Tag: yadda ake

  • Ina Alwala, Na Haɗiye Ruwa Garin Kurkure Baki, Yaya Lafiyar Azumina?

    Ina Alwala, Na Haɗiye Ruwa Garin Kurkure Baki, Yaya Lafiyar Azumina?

    Amsa: Mutumba zai rama azumi ba, idan ya haɗiye ruwa lokacin kurkurar baki, bada ganganci ba; a cikin alwala ko ba acikin alwala ba.

    Hujja: “Allah ya yafewa al’ummata abubuwa guda uku, kuskure da mantuwa da kuma abinda aka tilasta su a kai”.

    Marawaici Ibn Abbas, Sunan Ibn Maajah, Sahihu Ibnu Hibban, Mu’ujamu Ɗabara’ni.”Ba ku da laifin abinda kuka yi bisa kuskure, sai abinda zuciyarku tayi da gangan”. Suratul Ahzab aya 5.

    Domin karanta cikakken bayani akan Idan Na Ɗanɗana Miya, Na Tofar Ban Haɗiye Ba, Ya Batun Azumina? danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Azumin Ranar Arfa danna nan.

  • Shin Rashin Yin Sallah A Cikin Jama’a Na Lalata Azumi?

    Shin Rashin Yin Sallah A Cikin Jama’a Na Lalata Azumi?

    Amsa: Rashin yin sallar jam’i baya lalata azumi, matsawar mutum yana yin sallar a kan lokaci; kawai dai yana tabka asarar lada mai yawa.

    Hujja: “Sallar mutum acikin jama’a, tafi sallarsa shi ɗaya a kasuwa ko gida da lada ashirin da biyar ko lada ashirin da bakwai”. marawaici Abu Huraira, Ibn Umar, littafi Sahihul Bukhari.

    Domin karanta cikakken bayani akan Ina Alwala, Na Haɗiye Ruwa Garin Kurkure Baki, Yaya Lafiyar Azumina? danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Abubuwan Da Ba Sa Ɓata Azumi danna nan.

  • Abubuwan Da Ba Sa Ɓata Azumi

    Abubuwan Da Ba Sa Ɓata Azumi

    Ɓata Azumi – Kasancewar azumi ibada ce, ibada ce da ake kusantar Mahalicci da ita. Sanin kowane ɗaya cikin ɗaiɗaikun mutanen dake karatu kuma suna fahimtar karatun cewa; ba manufar Ubangiji ba ce ƙuntata musu a cikin rayuwa, ba sauƙi ake nufin su da shi.

    Hakan ya sanya, aka halattawa mai yin azumi wasu al’amura, ko kuma idan mai azumi ya tsinci kansa cikin wasu, to ba komai a kansa. Cikin waɗannan abubuwa akwai:

    1. Idan alfijir ko safiya ta riski mai azumi da janaba ta kusantar iyalinsa a cikin wannan dare, to babu komai na ramuwa a kansa, kuma azuminsa yana nan, abin da ke kansa kawai shi ne wanka.

    Domin hadisi ya tabbata daga Nana A’isha Radiyallahu Anha cewa, “Lalle Ma’aiki (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya kasance alfijir yana samunSa alhali da janabar saduwa da iyalinsa da dare, sannan ya yi wanka ya ci gaba da azuminSa”. (Bukhari 4/123, Muslim 1109).

    2. Asuwaki, yin asuwaki ga mai azumi halattaccen abu ne, domin a kansa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) cewa ya yi, “Da ba don kada na tsaurarawa al’ummata ba, da na umarce su da yin aswaki a yayin kowacce alwala”. (Bukhari 2/311, Muslim 252).

    A nan, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) bai keɓance mai azumi da waninsa ba; da wannan sai ya zamto dalili ne dake nuni a kan halaccin yin aswaki ga mai azumi. Haka zalika, wannan hukuncin ya game kowane lokaci; kafin faɗuwar rana ko bayanta.

    Game da irin asuwakin da za a yi amfani da shi; babu bambanci tsakanin ɗanye ko busasshe; domin a kan haka ne Imamul Bukhari ya yi babi a cikin ingantaccen Littafinsa a kan yin amfani da ɗanye ko busasshen asuwaki. Ibn Sirin ya ce; “Babu laifi ga mai yin azumi ya yi amfani da ɗanye ko busasshen asuwaki”. Sai aka ce masa; ai ɗanye yana da ɗanɗano. Sai ya ce; “Shin ruwa ba shi da ɗanɗano amma kuke kurkure baki da shi?”.

    Wannan kuma ita ce magana mafi rinjaye a wurin malamai; domin da aka ambaci Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) na yin asuwaki, ba a bambance ɗanye ko busasshe ba; ga mai azumi ko maras azumi ba. Bisa haka, mai azumi zai iya goge baki da man goge haƙora na zamani; kasancewar yadda ɗanyen asuwaki yake da shi. Sai dai kuma ya kamata a yi hattara kada a haɗiye”.

    3. Shaƙa ruwa da kurkurar baki, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya kasance yana shaƙa ruwa tare da kurkure bakinsa, alhali yana azumi; sai dai ya hana wuce gona da iri wajen yin hakan da cewa; “………ka kai matuƙa wajen shaƙa ruwa sai idan kana azumi”. (Tirmizi 3/146, Abu Dawud 2/308).

    4. Runguma da sumbata ga mai yin azumi, Nana A’isha (Radiyallahu Anha) ta ce; “Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya kasance yana sumbata, kuma yana runguma alhalin yana azumi, sai dai shi ya kasance ya fi ku mallakar kansa daga sha’awa”. (Bukhari 4/131, Muslim 1106).

    Amma an karhanta yin hakan ga saurayi ban da tsoho, dogaro da hadisin Abdullahi Ibn Amru Bn Ass (Radiyallahu Anhu) wanda ya ce; “Mun kasance wajen Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) sai wani matashi ya zo, sai ya ce; “Ya Manzon Allah, zan iya sumbata alhali ina azumi?”. Sai Ya ce masa “A’a”. Sai wani dattijo ya zo, ya ce; “Zan iya sumbata alhali ina azumi?”. Sai Ya ce masa “Eh”. Sai muka dinga kallon junanmu, sai Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Shi dattijo yana iya mallakar kansa”.
    Da wannan hadisin malamai suka kafa hujja wajen rungumar mace, amma ba kowa ba, dattijo kaɗai ke iya yi.

    5. Ƙarin jini ko allura idan ba ta ƙoshi ba ce, ko sanya maganin ciwon idanu, Imam Hasanul Basri ya ce; “Babu laifi mutum ya ɗiga magani a hancinsa idan bai kai zuwa ga maƙoshinsa ba……”.

    6. Ƙaho, ya zo cikin hadisin Abdullahi Ibn Abbas (Radiyallahu Anhu) cewa, “Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya yi ƙaho alhalin yana azumi”. (Bukhari 4/155).

    7. Ɗanɗana abinci, ya halatta mai azumi ya ɗanɗana abinci amma kar ya wuce maƙogwaro, domin ya zo daga Abdullahi Ibn Abbas (Radiyallahu Anhu) cewa: “Babu laifi da ɗanɗana ruwan khal ko wani abu matuƙar dai bai shiga maƙogwaronsa ba alhalin yana azumi”. (Bukhari 4/154).

    8. Zuba ruwan sanyi a kai ko a jiki, Imam Bukhari ya yi babi a cikin ingantaccen Littafinsa mai taken “Babin wanka ga mai azumi”, inda ya kafa hujja da dalilai kamar haka: Ibn Umar ya jiƙa kaya da ruwa ya sanya alhali yana azumi. Haka Imamu Sha’abiy ya shiga banɗaki alhali yana azumi. Hasanul Basri ya ce: “Babu laifi, da kurkurar baki da jiƙa jiki ga mai azumi”.
    Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya kasance yana zuba ruwa a kayansa saboda ƙishirwa ko zafin rana alhali yana azumi.

    9. Haɗiye yawu ma ba ya ɓata azumi.

    10. Mutumin da yake azumi, sai ya kalli matarsa ba tare da ya taɓa ta ba, sai ya fitar da maniyyi, to azuminsa na nan. Dalili kan wannan shi ne hadisin Jabir Ibn Zaid (Radiyallahu Anhu) a inda ya ce: “Wanda ya kalli mace, ya fitar da maniyyi, ya ci gaba da azuminsa, babu komai a kansa”.

    Imamus Shafi’i, da Imamus Thauri, da Imamul Auza’i duk sun tafi a kan cewa; babu wani dalili da ya zo cewar fitar da maniyyi kaɗai yana karya azumi, ba tare da jima’i ba. Amma idan jima’i ne ko an fitar da maniyyi ko ba a fitar ba; to yana karya azumi, kuma sai an yi kaffara. Haka kuma wanda ya sumbaci matarsa, sai ya fitar da maniyyi; shi ma azuminsa na nan, wannan shi ne zance mafi rinjaye.

    Sai dai wasu daga cikin malaman Malikiyya suna ganin fitar da maniyyi ta hanyar kallo ko runguma yana karya azumi; kuma akwai ramuwa da kaffara a kai. Amma idan maniyyi ne kawai, akwai ramuwa ba tare da kaffara ba. Sun kafa hujjar cewa abin da ake buƙata a jima’i shi ne fitar maniyyi; saboda haka fitar maniyyi ta wannan hanyar daidai yake da jima’i.

    Amma sauran malamai sun yi musu raddi da cewar hukuncin da nassin ya zo da shi; ya ambaci jima’i ne kawai, ba fitar da maniyyi ba. Sannan suka ƙara da cewar idan mutum ya yi jima’i ba tare da fitar da maniyyi ba; ai zai rama azumi kuma ya yi kaffara. Haka kuma, da a ce fitar da maniyyi ne kawai, da sai a ce mai barci ma idan ya yi mafarki; ya fitar da maniyyi, sai ya yi kaffara. Wallahu a’alam.

    11. Shafa mai ko turare ba sa karya azumi, kamar yadda ya zo daga fatawar Abdullahi Ibn Mas’ud (Radiyallahu Anhu) cewa; “Idan ɗayanku yana azumi, zai iya shafa mai, kuma ya taje kansa”. Haka kuma Abu Ƙatada Al’ansari (Radiyallahu Anhu) ya ce; “Mustahabbi ne mutum ya shafa mai domin ya kawar da kura daga jikinsa”.

    Cikin malaman Mazhabar Malikiyya kuwa, Mutraf, da Abdulhakam, da Asbag duk sun ce ya halatta a shafa mai; kuma ba su bambance tsakanin mai ƙamshi da marar ƙamshi ba.

    Haka kuma sanya kwalli shi ma ba ya karya azumi; kamar yadda Imam Alzuhri, Ibn Majishun; da Mutraf, da Asbag, da Laith da Ibn Habib duk sun ce babu laifi.

    12. Shaƙar maganin asma ma ba ya karya azumi; kamar yadda Ibn Taimiyya da sauran malamai kamar sa Ibn Baz da Uthaimin da sauransu suka faɗa game da mai asma, zai iya shaƙa

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ramuwar Azumin Ramadan danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Azumin Kwanaki Shida A Watan Shawwal danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Guziri Ga Mai Azumin Ramadana (Bisa Koyarwar Alƙur’ani Da Sunnah); wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi; Don karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Waɗanne Abubuwa Ne Ke Lalata Azumi A Ɓoye?

    Waɗanne Abubuwa Ne Ke Lalata Azumi A Ɓoye?

    Amsa: Abubuwan dake lalata azumi a ɓoye su ne:

    Akwai yi da wani da shaidar zur da gulma da ƙin yin sallah sai lokacinta ya wuce, babu wani dalili na shari’ah, ƙin yin sallah kwata-kwata.

    Hujja: “Wanda duk bai bar zancen zur ba, da aikata zur, da yiwa mutane mummunar fassara; Allah baya buƙatar yabar abincinsa da abin shansa”.

    Marawaici Abu Huraira, littafi Sahihul Bukhari da Sahihu Muslim.

    Domin karanta cikakken bayani akan Shin Rashin Yin Sallah A Cikin Jama’a Na Lalata Azumi? danna nan

    Domin karanta cikakken bayani akan Dalilan Wajabcin Azumin Ramadana danna nan.

  • Waɗanne Abubuwa Ne Na Fili Da Ke Karya Azumi?

    Waɗanne Abubuwa Ne Na Fili Da Ke Karya Azumi?

    Amsa: Abubuwan fili da suke karya azumi su ne:

    Cin abinci ta hanyar tauna ko haɗiya.

    Shan ruwa ko wani abin sha mai kama da ruwa.

    Kwanciyar aure ga masu aure.

    Fitar da maniyi ga wanda ba shi da aure ta hanyar kallace-kallace a fili ko mujalla ko wayoyin hannu ko talabijin.

    Sauraran labaran batsa, ko na motsa sha’awa kai tsaye daga wani ko ta hanyoyin sadarwa da gangan.

    Hujja: “Wanda yaci, ko ya sha, ko ya kusanci iyalinsa, ya karya azuminsa”.

    Marawaici: Abu Huraira, littafi Sahihul Bukhari da Sahihu Muslim, Sunan Abu Dawud, Sunan Turmuzi, Sunan Nassa’i Sunan Ibn Maajah.

    Domin karanta cikakken bayani akan Waɗanne Abubuwa Ne Ke Lalata Azumi A Ɓoye? danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Azumin Watan Ramadana 2 danna nan.

  • Falalar Azumin Watan Ramadana 2

    Falalar Azumin Watan Ramadana 2

    Azumin watan Ramadana na da falala mai yawa, daga cikin falalar akwai:

    1. Azumi garkuwa ne. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam); ya umarci wanda sha’awar aure ta yi tsanani gare shi da ya yi azumi, sai ya sanya azumin garkuwa ne ga sha’awar; domin cewa shi azumi yana kange gaɓoɓi daga sha’awa.

    2. Azumi sababin shiga Aljanna ne, sannan kuma yana nesantar da bawa daga wuta; kamar yadda ya zo cikin hadisin Abu Umamata (Radiyallahu Anhu) ya ce; “Ya Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) shiryar da ni kan aikin da zai kai ni ga shiga Aljanna”. Sai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasalam ya ce; “Na hore ka da yin azumi, ba shi da tamka”. (Imam Ahmad 5/255-258. Ibnu Hibban 929).

    Haka zalika, ya zo cikin hadisin da Imam Bazzar ya fitar cikin littafinsa cewa; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce da Huzaifah; “Ya Huzaifa, duk wanda ya cika da azumin yini ɗaya mai nufin yardar Allah, Allah zai shigar da shi Aljannah”.
    Game da nesantar da bawa daga wuta kuwa, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Babu wani bawa da zai yi azumi na kwana ɗaya domin neman yardar Allah, face Allah ya nesantar da fuskarsa daga wuta tsawon shekaru saba’in”. (Bukhari, 6/35. Muslim, 1153).

    A hadisin da Tirmizi ya fitar, cewa ya yi, “Duk wanda ya yi azumin kwana ɗaya domin neman yardar Allah; Allah zai sanya tazara tsakaninsa da wuta kamar tazarar sama zuwa ƙasa”.

    A wani hadisin kuma ya ce; “Azumi garkuwa ne da bawa zai kare kansa daga wuta”. (Imam Ahmad 3/241).

    3. Ana sakanya wa mai azumi da lada ba tare da ƙididdiga ba.

    4. Mai azumi yana da farin ciki biyu. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ambata cikin wani hadisi cewa; “……. Kuma mai azumi yana da farin ciki biyu: idan ya yi buɗa-baki yana da farin ciki; haka idan ya haɗu da Ubangijinsa zai yi farin ciki da azuminsa”. (Bukhari 1805, Muslim 163).

    5. Warin bakin mai azumi ya fi turaren almiski ƙamshi a wajen Allah. Kamar yadda hadisi ya tabbata daga Abu Huraira (Radiyallahu Anhu) cewa, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Dukkan aikin ɗan Adam a gare shi ne, ban da azumi, domin nawa ne, kuma ni zan sakanya masa, azumi garkuwa ne.

    Idan ya kasance ranar azumin ɗayanku, to kada ya yi batsa, kada ya yi jahilci (shirme); idan wani ya zage shi ko ya neme shi da faɗa, to ya ce masa “Ni azumi nake yi”. Na rantse da wanda ran Muhammad ke hannunsa; warin bakin mai azumi ya fi turaren almiski ƙamshi a wajen Allah.

    Kuma mai azumi yana da farin ciki biyu; idan ya yi buɗa-baki yana da farin ciki; haka idan ya haɗu da Ubangijinsa zai yi farin ciki da azuminsa”. (Bukhari 1805, Muslim 163).

    6. Azumi da Alkur’ani suna ceton ma’abocinsu, kamar yadda ya zo cikin hadisi cewa; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce, “Azumi da Alkur’ani za su ceci bawa ranar ƙiyama, azumi zai ce; Ya Ubangiji, na hana shi abinci da sha’awarsa, ka ba ni cetonsa…………….”.

    7. Azumi yana kankare zunubai, Bukhari da Muslim sun fitar da hadisi daga Huzaifata Bin Yaman (Radiyallahu Anhu) cewa; Umar Bin Khaɗɗab (Radiyallahu Anhu) ya ce; “Wane ne wanda ya kiyaye hadisin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) wanda ya yi magana a kan fitina? Sai Huzaifa ya ce; “Ni ne. Na ji Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) yana cewa; “Fitinar da mutum zai samu a cikin iyalansa, da dukiyarsa, da makwancinsa, sallah da azumi da sadaka suna kankare su”.

    8. Ƙofar Rayyan ta masu azumi ce, kamar yadda ya zo a hadisin Sahal Ibn Sa’ad (Radiyallahu Anhu) cewa; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Tabbas a cikin Aljanna akwai wata ƙofa, ana ƙiranta Rayyan, masu azumi ne za su shige ta ranar ƙiyama; babu wanda zai shige ta sai su, kuma idan suka shige ta za a rufe ta, babu wanda zai ƙara shiga. Kuma duk wanda ya shiga zai sha ruwa; kuma duk wanda ya sha ruwan, ba zai ƙara jin ƙishirwa ba har abada”. (Bukhari 4/95, Muslim 1/52).

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Watan Ramadana 1 danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Azumin Watan Muharram danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Guziri Ga Mai Azumin Ramadana (Bisa Koyarwar Alƙur’ani Da Sunna); wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Dalilan Wajabcin Azumin Ramadana

    Dalilan Wajabcin Azumin Ramadana

    Wajabcin Azumin Ramadana – Allah Maɗaukakin Sarki, ya wajabta azumin Ramadana; a inda ya ce; “Ya ku waɗanda suka yi imani! An wajabta muku azumi kamar yadda aka wajabta shi ga waɗanda suka gabace ku; wala-alla kwa sami taƙawa”.

    Sanannen hadisin nan, wanda Imam Muslim ya fitar cikin littafinsa, daga Umar Bin Khaɗɗab (Radiyallahu Anhu); da kuma hadisin da aka yi tarayya wajen fitarwa tsakanin Imamul Bukhari da Muslim; daga Abu Abdulrahman Abdullahi Bn Umar Bn Khaɗɗab (Radiyallahu Anhu) duk sun bayyana wajibcin yin azumin watan Ramadana.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Sharuɗan Wajabcin Azumin Watan Ramadan danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Azumin Ranar Arfa danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Guziri Ga Mai Azumin Watan Ramadan (Bisa Koyarwar Alƙur’ani Da Sunnah); wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Falalar Watan Ramadana 1

    Falalar Watan Ramadana 1

    Falalar Watan Ramadana – Hadisi ya tabbata daga Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) cewa, “Wanda ya azumci watan Ramadan, yana mai imani da neman lada, za a gafarta masa zunubansa da suka shuɗe”.

    Haka nan, a wani hadisi, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Idan watan Ramadan ya shigo, ana buɗe ƙofofin rahama da ƙofofin Aljanna, kuma ana rufe ƙofofin Jahannama; kuma ana ɗaure shaiɗanu”. Haka kuma an rawaito daga Anas Ibn Malik Radiyallahu Anhu cewa; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Lalle wannan wata na Ramadana, haƙiƙa ya halarto muku, a cikinsa akwai wani dare wanda ya fi watanni dubu alheri. Duk wanda aka haramta masa (samun alherin dake cikinsa); haƙiƙa an haramta masa alheri dukkansa. Kuma babu wanda ake haramta wa alherinsa sai wanda ba shi da rabo”. (Sunan Ibn Majah 1644).

    A dunƙule, za mu iya lissafo wasu cikin manyan falalolin watan Ramadan kamar haka:

    1. A cikinsa Allah ya saukar da Alkur’ani daga Lauhul Mahfuz, zuwa saman duniya.

    2. Wata ne da ake ɗaure shaiɗanu, ayyukan sharri suna ƙaranci a ban-ƙasa. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasalam ya ce; “Idan watan Ramadan ya zo, sai a buɗe ƙofofin Aljanna, sannan a rufe ƙofofin wuta, kuma a kulle shaiɗanu”. (Bukhari 4/97, Muslim 2/757).

    Dukkan wannan yana kammaluwa daga lokacin da daren farko na wata mai albarka ya shigo, saboda faɗin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam)cewa; “Idan daren farko na Ramadana ya kasance, sai a kulle shaiɗanu da kangararrun aljanu, a rufe ƙofofin wuta, babu wadda za a bari daga cikinta, a buɗe ƙofofin Aljanna ba za a bar ko ɗaya a rufe ba. Sai wani mai kira hhya yi kira; “Ya mai neman alheri matso kusa, Ya mai neman sharri yi nesa!

    Kuma Allah yana da wasu ‘yantattu daga wuta, wannan kuwa yana faruwa a kowanne dare”. (Tirmizi 682, Ibnu Majah 1642).

    3. A cikinsa ne ake samun dare mafi daraja, wato Daren Lailatul Ƙadri. Anas Ibn Malik (Radiyallahu Anhu) ya ce, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce, “Lalle wannan wata na Ramadana, haƙiƙa ya halarto muku, a cikinsa akwai wani dare wanda ya fi watanni dubu alheri. Duk wanda aka haramta masa (samun alherin dake cikinsa), haƙiƙa an haramta masa alheri dukkansa. Kuma babu wanda ake haramta wa alherinsa, sai wanda ba shi da rabo”. (Sunan Ibn Majah 1644).

    4. Amsar addu’a da kuma ‘yanta bayi daga wuta a kowanne dare cikin watan Ramadana.

    5. Gafarta zunubai, kamar yadda ya zo cikin hadisin da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) cewa, ya hau minbari sai ya ce, “Amin! Amin! Amin!”. Sai aka tambaye shi, sai ya ce, “Haƙiiƙa Jibrilu (Alaihis Salam) ya zo ya ce mini: “Duk wanda ya riski watan Ramadan bai yi abin da za a gafarta masa ba, har aka shigar da shi wuta, to Allah ya nisantar da shi daga rahamarsa,”. Ka ce “Amin”. Sai na ce, “Amin”….(Imam Ahmad 2/246).

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Azumin Watan Ramadana 2 danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Gaggauta Buɗa Baki danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Guziri Ga Mai Azumin Ramadana (Bisa Koyarwar Alƙur’ani Da Sunnah) wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Sharuɗan Wajabcin Azumin Watan Ramadan

    Sharuɗan Wajabcin Azumin Watan Ramadan

    Azumin watan Ramadan yana sauka a kan wasu, sakamakon waɗansu dalilai da Shari’a ta aminta da su; shi ya sa wajen ci gaba da ayar da ta gabata, malamai suka bayyana ire-iren waɗannan mutane, tare da dalilan. Ci gaba da bayani, sai Allah ya ce; “Waɗansu kwanaki ne ababan ƙidayawa.

    To wanda ya kasance mara lafiya a cikinku, ko a kan wata tafiya; to (idan ya sha ruwa) sai ya rama a waɗansu kwanakin na daban, har ma waɗanda za su iya yin azumin; su ba da fansa ta ciyar da abinci ga miskini guda ɗaya, to dukkan wanda ya ƙara (a kan abincin miskini), to wannan ya ƙara wa kansa alheri.

    Amma ku riƙa yin azumin shi ne ya fi alheri a gare ku, in har kun kasance kuna sani”. Watan Ramadan shi ne wanda aka saukar da Alqur’ani a cikinsa, shiriya ce ga mutane, kuma ayoyi bayyanannu na shiriya, kuma mai rarrabewa tsakanin ƙarya da gaskiya. Don haka dukkan wanda ya halarci watan cikin ku, to ya azumce shi. Kuma wanda ya kasance marar lafiya, ko a kan tafiya, (to idan ya sha ruwa) sai ya rama a waɗansu kwanaki na daban.

    Allah yana nufin sauƙi a gare ku, kuma ba ya nufin tsanani a gare ku. Don haka ku cika adadin (kwanakin Ramadan); kuma domin ku girmama Allah bisa ga shiryar da ku da ya yi, kuma ku zamo masu godiya gare shi. Kuma idan bayina suka tambaye ka game da ni, to ni kusa nake (da su); ina amsa kiran mai kira, da zarar ya kiraye ni. To su nemi amsawata, kuma su yi imani da ni, domin su shiryu.

    An halatta muku saduwa da matayenku a daren watan Azumi, su sutura ce gare ku, ku ma suturu ce a gare su. Allah ya san ku kun kasance kuna ha’intar kawunanku, sai ya dawo da ku, kuma ya yi muku afuwa. To a yanzu ɗin ku sadu da su (da daddare), kuma ku nemi abin da Allah ya rubuta muku; kuma ku ci, kuma ku sha har farin zare ya bayyana daga baƙin zare na alfijir; sannan ku cika azumi zuwa dare, kuma kar ku sadu da su alhali kuna i’itikafi a masallaci.

    Waɗannan iyakoki ne na Allah, kada ku kusance su! Kamar haka ne, Allah yake bayyana ayoyinsa ga mutane; don su zamo masu taƙawa” (Bakara: 184 – 187).

    Waɗannan ayoyi a dunƙule sun yi bayanin waɗanda shari’a ta dauƙe musu azumin watan Ramadan; sakamakon wasu dalilai da karɓaɓɓu ne a Shari’a da sharaɗin bayan waraka daga waɗannan al’amura; sawa’un rashin lafiyar da za ta hana yin azumin ne, ko mace mai shayarwa ko juna (kamar yadda wasu malamai irin su Ibn Taimiyya da almajiransa; Auza’i, Hasanul Basri da Ibrahimul Nakha’i suka tafi a kan su ma marasa lafiya ne), ko matafiya ne; to za su rama waɗannan azumi da suka sha bayan kwanakin azumin, ma’ana bayan Ramadan.

    Sannan a cikin su, akwai bayanin waɗanda za su ciyar da miskinai abinci, sakamakon rashin lafiya; ko tsufa da mai ciki ko shayarwa bisa fatawar Abdullahi Ibn Umar, Abdullahi Ibn Abbas da Ishaq Ibn Rahawaihi; kamar yadda Sheikh Nasiruddeen Albani ya fitar a cikin littafinsa Irwa’ Alghalil 4/18 – 24).

    Shahid dai, waɗannan ayoyi ƙunshe suke da cikakkun bayanai game da wajabcin azumin Ramadana; da kuma nuni a kan waɗanda azumin ya wajaba a kansu, misali dukkanin musulmi, baligi, mai hankali; kuma wanda yake da ikon yi, mazaunin gida. Sannan an bayyana matakan da aka bi wajen shar’anta shi, da kuma waɗanda azumin ya zama wajibi a kansu. Domin neman cikakken bayani, sai a tuntuɓi malamai a majalisunsu domin jin yadda abin yake.
    A gefe guda kuma, akwai waɗanda azumin Ramadana ya sauka a kan su, ma’ana, su azumin Ramadana bai wajaba a kan su ba.

    Cikin irin waɗannan akwai:

    i. Kafiri.

    ii. Yaro, amma za a iya umartar sa da yin azumin domin ya saba.

    iii. Mahaukaci, wannan kuwa koda balagagge ne, domin ba ya cikin hankalinsa. Kuma Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasalam ya ce, “An ɗauke alƙalami a kan mutum uku: mai barci har sai ya farka, yaro har sai ya balaga, da mahaukaci har sai ya warke”. (Sahihul Jami’ al-Saghir (3513).

    iv. Tsoho, amma zai bayar da mudun-nabi guda biyu, ko ya ciyar da miskini dafaffen abinci a madadin kowacce rana.

    v. Marar lafiya, sai dai akwai ramuwa a kansa bayan ya warke, wannan kuwa ko da bayan shekara nawa ne. Amma cutar da ƙwararrun likitoci suka tabbatar ba za a warke ba, sai dai kawai a ciyar a madadin kowacce rana.

    vi. Matafiyi, zai yi ramako bayan Ramadana.

    vii. Mai jinin haila ko jinin biƙi, amma ita ma akwai ramuwa a kanta.

    viii. Mace mai ciki ko shayarwa, ita ma za ta iya ajiye azumi idan tana tsoron cutuwarta ko cutuwar abin dake cikinta, ko abin da take shayarwa idan ta ci gaba da azumin.

    An rawaito hadisi daga Anas Ibn Malik Al-Ka’abi (Radiyallahu Anhu) cewa, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce, “Haƙiƙa Allah ya ɗauke wa matafiyi rabin sallah, kuma ya ɗauke azumi ga matafiyi da mai ciki da mai shayarwa”. (Sunan Ibn Majah, (1667).

    A nan malamai suka yi bayanin cewa, idan matuƙar dai matafiyi da mara lafiya za su rama azumi, to babu abin da zai sa a ce mai ciki ba za ta rama ba.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tsayuwar Watan Ramadan danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Dake Cikin Yin Sahur danna nan.

    Wannan bayanin anciro shi ne daga Littafin Guziri Ga Mai Azumin Ramadana (Bisa Koyarwar Alƙur’ani Sa Sunnah); wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tsayuwar Watan Ramadan

    Tsayuwar Watan Ramadan

    Tsayuwar Watan Ramadan – Azumin Ramadana yana tsayuwa ne da ganin jinjirin watan Ramadana; wato ba a amfani da ƙirgen kalanda ko lissafin taurari ba; a’a, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya alaƙanta yin azumin ne da ganin watan na Ramadana.

    Hadisi ya tabbata daga Abu Hurairata Radiyallahu Anhu cewa, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce, “Ku yi azumi domin ganin sa (wato Ramadan), kuma ku sha ruwa domin ganin sa (wato Shawwal). Idan watan ya faku a gare ku (ba ku gan shi ba), to ku cika Sha’aban kwana talatin”. (Sahihul Bukhari (1909), Sahihuul Muslim (1081).

    Wani abu muhimmi shi ne, ba sai kowa ya ga watan Ramadan ba sannan ya ɗauki azumi; ana iya ɗaukar azumi ko da mutum ɗaya ne ya ga watan. Domin hadisi ya tabbata daga Abdullahi Ibn Umar (Radiyallahu Anhu) cewa; “Mutane sun yi ƙoƙarin ganin jinjirin wata; sai na gaya wa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) cewar, “Ni na ga wata”. Sai Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ɗauki azumi, kuma Ya umarci al’umma da su ɗauka”. (Sunan Abu Dawud, 2342. Hakim, 423, da Ibn Hibban 3438).

    Faɗakarwa:

    Son zuciya da jahilci kan hana wasu tashi da azumi da hujjar cewa shugabanni ba adalai ba ne; alhali Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ba da dama a bi su hatta sallah, ballantana azumi. Bisa haka, idan adali ya shaida ya ga wata; kuma shugaba ya aminta da ganinsa, to wajibi ne a tashi da azumi.

    Dangane da sauƙe azumin kuwa, sai mutane biyu sun shaida cewar sun ga watan Shawwal; sannan a ajiye kamar yadda aka rawaito daga Abdulrahman Ibn Zaid Ibn Khaɗɗab; yayin da ya yi wa mutane huɗuba a ranar shakku (wato ranar da ake kokwanton ko Ramadan ne ko, ba Ramadan ba ne) .

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Watan Ramadana 1 danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Ciyar Da Mai Azumi danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Guziri Ga Mai Azumin Ramadana (Bisa Koyarwar Alƙur’ani Da Sunnah); wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken Littafin danna nan.