabi da suna ‘Marken Bade’).

    A ƙarshe, ina da ra’ayin cewar muhimmancin buƙatar bibiyar tarihin manyan tafarkan da suke sadarwa zuwa biranen mu tamkar na sanin tarihin biranen ne.

    Karanta Yadda Aka Yi Bautar Kurmin Jakara A Kano

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tarihin Malam Ɗankwandarai

    Tarihin Malam Ɗankwandarai

    An haifi Malam Isa Ɗankwandarai a garin Sankara a Ƙauyen Kwandarai. Ya yi tafiye-tafiyen neman karatu har Ubangji Maɗaukakin Sarki Ya hore masa Alƙur’ani; kuma ya yi fice tsakanin makaranta a wannan fage.

    Ya je ƙasar Bima neman karatu har ya kwashe wani lokaci a can. A lokacin da shahararren masanin Alƙur’ani nan Gwani Hamad ya bayyana a birnin Kano; Malam Isa Ɗankwadarai na cikin malaman da suka zama almajiran sahun gaba a wurinsa.

    Wannan ya sa shi yin fice a fagen karatun Alƙur’ani bisa ƙa’i’doji karatu da ilimi Tajwidi har sai da mahaddata suka riƙa zuwa gari da gari don naƙaltar wan nan ilmi a wurinsa.

    Malam Ɗankwandarai ya shahara wajen sanin girman malamai, domin shi ne ya yi wa Gwani Hamad kyautar doki da kayan abinci da sauran hidima akai-akai har sai da ya samu matsayi a wurinsa Ya kasance mutum ne mai taushin hali, ba ya fushi, ga yawan ciyarwa ga almajirai. Ya kasance yana yawan yiwa ‘ya’yansa da almajiransa wasiyya da riƙe Alƙur’ani.

    Saboda kyakkyawar dangantakar sarakuna da makaranta Alƙur’ani kuwa an ce Sarki Sunusi ne ya dawo da shi Kano; ya ba shi wuri don ya gina tsangayarsa.

    Cikin manyan almajiransa akwai Gwani Ɗanbirni da Gwani Saleh Ɗanzarga Ya rasu a zamanin mulkin Sarkin Kano Ado Bayero a shekara ta 1984.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Gwani Ɗanbirni danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Taƙaitaccen Tarihin Kamilu Almajirin Mawaƙa danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tarihin Malam Attahiru Shehu Na Liman (Limamin Masallacin Shehu)

    Tarihin Malam Attahiru Shehu Na Liman (Limamin Masallacin Shehu)

    An haifi Malam Attahiru a farko-farkon sarautar sarkin musulmi Abubakar na uku. Malam Attahiru ya taso cikin tarbiyyar addini wurin mahaifinsa.

    Kasancewar gidansu gida ne na ilmi da yaɗa shi, ya sa shi gadar wannnan sana’a ta koyar da Alƙur’ani da ilmi. Duk da cewa a halin yanzu Malam Attahiru shi ne Limamin Masallacin Shehu da ke Sakkwato, duk da haka makarantarsa ba ta gushe ba ta na yaɗa addini a cikin garin Sakkwato tare da taimakon ‘yan uwansa musamman ma Malam Abubukar da Malam Ibrahim da Malam AbdurRahman da Malam Ahmad Zaruƙu.

    Malam Attahiru Na Liman tsatson Alƙali Abubakar Ladan Rame ne, wanda ɗan Gwaggon Shehu Usmanu Ɗan Fodiyo ne. Wannan zuriya mai albarka ta cigaba da jiɓintar koyar da addini da alƙalanci har zuwa kan Malam Attahiru Shehu Na Liman (Limamin Masallacin Shehu da ke Sakkwato na yanzu).

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Malam Buhari Siriddawa (Sarkin Malaman Sakkwato) danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Adalci, Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tarihin Alaramma Malam Salihu Ɗangalinja

    Tarihin Alaramma Malam Salihu Ɗangalinja

    An haifi Malam Salihu ɗan Dawuda a girin Galinja da ke Kanon Dabo a shekarar 1920 zamanin Sarkin Kano Usman. Mashahurin mahaddaci mai baiwar tilawa da kaifin basira.

    Malam Salihu Ɗangalinja ya yi tafiye-tafiyen neman karatu cikin ƙasar Gumel da Haɗeja; da garuruwa irin su Mainabindi da Kalali da Unguwar Jibrin.

    Bayan Malam Ɗan Galinja ya samu AIƙur’ani, sai kuma ya tsunduma cikin fannonin ilmin Fiƙhu da tajwidi. Ya karanta littafai irinsu Hidayatul Rahman wajen malaminsa Shehu Rabi’u Ɗantinki da Malam Husaini Gwauron Dutse. Saboda irin baiwarsa ta karatu an ce a lokacin ƙuruciyarsa zai yi wuya a lissafa manyan tsangayun da ya je ya sha fari ya tashi; Wannan ya sa sa’o’insa su ka sallama masa.

    Malam Salihu mutum ne mai yawan haƙuri da kawaici da kyautatawa ga almajiransa. Bayan girma ya kama shi sai ya kafa tsangayarsa da ke garin Ƙarfi a inda makaranta ke turuwa don sanin Alƙur’ani daga gare shi. Wadda hakan ya canza yanayin rayuwar mutanen Ƙarfi saboda maƙwabtakar da suka yi da ma’abota Alƙur’ani.

    Malam Salihu Ɗan Galinja ya kasance yana yi wa ‘ya’yansa da almajiransa wasiya da riƙo da Alƙur’ani da kaucewa kwaɗayin duniya.

    Malam Salihu ya rasu a shekarar 1997 ya bar ‘ya’ya da dama, kaɗan daga cikin mazan su ne:-

    • Halifansa Malam Kabir Ɗan Galinja
    • Malam Nafiu Ɗan Galinja
    • Malam Ɗahiru Ɗan Galinja, da ‘ya’ya mata guda tara.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Mahiru Sharif Bala danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙu’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tarihin Alaramma Malam Salisu Ɗanruwantsa

    Tarihin Alaramma Malam Salisu Ɗanruwantsa

    An haifi Alaramma Malam Salisu ɗan Malam Ahmad ɗan Usmanu ɗan Ahmad a garin Ruwantsa. An ce asalin zuriyarsu sun fito daga ƙasar Mali, Alaramma Malam Salisu ya taso a garin Ruwantsa a inda ya fara karatu a wurin Malam Abdul’Aziz ɗan Malam Ibrahim.

    Lokacin da ya ƙara datawa kuma idonsa ya yi ƙwari, sai tsananin kwaɗayinsa ga Alƙur’ani ya ƙaru, ya ƙara duƙufa. Malam Salisu ya kasance tun ƙuruciyarsa ba ya zama wuri guda face yana tsakanin wancan gari da waccan tsangaya izuwa waccan cibiya ta makaranta. Wannan ya ba shi damar huɗuwa da gwarazan malaman zamaninsa irin su Malam Haruna Ningi wanda a wurinsa ne ya haddace AIƙur’ani Mai Girma.

    Koda Alaramma Malam Salisu ya sami labarin bayyanar Gwani Hamad a garin Taura kuwa; sai ya zabura ya haɗa kayansa ya nufe shi kuma ya kamfata daga marmaron ilmin Gwani Hamad. Daga nan kuma ya wuce garin Malamawa wurin Bajimin malami Malam Abdullahi. Malam Sal ısu bai gushe ba yana kutsawa cikin kowane loko da saƙo na ƙasar Kano da kewayenta; har sai da ya dangana da garin Insharuwa cikin Jamhuriyar Nijar.

    Bayan Dawowar Malam Salisu daga ƙasar Nijar ne ya yi aure a mahaifarsa. Daga nan ne ya taso tare da Wani adadi na almajiransa ya dawo Kano ya sauka Unguwar ƙofar Wambai; wurin Malam AbdulKarim inda ya karanta ilimin Tajwidi da Fiƙihu. Manyan malaman Malam Ɗanruwantsa sun haɗa da Shehin Malami Rabi’u Ɗantinki da Shehu Mai Hula. Bayan nan ne kuma ya sake zabura izuwa garin Ɗabbatta wurin babban malami Malam Adam; don sanin ilimi littafin Shaɗibiyya da ilmin Rasmu.

    Sannan ya sake dawowa birnin Kano karo na biyu a inda ya sauka a wurin Malam Garba Tudun Nufawa.

    Ya zauna shekaru biyu a wurinsa yan karantar Alfiyyar ɗan Malik. A lokaci guda kuma, shi Malam Garba Tudun Nufawa (Malam Abubakar Ramadan) yana koyon ilmin Tajwidi da Kira’o’i a wurinsa; Daga nan ne ya koma Unguwar Yakasai ya kafa makarantarsa a shekarar 1945.

    Bayan ya tumbatsa da ilmi da Alƙur’ani; daga bisani kuma ya koma Gwauron Dutse kusa da Masallacin Juma’a na Sheikh Is’haka Rabiu a matsayin Na’ibin Limamin Masallacin.

    A takaice dai zamu iya cewa Malam Salisu Ɗanruwantsa shi ne magajin kambin Shehi Rabiu Ɗantinki a fagen ilmin Alƙur’ani; da ƙira’o’i a faɗin Kanon Dabo. Tsangayarsa ta shahara da tsare-tsare masu ban sha’awa tare da sanya cigaban zamani a Wasu ɓangarori daban-daban. Alal misali, akwai tsarin azuzuwa inda ake sanya yara goma sha bakwai; a Kowane aji ana biya musu rabin sumuni da safe har sai sun haddace. Da yamma kuma a ƙara musu rabi don a samu kyakkyawar haddar AIƙur’ani.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Alaramma Gambon Takai danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙu’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tattali da Kulawar Ɗanƙwairo da Majiɓintansa

    Tattali da Kulawar Ɗanƙwairo da Majiɓintansa

    Kamar yadda tarihin rayuwar Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya tabbatar; shi mutum ne mai kula da ciyarwa da shayarwa da tufasarwa da samar da muhallai na zaman iyalinsa da makusantansu; da sauran waɗanda suke majiɓinta a gare shi.

    Sannan yakan yi wa iyalinsa tarbiyya gwargwadon yadda addinin Musulunci da al’adu kyawawa na Hausawa suka tanada.

    Mutum ne kuma wanda yake fafutukar haɗa kan dukkan zuriyyarsa da yi musu addu’a su zauna salim alim; ba ƙyama ko faɗa ba wata hauragiya ko ƙiyayyar juna. Haƙiƙa, wannan wata hanya ce ta wanzar da zuriyya bisa haƙuri don ta zama tsintsiya maɗaurinki ɗaya.

    Musa Ɗanƙwairo kamar yadda ya tashi, ya gani a gidansu, ya himmatu ta fuskar yin noma da duka ayyuka na gona; don samar da abinci da abubuwan masarufi waɗanda suka zamanto abokan zama.

    Sau da yawa; Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ba ya buƙatar duk wani abu da zai hana shi yin noma a kowace faɗuwar damina. Ta haka Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun ya nuna ba ya son jama’arsa ta tagayyara. Saurari wata damuwa ta makaɗa Musa

    Ɗanƙwairo a sa’ilin da Damina Bakolori ya tauye shi a yin noma a wata damina:

    Jagora(Daudu): Allah shi ka kawo komi,
    : Yaƙin Dam Bakolori ya ci mu,
    ‘Y/Amshi: Sai in faɗa ma Mamman,

    : Ban da gida yanzu ban da gona, Jagora(Daudu): Yanzu cikin damina ni kai ta shirin,
    ‘Y/Amshi: Gyaran wurin da za ni bacci, Jagora(Daudu): Yanzu gidan Makaɗa ya zamo gurbi na ƙwarai,

    : Wanda ad da zurhi,
    ‘Y/Amshi: Sarkawa su sukai da taru,

    Jagora(Daudu): Sarkin Daura ko da damina,
    : Sai kai ta shirin tariyab baƙi,
    ‘Y/Amshi: In wasu sun kore mu mu taso,

    : Muhammadu in wasu sun kore mu mu taso,
    Jagora(Daudu): Ba ni zama inda babu gona,
    ‘Y/Amshi: Ba ni zama inda ba abinci,

    : Babban jigo na Yari,
    : Uban Shamaki tura haushi.
    (Ɗanƙwairo, Waƙar Babban Jigo, ta Sarkin Daura, Alhaji Muhammad Bashar (1966-2007)

    Bayan harkokin noma, makaɗa Musa Ɗanƙwairo kuma ya yi kiwon shanu da tumaki; da awaki da Kaji da sauran dabbobi da tsuntsaye. Ya ƙaura ya bar wa iyalinsa yin waɗannan sana’o’i.

    Domin karanta cikakken bayani akan Rasuwar Makaɗa, Sarkin Kiɗan Maradun Alhaji Musa (Ɗanƙwairo) Usman Ɗankwanagga a 1991 danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun; A Aiwatar Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tarihin Shehun Malami Muhammad Rabi’u Ɗan Tinki (1897-1959)

    Tarihin Shehun Malami Muhammad Rabi’u Ɗan Tinki (1897-1959)

    Malam Rabi’u ɗan Yunusa ɗan Alhasan ɗan Baru. An haife shi a garin Tinki a cikin ƙaramar hukumar Bici da ke Jihar Kano cikin shekarar 1897.

    Malam Rabi’u ya taso ciki ƙuruciya manisanciyar wargi da wasanni irin na matasa. Ya yi karatu a gaban mahaifinsa. Muhammad Rabi’u Ɗan Tinki ya kasance mutum ne mai yawan haƙuri da kawaici da yawan sabo da jama’a. Ya haddace Alkur’ani tun yana ɗan shekara goma sha huɗu. Sannan ya fara karatun littatafai irin su Ahalari da lziyya.

    Daga nan ya nemi izinin muhaifinsa ya bi wani baƙon mashahurin malami da ake kira Malam Kunta. Bayan ya zauna tsawon lokaci a wurinsa, sai ya nemi izini zuwa wajen Mahiru Kalla mutumin Damagaram cikin Jamhuriyar Nijar.

    Ya zauna a wajensa tsahon lokaci har ya sauke litlatafai da yawa a fannin ilimin ƙira’a da Tawhid da litlafai irinsu Nuniyar Sakawiy da Hidayatussibiyan da Tuhfatul adfal da Mukaddimat Jazary, da Shadibiyya da Lamiyyatul Kira ‘at.

    Shaihun malamin bai gushe ba yana kutsawa cikin fagagen ilmai da gogayya da malamai har sai da ya dangana da garin Maiduguri ya yi karatu a wurin Mahiru Ahmad. Daga nan ya dawo Kano ya sauka Haɗejiya ya kara dukuta a gaban Malam Is’hak daga bisani ya dawo Kano ya cigaba da koyarwa.

    A lokacin da Malam Ɗantinki ya samu labarin Mahiru Hamid, sai ya nemi izinin ya zama almajirinsa. A nan ma ya karanta littafai da dama musamman fannin dabti wanda shi ma ɓangare ne na ilimin Rasmu da ilimin wasullan Alkur’ani.

    Abokan karatun Shehi Rabi’u wurin Gwani Hamid sun haɗa da Malam Ɗan Gunduwawa da Malam Aliyu Mai Kwaro da Malam Ɗan Karofin Yashi da Malam Yunus Ɗan Gumel da Malam Ɗan Kanuri da Malam Isah Ɗan Kwandarai da Malam Sabo Ƙofar Wambai da Malam Umar Ɗan Mai-Rigar-Fatu.

    A halin yanzu tsangayarsa ta cigaba da bunƙasa kuma ta yi rassa a hannun ɗan sa Halifa Sheikh Is’haka Rabi’u.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Gwani Saleh Danzargu danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Taƙaitaccen Tarihin Samuwar Waƙoƙin Baka a Ƙasar Hausa danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tarihin Gwani Saleh Ɗanzargu

    Tarihin Gwani Saleh Ɗanzargu

    An haifi Gwani Saleh ɗan Abdullahi jikan Abdullahi a Ƙasar Jahun. Mahaifin sa ya rasu yana ƙaramin yaro, don haka sai mahaifiyar sa ta koma da shi garin Zarga ta kuma kyautata tarbiyar sa.

    Gwani Saleh ya taso da kaifin basira da son Alƙur’ani. Don haka ya lazimci makarantan garin Zarga irinsu Malam Abdullahi har Ubangiji Ya hore masa Alƙur’ani ya haddace shi yana ɗan shekara tara (9). Gwanin Alƙur’ani ma’abocin ƙan-ƙan da kai da gaskiya da riƙon amana. An ce tun yana ɗan shekara sha biyu ya sha fari.

    Gwani Saleh ya yi tafiye-tafiye na neman karatu a inda yazo Kano ya sauka a tsangayar Gwani Nadudu. Daga bisani kuma ya lazimci mashahurin malami Malam Aliyu Basakkwace ya karanci Fiƙhu da Hadisi da tafsiri Shaharar da tsangayarsa ta yi ya sanya makaranta daga nisan duniya yin takakkiya don ɗosana daga haskenta. Manyan abokanen karatun Gwani Saleh sun haɗa da:-

    • Gwani ɗan Kwandarai
    • Gwani Ɗan birni
    • Gwani Daudu

    Game da yawan almajiran da suka samu Alƙur’ani a hannun sa kuwa, wannan ɗan littafi ba zai ɗauke ambaton su ba, sai dai mu yi ishara ga waɗansun su:

    • Malam Muktari Abdullahi
    • Yayan sa Gwani Yahuza da Gwani Lawi
    • Malam Husaini Rijiyar Lemo
    • Malam Sham’unu
    • Malam Ibrahim Maidarasu

    Gwani ya rayu cikin karamci da girmamawa daga maƙwabtan sa, musamman ma Alhaji Sunusi Ɗantata da al’umar Unguwar ƙoƙi da kewayenta. A halin yanzu wannan tsangaya tana ƙarƙashin kulawar ɗan sa Gwani Yahuza inda ta ƙara bunƙasa ta hanyar shigo da tsarin ilmin zamani, ɓangaren firamare da sakandare. A lokaci guda kuma, ga tsohon tsarin tsangaya na gudana da makaranta da mahaddata.

    Gwani Yahuza ya samu gogayya da wayewa ta zamani a inda ya dangana da ƙasar Masar don karatun sa na digirin farko. A halin yanzu Gwani Yahuza ɗaya ne daga manyan alƙalai na musabaƙar Alƙur’ani ta ƙasa. Gwani Yahuza shi ne ɗan Najeriya na farko da ya karɓi kyautar girmama mahaddata Alƙur’ani daga ƙasar Saudi Arebiya. Baya ga wannan rassa na makarantar akwai majalisai a unguwannin Gwammaja da Kurnar Asabe da Ƙoƙi.

    Ita wannan makaranta ta Gwammaja, Gwani Lawi ne ya kafa ta mai suna Ma’ahad Gwani Lawi Litahfizil Ƙur’anil Karim.

    Gwani Lawi ya yi babbar Diflomarsa a Jami’atul Ƙur’anil Karim da ke Sudan, kuma shi ne wan da ya kafa ƙungiyar Mahaddata Alƙur’ani ta farko a Najeriya, mai suna Rabiɗatul Huffazil Ƙur’ani, Nigeriya. Gwani Sale Ɗanzarga ya bar ‘ya’ya goma sha biyu, maza da mata.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Malam Ɗankwandarai danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Farko Na Nijeriya (1500 BC- 500 AD) danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tarihin Sheikh Malam Muhammad Ɗan Almajiri

    Tarihin Sheikh Malam Muhammad Ɗan Almajiri

    An haifi babban malami Muhammad ɗan Malam Adamu a Ƙasar Kazaure. Malam Muhammad ɗan Almajiri ya fara karatu a gaban mahaifinsa Malam Adamu.

    Malam ya yi tafiye-tafiyen neman Alƙur’ani har sai da ya dangana da garin Bajanwa a ƙasar Katsina wajen Malam AbdusSamad a inda ya yi karatun Alƙur’ani wurinsa. Daga nan ne Malam AbdusSamad ya tafi da shi izuwa garin Rawayau wurin mashahurin malamin nan Malam Goji. Daga Rawayau, ya bazama izuwa Unguwar Ciranci cikin Birnin Katsina don ƙara gogewa da Alƙur’ani.

    Malam Ɗan Almajiri ya zo Kano a inda ya sauka a unguwar Fagge wajen babban malami Malam Ibrahim Badamagare a inda ya karanci fiƙhu da Nahwu. Malaman Sheikh Ɗan-almajiri a Kano sun haɗa da Malam tijjani Zangon Barebari. Malam ya rasu a shekarar 1960.

    Makarantar marigayi Ɗan Almajiri ta yi fice tsakanin makarantun Alƙur’ani da yawan almajirai da tsare-tsare masu ban sha’awa. Wan nan ya sa ta yi rassa da ɓangarori daban-dabun. An kafa wan nan makaranta ne a shekarar 1945.

    Almajiran Malam Ɗan-almajiri sun haɗa da Malam Ɗan-Inna da ‘ya’yansa. Malam ya rasu ya bar ‘ya’ya 14; bakwai maza bakwai mata. Bayan rasuwar sa sai Malam Haruna Rashid ya jiɓinci gudanar da ita kuma ta cigaba da bunƙasa a hannunsa da hannun wasu almajiransa musamman a wasu jihohi cikin tarayyar Nijeriya. Kaɗan daga rassan makarantar marigayi Malam Ɗan almajiri su ne:-

    – Makarantar Alƙur’ani da Islamiyya, Kaduna
    – Makarantar Alƙur’ani da Islamiyya, Katsina
    – Makarantar Alƙur’ani da Islamiyya, Bauchi
    – Makarantar Alƙur’ani da Islamiyya, Lagos

    Domin karanta cikakken bayani akan Tarihin Sheikh Is’haƙ Rabi’u Khadimul Alƙur’ani danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Asalin Sunan Ƙabilar Ƙuraish danna nan.

    Wannan bayanin anciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙu’ani A Arewacin Najeriya Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.