Taƙaitaccen Tarihin Ƙasar Hausa

0
574

Alhassan (1981:1) ya bayyana Ƙasar Hausa ta asali tana Afirka ta Yamma; a farfajiyar dake tsakanin hamadar sahara da dazuzzukan da suka doshi gaɓar tekun Atilantika daga kudu.

Kuma ana kiran Ƙasar da suna Sudan ta Yamma, wato tsakanin Tafkin Chadi da gwuiwar Kogin Kwara daga yamma

A bayanin Ibrahim (1982:1); ya nuna cewa Ƙasar Hausa tana shimfiɗe ne a can Arewacin Nijeriya da kuma Kudancin Jamhuriyar Nijar a cikin Afirka ta Yamma. Daga gabas ta yi iyaka da ƙasashen Borno;

Haka ma daga yamma ta yi iyaka da ƙasashen Dahomey a gaɓar Kogin Kwara. Daga arewa ta yi iyaka da Ƙasar Adar a cikin Jamhuriyar Nijar; Daga wajen kudu kuma ta yi iyaka da ƙabilun Gwari da kuma ƙabilun kudancin Zariya da na kudancin Bauchi.

A wannan zamani a iya cewa Ƙasar Hausa yanki ne wanda ya mamaye dukkan Jihar Kano da Katsina da Arewaci Jihar Kaduna da wasu ɓangarorin Bauci da Gwambe da Neja da kuma kudancin Jamhuriyar Nijar.

Idan aka tayar da saiti daga Arewa zuwa Kudu; Ƙasar Hausa tana farawa daga Azbin har ya zuwa kusurwar Arewa maso Gabas da tsaunukan Jos. 

Daga nan sai ta shararo ta yi arewa maso yamma ta yi mahaɗa da ƙaton rafi na kogin Kabi. Daga wannan wuri ta karkata ta nufi arewa maso gabas har Azbin. (Birnin-Kudu, 2002:11-12 a cikin Sallau, 2013:481).

Ƙasar Hausa wadda take shimfiɗe a shiyyar Sudan ta Tsakiya, a tsari na gargajiya a iya cewa ta haɗa da ƙasashen sarakunan Katsina, Kano, Daura, Zazzau, Kabin Argungu, Gwandu, Gumel, Haɗejiya, Ƙwanni, Maraɗi da Tassawa.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Nazarin Matsalolin Aure a Ƙasar Hausa Daga Mahangar Zabiya Lawisa da Fatima Jalo Wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi.

Domin karanta cikakken bayani a kan Wane Ne Bahaushe? danna nan

Domin karanta bayani akan AL’ADAR BAHAUSHE danna nan

labarin da ya wuceWane Ne Bahaushe?
Labarin na GabaMa’anar Aure A Ƙasar Hausa