Tag: ƙasar Hausa

  • Shigowar Ƙananan Ƙabilu Ƙasar Hausa

    Shigowar Ƙananan Ƙabilu Ƙasar Hausa

    Sauran Ƙabilu

    Bayan waɗannan al’ummomi da aka yi bayani kan shigowarsu ƙasar Hausa akwai wasu ƙananan ƙabilu waɗanda suke maƙwabtaka da suka shigo. Misali, a kudancin Jihar Kaduna akwai ire-iren waɗannan ƙananan ƙabilu waɗanda suka haɗa da Katab da Morwa da Kaje da Kagoro da Jaba da Kaningkon da Ninzam da Ayu da Kadara da Gwari da Gwandara da Kagoma da sauransu.

    Akwai wasu kuma a yankin Filato waɗanda suka haɗa da Birom da Angas da Ganawuri da Sayawa da sauransu. A jihohin Bauchi da Gwambe akwai wasu ƙananan ƙabilun kamar Gerawa da Terawa da Jerumawa da Ganjuwa da Denawa da Kanakuru da Tangale da Waja da dai sauransu. A ƙasar Hausa ta yamma akwai wasu ƙananan ƙabilun da suke zaune a yankin Yawuri da Kwantagora waɗanda suka haɗa da Dakarkari da Kambari da Kamuku da dai sauransu.

    Shigowar Ƙananan Ƙabilu Ƙasar Hausa

    Akwai daɗaɗɗiyar dangantaka a tsakanin Hausawa da waɗannan ƙananan ƙabilu masu maƙwabtaka da ƙasar Hausa. Mafi yawa daga cikin waɗannan ƙananan ƙabilu sun zauna a ƙarƙashin mulkin sarakunan ƙasar Hausa waɗanda suke maƙwabtaka da su. Misali, ƙabilun da suke kudancin jihar Kaduna sun zauna a ƙarƙashin mulkin Sarkin Zazzau tun cikin ƙarni na goma sha takwas, wanda shi ya sa a yanzu ake kiran su da sunan ƙabilun kudancin Zariya (Adeleye, 1975:593).

    Ta wannan hanya ce al’ummomin waɗannan ƙananan ƙabilu suka riƙa hulɗoɗi da Hausawa. Ta hanyar waɗannan hulɗoɗi mafi yawa daga cikin al’ummomin waɗannan ƙabilu da suke maƙwabtaka da ƙasar Hausa koyon harshen Hausa wanda ya zama harshe na biyu gare su bayan harshen da suka gada.

    Haka kuma harshen Hausa ya zama harshen da kowa da kowa daga cikin su yake amfani da shi wajen sadarwa da kasuwanci da addini da sauran ma’amalolin rayuwa na yau da kullum a tsakaninsu da sauran al’ummomin da suke cikin ƙasar Hausa da kuma waɗanda suke maƙwabtaka da su. A sakamakon wannan dangantaka ne, a yanzu harshen Hausa yake ƙoƙarin mamaye waɗannan ƙananan harsuna da suke maƙwabtaka da ƙasar Hausa.

    Idan muka juya kan shigowar al’ummomin waɗannan ƙananan ƙabilu cikin ƙasar Hausa, za a ga mafi yawancinsu sun shigo a cikin ƙarni na ashirin. Wannan kuwa ya faru ne a sakamakon kafuwar mulkin mallaka wanda ya haɗa waɗannan al’ummomi wuri ɗaya a ƙasa ɗaya.

    Kamar yadda wasu daga cikin waɗannan al’ummomi suka shigo cikin ƙasar Hausa, akwai wasu Hausawa da suka yi ƙaura daga ƙasar Hausa suka shiga ƙasashensu. Misali, a sakamakon samun kuza da kwaranda a ƙasashen da suke kudancin Zariya da yankin Filato tun cikin shekarun 1920, an sami Hausawa waɗanda suka yi ƙaura daga Kano da Katsina da Zariya da Sakkwato suka koma waɗannan ƙasashe.

    A wuraren da suke zaune sun riƙa yin hulɗa da al’ummomin wuraren, wannan ya sa sun auri mata ‘yan ƙasar suka mayar da su Hausawa (Hira da GMW, a garin Godo- Godo da kuma MIM, a garin Kafanchan, a ranar 24/8/2004).

    Nason Al’adun Sauran Baƙi Kan Wanzancin Hausawa

    Sauran baƙi a nan ana nufin ƙananan ƙabilu waɗanda suke maƙwabtaka da Hausawa daga kudu da kudu-maso-gabas da kuma kudu-maso-yamma da ƙasar Hausa. Dangane da wannan bincike an duba ƙabilun Dakarkari da na kudancin jihar Kaduna da kuma ƙabilar Tera a jihar Gwambe.

    A nazarin da aka gudanar a waɗannan ƙabilu an fahimci nauyin al’adunsu cikin wanzanci ba shi da yawa. Wannan kuwa ya faru ne saboda yadda al’adun Hausawa suka taushe al’adunsu ta yadda a wannan zamani wasu daga cikin al’adunsu sun fara ɓacewa na Hausawa na maye gurbinsu. Amma duk da haka ga ɗan abin da aka samu.

    Magungunan da Wanzamai Suka Samo Daga Wurin Dakarkari

    Hausawa sun sami wasu magunguna daga wurin Dakarkari mazauna ƙasar Zuru a cikin Jihar Kebbi. Ire-iren waɗannan magunguna sun haɗa da na ƙarin ƙarfin azzakari. A wannan magani ana samo sauyoyin wani icce da ake kira jan yaro, sai a taho da su gida a sanya aska ko wuƙa a kankare su sosai.

    Daga nan sai a ɗebo gero daidai gwargwadon wanda idan an yi kunu da shi mutum zai iya shanye shi, sai a sanya wannan bayan sauyoyin jan yaro da aka ɗebo a cikin tukunya a tafasa a dama kunun salala. Wannan kunu ne mutum zai yi ta sha sannu a hankali zai ji azzakarinsa ya yi ƙarfi sosai.

    Wani magani da Hausawa suka samu daga Dakarkari shi ne, na nuna buwaya. Ana samun ƙanzon tuwo da aka yi a gidan wanda zai yi amfani da maganin, sai a ɗebo sassaƙen iccen gamji a daka shi.

    Daga nan sai a haɗa garin wannan magani da ƙanzon tuwo a sa a ruwa a cakuɗa su a yi mulmule uku, za a riƙa cin mulmule ɗaya a kullum har zuwa kwana uku. Idan aka yi haka mutum zai buwaya a duk duk wurin da yake. Idan aka yi kuskure aka ci sau huɗu, to mutumin zai zama maye (AGMSAZ, 21/5/2005).

    Magungunan da Wanzamai Suka Samu Daga Wurin Terawa

    Tera wata ƙabila ce wadda ake samu a wuraren da suka haɗa da garuruwan Gwani ta gabas da Gwani ta Yamma a Ƙaramar Hukumar Yamaltu-Deba a Jihar Gwambe. Al’ummar Tera tana tafiyar da al’adun wanzanci kamar yadda Hausawa suke tafiyar da nasu. Wannan dalili ya sa aka sami kamanci da bambanci dangane da yadda suke tafiyar da wannan sana’a a tsakaninsu.

    Haka kuma akwai fahimtar juna a tsakaninsu wadda ta haifar da musayar al’adu. A saboda wannan dalili ne wanzaman Hausawa suka sami maganin ƙurajen aski daga wurin Terawa.

    A lokacin da aka yi wa mutum aski don maganin ƙurajen aski, sai ya sami buri na hura-hura wadda ‘yan mata suke talla, ya shafa a wurin da aka yi masa aski. A duk lokacin da aka yi masa aski idan ya shafa wannan gari ƙurajen aski ba za su fito masa ba (MYHW, 13/8/1998).

    A taƙaice kamar yadda aka gani wannan babi an yi bayani ne kan nason da al’adun baƙi na kusa waɗanda suka haɗa da Fulani da Barebari da Buzaye da Nufawa da Yarabawa da ƙananan suka yi a kan wanzanci.

    An duba rawar da al’adun waɗannan baƙi suka taka wajen kawo wasu sauye-sauye dangane da yadda Hausawa suke gudanar da al’adunsu waɗanda suka shafi aski da cire belun-wuya da na mata da kaciya da tsaga da kuma magungunan gargajiya.

    Karanta Nason Al’adun Yarabawa A Kan Wanzancin Hausawa

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Shigowar Yarabawa Ƙasar Hausa

    Shigowar Yarabawa Ƙasar Hausa

    Yarabawa suna ne wanda Hausawa suke kiran mutanen da suke kudu-maso-yamma da ƙasar Hausa a tsohuwar Daular Oyo da Ijebu Ode da Ogbomosho da Egba da Ekiti da Ibadan da Ilori da sauran wurare da suke kusa da waɗannan ƙasashe.

    A halin yanzu mafi yawa daga cikin al’ummar Yarabawa suna zaune a kudu maso yammacin Nijeriya a jihohin Lagos da Oyo da Oshun da Ondo da Ogun da Ekiti da kuma a kudu maso yammacin jihar Kwara. Ana kuma samun su a ƙasashen Jamhuriyar Benin da Togo da Cote D’iɓoire da Saliyo.

    Akwai daɗaɗɗiyar dangantaka tsakanin Yarabawa da mutanen ƙasar Hausa, wadda tun farko ta kasuwanci ce. An sami bayanan da suka nuna akwai dangantakar kasuwanci a tsakanin Yarabawa da mutanen ƙasar Hausa a cikin ƙarni na goma sha takwas. A wannan lokaci ne wasu ‘yan kasuwa daga Ogbomosho suka shigo Kano kuma suka zauna a cikin birni.

    Wannan dangantaka ta ƙara ƙulluwa ta hanyar kasuwancin da aka riƙa yi a tsakanin mutanen ƙasar Hausa da na ƙasashen kudu waɗanda suke bin hanyar da ta bi Zariya zuwa ƙasar Nufe ta zarce zuwa ƙasashen Yarabawa. An sami ire-iren waɗannan Yarabawa a ƙasar Katsina da Zariya (Adeleye: 1975:592).

    Da yawa daga cikin Yarabawan da suke zaune cikin ƙasar Hausa a yanzu sun shigo ne a cikin ƙarni na ashirin a sakamakon kafuwar mulkin mallaka. A Kano an sami al’ummomin Yarabawa masu yawan gaske waɗanda suka shigo a farkon ƙarni na ashirin, kuma suna daga cikin mutanen farko waɗanda aka kafa unguwar Sabon Garin Kano da su.

    Sun shigo Kano da Zariya don yin aikin ginin hanyar jirgin ƙasa wadda aka kawo Kano, ko kuwa don yin aiki a tashar jirgin ƙasa, ko don yi wa Turawan Mulkin Mallaka aikace – aikace, ko kuwa don yin aiki a kamfanonin da Turawa suka kafa a waɗannan wurare. Wasu Yarabawan kuwa sun shigo ne don yin aikace-aikacen addini na Musulunci ko na Kirista.

    A sakamakon jin daɗin zama da suka yi a wasu garuruwan ƙasar Hausa musamman a Kano da Zariya da Katsina da Gusau da Sakkwato, sai wasu Yarabawan da suka shigo a matsayin ma’aikata bayan sun ajiye aiki suka yanke shawarar ci gaba da zama a waɗannan garuruwa. Wannan kuwa ya faru ne sakamakon jin daɗin zama da al’ummomin waɗannan wurare da suke zaune da kuma samun damar yin kasuwanci ba tare da fuskantar wata matsala ba.

    Misali, Alhaji Abdul’aziz Kehinde wanda yana ɗaya daga cikin al’ummar Yarabawa da suka fara shigowa Kano a cikin shekarar 1911, ya zo a matsayin ma’aikaci a tashar jirgin ƙasa. A shekarar 1925, sai ya ajiye aiki ya shiga harkar kasuwanci a nan Kano. Akwai ire-irensa masu yawa cikin garuruwa da ƙauyukan ƙasar Hausa, waɗanda bayan sun ajiye aiki, sai suka ci gaba da zama a wuraren da suke cikin ƙasar Hausa (Baƙo: 1990:104).

    Bunƙasar kasuwancin gyaɗa a cikin shekarar 1920 ya ƙara taimakawa wajen shigowar Yarabawa cikin ƙasar Hausa musamman a ƙasar Kano. Mafi yawanci daga cikin waɗannan Yarabawa suna yin kasuwancin gyaɗa ko tuƙa matocin da ake ɗauko gyaɗa daga ƙauyuka zuwa Kano. Haka kuma kafa kasuwar Sabon Gari a Kano cikin shekarar 1918 ya ƙara taimakawa wajen shigowar Yarabawa a garin Kano.

    Fitattu daga cikin Yarabawa ‘yan kasuwa waɗanda suka shigo Kano a farkon ƙarni na ashirin sun haɗa da Alhaji Muhammadu Salihu Olowo wanda ya zo daga Ilesha a cikin shekarar 1903. Da farko ya fara zama a unguwar Ayagi daga baya sai ya koma Sabon Gari cikin shekarar 1916. Yana daga cikin waɗanda suka taimaka aka gina masallacin Yarabawa na Sanmori – ad – deen a cikin shekarar 1925.

    Akwai kuma Alhaji Sani Giwa wanda ya zo Kano daga Abeokuta a cikin shekarar 1920. A duk faɗin Sabon Gari da kewaye Yarabawa da waɗanda ba Yarabawa ba suna ganin mutuncinsa saboda dattakonsa da karimcinsa da riƙe alƙawarinsa. Wannan ne ya sa shi zama Sarkin Yarabawa na farko a ƙasar Kano.

    Haka kuma akwai Mr.D.O.Sanya Olu wanda shi ma ya shiga Kano ne cikin shekarar 1920, kuma shi ne mutum na farko wanda ya fara kafa Otel a Sabon Garin Kano a shekarar 1939. Da farko sunan Otel ɗin Colonial Hotel, amma da aka sami ‘yancin kai, sai ya canja masa suna zuwa Paradise Hotel (Baƙo, 1990:) Waɗannan misalai ne kawai aka kawo don akwai ire-irensu masu yawa da suke zaune a cikin garin Kano da kewayenta.

    A garin Gusau ma akwai Yarabawa masu yawan gaske waɗanda suka shigo don yin harkar kasuwanci da sauran hulɗoɗi. An bayyana cewa tun kafin ƙarni na goma sha tara akwai Yarabawa waɗanda suke kasuwancin goro a ƙasar Hausa. A cikin ƙarni na ashirin musamman a cikin shekarar 1920 ne ake tsammanin Yarabawa masu yawa sun fara shigowa garin Gusau.

    A lokacin wasu sun shigo domin yin kasuwanci, wasu kuma sun shigo domin yin aikace-aikace a kamfanoni da ma’aikatun da Turawa suka kafa irinsu tashar jirgin ƙasa da dai sauran wurare.Yarabawan da suka shigo garin Gusau suna gudanar da kasuwanci iri daban-daban, misali matansu suna sayar da man ja da sabulun salo da man shafawa irin wanda suke yi, ana kiran sa da suna “Mai Zubi”.

    Su kuma mazan suna sana’o’i irin su gyaran kekuna da ɗinkin keke da ginin bulon siminti da yin aski da dai sauransu. Haka kuma wasun su sai suka shiga harkar sufuri. An bayyana cewa an ƙirƙiro yin hayar mota tasi a garin Gusau cikin shekarar 1969, kuma Yarabawa mazauna garin Gusau ne suka fara yin wannan sana’a. Daga cikin su akwai Alhaji Abdulatif S.Adegoke da Alhaji Afolabi da Mr.Ganiyu Raji (Usman, 2000:205, 206).

    A sakamakon daɗaɗɗar dangantaka tsakanin Yarabawan da suka shigo Gusau da Hausawan Gusau, wasu Yarabawan sun yi auratayya da mutanen da suka tarar wanda yin haka ya haifar da musayar al’adu. A halin yanzu Yarabawan da suke zaune a garin Gusau suna zaune a unguwannin Sabon Garin Gusau da Canteen da Tudun Wada da GRA da Sabon Fegi da Birnin Ruwa da Bakin Kasuwa da sauran wurare a cikin garin Gusau da kewaye (Usman, 2000:205).

    Kamar yadda Yarabawa suka shigo ƙasar Hausa, an sami Hausawa masu yawa waɗanda suka yi ƙaura daga ƙasar Hausa suka shiga ƙasar Yarabawa, kuma sun yi fiye da shekaru ɗari a wannan ƙasa.Ire-iren waɗannan Hausawa suna zaune a unguwannin Alaba da Agege da Obalande da Hausa Line a Lagos da kuma a Sabo Ibadan da Sasa a Ibadan da kuma a Shagamu da Ilori da dai sauran wurare a ƙasar Yarabawa.

    Daga cikin ire-iren waɗannan Hausawa mazauna ƙasar Yarabawa akwai Sarkin Hausawa Dogara wanda ya bayyana min ta hannun Sakatarensa cewa an haife shi a Lagos, mahaifinsa ma a Lagos aka haife shi. A halin yanzu yana daga cikin fitattun mutane masu faɗa-a-ji a jihar Lagos, don kuwa daga cikin matansa akwai wadda ‘ya ce ga Oba na Lagos.

    Bayansa akwai Sarkin Hausawa Alhaji Kabiru Garba wanda tsohon Hafsan Soja ne wanda ya yi ritaya, kuma yana zaune a Arewa House Ebute-Metta Lagos. A Ibadan akwai Sarkin Sasa Alhaji Haruna Mai Yasin wanda shi asalinsa mutumin Zakka ta ƙaramar hukumar Safana a jihar Katsina ne. A yanzu yana ɗaya daga fitattun mutane masu faɗa-a-ji a jihar Oyo.

    Don karanta Shigowar Nufawa Ƙasar Hausa danna nan

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Shigowar Nufawa Ƙasar Hausa

    Shigowar Nufawa Ƙasar Hausa

    Nufawa su ne mutanen da suke zaune a farfajiyar da ta haɗa kogin Kwara da kogin Kaduna. Da farko fatauci da noma da kamun kifi su ne manyan sana’o’insu na gargajiya. An bayyana cewa wurin da suka fara kafa cibiyar gudanar da mulkinsu na a Muregi wadda take a gefen mahaɗar kogin Kwara da kogin Kaduna.

    Da farko tsarin tafiyar da shugabancinsu tsari ne wanda yake ba kowane ƙauye damar tafiyar da mulkinsu na cin-gashin kansa. Wannan ne ya sa suke zaune a cikin rukuni-rukuni. Daga cikin waɗannan rukunoni babba daga cikin su wanda yake shugabancinsu shi ne rukunin “Beni-Nufe”.

    Akwai rukunonin ƙauyuka goma sha biyu waɗanda suka haɗu suka yi ƙasar Nufe, su ne kamar haka; Lafiya da Bida da Doko da Eso da Nufeko da Eda da Towagi da Yesa da Gaba da Panjuru. Daga baya sun haɗu a ƙarƙashin shugabancin ƙananan sarakunan “Beni-Nufe” (Bello, 1999:27).

    Dangane da shigowar Nufawa ƙasar Hausa yana da matuƙar wuya a ce ga lokacin da suka fara shigowa wannan ƙasa. Abin da aka sani shi ne, akwai daɗaɗɗiyar dangantakar al’adu da addini da kasuwanci a tsakanin Nufawa da mutanen ƙasar Hausa. Ta hanyar wannan dangantaka ‘yan kasuwa daga ƙasar Nufe suna safarar kayayyaki daga ƙasarsu da kuma waɗanda suka sawo daga kasuwannin ƙasashe maƙwabtansu don su sayar a kasuwannin ƙasar Hausa.

    Ire-iren waɗannan kayayyaki sun haɗa da kayan farin ƙarfe irin su ludduna da ‘yan hannu na mata da likkafun siradan dawaki da dai sauransu. Ta hanyar wannan kasuwanci wasu ‘yan kasuwa Nufawa suka kafa unguwar Ayagi a cikin Birnin Kano (Baƙo, 1990:72).

    Haka kuma an sami wasu ‘yan kasuwa Nufawa waɗanda suke fatauci a tsakanin ƙasar Hausa da ƙasar Nufe cikin ƙarni na goma sha bakwai da na sha takwas suna safarar kayayyaki irin su riguna girken Nufe da bindigogi da bayi da babanni da dai sauransu. Ire-iren waɗannan fatake wasunsu sun zauna a ƙasar Hausa zama na dindindin (Adeleye, 1975:592).

    Bayan waɗanda suka shigo ƙasar Hausa don yin kasuwanci, wasu Nufawan sun shigo ƙasar Hausa don neman ilimin addinin Musulunci. Wannan ya faru ne sakamakon karɓar addinin Musulunci da mafi yawancin Nufawa suka yi.

    An sami shigowar Nufawa da yawan gaske cikin garuruwan ƙasar Hausa musamman a cikin ƙarni na goma sha tara bayan jihadin Shehu Ɗanfodiyo. Sun shigo cikin wasu garuruwan ƙasar Hausa musamman Sakkwato wadda ita ce cibiyar Daular Sakkwato don neman ilimin addinin Musulunci (Bello, 1999:29).

    Sakamakon kafuwar mulkin mallaka a ƙasar Hausa a cikin ƙarni na ashirin an sami ƙarin shigowar Nufawa a wannan ƙasa. Sun shigo ne don neman ilimin zamani wanda Turawa suka kawo. Dangane da haka ne wasunsu sun shigo garuruwa irin su Sakkwato da Zariya da Katsina da Kano, don a wancan lokacin a waɗannan garuruwa ne aka fara kafa makarantun koyar da ilimin zamani a duk faɗin arewacin Nijeriya.

    Ana ɗaukar ɗalibai daga ko’ina cikin wannan yanki har daga ƙasar Nufe. Misali, a cikin shekarar 1935 daga cikin ɗaliban da aka ɗauka a Kwalejin Katsina akwai Nufawa cikinsu (Indabawa, 1997:200).

    A cikin wannan ƙarni dai an sami ƙarin shigowar wasu Nufawa a sassa daban-daban na ƙasar Hausa don neman aiki a ma’aikatun da Turawan Mulkin Mallaka suka kafa a wasu garuruwan da suke cikin ƙasar Hausa. An sami Nufawa waɗanda suka yi aiki a matsayin leburori da masinjoji da dai sauran ayyuka.

    Ga waɗanda suka sami damar yin karatun zamani an ɗauke su a matsayin akawu-akawu don su yi aiki a tashoshin jiragen ƙasa da dai sauran ayyuka. An kuma ƙara samun shigowar Nufawa cikin ƙasar Hausa bayan samun mulkin kai. Sun shigo don yin aikace – aikace a hukumomi da ma’aikatu da kamfanonin Gwamnatin Jihar Arewa.

    A Sakkwato ma akwai ire-iren waɗannan Nufawa kamar Malam Abdullahi Ndagi da Malam Mohammed Bello da Alhaji Abdullahi Jimada da dai sauransu. A Sakkwato Nufawa sun kafa ƙungiyar taimakon-kai-da-kai don haɗa kan dukkan Nufawan da suke zaune a Sakkwato da kewaye a unguwannin Anguwar Nufawa da Pategi da Kurmin Nufawa da Tako da dai sauransu (Bello: 1999:36, 48,50).

    Kasancewar mafi yawancin Nufawan da suka shigo ƙasar Hausa mabiya addinin Musulunci ne ya sa suka sami karɓuwa wurin al’ummar Hausawa. Wannan ya taimaka an sami musayar al’adu da auratayya a tsakaninsu.

    Kamar yadda Nufawa suka shigo ƙasar Hausa, an sami wasu Hausawa da suka yi ƙaura daga ƙasar Hausa suka koma ƙasar Nufe. Ire – iren waɗannan Hausawa sun je wannan ƙasa ne don yin kasuwanci da wasu hulɗoɗi.

    A sakamakon haka ne a yanzu akwai Hausawa masu yawa waɗanda suke zaune a garuruwa da ƙauyukan ƙasar Nufe, waɗanda suka haɗa da Bida da Katcha da Lafai da Agaye (Hira da GHM, a garin Bida, a ranar 18/8/2004). Ire-iren waɗannan Hausawa sun zama ‘yan ƙasa kuma suna magana da harshen Nufanci kamar yadda suke magana da harshen Hausa, kuma al’adunsu da na Nufawa na yi wa juna shigar giza-gizai.

    Nason Al’adun Nufawa Kan Hausawa

    Ayyuka irin na wanzancin Hausawa waɗanda Nufawa suke yi ba su da yawa kamar yadda aka same su a wurin al’ummomin Fulani da Barebari da Buzaye. Wannan dalili ne ya sa nason da aka samu na al’adun Nufawa cikin wanzancin Hausawa ba su da yawa ƙwarai. Amma kuma duk da haka akwai wasu fannoni na wannan sana’a waɗanda suka samo asali daga al’adun Nufawa.

    Cire Belun-wuya

    A al’adar Nufawa ba su damu da cire belun-wuya ba, maimakon cirewa suna ba da magani ne. Wannan al’ada ta yi naso a kan wasu Hausawa waɗanda suke zaune a ƙasar Nufe, don kuwa akwai waɗanda idan aka haifa masu jariri, maimakon wanzami ya cire belun, sai dai ya ba da magani wanda za a riƙa ba jaririn ya riƙa sha ko kuwa a ɗaura masa wani karhu a wuya (Hira da AGHM da AMB, Jihar Neja da AYAUB, Jihar Neja da HMA da YDG da AM da AD a ranakun 18 da 19 da 20 ga watan Agusta 2008).

    Wannan al’amari ya yi tasiri a kan wanzancin Hausawa saboda wasu wanzamai waɗanda suke yin ayyuka a ire-iren waɗannan gidaje suna rasa ayyuka. Wanda a dalilin haka abubuwan suke shigowa a wurinsu za su ragu.

    Askin Jarirai na Suna da Lokacin Yin sa

    Wani ɓangare wanda al’adun Nufawa suka yi naso a cikin wanzancin Hausawa shi ne ta fuskar askin jarirai na suna. A al’adar Nufawa ba dole ne a yi wa jariri aski a ranar suna ba, ana iya yin wannan aski a kowace rana kafin a yi suna ko bayan an yi suna. Wasu ma ba sa yi wa jariran da aka haifa maza ko mata askin ƙwaryar molo, a maimakonsa a lokacin da ta yi tsawo sosai, sai dai a daddatse ta da almakashi.

    Irin wannan al’ada ta yi tasiri sosai a kan wasu Hausawa waɗanda suke zaune a ƙasar Nufawa da ma wasu da suke zaune a wasu sassa na ƙasar Hausa, don kuwa a wannan zamani akwai wasu Hausawa waɗanda a lokacin da aka yi masu haihuwa, idan aka kwana biyu ko uku da haihuwar, sai su sanya wanzami ya yi wa abin da aka haifa namiji ko mace aski ba sa jira sai ranar suna.

    Wasu kuma ba sa yin askin sai bayan kwana ɗaya ko wuce haka da yin suna. Yin haka ya saɓa al’adar yin askin jariri a ƙasar Hausa (ADS da MMSAB da MLTG da HIAY da MHYB, a ranakun 18 da 19 da 20/8/2008).

    Nason Al’adun Nufawa ta Fuskar Ladar Aikin Wanzanci

    A al’adar Nufawa idan aka yi wani aiki wanda ya danganci aski ko kaciya ko ba da maganin gargajiya, waɗanda aka yi wa aikin ne suke biya, ba kamar a al’adar Hausawa ba, wadda idan aka yi haihuwa ko kaciya ‘yan’uwa da abokan arziki ne suke tattara kuɗi su biya wanzamin. Haka kuma hatsi ne kawai suke bayarwa, ba a sanya kayan yaji irin su barkono da kanwa da citta da makamantansu.

    Irin wannan al’ada ta yi naso a kan wasu Hausawa waɗanda suke zaune a ƙasar Nufawa domin kuwa a wannan zamani duk wanda matarsa ta haihu, shi ke biyan wanzamin da ya yi aski da sauran al’adun wanzanci, saɓanin yadda ake yi a ƙasar Hausa inda ‘yan’uwa da abokan arziki suke tattara kuɗi domin biyan wanzamin.

    Haka kuma tsaba kaɗai ake ba wanzami, ba a haɗawa da kayan yaji kamar yadda aka saba yi a ƙasar Hausa. Wannan al’amari ya yi tasiri a kan wanzanci saboda an sami akasi ta fannin abubuwan da ake biyan wanzami waɗanda suka saɓa da ire-iren waɗanda ake bayarwa a al’adar Hausawa (ADS da MMSA da MLT da HIAY da MHYB, 18 da 19 da 20/8/2008).

    Karanta Shigowar Buzaye Ƙasar Hausa

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Shigowar Buzaye Ƙasar Hausa

    Shigowar Buzaye Ƙasar Hausa

    Buzaye mutane ne waɗanda suke zaune rukuni-rukuni a cikin Hamadar Sahara da kuma a yankin Sahel da yake cikin Afrika ta Yamma.

    Buzaye sun kasu zuwa manyan rukunoni uku kamar haka; akwai na Tassili-ni-Ajjar da na Ahaggar da kuma na Adrar-n-Ifoghas (Labaran, 1975:1). Al’ummar Buzaye suna zaune a bisa tsarin zamantakewar rukunoni. Kowane rukuni yana tafiyar da harkokinsu a ƙarƙashin wasu shugabanni.

    Akwai Amanokal waɗanda su ne dattawa masu bayar da shawara kan dukkan abin da ya shafi al’ummarsu. Imajeghen su ne mayaƙa kuma suna ƙarƙashin ikon Imghad waɗanda su ‘ya’ya aka haife su. Akwai kuma “Ineslemen”waɗanda su suke yin sasanci da alƙalanci da tafiyar da harkokin addinin Musulunci a tsakanin Buzaye.

    Daga nan, sai Enadan watau baƙaƙen maƙera da Ikanawan masu ginin tukwane, daga ƙarshe sai baƙaƙen bayi da ake kira Iklan, idan suka sami ‘yanci ana kiran su da sunan Iderfan. Baƙaƙen Buzaye sun fi jajaye yawa (Hammani, 1975:194).

    Ko da yake mafi yawancin Buzaye makiyaya ne waɗanda suke yawace-yawace domin neman wuraren da za su yi kiwon dabbobinsu, waɗanda suka haɗa da raƙuma da awaki da tumaki da dawaki da jakuna da sauransu, amma wasu daga cikinsu kamar Enadan da Ikanawan da Iklan suna zaune a garuruwa irin su Agades wanda a yanzu shi ne babban birninsu da kuma Arlit da Tchivozum da Iferouom da Ingel da Adeɓbissinat da Tchimia da Tabelot da Aoudaɓas da Elmiki da Egadawel da Dabaga da dai sauransu (Hira da AHSAMA, 20/5/2005).

    Bayan kiwon dabbobi Buzaye suna yin noma da ‘yan aikace- aikacen ƙodago don samun kuɗin ɓatarwa kuma suna yin kasuwanci. Daga cikin abubuwan da suke nomawa akwai dabino da kayan marmari. Akwai tsohuwar dangantaka tsakanin Buzaye da Hausawa wadda ita ce ta taimaka wajen shigowar Buzaye ƙasar Hausa.

    An bayyana cewa sakamakon mamayewar da Larabawa suka yi ko’ina cikin ƙasar Buzaye, an tilasta wa wasu daga cikinsu yin ƙaura suka yiwo kudu har zuwa cikin ƙasar Hausa. Haka kuma shigowar Turawan Faranshi cikin ƙasar Buzaye wadda ta haifar da zanga-zangar da Buzaye suka yi daga shekarar 1916 zuwa 1918 ta ƙara taimakawa wajen yin ƙaurar Buzaye suka yi kudu har zuwa cikin ƙasar Hausa (Labaran, 1975:1).

    Bayan wannan an bayyana cewa dangantakar jini da al’adu da kasuwanci sun ƙara taimakawa wajen shigowar Buzaye ƙasar Hausa. Kafin zuwan Turawan Mulkin Mallaka na Faranshi da na Ingilishi a ƙasashen Sudan ta tsakiya, wasu al’ummomi haɗe suke da juna a ƙarƙashin sarki ɗaya. Zuwan Turawa da kuma ƙirƙiro iyakokin zamani ya raba al’umma ɗaya zuwa ƙasashe biyu.

    A iya ganin haka a tsakanin Maraɗi da Katsina da kuma tsakanin Tchibiri da Zamfara, inda Maraɗi da Tchibiri suka faɗa cikin Jamhuriyar Nijar, Katsina da Zamfara aka bar su cikin Tarayyar Nijeriya. Waɗannan al’ummomi waɗanda suke cikin ƙasar Hausa sun yi iyaka da ƙasashen Buzaye, wannan maƙwabtaka ta ƙara taimakawa wajen yin cuɗanya a tsakaninsu wadda ta haifar da auratayya. Ta haka ne aka sami shigar al’adun Buzaye cikin al’adun Hausawa, haka kuma aka sami shigar al’adun Hausawa cikin na Buzaye.

    Wani al’amari wanda ya ƙara taimakawa wajen shigowar Buzaye ƙasar Hausa shi ne yaƙin jihadin Shehu Usmanu Ɗanfodiyo wanda ya gudana a tsakanin shekarun 1804 zuwa 1809. A wannan yaƙi wasu Buzaye sun taimaka wa rundunar Shehu Ɗanfodiyo, wasu kuma suka taimaka wa sarakunan Gobir. An bayyana cewa Buzaye waɗanda ake kira Kel Geres da Itesan suna zaune a cikin ƙasar Hausa tun lokaci mai tsawo da ya gabata.

    A saboda haka sun ɗauka yawan rundunonin Gobirawa na da ƙarfi sosai wanda za su iya cinye rundunar Shehu Ɗanfodiyo da yaƙi. Wannan ne ya sa suka bayar da goyon bayansu ga Sarakunan Gobir. Amma Buzaye Ineslemen da magoya bayansu sun yi mubayi’a ga rundunar Shehu Ɗanfodiyo, kuma suka shiga aka yaƙi Gobirawa tare da su (Hammani, 1975:197,198).

    A Kano an bayyana cewa Buzaye ne daga Agades suka kafa unguwar Agadasawa a cikin Birnin Kano tun lokaci mai tsawo da ya gabata. An ƙara da bayyana cewa tsakanin shekarar 1916 zuwa 1919 Buzaye kimanin dubu talatin (30,000) suka yi ƙaura daga ƙasarsu suka shigo ƙasar Hausa. Waɗannan Buzaye sun baro ƙasarsu ne suka zauna a garuruwa da ƙauyukan cikin ƙasar Hausa.

    Wannan kuwa ya faru ne sakamakon zanga-zanga da tawayen da suka yi wa Turawan Mulkin Mallaka na Faranshi. Mafi yawa daga cikin ire-iren waɗannan Buzaye sun zaɓi su zauna a garin Kano da ƙauyukan da suke kusa da ita fiye da sauran garuruwan ƙasar Hausa kamar Zariya da Katsina da dai sauransu. Wannan kuwa ya faru ne saboda Kano ta fi sauran waɗannan garuruwa samun wuraren yin aikace-aikacen samun kuɗi, kuma a Kano akwai ‘yan uwa da abokan arziki waɗanda suke zaune a nan shekaru da dama da suka gabata.

    Waɗannan Buzaye suna zaune a wurare daban-daban cikin Birnin Kano musamman wuraren da suke da kamfanoni da gidajen attajirai waɗanda ake ɗaukar su aikin gadi, kuma suna sayar da shayi. Amma aikin gadi shi ne babban aikin da aka san mafi yawancin Buzaye da suka shigo ƙasar Hausa suke yi domin samun kuɗi (Baƙo, 1990: 138,140). Dangane da shigowar Buzaye ƙasar Katsina an sami bayanin da ya nuna sun shigo wannan ƙasa tun fiye da shekaru ɗari biyu da suka wuce. Waɗanda suka shigo suna da yawan gaske kuma a ƙasar Mani suka fara sauka.

    Daga can ne wasu suka ƙara yin kudu waɗanda a yanzu ana samun zuri’arsu a garuruwan da suke kusa da Katsina kamar Kaita da Jibiya da Mashi da Dutsi da Kankiya da Rimi da Charanci da Kusada da Ingawa da Musawa da Safana da Kurfi da Dutsin-ma da Batsari da kuma cikin Birnin Katsina da ƙauyukan da suke ƙarƙashin mulkin waɗannan garuruwa (Hira da MGƊ, a garin Mani, a ranar 14/7/2005).

    Ire – iren waɗannan Buzaye sun kasu zuwa kashi-kashi kamar haka; akwai masu tsagar ɗunkin huɗu da tukarci da makitanawa waɗanda su bayin Buzayen Tassawa ne. Wasu Buzayen sun shigo ƙasar Hausa ne a sakamakon kasuwancin da ya gudana tsakaninsu da mutanen ƙasar Hausa. Bayanai sun nuna tun kafin ƙarni na goma sha tara akwai hulɗar kasuwanci wadda aka gudanar ta hanyoyin kasuwanci waɗanda suka biyo cikin ƙasashen Buzaye.

    Daga nan suka ratsa ta cikin hamadar Sahara zuwa wasu sassan ƙasar Hausa da kewaye. A lokacin da ake gudanar da wannan kasuwanci Buzayen da suke shigowa ƙasar Hausa suna safarar kayayyaki daga ƙasarsu waɗanda suka haɗa da dabbobi da dabino da kanwa da balma da manda da kayan hawan dawaki irin su sirdi da linzami da mashinfiɗan sirdi da kayan ado da dai sauransu. Bayan sun sayar suna sayen kayayyaki daga ƙasar Hausa don kai wa kasuwannin ƙasarsu.

    Ire – iren kayayyakin da suke saye daga kasuwannin ƙasar Hausa sun haɗa da abinci kamar gero da dawa, suna kuma sayen suturu irin waɗanda aka saƙa a ƙasar Hausa da baba da shunin gadi da auduga da dai sauransu.

    Haka su ma Hausawa suna yin safarar kayayyaki daga ƙasar Hausa zuwa ƙasar Buzaye, kuma suna sawo kayayyaki daga wannan ƙasa zuwa ƙasar Hausa. Ta irin wannan kasuwanci ne wasu Buzaye suka yi zamansu a wasu garuruwa na ƙasar Hausa kamar Kano da Katsina da Zamfara da Gobir da kuma ƙauyukan waɗannan garuruwa (Labaran, 1975:11 – 15).

    Dalilin kasuwanci da wasu hulɗoɗi wasu Hausawa sun yi ƙaura daga ƙasar Hausa zuwa ƙasar Buzaye, kuma suna zaune a can shekaru da dama da suka wuce. Tsakanin Buzayen da suka shigo ƙasar Hausa da kuma Hausawan da suka shiga ƙasar Buzaye an sami dangantaka mai inganci wadda ta haifar da musayar al’adu da auratayya a tsakaninsu.

    A nan al’adun Buzaye waɗanda suka shafi aure da haihuwa da mutuwa sun shiga kuma suka yi naso cikin al’adun Hausawa. Haka nan ma irin wannan ta auku ga al’adun Buzaye. Wani babban al’amari da ya faru a sakamakon wannan cuɗanya shi ne, Buzayen da suka shigo ƙasar Hausa shekaru aru-aru da suka wuce, kuma suka yi zamansu cikin ƙasar Hausa sun rikiɗe sun koma Hausawa a harshe da adabi da al’adu, amma wannan al’amari bai shafi Hausawan da suka koma ƙasar Buzaye ba. Don kuwa ba su yada harshensu da adabinsu da al’adunsu ba.

    Nason Al’adun Buzaye A Kan Wanzancin Hausawa

    A wurin Buzaye ana gadon wani ɓangare na sana’ar wanzanci, haka kuma akwai sashen da ba sai an gada ba kowa yana iya yi. Waɗanda suka gaji yin sana’ar wanzanci su ne ake kira da sunan “aghachaou”, kuma su ne suke yin ayyuka irin su cire belun-wuya da kaciya da tsagar gado da ta kwalliya. Amma sauran ayyuka musamman aski kowa yana iya koyo ya riƙa ba dole sai wanda ya gada ba. Dangane da wannan bincike an gano akwai wasu al’adun Buzaye waɗanda suka yi naso cikin wanzancin Hausawa a waɗannan fannoni.

    Cire Belun-wuya

    A al’adar Buzaye a lokacin da aka cire wa jariri ko yaro belun-wuya, sai a jiƙa kanwa da ruwa a ɗiga wa wannan jariri ko yaron ruwan don maganin tsayar da jini da kuma saurin warkewar wurin da aka yi yankan. Haka kuma wanda aka cire wa belun zai sami sauƙin zafi da ciwo a cikin maƙogaronsa inda aka cire belun (AHSAMA, Jamhuriyar Nijar, a ranar 20 ga watan Mayu 2005).

    Wannan al’ada ta yi naso sosai a wurin Hausawa, don kuwa a wannan zamani a mafi yawancin sassan ƙasar Hausa idan aka cire wa jariri ko yaro belun-wuya, sai wanzamin ya umurci iyayen yaron da su jiƙa kanwa da ruwa a ba wannan jariri ko yaron ruwan ya sha domin maganin tsayar da jini da saurin warkewa da kuma sauƙin zafi da tsananin ciwo a cikin maƙogaro kamar yadda Buzaye suke amfani da shi (Hira da MASASKM, a fadar Sarkin Katsinan Maraɗi, Jamhuriyar Nijar, a ranar 2 ga watan Maris, 1998) .

    Aski Da Ladar Da Ake Biya

    A lokacin da aka haifi jariri, a al’adar Buzaye ana iya yi masa aski a kowace rana ake so, ba dole sai an keɓe wata takamaimar rana ba. Mafi yawancin lokaci Buzaye sun fi yi wa jariransu aski kafin ranar suna watau kwana biyu ko uku ko huɗu da haihuwa. Haka kuma a al’adarsu ba wanzaman gado ne suke yin irin wannan aski ba, baƙaƙen maƙera waɗanda su abokan wasan Buzaye ne suke yin irin wannan aski.

    Idan suka gama aski ba a biyan su da wasu kuɗi, suna ɗibar nama ne daga dabbar suna wadda aka yanka, sannan kuma ana ƙara masu da abinci (Hira da AAASA, Jamhuriyar Nijar, a ranar 20 ga watan Mayu, 2005).

    Irin wannan al’ada ta yi naso a cikin wanzancin Hausawa, don kuwa a wannan zamani akwai wasu Hausawa waɗanda ke yi wa jariran da aka haifa aski kwana biyu ko uku ko huɗu da haihuwarsu. Ire-iren waɗanda suke koyi da irin wannan al’ada ba sa bari sai ranar suna su yi wa jariransu aski.Haka kuma wajen biyan ladar askin suna biyan wanzamin da ya yi askin da abinci da naman dabbar suna kamar yadda Buzaye suke yi.

    Wannan al’ada ta yi tasiri a kan wanzanci saboda wanzaman Hausawa da suke yi wa ‘yan’uwansu waɗanda suka yi koyi da wannan al’ada ta saɓa yadda ake yin wannan sana’a a ƙasar Hausa a inda ba a yi wa jariri askin suna sai ranar suna ko bayan an yi suna (Hira da MGƊASASƘ, a fadar Mai Martaba Sarkin Ƙwanni-Birnin Ƙwanni, Jamhuriyar Nijar, a ranar 3 ga watan Maris 1998).

    Nason Al’adun Buzaye A Kan Tsagar Gado

    Akwai wasu Hausawa waɗanda saboda wasu dalilai suke barin tsagarsu ta gado su ɗauki irin ta Buzaye. Misali, a ƙasar Katsina akwai wasu daga cikin mutanen wannan ƙasa waɗanda suka bar yin tsagar gado irin ta Katsinawa watau bille suka ɗauki irin ta Buzaye. Wannan kuwa ya faru ne saboda irin muzantawa da ƙyama da wasu Hausawa suke nuna wa masu irin wannan tsaga ta Katsinanci.

    Saboda hulɗa wadda take tsakanin ire-iren waɗannan Katsinawa da Buzaye, sai suka riƙa kwaikwayon yin tsagarsu a matsayin wadda suka gada. A nan ma wannan al’ada ta Buzaye ta yi naso a kan sana’ar wanzanci saboda wanzaman Hausawa ne suke yi wa waɗannan Hausawa irin tsagar Buzaye, ba wanzaman Buzaye ne suke shigowa ƙasar Hausa don yin ire-iren waɗannan tsaga ta Buzaye.

    Nason Al’adun Buzaye Kan Aski

    Al’ummar Buzaye na yi wa ‘ya’yansu tukku a ƙeya wanda ba sa aske shi sai lokacin da wannan yaro ya yi girma sosai ya isa aure. Irin wannan al’ada ya yi tasiri a kan wasu Hausawa musamman waɗanda suke zaune a ƙasar Buzaye da kuma wasu sassan ƙasar Hausa waɗanda suke maƙwabtaka da ƙasar Buzaye irin su Katsina da Daura da Maraɗi da Ƙwanni da Kano da Zamfara.

    Wannan kuwa ya faru ne saboda a wannan zamani akwai wasu Hausawa waɗanda suke yi wa ‘ya’yansu irin wannan tukku a matsayin na gado (Hira da MGƊASASƘ, a Birnin Ƙwanni da kuma MASASKM, dukkansu a Jamhuriyar Nijar a ranakun 3 da 4 ga watan Maris 1998).

    Nason al’adun Buzaye a irin wannan aski ya fito ne saboda wanzaman Hausawa ne suke yi wa Hausawa waɗanda suka yi kwaikwayon yin irin wannan nau’i na aski ba wanzaman Buzaye ne suke shigowa ƙasar Hausa su yi wa Hausawa ba.

    Karanta Shigowar Barebari Ƙasar Hausa

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Shigowar Barebari Ƙasar Hausa

    Shigowar Barebari Ƙasar Hausa

    Barebari su ne mutanen da suke zaune a Arewa maso gabas da ƙasar Hausa a farfajiyar tabkin Chadi. Su ne suka kafa daular Kanuri ta Kanem Borno a shekaru ɗaruruwa da suka wuce. A bayanan da aka samu an bayyana cewa wannan daula ta fara baɓaka a cikin ƙarni na goma sha ɗaya lokacin mulkin Mai Umme (Hume) 1085 zuwa 1097.

    Ana tunawa da shi a matsayin wanda ya fara karɓar addinin Musulunci daga cikin sarakunan Kanuri. A yanzu babban birnin Barebari shi ne Borno ko Maiduguri. Daga wancan lokaci har zuwa cikin ƙarni na goma sha takwas wannan daula ta sami haɓaka da faɗaɗa a wurare da dama da suke cikin Sudan ta tsakiya. Ta sami damar mamaye al’ummomi masu yawa waɗanda suke iyaka da ita, wannan ne ya tilasta masu biyan kuɗin ƙasa ga sarakunan Barebari.

    Dangane da dangantakar da ta faru a tsakanin Barebari a ɓangare ɗaya da kuma al’ummomin ƙasar Hausa a ɗaya ɓangaren, a iya cewa da farko ta yaƙe-yaƙe ce don mallakar hanyoyin kasuwanci da suka ratsa ta cikin Hamadar Sahara zuwa Afrika ta Arewa. Dangantaka ta biyu ita ce wadda aka samu sakamakon haɓakar addinin Musulunci da ya shigo cikin waɗannan ƙasashe (Adeleye, 1975:557). Haka kuma ana sa ran addinin Musulunci ya shigo cikin ƙasar Hausa ta Borno tun kafin ƙarni na goma sha huɗu (Yahaya, 1988:8).

    Cikakkiyar dangantaka wadda ta ƙara taimakawa wajen shigowar Barebari ƙasar Hausa ta faru ne a ƙarshen ƙarni na goma sha shida. Hakan kuwa ya faru ne a sakamakon haɓaka da Borno ta yi ta fuskar addinin Musulunci, don kuwa a lokacin Borno ta zama cibiyar koyarwa da yaɗa addinin Musulunci wadda babu kamar ta a duk tsakiyar Sudan. Saboda haka ne mutanen ƙasar Hausa ta fuskar addinin Musulunci suka dogara kan malaman da suka fito daga Borno ko waɗanda suka yi karatun addinin Musulunci a ƙasar Borno.

    An sami shahararrun malamai masu yawan gaske waɗanda suka yi ƙaura daga Borno suka shigo ƙasar Hausa. Misali, mahaifan shahararren malamin nan wanda aka haifa a cikin shekarar 1595 mai suna Abu Abdullahi Muhammad b. Masanih b. Muhammad b. Abdullah b. Nuh al-Barnawi al-Katsinawi wanda kuma aka fi sani da suna Wali Ɗanmasani, sun yiwo ƙaura ne daga Borno, shi kuma an haife shi a Katsina. A halin yanzu zuri’ar wannan malami na zaune a unguwar Masanawa ta cikin birnin Katsina.

    Wannan ya bayyana mahaifansa ko kakanninsa suna cikin malaman da suka yiwo ƙaura daga Borno suka shigo Katsina a farkon ƙarni na goma sha shida. Bayan su akwai kuma masanin nan mai suna Muhammad b. Ahmad b. Abi Muhammad al-Tazakhti wanda aka fi sani da sunan Wali Ɗantakum, ya rasu a wajen shekarar 1529. Akwai kuma wani shahararren malami mai suna Makhluf b. Ali b. Salih al-Bilbali wanda ya rasu a cikin shekarar 1532. Waɗannan baƙi har yanzu suna nuna asalinsu Barebari ne don kuwa suna yi wa ‘ya’yansu tsagar fashin goshi irin ta Barebari (Usman, 1972:186,190).

    Dangane da shigowar Barebari Kano, an bayyana cewa, bayan shigowar ɗaiɗaiku tun lokaci mai tsawo da ya gabata, an sami shigowar wasu da yawan gaske a lokuta uku kamar haka:

    • A farkon ƙarni na goma sha biyar a sakamakon rashin zaman lafiya da ya faru a Daular Kanem da ta Borno da kuma buɗe hanyar kasuwanci daga Borno zuwa Kano wadda ta wuce zuwa yankin Gwanja, Barebari masu yawa sun shigo ƙasar Kano.
    • A tsakiya da ƙarshen ƙarni na goma sha takwas an sami shigowar Barebari cikin ƙasar Kano sakamakon fari wanda ya haifar da ƙarancin abinci da aka fuskanta a ƙasar Borno.
    • A sakamakon hare-haren da Rabeh ya riƙa kaiwa cikin Daular Borno a ƙarshen ƙarni na goma sha tara da kuma farkon ƙarni na ashirin ya ƙara taimakawa wajen shigowar Barebari cikin ƙasar Kano.

    Waɗannan Barebari ne suka kafa unguwannin Zangon Barebari da Malangari, haka kuma akwai waɗanda suke zaune a cikin wasu unguwanni kamar Fagge da ‘Yandoya da Gabari dukkan su a cikin Birnin Kano (Baƙo, 1990:72, 98,99).

    An sami bayanin daɗaɗɗiyar dangantaka tsakanin Barebari da mutanen Zariya, domin kuwa an bayyana cewa a cikin ƙarni na goma sha takwas har zuwa lokacin jihadi Daular Borno ta mamaye Zariya. Wannan ne ya sa aka sami zaunannen wakilin Mai na Borno a fadar Sarkin Zazzau wanda yake riƙe da muƙamin “Kachalla”. Wannan dangantaka ta ƙara taimakawa ƙwarai wajen shigowar Barebari ƙasar Zazzau.

    A dalilin haka ne Barebari suka sami sarautar Zazzau, wanda a yanzu daga cikin gidajen sarautar Zazzau akwai gidan Yamusa waɗanda asalinsu Babarbare ne. Ta fuskar addinin Musulunci, Barebari sun yi gagarumin aiki a ƙasar Zazzau da kewayenta, don kuwa daga cikin limaman Zariya, Limamin Kona ana ba da shi daga al’ummar Barebari (Hogben, 1967:118).

    Bayanan da aka samu dangane da ƙaura da shigowar Barebari ƙasashen Hausa na Yamma, wato Zamfara da Gobir, an bayyana cewa an sami shigowar Barebari a waɗannan ƙasashe a lokaci mai tsawo da ya gabata. An ce wasu malamai daga Borno sun shigo ƙasar Zamfara a cikin ƙarni na goma sha bakwai, kuma ana tsammani su ne suka shigar da wasu sarakunan Zamfara cikin addini Musulunci.

    Wasu daga cikin malaman Anka sun bayyana cewa asalinsu daga Borno suke. Waɗannan malamai Barebari suna da babban matsayi a ƙasar Zamfara don kuwa mafi yawanci su ne limamai a Anka (Nadama, 1977:185,186). Ƙaura da shigowar Barebari cikin ƙasar Zamfara ba ga malamai kaɗai ta tsaya ba, a cikin ƙarni na goma sha bakwai an sami wani ɗan sarki da ya yi gudun hijira daga Borno saboda wasu dalilai ya sauka a Fadamar Kanwa.

    Wannan ɗan sarki mai suna Modu Masika ya zo da tawagar dakaru Barebari masu yawan gaske, waɗanda daga cikin su akwai mahaya dawaki ɗari da ‘yan lifidda arba’in. An bayyana cewa waɗannan Barebari sun sauka a wannan wuri lokaci mai tsawo da ya gabata tun kafin zuwan Gobirawa Birnin Alƙalawa (Nadama, 1977:186,187).

    A ƙasar Zamfara akwai Burmawa waɗanda ake sa ran sun fi dukkan mutanen da suke ikirarin asalinsu Barebari ne yawa. Yana da matuƙar wuya a ce a lokacin da suka shigo ƙasar Zamfara daga Borno, amma bayanan da aka samu sun bayyana cewa a lokacin da suka shigo ƙasar Zamfara sun sauka a wuraren da suke kewayen gulbin Sakkwato.

    Shugaban tawagar waɗannan Barebari mai suna Zarra ya sauka a Ƙumcin Gizo, a inda aka ce ya aika wa Galadiman Borno da ya yi masa sarautar Sarkin Burmi. Daga Ƙumcin Gizo wasu suka yi gaba zuwa Jargaɓa, daga ƙarshe suka sauka a Bakura a farkon ƙarni na goma sha takwas. A wannan lokaci ne waɗannan Barebari Burmawa suka kafa wasu garuruwa a ƙasar Zamfara waɗanda suka haɗa da Rara da Riji da ‘Yar Tsakuwa.

    An tabbatar da a cikin ƙarni na goma sha takwas akwai Barebari ‘yan kasuwa da malamai masu yawa a garuruwan ƙasar Zamfara waɗanda suka haɗa da Birnin Zamfara da Kiyawa da Banga Tumfafi da Kamani da kuma ‘Yandoto (Nadama, 1977:191,192).

    Su ma Hausawa saboda kasuwanci da neman ilimin addinin Musulunci sun yi ƙaura daga ƙasar Hausa suka koma ƙasar Borno. Sakamakon shigar Hausawa ƙasar Borno an sami auratayya tsakaninsu da Barebari, amma duk da haka ba a sami abin da ya faru ga Barebarin da suka shigo ƙasar Hausa ba waɗanda suka rikiɗe suka koma Hausawa.

    Hausawan ba su koma Barebari ba, hasali ma dai mafi yawancin Barebari suna magana da harshen Hausa. Abin da ya faru shi ne, Hausawan suna magana da harshen Kanuri kamar yadda suke magana da harshen Hausa, kuma wasu al’adun Barebari sun shiga cikin al’adun Hausawa ta fuskar aure da haihuwa da mutuwa da sauran wasu ma’amalolin rayuwa na yau da kullum.

    Ire-iren waɗannan Hausawa suna zaune a unguwannin Hausari da Bulunkutu da Gwange da London-Ciki da Jajere duk a cikin Birnin Maiduguri da wasu garuruwa a cikin jihar Borno da Yobe. Haka kuma akwai wasu da suke zaune a Damagaram ta cikin Jamhuriyar Nijar (Hira da MSYB, a ranar 26/5/2005).

    Nason Al’adun Barebari a Kan Wanzancin Hausawa

    A wurin Barebari sana’ar wanzanci ta samo asali ne tun lokacin Annabi Muhammadu (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi), don kuwa sun bayyana cewa, ita kanta kalmar ‘wanzama’ sunan da suke kiran wanzami da shi, ta samo asali ne daga kalmar Larabci ta ‘hajam’ da ‘hajama’, ma’ana mutumin da yake yin ƙaho, ko ‘bessem kastama’ da harshen Barbarci.

    Sun ƙara da bayyana cewa, wani wanzami ya yi wa Manzon Allah ƙaho, a lokacin da ya fitar da jinin don zubarwa, sai ya ga ƙasa ta buɗe, da kuma ya ɗaga kansa sama, sai ya ga ita ma samaniya ta buɗe.

    Wannan ne ya sa shi tunanin cewa dukkan waɗannan halittu na Ubangiji suna buƙatar a zuba jinin Manzon Allah a cikinsu. Daga nan sai ya yanke hukuncin ya shanye wannan jini. Wannan dalili ne ya sa a yau ake danganta wanzamai da mutane waɗanda suke da jinin Annabi a cikin jikinsu, kuma aka riƙa danganta su da shariftaka (Sheriff, 2000:62).

    A al’adar Barebari ana gadon sana’ar wanzanci, haka kuma a wasu lokuta waɗanda suka yi gado sukan iya koya wa waɗanda ba su gada ba, amma shugaban wanzamai wanda suke kira da sunan ‘Zanna Ɗambusuma’, dole sai wanda ya gaji wannan sana’a ne ake naɗawa kuma Shehun Borno ne yake naɗa shi.

    A yanzu wannan sarauta tana hannun Zanna Ɗambusuma Madu Aji, kuma yana da mataimaka waɗanda kowanen su yana riƙe da irin tasa sarauta waɗanda suka haɗa da ‘grema’ da ‘fuwu’ da ‘kazalla’.

    A al’adar Barebari cikakken wanzami ko ‘wanzama’ ko’diyeji’ shi ne wanda ya koya kuma ya iya ayyuka irin su tsagar gado da cire belun-wuya da kaciya da ƙaho da yin tsagar ciki a ƙarƙashin cibiya da kuma bayar da magungunan gargajiya da sauran ayyuka waɗanda suka danganci kiwon lafiyar mutane (Sheriff, 2000:66). Idan aka nazarci wannan bayani za a fahimci akwai kamanci tsakanin wanzancin Barebari da na Hausawa. Wannan kamanci ya ƙara taimakawa aka sami nason al’adun wanzancin Barebari cikin na Hausawa.

    Wasu al’adun Barebari sun yi tasiri a kan al’adun wanzanci musamman ga Hausawa waɗanda suke zaune a ƙasashen Barebari kamar a Maiduguri da Damagaram da kuma a garuruwan da suke ƙarƙashin ikonsu. Haka kuma akwai wasu Hausawan ƙasar Hausa waɗanda al’adun Barebari suka yi tasiri a cikin rayuwarsu ta fuskar yadda suke tafiyar da al’adun da suka shafi ayyukan wanzanci.

    An sami irin wannan naso ne daga wurin wasu Barebari waɗanda suka shigo ƙasar Hausa daga ƙasar Borno ko dai don yaɗa ilimin addinin Musulunci ko kuwa don yin kasuwanci da wasu ma’amalolin rayuwa. Yanzu za a yi nazarin wasu daga cikin fannonin wanzanci a yi bayanin wuraren da al’adun wanzancin Barebari suka yi tasiri a kan na Hausawa.

    Cire Belun-wuya

    A al’adar Hausawa a lokacin da aka cire wa jariri belun-wuya ana ɗebo sauyar dashi da ta fid-da-tartsa a dafa a ba shi ya sha don maganin zafin da zai biyo baya, kuma wurin da aka yi yankan ya warke da sauri. Sakamakon zamantakewa a tsakanin Hausawa da wasu baƙi an sami wasu magungunan masu sauƙin yi fiye da wanda suke da farko.

    Misali, a al’adar Barebari bayan an cire wa jariri ko yaro belun-wuya, sai a daka ‘ya’yan bagaruwa a jiƙa garin da ruwa a ɗura masa wannan ruwa. Dalilin ba shi wannan ruwan magani shi ne don maganin zafin da zai biyo bayan cire belun kuma ya taimaka wajen tsayar da jini daga wurin da aka cire belun. Haka kuma zai taimaka sosai wajen saurin warkewar wurin da aka yi yankan (Hira da ZƊMA, a ranar 9 ga watan Janairu, 2008 a gidansa da ke a cikin garin Maiduguri).

    Irin wannan al’ada ta yi tasiri a kan wanzancin Hausawa, don kuwa su ma Hausawa musamman waɗanda suke zaune a ƙasar Barebari da kuma wasu sassa na ƙasar Hausa irin su Katsina da Zamfara da Kano da Daura a lokacin da aka cire wa jariransu belun-wuya suna ba su irin wannan magani don koyi da Barebari (Hira da SASN, a ranar 10 ga watan Janairu, 2008 a gidansa da ke a unguwar Bulunkutu cikin garin Maiduguri.

    Tasirin Magungunan Barebari a Kan Wanzanci

    Wani ɓangare na al’adun Barebari wanda ya yi naso a kan wanzancin Hausawa shi ne ta fuskar maganin gargajiya. A wannan ɓangare an bayyana wanzaman Hausawa sun sami magani daga wurin wanzaman Barebari wanda zai taimaka wa wanzami idan yana yin aski wanda ake yi wa askin ba zai ji zafi ko wata takura ba.

    Kamar yadda aka sami bayani an ce wannan magani ya samo asali ne daga wurin wani wanzami Babarbare wanda saboda yadda ya iya aski kuma labarinsa ya kai ko’ina cikin ƙasar Borno.

    Da Shehun Borno ya sami labarin wannan wanzami, sai ya gayyace shi da ya zo don yi masa aski. A lokacin da aka gaya masa, sai ya je wurin mahaifinsa ya sanar da shi. Daga nan ne sai mahaifin wannan wanzami ya shawarce shi da ya samo mullin giginya wanda yake ɗauke da ‘ya’yan giginyar a daka shi cikin turmi a jiƙa cikin ruwa ya riƙa wanke hannuwansa da ruwan maganin.

    Ya bayyana masa cewa yin haka zai taimaka idan yana yi wa mutane aski ba za su ji zafi ko wata takura ba. Da ya bi wannan shawara ta ƙara taimaka masa samun ɗaukaka a wurin Shehun Borno wadda ta kai har aka ba shi sarautar wanzamai watau “Zanna Ɗambusuma”.

    Daga baya, sai sauran wanzamai suka gano wannan asiri su ma suka riƙa yi wanda ya taimaka masu wajen gudanar da wannan sana’a. Sannu a hankali ta hanyar cuɗanya tsakanin wanzaman Hausawa da na Barebari, sai su ma suka sami wannan asiri wanda har a wannan zamani suna amfani da shi (Sheriff, 2000:63).

    Nason Tsagar Gado ta Barebari a Kan Wanzancin Hausawa

    Al’adar da ta danganci tsagar gado irin ta Barebari ta yi tasiri a kan wasu Hausawa. Ta wannan fuska akwai wasu Hausawa musamman a ƙasar Katsina, waɗanda asalin tsagarsu ta gado billen Katsinanci ce. A wannan zamani saboda an ɗauki dukkan mai irin wannan tsaga ta billen Katsina matsayin Bamaguje wanda wasu mutane sukan muzanta, sai wasu masu irin wannan tsaga suka bar yin tsagar gaba ɗaya, amma waɗanda suke sha’awar tsagar, sai suka bar yin irin wannan tsaga suka ɗauki wata tsagar gado suka danganta da zuri’arsu.

    Daga cikin ire-iren waɗannan tsage akwai ta Barebarin Katsina da fashin goshi waɗanda dukkan su asalinsu tsagen gado ne da ake yi wa wasu mutane don su bayyana asalinsu Barebari ne. Wannan al’ada ta yi tasiri cikin al’adun wanzanci saboda wanzamai Hausawa ne suke yin ire-iren waɗannan tsaga, ba wanzaman Barebari ne suke shigowa ƙasar Hausa ba.

    A wannan zamani yana da wuya a ƙasar Katsina a bambance tsakanin waɗannan Barebari da kuma Katsinawa waɗanda suka bar yin tsagarsu ta asali suka ɗauki irin wannan tsaga ta Barebarin Katsina.

    Danna nan don karanta Nason Al’adun Baƙi Maƙwabta Na Kusa A Wanzancin Hausawa

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Ƙaura Da Shigowar Baƙi Ƙasar Hausa

    Ƙaura Da Shigowar Baƙi Ƙasar Hausa

    Tun cikin shekarun 1960 zuwa wannan lokaci masana da manazarta da ɗalibai masu binciken tarihi suke ta kai-kawon nazari kan ƙaura da shigowar baƙi da kuma sakamakon da wannan ƙaura ta haifar ga al’ummomi daban-daban da suke cikin faɗin Nijeriya.

    Saboda haka ne ire-iren waɗannan masana da manazarta da ɗalibai suka kawo irin tasu fassarar kan kalmar ƙaura. Misali,”ƙaura na nufin tashin mutane daga ƙauyuka ko garuruwa zuwa manyan birane, wasu na wani ɗan lokaci (ci-rani), wasu kuma sun koma don su yi zama na dindindin a wannan sabon wuri” (Osaghae, 1994:20).

    Wani masanin kuma yana ganin ƙaura a matsayin “tashi daga wata gundumar mulki zuwa wata, wadda sakamakon wannan ƙaura yake samar da sabon wurin zama na dindindin” (Prothero, 1981:51).

    A wata fassarar kuwa ana ganin ƙaura a matsayin “mutum ko ƙungiyar mutane masu yawa su yi sauyin wurin zama su koma wani wuri na daban wanda za su yi zama na dindindin, amma ba irin sauyin wurin da makiyaya ko ‘yan ƙodago ko ‘yan ci-rani da makamantansu suke yi ba waɗanda ba sa yin zama na dindindin a sabon wurin da suka koma” (Bello, 1999:1).

    Dangane da haka ne wannan nazari ya yi ƙoƙarin kawo bayani kan ire-iren baƙin da suka yi ƙaura daga ƙasashensu na asali waɗanda suke maƙwabtaka ta kusa da ƙasar Hausa. Waɗannan baƙi sun haɗa da Fulani da Nufawa da Barebare da Buzaye da Yarabawa. An kuma kawo bayanan dalilan da suka sa sanya su zaɓar ƙasar Hausa a matsayin wurin da suka ga ya dace su zauna don ci-rani ko don su yi zama na dindindin.

    Idan muka dubi ire-iren baƙin da suke zaune a ƙasar Hausa kuma aka waiwayi tarihi, za a fahimci sun shigo ƙasar ne a lokuta daban-daban. Dangane da wannan nazari an kasa waɗannan lokuta zuwa biyu. Lokaci na farko ya fara daga ƙarni na goma sha huɗu zuwa ƙarni na goma sha takwas. Lokaci na biyu kuma ya fara daga farkon ƙarni na goma sha tara zuwa ƙarni na ashirin.

    Idan muka ɗauki lokaci na farko watau ƙarni na goma sha huɗu zuwa ƙarni na goma sha takwas lokaci ne da ƙasashen da a yanzu ake kira ƙasar Hausa kowace daga cikinsu take cin gashin kanta. A wancan zamani babu abin da a yanzu ake kira haɗaɗɗiyar ƙasar Hausa, kowane Sarki na mulkin iyakar riƙonsa,tsakaninsa da sauran sarakuna danginsa maƙwabta na kusa da na nesa sai yaƙi.A lokacin kuma hamayya a tsakanin waɗannan sarakuna don mallakar hanyoyin kasuwanci da tattalin arzikin wannan ƙasa ya zama ruwan dare.

    Wannan kuwa ya faru ne saboda dukkan ƙasar da ta mallaki babbar kasuwa za ta jawo baƙin ‘yan kasuwa daga sassa daban-daban.Wannan irin damar ce Katsina ta samu a wajajen tsakiyar ƙarni na goma sha biyu, inda fatake Larabawa da Azbinawa da Wangarawa suka riƙa haɗuwa.A wannan lokaci saboda yawan yaƙe-yaƙe da sarakunan Kano suka yi fama da shi ta rasa wannan dama (Ibrahim,1982:74-75).

    Haka abubuwa suka yi ta faruwa sannu a hankali baƙi suna ta shigowa cikin ƙasar Hausa a wannan lokaci daga ƙasashe maƙwabta na kusa don yin kasuwanci da wasu hulɗoɗi. Daga cikin ire-iren waɗannan baƙi akwai Fulani da Barebari da Buzaye da Nufawa da Yarabawa.

    Lokaci na biyu da baƙi suka shigo ƙasar Hausa watau farkon ƙarni na goma sha tara zuwa na ashirin, shi ne lokacin da aka yi jihadin Shehu Usman Ɗanfodiyo a cikin shekarun 1804 zuwa 1809. Wannan jihadi da kuma kafuwar Daular Sakkwato ya taimaka ƙwarai wajen ƙara shigowar baƙi ƙasar Hausa, misali Buzaye da Adarawa daga arewacin ƙasar Hausa (Hammani, 1975:197-198).

    A babi na biyar da na shida za a bi diddigin shigowar waɗannan baƙi ƙasar Hausa da kuma yadda wasu al’adunsu suka yi naso cikin al’adun Hausawa musamman sana’ar wanzanci a wannan zamani.

    Domin Karanta Tattalin Arziƙin Ƙasar Hausa danna nan

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tattalin Arziƙin Ƙasar Hausa

    Tattalin Arziƙin Ƙasar Hausa

    Ƙasar Hausa kamar kowace ƙasa tana da manyan hanyoyi da dama waɗanda suke taimaka wa tattalin arzikinta bunƙasa. Daga cikin waɗannan hanyoyi akwai waɗanda aka gada tun iyaye da kakanni, wato su ne na asali. Ire-irensu sun haɗa da noma da kiwo da fatauci da sana’o’in gargajiya. Bayan waɗannan akwai waɗanda aka samu sakamakon cuɗanya tsakanin Hausawa da wasu baƙin al’ummu kamar sana’ar kanikanci da kafinta da ɗinkin keke da mesin da dai sauransu.

    Noma

    Hausawa suna yi wa noma kirari da suke cewa “noma na duƙe tsohon ciniki kowa ya zo duniya kai ya tarar”. Wannan kirari na bayyana sana’ar noma daɗaɗɗiya ce a wannan duniya ba wai ga Hausawa kaɗai ba. Wannan ne ya sa idan ana maganar tattalin arzikin ƙasar Hausa, noma ne za a fara kawowa don kuwa shi ne ƙashin bayan tattalin arzikin wannan ƙasa.

    Wannan kuwa ya faru ne saboda sana’a ce wadda kowa-da-kowa yake yi talaka da saraki, attajiri da matalauci, maza da mata, babba da yaro don a sami abincin da za a ci da kuma wanda za a sayar don yin hidimomin yau da kullum. Saboda haka ne manoma a dukkan faɗin ƙasar Hausa da kewayenta suke samun wurare masu nagarta waɗanda suka haɗa da fadama da jigawa don noma amfanin gona mai kyau.

    Al’ummar Hausawa na yin noma iri biyu, na abinci da na kasuwa. Kayan noma na abinci sun haɗa da gero da dawa da masara da maiwa da dai sauransu, na kasuwa kuma sun haɗa da auduga da gyaɗa. Haka kuma ƙasar Hausa tana da albarkar da ake noma wasu abubuwan kamar rogo da dankali da sauransu (Nadama, 1977:90 – 92).

    Kiwo

    Kasancewar ƙasar Hausa shimfiɗaɗɗiya ce ga kuma sarari da ciyayi a ko’ina ya sa kusan a kowane gida ana kiwon dabbobi ko tsuntsaye. Hausawa na tsare dabbobi da tsuntsaye a gidajensu ta hanyar ba su abinci ko kuma a kora su zuwa daji don su nemi abinci a can. Ire-iren dabbobin da Hausawa suke kiwo sun haɗa da shanu da tumaki da awaki don cin namansu da kuma sayarwa.

    Haka kuma ana sayar da fatunsu da ƙiragansu don yin amfani da su. Ana kuma ɗaukar kashin da suka yi don kaiwa gona a matsayin takin da zai ƙara wa gona albarkar ƙasa. Bayan waɗannan dabbobi, Hausawa na kiwon dawaki don hawa na ƙawa da jin daɗi. Haka kuma suna kiwon jakuna da alfadarai don ɗaukar kaya da yin wasu ayyuka irinsu fatauci. Ire-iren waɗannan dabbobi dukkansu ana kiran su da sunan dabbobin gida.

    Bayan dabbobi Hausawa suna kiwon tsuntsaye irin su kaji da agwagi da zabi don cin namansu da ƙwayayensu da kuma sayarwa. Haka kuma saraki da attajirai suna kiwon tsuntsaye na alfarma irin su aku da ɗawisu da kanari don sha’awa da nishaɗi.

    Fatauci

    Tun kafin wannan zamani al’ummar Hausawa suna da irin nasu tsari wajen tafiyar da harkokin kasuwanci. Wannan tsari ana iya dubansa ta fuska biyu, kasuwancin cikin gida da kuma na waje. A cikin gida akwai kasuwanni na garuruwa waɗanda ake tafiyar da harkokin kasuwanci ta hanyar furfure. A irin wannan kasuwanci ana musayar abubuwan sayarwa ne, misali manomi ya ba masaƙi kayan gona don ya amshi kayan saƙa, ko ya ba makiyayi don ya amshi wata dabba da sauransu.

    An daɗe ana yin irin wannan tsari na cinikayya a ƙasar Hausa har zuwa cikin ƙarni na goma sha takwas da aka shigo da hanyar yin amfani da kuɗin wuri da biringizau don yin saye da sayarwa a duk faɗin Afrika ta Yamma (Nadama, 1977:137 – 138). Ta fuskar kasuwancin wajen ƙasar Hausa ‘yan kasuwa daga ƙasar Hausa na yin fataucin kayayyaki daga wannan ƙasa zuwa garuruwan Adar da Azben da Nufe da ƙasashen Yarabawa da Gwonja.

    Bayan sun sayar da kayayyakinsu a can, suna kuma sawo wasu kayayyakin daga waɗannan ƙasashe su kawo ƙasar Hausa don su sayar. Ire-iren kayayyakin fatauci da suka riƙa saye daga ƙasar Hausa suna kaiwa waɗannan ƙasashe, sun haɗa da daddawa da kayayyakin sutura irin waɗanda aka saƙa a ƙasar Hausa da kuma shunin gadi da baba da dabbobi da sauransu.

    Haka kuma suna sawo kayayyaki irinsu bindigogi da kayan albarushi da riguna girken Nufe da kayan ƙarau daga ƙasar Nufe. Suna kuma sawo balma da kanwa da dabino da dawakin Azbin da awaki da tumaki da raƙuma daga ƙasashen Adar da Azbin da kuma Borno.’Yan kasuwar da suke zuwa fatauci kudu watau ƙasashen Yarabawa da Gwonja suna sawo goro don kawowa ƙasar Hausa da maƙwabtanta na arewa don sayarwa (Nadama, 1977:142 – 143).

    Sana’o’in Gargajiya

    Kafuwar garuruwa a ko’ina cikin ƙasar Hausa da kuma bunƙasar da noma ya samu ya ƙara taimakawa wajen samuwar sana’o’in gargajiya inda ake ƙera da kuma sarrafa kayayyaki iri daban-daban domin amfanin mutanen ƙasar Hausa da maƙwabtansu na kusa da kuma na nesa. Ire-iren waɗannan sana’o’i sun haɗa da ƙira da saƙa da rini da jima da dukanci da sassaƙa da sauransu.

    Akwai kuma sana’o’in da ake yin ayyukan taimaka wa rayuwa kamar wanzanci da fawa da ɗori da sauransu. Bayan waɗannan akwai ƙananan sana’o’i waɗanda mata suke tafiyar da su kamar kaɗi da kitso. Waɗannan sana’o’i na gargajiya sun taimaka matuƙa gaya wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasar Hausa. Yanzu za a ɗauke su ɗai-ɗai da ɗai-ɗai domin ganin yadda suka taimaka wa tattalin arzikin ƙasar Hausa.

    Ƙira

    Ƙira sana’a ce wadda aka fi yi a lokacin rani domin tanadar kayan aikin noma, amma duk da haka ana yin ta a kowane lokaci na shekara domin samar da kayan amfanin gida na yau da kullum. Maƙera sun kasu zuwa kashi biyu, akwai maƙeran baƙi da maƙeran fari. Maƙeran baƙi su ne suke tono tama su narka ta don ta zama ƙarfe wanda suke amfani da shi domin yin nau’o’in kayan ƙira.

    Ire-iren kayayyakin da maƙeran baƙi suke yi sun haɗa da fartanya da masassabi da gatari da lauje da sungumi da adda da dai sauransu domin yin ayyukan gona. Haka kuma maƙeran baƙi suna ƙera takubba da gariyo da tsitaka da masu da kibau da sauran kayayyakin da ake amfani da su wajen yin farauta da yaƙi.

    Bayan waɗannan suna yin kalaba da wuƙaƙe ƙanana da manya waɗanda ake amfani da su wajen yin ayyukan cikin gida na yau da kullum. Haka kuma su ne suke samar da kayan aikin wanzanci waɗanda suka haɗa da asake domin yin aski da kaciya da kuma kalaba wadda ake amfani da ita wajen cire belun-wuya. Suna kuma yin askar tsaga wadda ake amfani da ita wajen cire angurya a farjin mata da yin tsagar gado da ta magani da ta kwalliya da sauransu.

    Saƙa

    Saƙa sana’a ce wadda ake sassarƙa zare ko gashi ko ɓawo ko kaba don a mayar da su wani abu mai faɗi kamar tufafi ko shimfiɗa. Saboda haka a iya cewa, saƙa ta kasu zuwa iri biyu, ta tufafi da ta kayan shimfiɗa. Ana amfani da zaren auduga ne wanda mata suke kaɗawa domin saƙar tufafi.

    Masaƙa wato masana’antar da ake sarrafa zare domin yin sutura ita ma ta kasu zuwa iri biyu. Akwai masaƙar tsaye wadda mafi yawanci mata ne suke amfani da ita don yin saƙar gwado ko zanen kujera ko ɗan goyo wanda ake goya jarirai. Akwai kuma masaƙar zaune wadda maza ne suka fi yin amfani da ita wajen yin saƙar sauran abubuwa.

    Hakika wannan sana’a tana da matuƙar muhimmanci a ƙasar Hausa domin kuwa ba domin ita ba da an riƙa tafiya tsirara. Wannan a fili yake, sutura ita ce alamar da take bayyana bambanci a tsakanin mutum da dabba. A cikin mutane ma da sutura ake iya rarrabe bambancin al’adu.

    Da ita ake gane cikakken mutum da akasinsa. Haka kuma da ita ake sanin mawadaci da mabuƙaci. Masana’antar saƙa ta taimaka sosai wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasar Hausa. Wannan kuwa ya samu ne sakamakon kayayyakin da ta riƙa samarwa waɗanda ake sayarwa a kasuwannin cikin gida da na ƙasashe maƙwabta (Alhassan, 1982:52-54).

    Jima

    Jima sana’a ce wadda ake sulluɓe fata don a fitar da gashin da yake jikinta. A irin wannan masana’anta da ake kira majema ana sauya fata daga halinta na asali na gashi da kaushi a sarrafa ta, a gyara ta yadda za ta yi laushi kamar sutura.

    Bayan an gyara fata ta yi kyau ana sayar da ita ga dukawa, kuma mafi yawancin fatar da aka gyara tana daga cikin manyan muhimman hajoji da ake safararsu daga ƙasar Hausa zuwa ƙasashe maƙawabta na kusa da na nesa. Ana yin wannan safara tun lokaci mai tsawo da ya gabata kafin shigowar Turawa wannan ƙasa.

    Irin wannan fata na daga cikin kayayyakin da aka riƙa fataucinsu daga Kano da Katsina da Zamfara da Sakkwato ana ƙetare hamadar Sahara da su ana kaiwa Morocco da sauran ƙasashen da suke arewacin Afrika ana sayarwa. Daga nan ne kuma Turawa suke sayen ta su kai ƙasashensu inda suke sarrafa ta domin yin jikunkuna da takalma da riguna maganin sanyi da sauran abubuwa waɗanda kuma suke kawo wasu daga cikinsu zuwa ƙasashen Afrika da sauran ƙasashen duniya don sayarwa.

    Dukanci

    Dukanci sana’a ce wadda ake sarrafa fata don mayar da ita wani abu na amfanin yau da kullum. Ire-iren abubuwan da dukawa suke yi sun haɗa da jikunkuna da takalman fata da igiyar linzamin doki da burgami da zabira wadda ake zuba kayan wanzanci da jakar zuba ma dawaki dawa ko dusa. Haka nan kuma suna yin warki da gafaka da tandun kwalli da kuben wuƙa da na takobi da sauran abubuwa.

    Bayan dukawa sun yi waɗannan abubuwa suna sayar da su ne ga waɗanda suke buƙata da kuma masu yin sari waɗanda suke kaiwa kasuwanni na cikin gida da na waje. Haka kuma ‘yan kasuwa na waje na shigowa cikin ƙasar Hausa don sayen ire-iren waɗannan kayayyaki da dukawa suka sarrafa.Wannan masana’anta ta dukanci ta bayar da gagarumar gudummuwa wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasar Hausa.

    Rini

    Rini na nufin sauya launin tufa ko zare don ya zama wani iri. Ana kiran masana’antar da ake yin rini marina. Abubuwan da ake amfani da su wajen yin rini sun haɗa da muciya da kwatarniya da guga da itace da ƙaiƙayi da ɗan kutuɓu da baba da katsi da shuni da zarta da marina da ruwa.

    Wannan masana’anta ta taimaka sosai wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasar Hausa. An fahimci haka ne kuwa ta la’akari da kayan rini irin na ƙasar Hausa na daga cikin muhimman abubuwan da fatake suke yin safararsu daga ƙasar Hausa zuwa ƙasashen maƙwabta don sayarwa.

    Sassaƙa

    Sassaƙa sana’a ce wadda ake gyara icce don a mayar da shi wani abu na amfani. Masassaƙan ƙasar Hausa na sassaƙa turmi da taɓarya da kujerar zama ta mata da kujerar gwado ta maza da ƙotar fartanya da ta masassabi da ta gatari da ta garma. Haka kuma masassaƙa suna sassaƙa akushi da ƙoshiyar dama fura da ludayin itace da allunan karatun Alƙur’ani mai girma da dai sauran abubuwa masu yawan gaske.

    Wannan sana’a ta sassaƙa tana taimaka wa tattalin arzikin ƙasar Hausa matuƙar gaske. A iya ganin haka ta yadda take samar da wasu kayan aiki ga sauran masana’antun gargajiya. Misali, manoma na amfani da ƙotoci, wanzamai na amfani da ƙoshiya don cire belun-wuya, makaɗa na amfani itacen da ake yin kayan kiɗa, masaƙa na amfani da gwafa wadda ake kafa masaƙa ta zaune da ta tsaye da sauran abubuwa.

    Wanzanci

    A Hausance, sana’ar “wanzanci” tana nufin amfani da askar aski domin yin aski da gyaran fuska da yin kaciya da kuma amfani da kalaba da ƙoshiya don cire belun-wuya. Sana’ar wanzanci ba ta tsaya a nan ba don kuwa ana amfani da ‘yar tsaga don yin ƙaho da cire angurya a farjin mata da yin tsagar gado da ta kwalliya da ta magani.

    A sana’ar wanzanci dai ana yin hujen kunne da yanke yatsan cindo (shiddaniya) da yanke linzami a cikin bakin jarirai da wasu ayyuka da dama. Haka kuma masu yin sana’ar wanzanci na bayar da magungunan gargajiya ga waɗanda suke buƙata.

    A taƙaice a iya cewa sana’ar wanzanci ta taɓo aikin likita a ƙasar Hausa kafin zuwan asibitin zamani. Dalili kuwa shi ne wani daga cikin ayyukan wanzanci shi ne kula da lafiya musamman ta jarirai da ƙananan yara, ta wani fannin ma har da lafiyar manya. Masu yin ire-iren waɗannan ayyuka ana kiran su wanzamai waɗanda dole su kasance masu cikakkiyar lafiya, masu hankali da natsuwa.

    A mafi yawanci maza ne suke yin sana’ar wanzanci, amma ana samun wasu mata waɗanda saboda rashin wani namiji a gida, ko kuma don wani dalili sukan koyi wannan sana’a daga mahaifansu. Ana gadon wannan sana’a a wajen iyaye ko kakanni na wajen uba. A gargajiyance yana da matuƙar wuya a sami wani mutum wanda bai gaji wannan sana’a ba yana yin dukkan ayyukan wanzanci.

    A wannan zamani ana samun waɗanda kan koyi yin askin zamani na saisaye wanda suke yi da kayan askin zamani, amma iyakarsu askin don kuwa ba sa iya yin sauran ayyukan wanzanci. Haka kuma wajen yin ayyukan wannan sana’a gado na taka muhimmiyar rawa, don kuwa kowane wanzami yana da gidajen da yake zuwa don gudanar da ayyukansa. Wani wanzami daban ba ya zuwa gidan da wani wanzami ɗan’uwansa yake yin aiki ya yi.

    Kowane gida ko zuri’a suna da wanzamin da suka gada wanda yake yi masu aiki, daga shi sai ‘ya’yansa ko wani da ya wakilta ne kaɗai suke iya zuwa waɗannan gidaje nasa don yin waɗannan ayyuka. Haka su ma masu gidajen ba sa kiran wani wanzami daban don yin ayyukan wanzanci a gidajensu dole sai wanda suka gada tun asali daga iyayensu.

    Wani tsari mai ban sha’awa dangane da aiwatar da sana’ar wanzanci shi ne, wanzami ba shi da iyakar ƙasar da zai riƙa gudanar da ayyukansa. Yana iya fita daga garinsu ko ƙasar dagacinsu ko hakiminsu ko sarkinsu, kai a wannan zamanin har jiharsu ya tafi wuraren da mutanensa suke domin yi masu ayyukan wanzanci.

    Misali, idan Bahaushe ya auri Bafulatana wadda ita a al’adarsu mace ba ta yin haihuwar fari a gidan mijinta, sai dai ta tafi goyon-ciki gidan mahaifanta. To, idan ta haihu ba mahaifanta ne za su kira wanzami ba, mijinta ko mahaifansa ne za su kira wanzaminsu na gida don ya yi ayyukan. Haka kuma a wannan zamani idan mutum na aikin Gwamnati a wani gari, idan matarsa ta haihu sai ya aiko garinsu don wanzaminsu na gida ya je domin yin ayyukan.

    Misali, lokacin da nake gudanar da wannan bincike, da na ziyarci Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya na sadu da Dr.Kabir Chafe wanda shi ne Shugaban Sashen Koyar da Tarihi kuma Shugaban Tsangayar Fasaha da Zamantakewa na wannan Jami’a. A lokacin da nake tattaunawa da shi ya bayyana min cewa, a duk lokacin da aka haihu gidansa nan Zariya, yana aikawa garinsu Tsafe don wanzaminsu na gida ya zo ya yi ayyukan wanzanci.

    Ni ma a halin yanzu mutanen da nake yi wa aikin wanzanci waɗanda kuma muka gaji juna waɗanda suke aikin Gwamnati a Katsina da Abuja da Kaduna da sauran wurare, idan matansu suka haihu suna aikowa don in je waɗannan garuruwa da suke don yin aikace-aikacen wanzanci.

    A wani lokaci takan kama a sauya wanzamin da aka gada. Dalilan da kan sa a yi wannan sauyi sun haɗa da sauyin wurin zama. Wato idan mai gida ya tashi daga garinsu ya koma wani gari da yake nesa da garinsu na asali, to a sabon wurin da ya sauka idan aka yi masa haihuwa, ko yana bukatar a yi wa wasu yaransa kaciya ko dai wata bukata ta aikin wanzanci a gidansa, sai ya nemi wani wanzami don ya yi masa waɗannan ayyuka. Daga wannan lokaci shi wannan wanzami ya zama na gidansa, sai kuwa idan wani dalilin ya tilasta a sauya shi.

    Haka kuma idan wanzamin gida ya rasu ko wata lalura ta rashin lafiya ta same shi, idan ba shi da mai gadonsa sai waɗanda yake yi wa aiki su sami wani wanda zai maye gurbinsa. Shi ma daga nan ya zama wanzamin waɗannan gidaje. Idan kuma rashin fahimtar juna ko wani saɓani ya shiga tsakanin wanzamin gida da mai gidan da yake yi wa aiki, misali maita ko siyasa ko aure da sauransu sukan tilasta a sauya wanzami.

    Idan ba ta waɗannan hanyoyi da aka yi bayaninsu ba, matuƙar wani wanzami ya yi shisshigi ya shiga gidajen da wani wanzami yake yin aiki ba tare da izininsa ba, ɓarna na iya shiga. Domin kuwa kowannensu zai yi ta ƙoƙarin yin ire-iren surkulle da sihirce-sihircen da ya iya domin nakasa abokin hamayyarsa ko ya lalata ayyukan da ya yi.

    Wanzaman Hausawa sun kasu zuwa rabo biyu. Akwai wanzaman gado da wanzaman ƙoƙo. Wanzaman gado su ne waɗanda suka gaji yin sana’ar wanzanci a wajen iyayensu da kakanninsu, kuma suna yin dukkan ayyukan wanzanci waɗanda suka haɗa da yin aski da kaciya da cire belun-wuya da cire angurya da bayar da magungunan gargajiya da yin tsagar gado da ta magani da ta kwalliya.

    Ire-iren waɗannan wanzamai ne suke gadon gidajen da za su riƙa yin ayyukan wanzanci. Haka kuma daga cikin irinsu ne ake naɗa Sarkin Aska ko Magajin Aska. Idan buƙatar aikinsu ta tashi a mafi yawancin lokaci a gidajensu ake zuwa don a sanar da su wuri da lokacin da ake bukatar su je don yin ayyukansu.

    Kuma a mafi yawancin lokaci ire-iren waɗannan wanzamai ba su da rainuwa domin kuwa duk abin da aka ba su a matsayin ladar aikinsu, sai su karɓa suna masu yin murna da godiya. An bayyana cewa dalilin haka shi ne suna yin waɗannan ayyuka ne don gado ba don ladar da ake biyan su ba.

    Su kuma wanzaman ƙoƙo ba sa yin dukkan ayyukan wanzanci, iyakar ayyukan da suke yi sun haɗa da aski da gyaran fuska. Wanzaman ƙoƙo barorin wanzaman gado ne. A wani lokaci irinsu na yin ƙaho, kuma irinsu ne suke yawo da zabira rataye a kasuwanni da cikin garuruwa suna neman wanda za su yi wa aski ko gyaran fuska ko ƙaho.

    Haka kuma ire-iren waɗannan wanzamai ne suke yin rumfuna a kasuwanni da shaguna a cikin garuruwa domin yi wa mabuƙata aski da gyaran fuska. Idan suka yi wa mutum ayyukansu suna gaya masa adadin kuɗin da zai biya ba kamar wanzaman gado ba. Hausawa na yi wa ire-iren waɗannan wanzamai kirari kamar haka:

    Wanzaman ƙoƙo a ci tuwo a yi aski,

                                     Cire belun-wuya da belun-mata sai ‘yan gado”.

    Ba a tsakanin Hausawa kaɗai ake yin sana’ar wanzanci ba, akwai al’ummomi da ƙabilu masu yawa waɗanda ake yi masu ire-iren ayyukan wanzanci. Wasu ana yi masu dukkan ayyukan ne, wasu kuwa ana yi masu waɗansu ne daga cikin ayyukan kawai.

    Wannan dalili ne ya sa kowace al’umma ko ƙabila tana da sunan da take kiran wanzami ko mai yin ayyuka irin na wanzanci. Misali, Larabawa suna kiran wanzami da sunan al-Hallaƙ. Fulanin da suke zaune a ƙasar Hausa suna kiran sa da sunan wanzamijo, su kuma Fulanin da suke zaune a gabacin ƙasar Hausa a Yola da Gwambe suna kiran sa da sunan wanjam ko wanjamjo.

    Turawan Ingilishi suna kiran sa da sunan barber, su kuma na Faranshi suna kiran sa da sunan coiffure ko coifere. Barebari suna kiran wanzami da sunan diyeji ko wanzama, shugaban wanzamai kuma suna kiran sa da sunan Zanna Ɗambusuma. Buzaye kuma suna kiran wanzami da sunan aghachaou, su kuma Adarawa na kiran sa da sunan wanzami. Su kuma Yarabawa na kiran wanzami da sunan bonjamo, wanda yake yin aski kawai kuma suna kiran sa da sunan fari-fari ko akola. ’Yan ƙabilar Ekoi waɗanda suke zaune a Jihar Cross Riɓer suna kiran wanzami da sunan anu-uka.

    Nufawa kuma suna kiran sa da sunan gozan. Su kuwa ‘yan ƙabilar Ibo suna kiran mai yin aski da sunan okpa-isi, wanda yake yin kaciyar maza kuwa suna kiran sa obe-ugwu, wanda yake yin tsagen gargajiya kuma suna kiran sa da sunan ogbu-ichi. Dakarkari waɗanda suke zaune a ƙasar Zuru da kewaye a Jihar Kabi na kiran wanzami da sunan sah’pana ko u’oro.

    Idan muka ƙetara a ƙasashen da suke Afrika ta Gabas za mu ga akwai wasu ƙabilun waɗannan ƙasashe waɗanda suke aiwatar da ire-iren ayyukan wanzanci da ake yi a ƙasar Hausa kamar yadda Hausawa suke yi. Wasu daga cikin al’ummomin waɗannan ƙasashe na cire belun-wuya da belun-mata da yin askin suna ga jarirai da dai sauran ayyuka irin waɗanda wanzaman Hausawa suke yi.

    An ce kamar yadda wanzaman Hausawa suka gaji yin wannan sana’a, al’ummomin waɗannan ƙasashe masu yin waɗannan ayyuka suna yin gado ne a wurin mahaifansu. Akwai waɗanda suke koyon yin waɗannan ayyuka bayan sun girma, ire-irensu suna bayyana cewa iskoki ne suka sanar da su hikimomin yin waɗannan ayyuka (Hira da JMT da PMT da KMK da AGU a ranar 20/12/2004 da MEHT a ranar 22/12/2004). A Uganda ƙabilun Sabiny da Kapchori, a Kenya kuwa ‘yan ƙabilar Kisii, a Tanzania kuma ‘yan ƙabilar Wakurya ne suke yin ire-iren ayyukan wanzanci na Hausawa.

    A gabacin Afrika ana amfani da harshen Swahili a matsayin harshen ƙasa a ƙasashen Uganda da Kenya da Tanzania don yin hulɗoɗin gwamnati da harkokin yau da kullum a tsakanin al’ummomin waɗannan ƙasashe. A saboda haka akwai sunayen da ake kiran wanzami ko mai yin ayyuka irin na wanzami a waɗannan ƙasashe. Misali, ana kiran mai cire belun-wuya da sunan kukata-kilimi, mai yin aski kuma kinyozi.

    Shi kuma mai yin kaciyar maza ana kiran sa da sunan tohara ya wanaume, mai yin kaciyar mata kuwa tahora ya wanawake ko ngariba. Shi kuma mai yin tsagar gado ana kiran sa da sunan ndonya ko makonde, mai yin tsagar kwalliya kuwa alama za nyuso (Hira da AGU, a ranar 20/12/2004 da kuma MEHT], a ranar 22/12.2004).

    Bayan waɗannan sana’o’i waɗanda mafi yawancinsu maza ne suke aiwatar da su, akwai waɗanda mata ne kawai suke yin su kamar kaɗi wanda ake yi don samar da zare da abawa ga masana’antar saƙa. Haka kuma mata ne suke yin sana’ar kitso ga ‘yan uwansu mata. Suna yin salon kitso iri-iri don yin kwalliya ga kan mata wanda suke ƙara masu kyau da jawo hankalin maza.

    Akwai kuma sana’ar tauri ko koda wadda mata suke amso hatsi don yin dakau na fura ko garin da za a yi amfani da shi don yin abinci. Waɗannan sana’o’i waɗanda mata suke yi suna taimaka wa matan yin hidimominsu na yau da kullum da kuma yin bikin dangi ba tare da sun dogara da wani ba.

    Shigowar baƙi ƙasar Hausa wato Larabawa da Turawa sun taimaka wa tattalin arzikin ƙasar Hausa ya ƙara bunƙasa.Wannan kuwa ya faru ne ta yadda aka sami shigowar wasu sababbin sana’o’i waɗanda wasun su ci gaba ne ga waɗanda Hausawa suke yi kafin zuwan waɗannan baƙi.

    Ire-iren waɗannan sana’o’i sun haɗa da ta makanikanci don yin gyaran kekuna da babura da motoci da rediyo da rikoda da talabijin da kwamfyuta da wayar hannu da dai sauransu. Akwai kuma masana’antar kafinta wadda ci gaba ce ga sana’ar sassaƙa ta gargajiya. Kafintoci na sassaƙa kujerin zama na zamani da tebura da tagogi da ƙofofin ɗaki da yin rufin ɗaki wanda ake amfani da katako da kwanon rufi da dai sauran ayyuka don a ƙara sauƙaƙa rayuwar yau da kulllum.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Addinin Mutanen Ƙasar Hausa

    Addinin Mutanen Ƙasar Hausa

    Hanyar bauta wa wani abu wanda mutum yake tsammanin shi ne zai biya masa bukatun rayuwar yau da kullum shi ne addini. Addinin farko na mutanen ƙasar Hausa shi ne addinin gargajiya, wato tsafi ta hanyar bautar iskoki ko mutanen ɓoye da kuma bori da camfi.

    Irin wannan addini ya faru ne ta bin wasu hanyoyi da mutane suka ƙaga wa kansu ta bautar waɗansu abubuwa don cimma biyan buƙatunsu na rayuwa. Wannan hanyar bauta ta daɗe ƙwarai a dukkan sassan duniya ba ƙasar Hausa kawai ba. Mutanen da suka fara zama a duniya ne suka ƙirƙiro ta, daga nan sai abin ya zama al’ada ga sauran ƙabilun da suke biye da su har ya zo ga Hausawa.

    A sakamakon shigowar addini Musulunci cikin ƙasar Hausa da kuma karɓar sa da mafi yawancin Hausawa suka yi, irin wannan addini ya sami rauni. Amma duk da haka ba a bar yin wasu abubuwa waɗanda suka danganci addinin gargajiya na Hausawa ba. Don kuwa za a ga yana yin tasiri a kan wasu al’amuran da suka shafi rayuwar wasu Hausawa ta yau da kullum.

    Idan muka waiwaya muka duba yadda al’ummar Hausawa suka gudanar da addininsu na gargajiya, za mu ga ba wai suna sassaƙa wani gunki ne suna bauta masa ba, a a, suna yin bautarsu ne ta hanyar yin tsafi. Bauta ta hanyar tsafi tana nufin bauta wa wani iska da aka ɗauka yana zaune a wani wuri na daban. Ire-iren wuraren da aka ɗauka iskoki suna zama sun haɗa da wata kwankwamar dutsi ko cikin wata sarƙaƙƙiya ko wurin wata tsohuwar bishiya, irinsu kuka da tsamiya da marke da dai sauransu.

    Misali, a Kano an bauta wa iska Tsumburbura wanda aka ɗauka ya zauna a Dutsen Dala, Kainafara-Arnan Birchi suna bauta wa iska Ɗantalle wanda suka ce yana zaune a cikin Dutsin Birchi. Arnan Kwatarkwashi kuma suna bauta wa Ƙunƙurutu wanda suka ɗauka yana cikin Dutsin Kwatarkwashi, arnan Sauna kuma suna bautar Magiro.

    Haka kuma a duwatsun Kufena ta Zariya mazaunan farko a wannan wuri sun ɗauka akwai wasu iskoki da suke zaune a wannan wuri. Saboda suna biya masu buƙatunsu shi ya sa suke bauta masu. A ƙasar Katsina ma akwai wasu arna da suke bautar Magiro a Safana da Ɗan-musa da Ƙanƙara da Dutsin-ma wanda suka ce yana zama a wurin tsamiya mai sarƙaƙƙiya da duhu, kuma ba mai iya zuwa wurin da yake sai masu yi masa hidima

    Bayan addinin gargajiya sai addinin Musulunci wanda addini ne da Allah Maɗaukakin Sarki ya aiko ta hannun Annabi Muhammadu (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi) don ya zama hanyar shiriya ga al’ummomin duniya, ya kuma zama hanya madaidaiciya a gare su. Wannan kuwa ya faru ne a cikin shekara ta 610 Miladiyya.

    Addinin Musulunci ne ya biyo bayan addinin Kirista wanda Allah Maɗaukakin Sarki ya aiko ta hannun Annabi Isa, Allah ya ƙara yarda da shi. An sami shekaru ɗari shida a tsakanin waɗannan addinai (Ibrahim, 1982:63 da Gusau, 2005:18-19). Ba kamar sauran addinan da suka gabace shi ba, addinin Musulunci an aiko da shi zuwa ga dukkan al’ummomin duniya don ya zama hanyar shiriya ga kowa.

    Annabi Muhammadu (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi) ya fara da kiran ‘yan’uwansa zuri’ar Banu Hashim don su karɓi wannan addini. Wasu suka karɓa wasu kuwa suka ƙi. Sannu a hankali yana wa’azi shi da waɗanda suka fara ba shi goyon baya, cikin ɗan ƙanƙanin lokaci sai da dukkan ƙasashen Larabawa suka amshi addinin Musulunci.

    Wannan ne ya sa aka kafa Ƙungiyar Al’ummar Musulmi wadda take da cibiya a Birnin Madina, Annabi shi ne shugaban wannan al’umma. Dukkan abin da zai zartar, sai ya yi shawara da sahabbansa. Wajen tafiyar da wannan al’umma ba a nuna ƙabilanci ko fifiko a tsakanin jama’ar da suke cikinta. Abin da ta sa gaba shi ne haɗin kai da son juna da nuna ‘yan’uwantaka a tsakanin Musulmi. Babban tsarin mulkin wannan al’umma shi ne shari’ar Musulunci. Kafin Annabi ya yi ƙaura, ya bar wa al’ummar Musulmi Alƙur’ani mai tsarki da kuma Hadisai don su yi masu jagora dangane da addininsu (Ibrahim, 1982:63).

    Manyan shika – shikan addinin Musulunci biyar ne:

    • Shaidawa ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma Annabi Muhammadu (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi) bawansa ne kuma manzonsa ne.
    • Tsayar da salla.
    • Bayar da zakka.
    • Yin azumin watan Ramalana.
    • Ziyartar ɗakin Allah don yin aikin Hajji ga wanda ya sami iko.

    Bayan ƙaurar Annabi Muhammadu (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi) da kuma zaɓaɓɓun halifofi huɗu da suka biyo bayansa. An sami wasu daga cikin sahabbai da wasu malamai da suka biyo bayansu, sun kawo hanyoyin da suke ganin ya dace a riƙa yin aikace-aikacen addini don samun sakamako mai kyau a duniya da lahira. Wannan ne ya sa aka sami ɗariƙu da ƙungiyoyin addini mabambanta masu yawa waɗanda suke da magoya baya a ko’ina.

    Daga cikin ire-iren waɗannan ɗariƙu akwai Ƙadiriyya da Tijjaniyya da dai sauransu da dama. Haka kuma akwai ƙungiyoyin addini waɗanda suka haɗa da Ƙungiyar Jama’atu Izalatul Bid’a wa Iƙamatus Sunna wato Ƙungiyar Kawar da Bidi’a da Tsayar da Sunna. Akwai kuma Ƙungiyar ‘Yan’uwa Musulmi (Shi’a). Waɗannan ɗariƙu na Ƙadiriyya da Tijjaniya suna da magoya baya sosai a cikin ƙasar Hausa. Haka su ma waɗannan ƙungiyoyi suna da nasu magoya baya a sassa daban-daban na ƙasar Hausa (Ibrahim, 1982:98-99, ‘Yanɗaki, 1997:46-50 da Suleman, 1997: 58-59).

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Farfajiyar Ƙasar Hausa Jiya Da Yau

    Farfajiyar Ƙasar Hausa Jiya Da Yau

    Wannan babi yana ƙunshe da bayanan da suka danganci farfajiyar ƙasar Hausa a jiya da yau. An kuma duba yanaye-yanayen ƙasar Hausa dangane da mutanenta da halin zamantakewa da shugabanci da addininsu da kuma hanyoyin tattalin arzikinsu. Daga nan sai aka yi bayani kan ƙaura da shigowar baƙi ƙasar Hausa da matsayin Hausawa a yau.

    Farfajiyar Ƙasar Hausa Jiya da Yau

    Yana da matuƙar mahimmanci kafin mu baje kolin wannan nazari mu yi waiwaye domin sanin wurin da ƙasar Hausa take a jiya da kuma a yau. Ƙasar Hausa ta asali tana a Afrika ta Yamma ne, a farfajiyar da take tsakanin hamadar Sahara da dazuzzukan da suka doshi gaɓar tekun Atlantika daga kudu. Kuma ana kiran ƙasar da sunan Sudan ta Yamma, wato tsakanin Tafkin Chadi da gwiwar Kogin Kwara a can Yamma (Alhassan, 1982:1).

    A wata faɗar kuma an bayyana cewa ƙasar Hausa tana shimfiɗe ne a can Arewacin Nijeriya da kuma kudancin Jamhuriyar Nijar cikin Afrika ta Yamma. Daga Gabas ta yi iyaka da ƙasashen Borno. Daga Yamma ta yi iyaka da ƙasashen Dahomey a gaɓar Kogin Kwara. Daga Arewa ta yi iyaka da ƙasar Adar a cikin Jamhuriyar Nijar. Daga wajen Kudu kuma ta yi iyaka da ƙabilun Gwari da kuma ƙabilun kudancin Zariya da na Kudancin Bauchi (Ibrahim, 1982:1).

    Ƙasar Hausa wadda tana shimfiɗe a shiyyar Sudan ta tsakiya, a tsari irin na gargajiya a iya cewa ta haɗa da ƙasashen sarakunan Katsina da Kano da Daura da Zazzau (idan aka ɗebe kudancin Zazzau) da Argungu da Gwandu da Gumel da Haɗejiya da Ƙwanni da Maraɗi da Tassawa.

    Ni kuma a nawa hasashen ina ganin a yau, ƙasar Hausa yanki ne wanda ya mamaye dukkan Jihohin Katsina da Kano da Zamfara da Sakkwato da Arewacin Jihar Kaduna da wasu ɓangarori na Jihohin Kabi da Bauchi da Gwambe da Neja da kuma kudancin Jamhuriyar Nijar.

    Yanaye-Yanayen Ƙasar Hausa

    Mafi yawancin sassan ƙasar Hausa yana shimfiɗe ne kuma yana da yawan sarari, amma duk da haka akwai tsaunuka da tuddai a wasu wurare kamar Dutsin Dala da na Gwauron Dutse a Kano da Dutsin Dutsin-ma a jihar Katsina da Dutsin Kwatarkwashi a jihar Zamafara da Duwatsun Kufena a Zariya da sauransu.

    Akwai ‘yan dazuzzuka waɗanda suka haɗa da dajin Rugu wanda ya ratsa jihohin Katsina da Zamfara da dajin Falgore wanda ya ratsa jihar Kano da wani ɓangare na lardin Zazzau a jihar Kaduna. Yanayin dajin da yake a ƙasar Hausa iri biyu ne, da wanda ake kira “Sahel”, wato irin dajin da ake samu a arewa, da kuma dajin “Savanna” wanda ake samu a kudancin ƙasar.

    Akwai ƙarancin itatuwa a dajin “Sahel” kuma mafi yawancinsu gajeru ne. A lokacin rani da yawa daga cikin ganyayen da suke wannan daji sukan kakkaɓe, idan kuma damina ta kusa zuwa sai su fara tohuwa. Ciyawar da ake samu a wannan daji dabbobi kan cinye rabi su tattake rabin, amma da an yi ruwan tohon geza duk sai ta tsiro a ko’ina. Wuraren da wannan daji ya mamaye sun haɗa da dukkan kudancin Jamhuriyar Nijar da arewacin ƙasar Hausa a sassan jihohin Katsina da Kano da Jigawa da Zamfara da Sakkwato da Kabi.

    Daga dajin “Sahel” idan aka yi kudu kaɗan sai dajin “Savanna”. A irin wannan daji, itatuwa sun fi tsawo da kusanci da juna, haka kuma ana samun ganyaye da ciyayi da suke shekara cikin ɗanyantakarsu wato kore. Ana samun yanayin irin wannan daji a kudancin jihar Katsina da Lardin Zazzau a jihar Kaduna da Lardin Kabi da Yawuri a jihar Kabi da Kwantagora a jihar Neja (Alhassan, 1982:2-3).

    Duk faɗin ƙasar Hausa manyan koguna biyu ne suka ratsa ta cikinta da kogin Rima da kogin Haɗejiya. Kogin Rima shi ne ya taso daga ƙasar Zamfara ya malala ya yi Arewa zuwa cikin Jamhuriyar Nijar, daga nan sai ya karkata kudu ya bi ta yammacin Sakkwato ya je ya faɗa cikin kogin Kwara. Kogin Haɗejiya kuwa ya fara daga ƙasar Kano ya gangara ya yi gabas, ya bi ta Jama’are a jihar Bauchi, ya bi ta Gashuwa da Gaidam a jihar Yobe ya faɗa tabkin Chadi (Alhassan; 1981:3).

    Ta fuskar yanayin shekara ƙasar Hausa tana da yanayi iri biyu, lokacin damina da lokacin rani. Ana samun ruwan sama a lokacin damina wanda yakan fara daga watan bakwai na Hausa (Mayu) zuwa watan sha ɗaya na Hausa (Oktoba), kuma ruwan da ake samu ba mai yawa ne ƙwarai ba, amma duk da haka yana da albarka da biyan buƙatun manoma. Shi kuma lokacin rani yana farawa daga watan goma sha biyu na Hausa (Nuwamba) zuwa watan shida na Hausa (Afrilu), ya kuma rabu biyu wato lokacin ɗari da lokacin zafi ko bazara.

    Mutanen Ƙasar Hausa

    Mutanen ƙasar Hausa su ne ake kira Hausawa waɗanda masana da manazarta daban-daban suka kawo ra’ayoyinsu kan waɗanda suke ganin cewa su ne Hausawa. A ra’ayin wani masani ya bayyana cewa Hausawa su ne mutanen da suke zaune a ƙasar Hausa tun tuni, kuma suna magana da harshen Hausa a matsayin harshen uwa (Ibrahim, 1982:1)

    Wani masanin kuma yana ganin, Hausawa sun haɗa da mutanen nan waɗanda saboda ƙaura da magabatansu suka yi daga ƙasar Hausa zuwa wasu sassa da ke maƙwabtaka ta kusa ko ta nesa da ƙasar Hausa, ko da kuwa ba sa magana da harshen Hausa ko yin al’adun Hausawa sun ɗauka su Hausawa ne. Misali, Abakwariga da suke zaune a Jihar Taraba ta Nijeriya da kuma wasu da suke iƙirarin su Hausawa ne waɗanda suke zaune a ƙasashen Cote de Voire da Burkina Faso da Mali (Adamu, 1974:3).

    Akwai kuma waɗanda saboda ƙaura da magabatansu suka yi zuwa ƙasar Hausa sun manta da harshensu da adabinsu da al’adunsu na asali sun ɗauki na Hausawa. A taƙaice sun koma Hausawa a harshe da adabi da al’ada. Misalin ire-iren waɗannan mutane sun haɗa da Barebari da Kambarin Barebari da Barebarin Katsina da Buzaye da wasu Fulani (Adamu, 1974:4).

    Wani masanin kuma ya bayyana cewa Hausawa dai su ne mutane waɗanda harshensu shi ne Hausa, sannan dukkan al’adunsu da tadodinsu na Hausa. Haka kuma addinin Musulunci ya yi cikakken tasiri a kansu (Magaji, 1986:3).

    Mutanen ƙasar Hausa suna tafiyar da hanyoyin zamantakewarsu da shugabancinsu da addininsu da tattalin arzikinsu don cimma burin rayuwarsu na yau da kullum daidai da yanaye-yanayen ƙasarsu. Wannan ne ya ƙara taimaka masu suka kai ga matsayin da suke a yanzu, ya kuma ƙara taimakawa wajen shigowar baƙi wannan ƙasa.

    Danna don karanta Sana’ar Wanzanci Da Sauye-sauyen Zamani Jiya Da Yau (Shimfiɗa) 

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Adabin Kasuwa A Ƙasar Hausa

    Adabin Kasuwa A Ƙasar Hausa

    A wannan babin an yi ƙoƙarin bin yadda aka samar da adabin kasuwa a ƙasar Hausa. Abin nufi, bayan ganin yadda fasalin adabin kasuwa ya kasance a sassan duniya daban-daban, da kuma ganin irin yadda ya samu ga maƙwabtanmu, Inyamurai, sai kuma mu gangaro domin ganin yadda ya samu a ƙasar Hausa.

    Don haka, a wannan babin an dubi irin zangunan da Adabin Kasuwar Kano ya shiga a ƙasar Hausa, da kuma irin rawar da ya taka wajen ginuwar wani ɓangare na ƙagaggun labaran Hausa.

    Samuwar Adabin Kasuwar Kano

    Daga abubuwan da aka gani a babin da ya gabata ke nan ba abin mamaki ba ne idan aka ci karo da Adabin Kasuwa a Amurka ko Turai ko Rasha ko cikin ƙasashen Asiya ko Larabawa, kai ko ma ina ne a cikin duniya.

    Hakan na faruwa ne ganin cewa ai ba ƙasashen Turawa ko waɗanda suka ci gaba ne ke da damar su samar da adabin kasuwa su kaɗai ba, haka kuma ba dole sai harshen Ingilishi ko wani harshen da ya sami ci gaba kaɗai ne zai iya samar da shi ba; kowace ƙasa, kuma kowane irin harshe zai iya samun adabin kasuwa a cikin wani zangon rayuwar adabin. Domin inganta bincike, ya dace mu bi salsala, mu ga yadda aka samar da abin da yawanci ake kira Adabin Kasuwar Kano tsakanin Hausawa.

    Rayuwar Farko : 1984-1989

    Abin da aka daɗe ana kira Adabin Kasuwar Kano ya samo asali ne a farkon shekarun 1980, kuma wannan shekaru a ƙasar Hausa ko Arewacin Nijeriya baki ɗaya, shekaru ne masu tarihi a ɓangaren samuwar ilmin boko da rubutu.

    A daidai wannan zangon rayuwa ne ɗaliban UPE, shirin gwamnatin tarayya da aka soma daga 1976 domin ba kowane yaro damar samun ilimin furamare kyauta, suka fara shiga kasuwar rubutu da karatu da rububin abubuwan karantawa, domin ɗaliban farko na wannan shiri sun baro firamare a shekarar 1982, daga wannan lokaci har zuwa 1984, an yaye ɗalibai har kashi huɗu. Saboda haka an samar da sababbin makaranta da suke buƙatar abin karantawa.

    Haka wannan zango ya zo daidai da lokacin da babban kamfanin wallafa da ɗab’i a ƙasar Hausa wato NNPC ya soma shiga tasku, ya soma sukurkucewa da neman durƙushewa. A daidai wannan lokaci kamfanin NNPC ya daina buga littattafan hira da nishaɗi, bayan kuma ga dubban matasa da aka yaye daga shirin na UPE sun antayo cike da  shauƙin irin waɗannan littattafai da babu su.

    Wannan shiri na UPE, duk da cewa bai zaunu da gindinsa ba, amma ya samar da sababbin makaranta a farkon shekarun 1980. Kuma a daidai wannan lokaci sai ga shi tattalin arziƙin Nijeriya ya ƙara inganta, saboda gano man fetur da aka yi, ya ƙara wa ƙasar hanyar samun kuɗaɗen shiga masu yawa.

    Bincike kuma ya nuna cewa duk lokacin da irin wannan harka ta kasance haka, wato ga masu ilmi gwargwado, sa’annan ga ‘yan kuɗi a hannun jama’a, kamar yadda muka gani a fasalin Adabin Kasuwar Kitsch na Jamus, sai ka ga hanyoyin samar da adabi, mai kyau ko maras kyau, suna wadatuwa.

    Da yake tun can azal akwai kayayyakin rubutu da ɗab’i gwargwado a ƙasar Hausa, sai ya ba matasa damar da suka tsunduma cikin wannan harka ta wallafa littattafai ba ji ba gani, kamar yadda Furniss (2001) ya yi nuni. Sai dai ko kafin shekarar 1984 da littafin Rabin Raina na Talatu Wada Ahmed ya fito kasuwa akwai ɓirɓishin rubuce-rubuce na soyayya a ƙasar Hausa.

    Idan ba a manta ba a shekarar 1978 kamfanin NNPC ya shirya gasa da ta samar da littattafai a shekarar 1980, kamar su Mallakin Zuciyata na Sulaiman Ibrahim Katsina da So Aljannar Duniya na Hafsat Abdulwaheed da kuma Amadi na Malam Amah na Magaji Ɗambatta, (Haruna, 2009).

    Sai dai abin lura shi ne waɗannan littatafai daga gasa suka fito, wato sai da aka yi shiri da tsari, haka kuma na hukuma ko kamfani ne, don haka sun biyo tsari da ingancin da ya bambanta su da adabin kasuwa. Ke nan za a iya cewa waɗannan littatafai na gasar 1978 sun dai nuna hanya ne na irin adabin da zai iya biyo bayansu, ba su ne farkon adabin na kasuwa a ƙasar Hausa ba.

    A ɗaya ɓangaren kuma an danganta littafin Rabin Raina na Talatu Wada Ahmed da tushe ko tubalin samuwar adabin kasuwa a ƙasar Hausa saboda yanayin da ya samu da kuma yadda ya shiga kasuwa. Shi ma ba wai zama aka yi domin assasa wannan fage na adabin kasuwa ba tattare da shi ba.

    Kamar yadda a karo na farko wadda aka danganta aikinta da Adabin Kasuwar Kano, Talatu ta bayyana wa Mujallar Garkuwa (2000) yadda ta samar da littafin, ta ce ita ba ta san da wani abu wai shi adabin kasuwa ba lokacin da take rubuta littafinta. Ta ƙara da cewa ta dai rubuta shi ne a lokacin tana makarantar WTC Katsina, tana aji uku, wato wajajen shekarar 1980.

    Ta kuma rubuta shi ne daga gyauron labaran da take ba ‘yan uwanta ɗalibai lokacin suna makaranta can da dare kafin su yi barci. Bayan ta gama sakandire ne ta fitar da shi ta hanyar aika shi gidan rediyon tarayya Kaduna domin a karanta a shirin Shafa Labari Shuni, amma aka daɗe ba a karanta shi ba, daga baya ta miƙa wa wani kamfanin bakin hanya da ake kira Ogwu a Kaduna domin ya buga mata shi.

    Kamfanin Ogwu ya buga, ya kuma shiga sayar da littafin da ya ga mutane sun dami suna son su karanta. A lokacin da Kamfanin Ogwu ya shiga sayar da littafin, ita Talatu tana Kwalejin Ilmi ta Kafanchan wajen ƙaro ilmi, a can ne wata ƙawarta ta zo da littafin, tana yi mata bayanin yadda littafin ya yi kasuwa, ita ba ta ma sani ba. Wannan daɗin abin da ya faru ya sa ta koma gida ta ji abin da ya auku.

    Mahaifiyar Talatu ta ba ta kuɗin da aka samu, ta yi murna ƙwarai da ganin arzikin da wannan littafi ya jawo mata. Daga wannan lokaci ne ta shiga sake buga littafin, ana watsawa a cikin ƙasar Hausa, ta yadda abin ya dinga ba ta mamaki na ganin cewa mutane, musamman masu sayar da littatafai daga ko ina a faɗin ƙasar Hausa ke kira ko yo saƙon don Allah ta aika masu da kwafe 500 ko dubu ko dubu biyu ko ma fiye.

    Fitar wannan littafi da yanayin da ya samu kan sa lokacin bugu da sayarwa da kuma hanyoyin da aka bi aka samar da shi ya nuna wa sauran marubuta cewa ashe akwai wata hanyar rubutu da wallafa littattafai ba dole sai ta bin kamfanonin bugu da wallafa na gwamnati ba.

    Saboda haka daga samuwar wannan littafi na Rabin Raina a shekarar 1984 za mu iya cewa akalar adabin hira ko ƙagaggen labari ta soma sauyawa, kuma a iya cewa daga wannan lokacin ne Adabin Kasuwar Kano ya fara ginuwa. Sai dai abin da ke da muhimmanci a nan shi ne ba wai zama aka yi ba domin a tsara da gina wannan fasali na Adabin Kasuwar ta Kano ba, abu ne da ya kasance caccakuɗe, kuma tattare da abubuwa mabambanta da suka haɗa da :

    • Tun da farko dai akwai matsalar abubuwan karantawa a makarantu da kuma tsakanin sababbin makaranta kamar yadda muka yi bayani.
    • Ga halin da kamfanin NNPC ya shiga daga farkon shekarun 1980 da rashin buga littatafan hira.
    • Ga kuma ɗaruruwan ‘yan makaranta da waɗanda suka kammala makarantun, sun kuma rubuta littattafai masu yawa, ba wurin buga su, balle a san da su.
    • Shirin gidan Rediyon Tarayya Kaduna na Shafa Labari Shuni da wasu da dama a gidajen rediyon jihar Kano da Katsina da Sokoto da wasu wurare da dama ya taimaka wajen fito da waɗansu daga cikin marubutan da ke ɓoye.
    • Bugun littafin Talatu na bakin kasuwa da yadda ya sami karɓuwa ya sanya wasu, ƙila suka ce su ma bari su gwada bugawa da sayarwa.

    Saboda haka littattafan da ake ta yayatawa a halin yanzu a matsayin waɗanda suka biyo bayan littafin Talatu daga 1984, ba wai shawara suka yi da juna ba, kuma ba su san wani na yin irin wannan aiki ba, kamar yadda bincike ya nuna a halin yanzu. Ke nan jawabin da Malumfashi, (1994) ko wanda Adamu, (1996) da Adamu (2000) suka yi na lissafa littatafan da suka biyo na Talatu kamar haka ba daidai ba ne, sai dai daga littafin Talatu na Rabin Raina sai:

    • Ibrahim Hamza Abdullahi da Soyayya Gamon Jini a 1986.
    • Idris S. Imam da In Da Rai a 1987.
    • Balaraba Ramat da Budurwar Zuciya a 1987.
    • A.M Zaharadden da Kogin Soyayya a 1988.
    • Idan so cuta ne, na Yusuf M. Adamu a 1989.

    An yi wannan hasashe bisa hujjar da ta nuna cewa babu wani bincike da ya tabbatar da jeruwa da daidaituwar wannan tsari ko kuma wani bayani da ya ce an tattauna tsakanin waɗannan mutane na biyo sahun Talatu Wada.

    Bari mu yi nazarin batun da kyau, tun da farko dai garuruwan marubutan daban-daban suke, Talatu na Kaduna, Ibrahim Hamza na Kano, Idris S. Imam kuwa tun 1984 aka buga littafin nasa ba wai a 1987, Balaraba kuwa ko kafin ta shigar da littafinta na Budurwar Zuciya a layin adabin kasuwa ta fuskar shiga ƙungiyar Raina Kama, an riga an buga littafin a Zaria,(Gaskiya Corporation a 1984).

    Haka shi ma Zaharradeen a Kano yake, shi kuwa Yusuf Adamu yana ɗalibta a Sakkwato ne ya shigo da nasa littafin. Haka kuma daga binciken da aka gudanar an fahimci cewa ko kafin Ibrahim Hamza Abdullahi da littafinsa na Soyayya Gamon Jini a 1986, an samar da Hannunka Mai Sanda I na Ƙamarradeeen Imam a 1985, me ya sa ba a shigar da shi cikin layin na farko ba? Haka kuma a tsakanin 1984 da aka samar da littafin Talatu, ba wai littattafai huɗu ne kurum suka yi tashe ba, guda 13 ne.

    Ke nan ba wata ƙungiya ba ce ko kuma wani taro aka yi ba aka ce a samar da wannan abu da aka kira Adabin Kasuwar Kano daga baya. Shi kuma Malumfashi (1994) da ya kira shi da wannan suna, ya yi haka ne daga abin da ya gani masu kama da juna tsakanin littattafan da irin waɗanda aka samar a Onisha kamar yadda ya bayyana daga baya, (Malumfashi, 2004).

    Kamar yadda muka gani can baya, rayuwar adabi takan shiga cikin wani sauyi ne na wani lokaci, daga baya kuma ta kasance cikin wani tsari na daban, irin wannan shi ne ya faru da abin da aka kira Adabin Kasuwar Kano yanzu. Sai dai wani abu da za a yi la’akari da shi, shi ne, yawancin matasan da suka yi tashe a wancan lokaci a wannan fage ba su yi amfani da kamfanonin ɗab`i da ake da su don bayyanar da ayyukansu na adabi ga jama’a ba, ba don komi ba kuwa sai don ba wani kamfani da ya damu ya buga ire-iren waɗannan littattafai.

    Ba kuma wai don ba su da kasuwa ko kuma ba su sami karɓuwa ba a tsakanin al`umma ba, a a, a tsakanin shekarun 1978-1982 ba abin da ya fi tashe da karɓuwa irin labaran da wasu suke rubutawa, suna aika wa gidajen rediyoyi daban-daban ana karantawa. Ba wani abu ya jawo hakan ba sai ganin litattafan da aka samar daga gasar da aka shirya a 1978 da suka samar da litattafan soyayya na farko da za a iya kira `yan zamani, sun yi tasiri ga rayuwar irin waɗannan matasa.

    Sai dai da alama amfani da aka yi da kafar rediyo, wadda ta sanya ƙagaggun labarai irin waɗannan suka sami martaba, ba wai kawai tsakanin waɗanda suka yi boko ba kurum, har ga waɗanda aikinsu shi ne sauraron rediyo, ba su iya karatun ba.

    Bisa wannan tafarkin aka shiga samar da sababbin marubuta, wasu ta hanyar kwaikwayon abin da aka rubuta, suka aika gidajen rediyoyin, wasu kuma ta sake wa tatsunniyoyi da labaran Hausa fasali, wasu ko ta kwaikwayo ko ɗaukar fasalin wasu labaran Ingilishi ko fassara kai-tsaye ko kuma naɗe fina-finan Indiya da na Turawa zuwa takarda.

    Cikin ɗan lokaci ƙanƙani sai ga kabod-kabod na gidajen rediyoyin nan sun cika maƙil, wasu ma suka shiga ƙonawa, wanda ya sa masu rubutun suka shiga guna-guni idan ba a karanta nasu labaran ba. Sai dai kuma waɗanda Allah ya tarfa wa garinsu nono daga cikin waɗanda aka karanta nasu a gidajen rediyoyin, sai ga shi sun fara samun suna da ɗaukaka.

    Wannan ya jawo wasiƙu suka shiga gilmawa zuwa gare su, ana yaba masu, ta haka kuma aka ga cewa ga wata kafa ta samu ta kashe waccan ƙishirwa ta rashin labaran Hausa da ta addabi matasa, ta yadda a tsakanin shekarar 1984 zuwa 1998 marubuta da sababbin littatafai suka baje kasuwarsu a ƙasar Hausa.

    Idan aka yi nazari sosai za a ga ko da Talatu ta bayyana a 1984 a Kaduna, ba a Kadunar ta tsaya ba, domin littattafan sun baje duk faɗin ƙasar Hausa, musamman a Kano da suka dasa rayuwarsu. A Kanon akwai irin littafin Talatu Wada da ya riga ya shiga kasuwa shi ma kafin ma bayyanar na Talatu, wato Wasiyar Baba Kere na Ibrahim Sale Gumel, a kuma wannan shekara ta 1984, an sami ɗan uwan na Talatu, wato In Da Rai Da Rabo na Idris S. Imam.

    Saboda haka ko da Ƙamarradeen ya shigo da nasa littafin a 1985, ba dole ba ne ya san da abin da Talatu ta yi ko kuma sauran da suka riga nata shiga kasuwa; musamman ganin cewa ɗa ne ga marigayi Abubakar Imam, kuma yana aiki da kamfanin Huda-Huda da ke Zaria, waɗanda su ne mawallafansa.

    Yadda Kano ta shigo cikin harkar da litatattafan da ‘yan Kanon suka samar bai rasa nasaba da suna da tashe da littafin Talatu da na Idris da Ibrahim suka yi a kasuwar Kanon. Littattafai goma sha uku ne suka wanzu a wannan lokaci a tsakanin 1986 zuwa 1989. Ga alama kuma su ne suka sanya Kano ta sami karɓuwa da tagomashi a wannan harka ta yadda daga baya Gusau ta shigo sahu, Kanon ta sake bayyana daga can kuma sai Sakkwato tare da Yusuf Adamu.

    Ga jerin waɗannan littattafai da suka kasance na farko ko suka kasance jijiyar da ta gina wannan sabon yanayin rubutu na Adabin Kasuwar Kano. Daga marubuta waɗannan littattafai an fahimci marubuta mata guda biyu suka wanzu, sauran kuma duk maza ne.

    LAMBA LITTAFI MAWALLAFI SHEKARA
    1 Wasiyyar Baba Kere Ibrahim Saleh Gumel 1983
    2 In Da Rai da Rabo Idris S. Imam 1984
    3 Rabin Raina Talatu Wada Ahmed 1984
    4 Hannunka Mai Sanda 1 Ƙamaruddeen Imam 1985
    5 Soyayya Gamon jini Ibrahim Hamza Bici 1986
    6 Daji Bakwai Abba Ado Ɗandago 1987
    7 In Da Rai… Idris S. Imam 1987
    8 Kogin Soyayya Ahmed Mahmoud Zaharaddeen 1988
    9 Turmi Sha Daka Kabiru Ibrahim Yakasai 1988
    10 Budurwar Zuciya Balaraba Ramat Yakubu 1989
    11 Soyayya Danƙon Zumunci Bashir Sanda Gusau 1989
    12 Tsalle Ɗaya… Idris S. Imam 1989
    13 Idan So Cuta Ne Yusuf M. Adamu 1989

    Wannan bayani an ciro shi ne daga rubutaccen kundi mai taken: ADABIN KASUWAR KANO: Nazari da Sharhi Game da Ƙagaggun Labaran Hausa (1984-2008) wanda Bashir Abu Sabe 07/211111002 (M.A Hausa Studies) USMANU ƊANFODIYO UNIVERSITY, SOKOTO, NIGERIA ya wallafa.

    Danna nan don karanta Jigogin Adabin Kasuwannin Ƙasashe

    Edita@rumasau-kallamu