Takaiceccen Tarihin Rayuwar Dr. Yahaya Tanko

0
421

Rayuwar Yahaya Tanko A Taƙaice

Wanda Aka Gabatar A Taron Walima Wanda Majalissar Mata Ta Shirya A Ɗakin Taro Na Tsangayar Kimiyya Ta Jami’ar Bayero Ranar Lahadi 27 Ga J/Sani=26 Ga Maris 2017

Ƙuruciya da Aure:

  • An haife shi unguwar Bakinruwa ƙaramar hukumar Dala a 1951
  • Yayi ƙuruciyarsa rabi a Bakinruwa rabi a unguwar kakanisa yakasai, bayan rasuwar mahaifinsa.
  • Ya yi aure a shekarar 1974

Karatu Da Tarbiyya:

  • Ya fara samun tarbiyya a hannun mahaifansa.
  • Yana da kimanin shekar biyar mahaifinsa ya sa shi a makarantar allo ta Alhaji Malam Isa a unguwar ‘yar kasuwa kan titin kasuwar kurmi zuwa goron dutse.
  • Karatun ƙawa’idi a wurin Malam Abdu na unguwar ‘yan muruci.
  • Makarantar dare ta Islamiya ta Malam Baba Baƙinruwa.
  • Makarantar Ulumiddini ta Alhaji Sunisi Ɗantata a shekarar 1960, a wannan lokacin yana da kimanin shekara takwas ko tara a duniya.
  • Makarantar “Judicial School ta Shahunci 1964-1968. A sannan yana da shekara sha 12 a duniya.
  • Yayi wta tafiya ta ziyarar ‘yar uwarshi a mina (Jihar Neja) a 1970.

Koyon Sana’a Da Kasuwanci:

  • a sanda yake uruciya mahaifiyarsa takan dora masa tallan acma/acamo. A sanda yake “Judicial” mahaifinsa yana koya masa sana’ar gidansu, watau dinkin keke. Bayan rasuwarsa a shekarar 1967, daga shekarar 1968 zuwa shekarar 1970 kwunsa ya sa shi harkar kasuwanci. Ya yi kasuwanci a wani kanti cikin asibitin Murtala. Ya yi kasuwanci a wani kanti a Galadima Road Sabongaroi. Ya kuma yi ciniki a wani dan kanti na katako a cikin lungun kurna a unguwar yakasai. A sanda yake makarantar SAS,  mahaifiyarsa takan dora masa dubulan/cincin mai nama daga Bakin ruwa ya kai kantin asibiti.

KARATU:

Ya fara karatun Alkur’ani a makarantar Alhaji Malam Isa, unguwar ‘yar Kasuwa.

Ya fara karatun Ilimin (Ahlari/Kawa’idi) a wurin M Abdu a Unguwar ‘Yan muruci.

Ya fara karatun Islamiyya a                       a unguwar Koki 1960.

An sa shi a makarantar K Shari’ah ta shahunci 1964-1968.

Yayi karatun Ilimi na a zure a hanin kakansa Malam Abdur Razak, alkalin Ringim.

Ya sauke AlQur’ani a makarantar malam Abdu mai ‘yan makaranta wadda take a Yakasdai.

Ya je Makarantar Nazarin Harshen Larabci (SAS) a 1971.

Yaje Abdullahi Bayero College (Diploma in Arabic Hausa and Islamic Studies) 1975-1978.

Digirin farkao a Bayero University (Hausa Islamic Studies) 1980-1983.

Digiri na biyu a Bayero University (Isalmic Sturdies) 1988-1981.

Kwas na horar da Limamai a jami’ar Al Azhar (Nov-jan) 1994-1995.

Digiri na uku a Bayero University ( Islamic Studies)  2011.

Koyarwa A Makarantun Gwamnati:

  • ya fara koyarwa a makarantar firamare ta Dwanau,1974-1975.
  • Koyarwa a makarantar koyon harshen Larabci (SAS) , 1978-9179.
  • Ma’aikatar Ilimi ta jihar Kano ta bayar dashi aro domin koyar da IRK a “Federal Governent Coliege Kano” 1979-1980.(sai ya tafi kartu)
  • Koyarwa a makarantar mata ta Arabiyya Ɗanbatta 1884-1985
  • Koyarwa a Gumel A.T.C (Kano State Higher Institute of Education) 1985-1960
  • Koyarwa a “College of  Edukation Kumbotso”, wadda a yanzu ake kira “Sa’adatu Rimi College” 1987-1992.
  • Koyarwa a “Aminu School Of Islamic Legal Studies” Kano State polytechnic 1999-Febuary 2015.

Koyarwa A Makarantun Islamiyyah:

  • Ya koyar a makarantar Islamiyya ta Yola da yamma.
  • Ya koyar a makarantar Islamiyya ta dare a unguwar  Mai Aduwa.
  • Ya buɗe makarantar Iasamiya ta dare a idansa B/R
  • Ya koyar a makarantar koyar da matan aure ta dare ta Gumel
  • Ya koyar  a makarantar koyar da matan aure ta ƙungiyar  Da’awa da yamma.
  • Ya koyar a makarantar koyar da matan are  ta Ƙungiyar Huɗaibiyya

Limanci

  • Ya fara yin na’ibin limanci Juma’a  tsohuwar Jami’ar Bayero tun 1991,
  • An naɗa shi na’ibin limanci Juma’a a masallacin Umar bin Khaɗɗab a shekarar 1998
  • Yayi limacnci a masallacin Muntada, wanda aka fi sani da Masallacin VC na sabuwar Jami’atun 1998.
  • Yana limanci a masallacin Nana A’ishah FCE

Gudanar Da Gwamnati:

  • A sanda yake koyarwa a BYK ya nemi hutu daga Jami’a ya yi aiki a Hukumar Zakka ta Jihar Kano, a matsayin kwamishina, ya kuma yi aiki a Hukumar Shari’a a matsayin babban darakta 2004-2011.

Darussa A Masallatai:

  • Masallacin Juma’a na Jami’ar Bayero tsohuwa.
  • Masallacin Jami’ar bayero sabuwa.
  • Masallacin Juma’a na Umar bin Khaɗɗab.
  • Masallacin Nana A’isha na kan titin FCE Ƙofar Ɗakawuya.
  • Masallacin Khalid BIN Alwalid na cikin Unguwar Ɗakawuya

Littafai Da Maƙaloli:

A. Liittafai:

  1. Kayyaɗe Iyali Da Matsayinsu A Musulunci                          1988
  2. Matsayin Kuɗin Ruwa Da Bashin Banki A Msulunci          1993
  3. Zaman Aure A Musulunci                                                       1992
  4. Tarbiyar Yara A Musulunci                                                     1994
  5. Matan Annabi        “Wives of the Prophet                           1994
  6. Bankin Musulinci Wanda Babu Ruwa                                  1994
  7. Addu’o’in Annabi A Wni Da Dare                                         1995
  8. Shin Bankin Yan Kasuwa Ne?                                                 1995
  9. NASIHA Ga Musulmai A Kan Gardamar Watan Azumi     1997
  10. Matan Sahabbai Na Ɗaya                                                       1997
  11. Kasuwanci A Musulunci                                                          1997
  12. Tsaraba Ga Mawadata Da Mabuƙata                                  2004
  13. Muhimmacin Lokaci Ga Musulmi                                         2005
  14. Siyasa A Musulinci “Politics In Islam”
  15. A Brief abaut Busuness in Islamic Banking, on the Basic of Shari’ah  and  Jurisprodence.  2011
  16. Darul Umma For Publishing, Kano.
  17. (in Arabic)                                                                           2012
  18. Matrimonial Liife  in Islam                                                      2016
  19.                                                                                            2016
  20.                                                                                            2017
  21.                                                                                            2017
  22. Ladaban Zama Da Kishiya A Musuluci                                 2019
  23. Kamanin Annabi Siffofinsa da Ɗabi’unsa Domin Koyi da shi  2020

B. Maƙaloli:

1- “Zakatul As’humi Was Sanadat, Wat ta’amulu Biha Fis Shari’atil Islamiyyah”

Journal of Islamic Studies vo1: 1 NO:1, 2007.

2- Murabaha to the Purchase Order in the Juristic Perspective

“Bai’ul Murabahati Li Amirin Bis Shira’i.

Jornal of Islamic Sturdies

Department of Islamic Studies, BUK.

A paper presented at a conference organized y Al Muntada Nigerian Office 1998

  1. Islami Foundation of Nngeria, Kano.
  2. Concil of Ulama, Kano.
  3. Hudabiyya Fondation Kano.
  4. Council for Adult Islamic Education in Rural Areas, Kano State.
  5. Wakili a kwamatin masallacin Jami’ar Bayaro.
  6. Gamayyar Ƙungiyar Haɗakar Bankin Ruwa.
  7. Haɗakan Zuriyyar Malam Isma’ila Yakasai.

Alhamdu lillah. A yanzu Yahaya Tanko Yana Bayar da darasai na littafai huɗu  a mako, a masallacin Umar bin Khaɗɗab da da littafan Sahihul Bukhari da Fathul Majid a masallatan Nana A’isha da na Khalid binil Walid a unguwar  Dukawuya FCE.

A yanzu Allah ya azurta Yahaya Tanko da zuryya mai yawa, ‘ya’ya da jikoki.

Ya yi ritaya a watan Febreru na shekara 2015 daga Jami’ar Bayero ta kano. Amma ya kama aikin kwantiragi da jami’ar Yusuf Maitama sule ta Kano.

labarin da ya wuceFalalar Zikiri
Labarin na GabaAzumin Annabi Dawud (Alaihis salam)
wikiHausa
wikiHausa kundin ilimi (insakulofidiya) ce da ke ilimantar da jama'a yara da manya da maza da mata wajen samun ilimi a saukake, cikin harshen Hausa.