Category: ILIMIN TARIHI

  • Haihuwar Annabi Muhammad (S.A.W)

    Haihuwar Annabi Muhammad (S.A.W)

    Shugabanmu Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) shi manzon Allah ne, zuwa ga mutane baki ɗaya, cikamakin Annabawa, shugaban Manzonnin Allah ne.

    1. Ya zo da addinin musulunci, wanda Allah ba ya karɓa (amsa) wanin addininsa ranar lahira.

    2. Yana daga cikin dangin ƙuraishawa, mafificiyar ƙabila, a cikin Makkah abar girmamawa.

    3. Dangantakarsa tana haɗuwa da Annabi Isma’il ɗan Annabi Ibrahim (Alaihis-salam).

    Sharihi; Annabi: shi ne wanda Allah (Subhanahu wata’ala) ya umarce shi da ya aikata wasu ayyuka akan kansa kuma wanda ya  kuɓuta daga dukkanin wani  aibu, sannan ɗa ne ba bawa ba, kuma namiji ba mace ba, lafiyayye ba mara lafiya ba. Sannan adadin Annabawa an samu saɓani; amma ruwaya mafi shahara ita ce, dubu dari da ashirin da hudu (124,000).

    Sai adadin sahabban annabi su guda dubu ɗari da ashirin da huɗu (124,000). Haka ma adadin taurarin da ke sama guda dubu ɗari da ashirin da huɗu (124,000) da adadin gashin da ake jinkin mutum guda dubu ɗari da ashirin da huɗu (124,00) da adadin numfashin da mutum yake yi a kowa ce rana guda dubu ɗari da ashirin da huɗu (124,000) ko kuma dubu ɗari da  uku da ɗari shida da tamanin (103,680). Sai adadin lomar da SA na layya yake yi a kowace rana idan an bar shi .

    Mazon: Shi ne wanda ya cika dukkanin sharaɗai na Annabta, sai Allah (Subhanahu wata’ala)  ya zaɓe shi mayar da shi a matsayin ɗan aiken Sa (Mazon) ma’ana , wanda zai dinga ba shi saƙo zuwa ga wasu mutane, umarni ne ko hani ne ta hanyar mala’ika zuwa gare shi ko shi (Manzon Allah) wasu sun ce ɗari da uku da goma sha uku (103) ko ɗari uku da goma sha uku (313). Bugu da ƙari kuma, daga cikinsu Al-ƙur’ani mai girma ya faɗi sunayen annabawa guda ashirin da biyar (25) daga cikinsu kamar haka:-

    Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam)

    Annabi Dauwuda (Sallallahu alaihi wasallam)

    Annabi Ibrahim (Sallallahu alaihi wasallam)

    Annabi Zakriyya (Alaihis-salam)

    Annabi Musa (Alaihis-salam)

    Annabi Ayuba (Alaihis-salam)

    Annabi Nuhu (Alaihis-salam)

    Annabi Sulaiman (Alaihis-salam)

    Annabi Isah (Alaihis-salam)

    Annabi Zulƙifil (Alaihis-salam)

    Annabi Yusuf (Alaihis-salam)

    Annabi Haruna (Alaihis-salam)

    Annbi Yunus (Alaihis-salam)

    Annabi Isma’il (Alaihis-salam)

    Annabi Yaƙub (Alaihis-salam)

    Annbi Adamu (Alaihis-salam)

    Annbi Ishaƙ (Alaihis-salam )

    Annabi Alyasa’u (Alaihis-salam)

    Annabi Iliyasu (Alaihis-salam)

    Annabi Salihu (Alaihis-salam)

    Annabi Idris (Alaihis-salam)

    Annabi Shu’aibu (Alaihis-salam)

    Annbi Yahaya (Alaihis-salam)

    Annabi Hud (Alaihis-salam)

    Annabi Luɗ (Alaihis-salam)

    Sannan kuma daga cikin su ne Allah (Subhanahu wata’ala) ya fitar guda biyar (5) ba su lamba ta Manzanni a ruwaya mafi, amma akwai ruwaya da ta nuna cewa guda goma (10) kamar haka:-

    Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam)

    Annabi Yusuf (Alaihis-salam)

    Annabi Ibrahim (Alaihis-salam)

    Annabi Yunus (Alaihis-salam)

    Annabi Musa (Alaihis-salam)

    Annabi Ishaƙ (Alaihis-salam)

    Annabi Nuhu (Alaihis-salam)

    Annabi Isma’il (Alaihis-salam)

    Annabi Isah (Alaihis-salam)

    Annabi Yakubu (Alaihis-salam)

    Sannan kuma ruwaya wacce ta nuna cewa ulul-azmi guda biyar ne su ne kamar haka;

    Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam)

    Annabi Ibrahim (Alaihis-salam)

    Annabi Nuhu (Alaihis-salam)

    Annabi Musa (Alaihis-salam)

    Annabi Isah (Alaihis-salam)

    Sannan alama ta uku (3) Yace: Yana daga cikin dangin ƙuraishawa kuma cikin garin Makkah abar girmamawa’’. Saboda guda goma sha biyu (12) kamar: Banu-Adnan Banu-Hashim, Banu-Abdulmudamllab, Kuraishawa Banu-Sa’ad Banu-Zuhra, Banu Ka’abu, da dai sauransa amma duk cikin waɗannan ƙabilu.

    Babu kamar ƙuraishawa a cikin garin  makkah, sannan asalin sunan garin makkah shi ne Bakka saboda zuwan annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) ya koma Makkah kamar yadda Alƙur’ani ya yi mana bayani a cikin Suratul Ali-Imrana aya casa’in da biyar (95). Haka ma garin Madinah kafin zuwan Annabi suna garin Yasrib, Saboda zuwan annabi ne ta koma Madinah, kamar yadda Alƙur’ani mai girma ya yi mana bayani a cikin Suratul Ahzab aya ta goma sha biyu (12).

    Don karanta kakannin manzon Allah SAW danna nan

    Haka kuma, a lambar ta huɗu (4), Yana cewa Dangantakar sa tana haɗuwa da (Annabi) Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) ne sai dai guda goma daga cikinsu. Sannan kuma a lamba ta uku yace “yana daga cikin dangin ƙuraishawa, a Makka abar girmamawa”. Saboda haka, Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) yana daga cikin mutanan garin Makka bakuraishe ne, haka kuma a cikin garin Makka akwai manyan-manyan ƙabilu har guda goma sha biyu (12)  a cikin garin kamar haka;

    Banu-Adnan

    Banu-Hashim

    Banu-Abdulmuɗallib

    Banu-Sa’ad

    Ƙuraishawa

    Banu-Zuhra

    Banu-Ka’ab

    Banu-Fahra

    Banu-Galib

    Banu Mudrakata

    Banu-Tamim

    Banu-Nadhir

    Haka kuma haihuwar Annabi ne ya sa garin Makka ta koma Makka wanda da can sunan garin Bakka kamar yadda ya zo a cikin Alƙu’ani mai girma a cikin suratul Ali-Imran aya ta casa’in da biyar (95), sannan kuma garin Madina kafin haihuwar Annabi sunan garin Yasriba, saboda zuwan Annabi ne ya sa garin ya zama Madina kamar yadda ya zo a cikin suratul Ahzab aya ta goma sha biyu.

    Bugu da ƙari kuma, dukkanin Annabawa larabawa ne in banda guda huɗu  daga cikin su su ne: Annabi Hud da annabi Yunus da annabi Salihu. Haka kuma wata rayuwar an ce daga kan Annabi Isma’il (Alaihis-salam) zuwa Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) akwai mutane guda Ashirin (20).

    Haka ma daga kan Annabi Adamu (Alaihis-salam) zuwa Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) akwai mutane Talatin (30), amma saninsu da rashinsu babu abbin da zai ƙara mana, saboda kawai kissa ta Israliyat ko Banu-Isra’il.

    Domin Karanta halayen annabi Muhammad danna nan

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Tarihin Hakimin Kudan Marigayi Alhaji Ishaƙ Muhd Ashir Kudan

    Tarihin Hakimin Kudan Marigayi Alhaji Ishaƙ Muhd Ashir Kudan

    An haifi mai girma Ishaƙ Muhammad Ashiru a garin Kudan a ranar 15/03/1944, shi ne ɗa na farko ga sarkin Kudan Muhammad Ashiru, Alhaji Ishaƙ ya yi makarantar allo tun yana ƙarami a garin Kudan. Tun yana ƙarami ne kuma aka kai shi makarantar elementare a shekara ta 1954-1958.

    Da ya gama ya wuce babbar makarantar firamare da ke Giwa a shekara ta 1958-1960. Daga nan sai ya zarce kwalejin gwamnati ta fasaha da ke Kano (Govt Tech Training School Kano) a 1964-1967. Ya wuce Kwalejin Horon Sojojin sama da ke Ingila (School of Tech Training Royal Airforce Newto England) a 1970. A inda ya samu takardar shaidar Diploma a kan gyaran injin jirgin sama.

    Bayan ya dawo gida, sai ya shiga aikin sojan sama, inda ya kai har W.O II (warrant officer II) a 1968. Ya yi ritaya a shekara ta 1977, bayan rasuwar mahaifin sa, Sarkin Kudan Ashiru. A shekara ta 1977, ya samu aikin ƙaramar hukumar Ikara. A shekara ta 1991 ya zama Sarkin Nassarawa, A shekara ta 2001 (30/06/2001) ya zama Sarkin Kudan a sakamakon zamowa Hakimi da ƙanin mahaifinsa Alhaji Haladu Yakubu ya yi, haka kuma Alhaji Ishaƙ Ashiru ya zama Hakimin Kudan Ciritawan Zazzau.

    Abubuwan ci gaba da aka samu a zamaninsa

    1. Shimfiɗa kwalta da ta ratsa garin Kudan gabas da yamma, kudu da arewa.

    2. Shimfiɗa kwalta daga Kudan zuwa Sundu.

    3. Kafa Asibitin ƙorama.

    4. Kafa makarantar firamare guda biyu a kudu da arewacin Kudan.

    5. Ƙarin fanfunan burtsatsai a garin Kudan.

    6. Ƙarin rumfunan kwano a kasuwar Kudan.

    7. Kafa barikin ‘yan Sanda.

    8. Kafa kamfanin buga bulo na farko.

    9. Kafa makaranta mai zaman kanta (Private School).

    Bugu da ƙari kuma, yana ɗaya daga cikin manya-manyan sarakunan Kudan waɗanda suka bayar da gudunmawa wajen samar da zaman lafiya haɗi da kula da tarbiyar mutanan da yake shugabanta a lokacin sa. Sannan kuma yana sasanta ma’aurata haɗi da ba su shawara akan zamantakewar auratayya, sannan kuma mutum ne mara girman kai, saboda idan wani abu ya faru na addinin wanda mas’alar ta zo gaban sa, to yana ɗaukar wayar sa ya tuntuɓi masana na wannan ɓangaran, kamar yadda marigayi malam Surajo Yunusa Kudan ya shaida mana a lokacin da yake raye.

    “Mai girma hakimin Kudan yana kiran sa a waya idan wani abu ya taso na addinin domin neman fatawa”, bugu da ƙari kuma ni ma kai na shaida ne, saboda a shekarata 2014 akwai wata mas’ala da ta taso wanda wani ya auri wata mace watan su biyar dai-dai sai ta haihu. Wanda aka kawo wannan mas’alar gaban sa, kuma ya yi hukunci akan haka, ni kuma ina gefe ɗaya a zaune, sai ya tambaye ni akan hukuncin da ya yanke, yaya addini ya tsara, nan take na duba abinda na ga hakan ya yi daidai.

    Sannan sai ya yi wa mutanan wajen jawabi cewa “kada ku ga na tambayi wannan yaron wani abu akan wannan mas’alar, saboda akwai wani littafi ne wanda ya rubuta akan irin wannan mas’alar, ya kuma turawa mai martaba sarkin Zazzau Dr. Shehu Idris har ma ya ɗauki nauyin buga littafin”.

    Sanna kuma dukkanin wanda ya ga ya yi shigar banza ko kuma ya yi askin banza ko kuma ya zo ya wuce ta gabansa ba tare da ya yi musu sallama ba ko gaisuwa ba, sai ya kira shi ya yi masa faɗa akan haka.

    Sannan kuma a shekara ta dubu biyu da ɗaya ne (2001) aka naɗa shi a matsayin sarkin Kudan, bayan sarkin Haladu Yaƙubu ya tafi, wanda ya yi mulki na tsawon shekara ashirin da shida, wato daga 1975-2001, Sannan kuma a shekara ta 2008 ne a sake naɗa shi a matsayin Ciritawan Zazzau kuma Hakimin Kudan.

    Mai girma Ishaƙ Muhammad Ashir ya samar da ci gaba a garin Kudan sosai tare da nuna ƙaunarsa ga mutanan garin, saboda haka tun daga rasuwar Mahaifin sa da kuma sarkin Kudan Haladu Yakubu da mutanan Kudan, mutanan Kudan suke raɗaɗin rabuwa da mai kishin su, har sai da Allah ya kawo musu mai girma Ishaƙ Muhammad Ashir, wanda ko yanzu mutum ya shiga garin zai tabbatar haka, wanda waɗan su suke ganin tunda aka mai da shi Ciritawan Zazzau kuma Hakimin Kudan, suka rasa sarkin mai kishin su haɗi da kula da al’amuran su tare da zama da su haɗi da zuwa gidan rasuwa ko suna.

    Mutanan garin Kudan ba su taɓa mantawa da irin alherin da mai girma Ishaƙ Muhammad Ashir ya yi musu ba, saboda an samu cigaba da yawa a garin, wanda furtawa a yanzu ƙauyanci ne, kawai mutum ya shiga garin zai gani ko kuma ya tambayi mutanan garin manyan zai ji ruwan amsoshi. Sannan kuma ya yi aure yana da mataye guda uku kamar haka;

    1. Halima

    2. Mariya

    3. Hindatu

    Sai kuma sunayen ‘ya’yan sa kamar haka;

    1. Usman (Ɗanladi).      10. Nafi’u

    2. Balarabe.                  11. Isma’il

    3. Mas’ud                     12. Gaddafi

    4. Nasiru                      13.   Imrana

    5. Abdulshahid             14. Umar

    6. Abubakar                 15. Yunusa

    7. Muzammil                16. Sha’awanatu

    8. Furaira(Hajiyayye)    17. Karimatu

    9. Aisha                       18. Shamsiyya

    10. Raliya                     19. Aliyu (Ɗan Asabe)

    (more…)

  • Tarihin Afirka Kashi Na Ɗaya

    Tarihin Afirka Kashi Na Ɗaya

    Afirka na da mutane biliyan ɗaya da miliyan ɗari huɗu da saba’in da huɗu da dubu ɗari biyar da uku da ɗari bakwai da saba’in (1,474,503,770). Idan aka kasa yawan mutane a duniya tana da kashi goma sha bakwai da ɗigo tara (17.9%) na mutanen duniya. Faɗin ƙasar Afirka ya kai 30.37mlsq/km. Wanda su kan su yammacin Turai (Western Europe) France, Germany, Spain da sauran su kawai 2.2mlsq/km.

    Wannan ƙasashe ba su kai ma Jamhuriyyar Congo (Democratic Republic of Congo) ba, idan ka haɗa waɗancan ƙasashen guda goma saboda faɗin ƙasarta ya fi 2.345 million km2. Algeria ita ce ƙasar da ta fi kowacce a Afirka. 

    Harsunan Afirka sun fi dubu biyu, akwai ƙasashe guda hamsin da huɗu (54), ana taƙaddama a kan ƙasashe guda biyu; Yammacin Sahara (Western Sahara) da Somali (Somali Land). Sauran ƙasashe hamsin da huɗu ɗin nan duk ƙasashen kansu ne, yawancin ƙasashen nan duka in banda Habasha (Ethiopia) da inda ya zama Eritiriya (Eretria) yanzu duk sun taɓa zama a ƙarƙashin mulkin mallaka, ko dai na France ko na Ingila ko na Jamus ko na Belgium ko Portugal.

    Misali ma dai ita Jamhuriyya Dimokaraɗiyyar Congo (Democratic Republic of Congo) ta na cikin ƙasashen duniya da suke da arzikin ƙasa kamar irin su Russia da China da Amurka. Belgium ce ta mallake ta. Kusan duk ƙasashen Afirka sun zo ƙarƙashin Turai, kuma su na da bambanci da yawa a tsakaninsu.

    Afrika ta Arewa sama da Sahara ke nan ƙasashen Larabawa ne waɗanda suka haɗa da Morocco da Algeria da Libiya da Tunisia da Misra, idan ka yo ƙasa da Sudan da Murtaniya da Yammacin Sahara (Western Sahara) ɗin nan ƙasashen Larabawa ne, sun daɗe su na da alaƙa da Turai tun kafin mulkin mallaka, tun da kamar ƙasar Tunusia, nan ne asalin ƙasar Cartage, wacce ta yi yaƙi da Rum. Shugaban wannan ƙasa Hanibal ya kai mu su mummunan hari sun yi gwagwarmaya sosai.

    A ƙasar kuma an taɓa samun Emperor na Rum daga Nubiya, saboda haka waɗannan ƙasashe su na da kyakkyawar alaƙa da Turawa ta shekaru ɗaruruwa ko dubunnai tun kafin zuwan Annabi Isah (A.S). Ƙasar Misra (Egypt) kowa ya san tarihinta, suna daga cikin tushen wayewar ɗan Adam. Marocco kuma idan aka bibiyi alaƙarta da Andalus da sauransu, ita ma tana da dogon tarihi. Waɗannan ƙasashe su na da alaƙa da Turawa, mutanensu su ma fararen fata ne. 

    Idan aka yi ƙasa daga arewa (Maghrib) za a zo Afrika ta Yamma an yi dauloli masu tarihi masu martaba, irin su; Ghana, Mali, Songhai, Borno, Benin, Sokoto da sauransu, an yi su kafin zuwan Turawa. Haka har Turawan suka gama abin da za su yi dai, suka tafi suka dawo wa da ‘yan Afrika mulki. 

    To amma me ya sa Afrika ta fi kowacce nahiya a duniya koma baya, kuma mai ya sa demokuraɗiyya ta ƙi kankama a Afrika, ko kuma menene ma ainahin shi wannan dimokuraɗiyya? Shin zai yiwu a Afirka?

    Shin samun ci gaba sai lallai ta Gwamnatin dimokuraɗiyya irin yadda Turawa suka fassara ta? Idan haka ne me ya sa aka zo aka kawowa mutanen Afirka wannan dimokuraɗiyya kuma ta ƙi ta yi mu su aiki?

    Wannan suna daga cikin dalilan da za a duba a tarihance, menene bambancin mutanen Afirka da sauran mutanen duniya da waɗannan abubuwan suka faru? Domin a fahimci wannan dole ne a duba tarihin ita kanta Afirka, kasancewarta da yadda ta zo ta zama har su Turawan nan suka mallake ta, kuma har yanzu ba su sakar mata mara ba (yadda ake ce wa).

    Har yanzu ƙasashen Afirka su na ta bilinbituwa sun kasa kama hanyar da za su samu ‘yanci da tattalin arziki. Kowacce ƙasa a cikin Afirka ta na da matsala, waɗanda ba su da matsalar wata ƙila za ka ga abu kaɗan idan ya same su sai su rushe. Kamar Libya lokacin da suka kori Gaddafi.

    Ƙasar Libiya Allah Ya yi mata albarka, mutanen ƙasar suna cikin jin daɗi, aka dinga zuga su da haɗin bakin shugaban ƙasar Amerika Barak Obama, wanda  shi ne baƙar fata na farko da ya shugabanci ƙasar da Hillary Clinton sakatariyar harkokin waje ta Amerika.

    Ruguza Libiya kuma ya yi tasiri a cikin Afirka, fitintinu da yawa suka damu mutanen Afirka tun daga maƙotanta irin su Nijar, Mali, Najeriya da Burkinafaso. Rushewar Libiya ta sa kayan yaƙi sun bazu kuma an shiga wani bala’i.  Gaddafin nan duk abin da ya yi wa mutanen ƙasarsa suka zo suka saurari Turawa suka bijire, yanzu ga shi ƙasar gaba ɗayanta ta rushe. 

    Wannan nazari da bayani an yi su ne don a fahimci, menene ya sa Afrika take cikin wannan matsala, a dalilin haka, shuwagabanni suke cewa ya kamata Afrika ta ɓullo da irin tata dimokaraɗiyyar.

    Ba za a iya ba da amsar duk tambayoyin da suka shafi matsalar Afirka a wannan nazarin ba, amma za mu kalli abin ta mahanga da za mu qyarawa kanmu fahimta na waɗannan abubuwa da suka faru a Afrika suka janyo Afrika ta zama yadda take, kuma an kasa samun bakin zaren a siyasance har yanzu.

    A siyasance babu cigaba a Afirka, wannan ya haifar da rashin cigaba na tattalin arziki. Idan aka kwatanta ƙasashen Afrika da sauran ƙasashen duniya irin su; South Korea, Singapore da Malaysia har ka zo kan ƙasa irin su Indonesia, ƙasashen Afrika su ne koma baya. 

    Saboda haka za mu bi abubuwan nan daki-daki mu duba mu ga me ya samu Afrika kafin ma mulkin mallaka, da kuma yadda aka cutar da mutane aka dinga cinikin bayi. Bayan su Turawa sun hana cinikin bayi sai kuma suka zo da ƙarfin soja su mallaki ƙasashen nan na Afirka.

    Ya aka yi aka ba su ‘yanci, waɗanne irin shugabanni ne suka ɓullo a waɗannan ƙasashen, da irin kisan gilalr da aka yi mu su.  Sai mu duba yadda ƙasashen da suke yin demokuraɗyiya, shin mutanen ƙasashen musamman masana a cikinsu suna alfahari da wannan tsarin demokuraɗiyya da ake son a tilasta ƙasashen Afrika lallai su yi shi.

    Kuma menene asalin demokuradiyya, rana ɗaya ko lokaci guda aka kafa shi, ko kuma an gina shi ne a tsahon lokaci. Kuma a wacce ƙasa aka fara shi saɓanin yadda Turawa suke nunawa.

    Domin karanta tarihin ranar demokuraɗiyya a Najeriya danna nan 

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Abubuwan Da Ya Kamata Ka Sani A Kan Android

    Abubuwan Da Ya Kamata Ka Sani A Kan Android

    Android shi ne ƙwararren masanin nan wato Andy Rubin kuma shi ne ya ƙirƙiri ko kuma mu ce shi ne shugaban ma da ya fara samar da wannan tsari na android. Haka kuma shi ya ba da wannan sunan ga aikin sa, lokacin yana aiki da kamfanin Apple kafin ya koma aiki da kamfanin Google.

    Tsarin android wannan wani kamfani ya samar da shi da ake kira android inc a shekara ta 2004 bayan an samar da kamfanin google wato kamfanin matambayi ba ya ɓata. Daga baya kamafanin na google ya saye shi a shekarar 2005 akan farashin dala milliyan hamsin $50 .

    Tsarin android an samar da shi ne kawai domin samar da masarrafar daukar hotuna, daga baya kuma aka mai da tsarin zuwa sanya shi a cikin wayoyi domin ganin hakan shi zai fi dacewa. Google ya gabatar da tsarin android a ranar 5 ga watan Nuwamba a shekarar 2007 wanda aka yi shi a mazubin tsarin Linux.

    Kamfanin samar da tsarin android na google yana da masu hulɗa da shi da suka haura adadin billion ɗaya a duniya, wanda Bahaushe ke cewa malala gashin tunkiya. Akan abubuwa daban-daban kamar wayar hannu da kuma wayar rataye wato tablets.

    Htc dream ko t-mobile g1 shi ne tsari na farko da aka fara sanyawa akan manyan wayoyi wanda tsarin android ya fara aiki akai wanda aka sake shi aka fara aiki da shi a shekarar 2008. Banda Tsarin android 1.0 da 1.1, duk wani tsari da zai biyo baya ana kiranshi da wasu sunayen ne saɓanin na da, kamar jelly bean, ko kuma ice cream sandwich, wani kuma honeycomb da lollipop.

    Mutane da dama suna tunanin wannan sunan na android da kuma alamar sa shi ake kira android, abun ba haka yake ba asalin sunan da ake kiran android Mascot da shin shi ne Bugdroid, ganin wannna ba zai zama sananne ba ko karɓuwa shi yasa kamafanin google suke kiran shi da wannan sunan na android.

    Cikin abubuwan da wannan kamfani da ke samnar da android ya fi shahara da shi shi ne wannan babbar kasuwar ta hada-hadar massarafai wato google play store wadda aka yi ƙiyasin tana da masarrafai fiye da billion 48 wanda kuma kullum yana samun ɗimbin masu halarta daga gurare daban-daban na duniya, wanda kuma mafi yawancin waɗannan masarrafai na kyauta ne.

    Haka kuma wannan kamfani dake samar da wannan tsari yana da wani tsari ko masarrafi dake a sararin samaniya wanda ake kira da NASA wanda aka sanya shi a sararin samaniya mai kama da mutum-mutumi na Nexus S wanda yakan yi amfani a tsarin wasu wayoyin kamar mutum-mutumin biredi mai suna “Gingerbread”.

    Haka kuma dukkanin mutum-mutuimin da kamfanin android ya samar ko kuma yake kama da alamar android shi ne namiji, shi kuma mai kama da siffar mace shi ne ake kira da Gynoid. Kamafanin dake samar da android wato Google shi ne kamfani na farko da ya ba da damar a san yadda ake haɗa application domin sanya shi ko kara shi akan wani tsarin na masarrafai.

    Wannan tsarin na kamfanin android an samar da shi a mazubai daban-daban wanda mafi yawanci suna tafiya ne bisa tsari. Wanda an samar da:

    1. Android Asto (1.0)
    2. Bender (1.1)
    3. Cupcake (1.5)
    4. Donut (1.6)
    5. Éclair (2.0)
    6. Froyo (2.2.x)
    7. Gingerbread (2.3.x)
    8. honeycomb (3.0)
    9. ice cream sandwich (4.0.x)
    10. jelly bean (4.x)
    11. Kit Kat (4.4)
    12. Lollipop (5.0-5.5.1)
    13. marshmallow (6.0 -6.0.1)
    14. Nougat (7.0 – 7.1.1)
    15. Oreo (8.0).
    16. New age (9.0.1)

    Yanzu kamfanin android yana samar da abubuwan da suke aiki na ban mamaki kamar google glass, watches da dai sauran su. Haka kuma nan gaba kamfanin da ke samar da tsarin android suna ta ƙoƙarin kawo wasu sabbin tsare-tsare na zamani wanda su ma za su iya zuwa da nau’in sunayen su.

    Domin Karanta Cikakken Bayani A kan Abubuwan Da Ya Kamata Ka Sani Dangane Da Twitter Danna nan.

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Ma’anar Damokuraɗiyya

    Ma’anar Damokuraɗiyya

    Ita dai damokuraɗiyya ana ganin cewa gwamnati ce wadda mutane suka zaɓe ta. Wannan ita ce fasasara mai sauƙi, amma wasu suna ƙalubalantar wannan. kuma su yanke hukunci ba tare da an tilasta musu ba. 

    Mutane za su yi zaɓe, su yi abin a cikin lumana, kuma kowacce ƙasa da irin nau’in gwamnatin da ta ɗauka na tafiyar da gwamnati mai adalci ko da ba a yi zaɓe ba. Bisa haka ne ma mutane irin su Muhammad Gaddafi yake ganin shi damokuraɗiyya yake yi saboda ya ba wa al’ummarsa duk irin abinda suke bukata, shi ma damokuraɗiyya ce. Kamar ƙasar Rasha da suke yi abubuwansu mai inganci, su ma suna ganin damokuraɗiyya ce. Ita damokuraɗiyya ta banbanta da yanayin da mutane suka ɗauki kansu. 

    Misali kamar mutanen China, suna ganin ƙasarsu ma tana bin damokuraɗiyya duk da cewa ba zaɓe suke yi ba da za a ce duk gari mutum ɗaya a zaɓe shi, a a sai dai ‘yan jami’yya ne  kawai suke yin zaɓe tare da bin ƙa’idoji na tabbatar da tsarin gwamnati, saboda China sun fi shekara dubu uku (3000) sun yi gwamnati mai inganci, wadda kafin a ɗauke ka aiki, sai ka nuna ƙwarewa (meritocracy), sun daɗe suna irin waɗannan abubuwan tarihi da ya ba su damarsu fito da tsarin da zai amfane su. 

    Saboda haka a ko ina za ka ga mutane suna da irin nasu tsarin na damokuraɗiyya ta yadda za su aiwatar da ita. Tun da haka kenan za a ce irin damokuraɗiyyarsu ba za ta zama irin ta ƙasashen turawa ba. A zaɓi shugaban ƙasa, da gwamna da ‘yan majalisa. In dai aka samu gwamnati mai inganci, mai adalci, mai kulawa da haƙƙin jama’a, shi kenan su wasu suna ganin cewa wannan damokuraɗiyya ce.

    Saboda haka, amana ce idan aka ɗauketa aka auna ta za a ga cewa wasu mutane ne suke damfarar jama’a su juya akalar gwamnati, duk da kana zaɓe amma ba ka da tasiri sai wasu mutane ƙayyadaddu da suke da kuɗi da ɗaurin gindi na wasu ƙungiyoyi, kamar yadda yake yanzu a Amurka take fuskantar barazanar yahudawa (Zionists) sun karɓe ƙasar sai yadda suke so, saboda suna da yadda za su yi, ba ka da damar cewa komai saboda suna da kuɗi da jaridu da abubuwa da za su iya hanaka samun wannan zaɓe, tun da ba kowa zai tsaya a zaɓe shi ya ci ba, sai ace damokuraɗiyya ce.

    Kuma akwai yawancin mutane da suke ganin cewa damokuraɗiyyar nan turawa ne suka ƙirƙireta kuma ya saɓa da tsarin musulunci. To amma shi fa tsarin musulunci nan ya danganta da wanda yake magana, misali, musulmin ƙasar India kimanin mutum miliyan ɗari biyu (200 miliyan) fiye da yawan musulmin ƙasashen Afirka, babu inda ya fi su yawan musulmi a duniya sai ƙasar Indonesia. 

      Shi wannan musulmin sai ya ce maka shi ya fi son tsarin damokuraɗiyya, saboda idan ba tsarin damokuraɗiyya ba, babu yadda zai iya gudanar da addininsa na musulunci. Saboda haka a ba wa kowa ‘yancin ya gudanar da addininsa yadda yake so shi musulmin India yake buƙata.  

    Amma kuma idan ka je ƙasar da musulmi ke da rinjaye, za su  ce mu a bar mu mu yi tsarin musulunci mu ɗabbaka shari’a, domin shi ne  zai yi mana dai-dai da yadda muke so. Don haka,  a nan an samu bambanci da damokuraɗiyya da yadda za a yi aiki da ita.

    Damokuraɗiyya kamar riga ce ko mota da za ka yi amfani da ita, ba lallai sai an bi tsarin yadda turawa suka kawo ba. Su turawan sun kawo wannan tsarin (liberal democracy) ne da a zo a yi zaɓe kuma duka abin da mutane suke so shi za ayi, kenan babu haƙƙin Allah. Tun da farko Kent ne ya zo da tsarin wayar da kai a kan babu Allah (enlightment) da suka ce kada mutum ya yarda da abin da ba ya ganinsa. 

    Tun daga nan turawa suka daina tunanin Allah cikin al’amuransu saboda waccan aƙidar ta (Enlightment philosophy). Allah da suke bauta masa shin “son zuciyarsu”, duk abin da zai tabbatar musu  da wannan son zuciyar da jin daɗi. Shi kuwa musulmi ai ba za su yarda da wannan ba. 

     Idan ka ba da zaɓi za a yi wannan, a misali ƙasar Misra, idan  ka zo ka ce za a yi damokuraɗiyya a yi zaɓe, mutanen Ikhwan su ne za su ci zaɓen, saboda haka turawa ba za su yarda a yi damokuraɗiyya a Egypt ba. Sun fi son a dinga mulki irin na soja ko sarakuna (mulukiyya) , wanda da wannan za su yi amfani su juya mutane yadda suke so. 

    Amma idan aka ce za ayi damokuraɗiyya to, tsari irin na Ikhwan ne zai tabbata. Musulmi da ‘yan ideology sun fito sun ce wai ‘yan Ikhwan ba mutanen kirki ba ne, saboda haka a nan za ka zaɓi Musulmi ‘yan Ikhwan ne ko maƙiya addinin Allah irin su Sise. Sai ka ga shugabannin larabawa suna goyon bayan Sise sun ƙi su goyi bayan Ikhwan, waɗanda za su tabbatar da adalci, su ba da dama a yi addinin gaskiya. Amma sai su goyi bayan Zionists don biyewa son zuciya, kawai.

    Ita damokuraɗiyya ba ya danganta da yadda ka ɗauketa, wanne tsari ka shigo da shi don ka tabbatar. Shi yasa ƙasar China da suka fi kowaɗanne mutane yawa, sun tafiyar da damokuraɗiyyarsu a kan tsari na tafiya da gwamnati mai kyau, kuma za a dauki mutane waɗanda suke da inganci su yi aiki. 

    Yanzu shi shugaban ƙasar China sai da ya yi shekara 30 yana aiki, tun daga kan matsayin Kansila ya fara, sai sun tabbatar da kai kwararre ne kafin ya zo kan shugaban ƙasa. To ka ga China da suka zo da ‘yan gurguzu (communist) ɗinsu dole ne ka ba su wannan matsayi na damokuraɗiyya, idan aka zo za a yi aiki ko na makaranta ne ko asibiti ko kwashe shara, sai sun fito da abubuwa an tambayi mutane domin a ji ra’ayinsu tare da bin diddigi a kan aiki. 

    Shi yasa masana ilimin kimiyyar siyasa suke cewa, ba za a ce China ba ta bin tsarin damokuraɗiyya ba, domin kowanne aikin gwamnati sai an tabbatar da ingancinsa, kuma sai an tambayi ra’ayin jama’a amma ba haka ba ne a ƙasar Amurka, ba ruwansu da wannan, kawai idan an yi zaɓe bayan shekara hudu an kori wannan an kawo wannan haka dai. To amma su China a tsarin damokuraɗiyyarsu da manufarsu shi ne ta yaya tattalin arziƙinsu zai juya ƙasar. Shi ya sa daga 1978 zuwa yanzu mutum sama da miliyan 500 sun fitar da su daga talauci. 

     Wane abu ne za su fito da shi da za su taimakawa mutane. Shi ya sa su a wurinsu duk wanda ya ce tsarinta ba ingantacce ba ne ya yaudari kansa. Domin sun ɗora sha’anin al’adunsu da tarihinsu. 

    Da wannan za mu fahimci cewa ita damokuraɗiyya nan da ake magana ba tsarin da za a ce don kana da gwamnati da aka yi zaɓe wai ka yi damokuraɗiyya, haka ne  ka yi demokuraɗiyya, amma akwai abubuwa da yawa da suka shafi wannan. Kamar irin abin  da yake faruwa a Indiya, ga shi nan Indiyan tun 1940 suka samu ‘yancin kai ba a taɓa gwamnatin soja ba, amma yanzu indiya ta lalace, saboda ‘yan Hindu masu aƙidar bambancin addini, waɗanda su ne mafi yawa suke tsangwamar musulmi saboda ƙiyayya. 

    Idan zaɓe ne , to an yi zaɓe a Indiya, kuma abin da suke so masu rinjaye (majority) su kashe mara rinjaye (minority). Wannan bai shigo cikin tsarin damokuraɗiyya ba, domin yadda aka ce, amma ana amfani da dangwalen masu rinjaye domin a cutar da marasa rinjaye (musulmi). Ya nuna cewa Indiya duk maganar da suka yin a damokuraɗiyya ba haka ba ne. 

    Bisa wannan, idan za ka yi maganar damokuraɗiyya, sai ka yi bibiya, menene ya shafi rayuwar al’umma, an samu ci gaba ko ba a samu ci gaba ba?

    Domin karanta tarihin damokuraɗiyya a Najeriya danna nan

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Tarihin Ranar Damokuraɗiyya A Najeriya

    Tarihin Ranar Damokuraɗiyya A Najeriya

    Alhamdulillah yau ranar damokuraɗiyya, tun lokacin da Mai girma Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya ayyana cewa duk ranar 12 ga Yuni ita ce ranar damokuraɗiyya a Najeriya, domin girmama gwagwarmayar da masu rajin tabbatar da tsarin damokuraɗiyya suka yi, na kawo wannan tsari har zuwa yanzu. Yana da kyau  a yi waiwaye kuma a duba menene ita kanta damokuraɗiyyar da kuma , me yasa muke cikin matsayin da muke ciki a Najeriya. Saboda maganar tattalin arziƙi da wasu abubuwa da suka shafi rayuwarmu. Da kuma ƙalubalen da muke ciki, har ya sa wasu suke ganin ai damokuraɗiyyar ba ma cin gajiyarta. 

    Za mu yi waiwaye a kan wannan mu duba mu wane yanayi ne ya fi dacewa da mu, sannan mu bibiyi ƙalubalen da fahimta ta wasu mutane irin su tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo da yake cewa ai mutanen Afirka sun ƙirƙiro tasu damokuraɗiyyar. Duk wannan suna cikin abin da yake ƙalubale a kanmu, kuma a matsayin mu na masu bibiyar al’amura, ya kamata mu yi nazari a kan wannan.

    Na farko, kamar yadda muka sani damokuraɗiyya mutane daban-daban suna da fahimta iri-iri a kanta. Ba wai a nan ƙasar tamu ba har a faɗin duniya baki ɗaya. Ana da fahimta daban-daban da ta shafi damokuraɗiyya hatta a ƙasashen yamma da suke ganin su ne asalinta, kuma ita ce aƙidarsu. Haka kuma ƙasashen mu na Afirka da ƙasashen Musulmi, wasu na ganin damokuraɗiyya kafirci ce ba musulunci ba ne. Da dai maganganu daban-daban. Wannan abu ne mai zurfi, kuma mai faɗi amma za mu taƙaita a kan misalai ƙalilan; domin samun haske a kan ma’anar damokuraɗiyya.

    MA’ANAR DAMOKURAƊIYYA

    Ita dai damokuraɗiyya ana ganin cewa gwamnati ce wadda mutane suka zaɓe ta. Wannan ita ce fasasara mai sauƙi, amma wasu suna ƙalubalantar wannan. Damokuraɗiyya wani tsari ne da zai kawo gwamnati mai inganci, kuma wanda mutane suke da damar faɗin albarkacin bakinsu, domin nuna sakamakon abin da aka yi musu, su fitar da ra’ayinsu, kuma su yanke hukunci ba tare da an tilasta musu ba. 

    Mutane za su yi zaɓe, su yi abin a cikin lumana, kuma kowacce ƙasa da irin nau’in gwamnatin da ta ɗauka na tafiyar da gwamnati mai adalci ko da ba a yi zaɓe ba. Bisa haka ne ma mutane irin su Muhammad Gaddafi yake ganin shi damokuraɗiyya yake yi saboda ya ba wa al’ummarsa duk irin abinda suke bukata, shi ma damokuraɗiyya ce. Kamar ƙasar Rasha da suke yi abubuwansu mai inganci, su ma suna ganin damokuraɗiyya ce. Ita damokuraɗiyya ta banbanta da yanayin da mutane suka ɗauki kansu. 

    Misali kamar mutanen China, suna ganin ƙasarsu ma tana bin damokuraɗiyya duk da cewa ba zaɓe suke yi ba da za a ce duk gari mutum ɗaya a zaɓe shi, a a sai dai ‘yan jami’yya ne  kawai suke yin zaɓe tare da bin ƙa’idoji na tabbatar da tsarin gwamnati, saboda China sun fi shekara dubu uku(3000) sun yi gwamnati mai inganci, wadda kafin a ɗauke ka aiki, sai ka nuna ƙwarewa (meritocracy), sun daɗe suna irin waɗannan abubuwan tarihi da ya ba su damarsu fito da tsarin da zai amfane su. 

    Saboda haka a ko’ina za ka ga mutane suna da irin nasu tsarin na damokuraɗiyya ta yadda za su aiwatar da ita. Tun da haka kenan za a ce irin damokuraɗiyyarsu ba za ta zama irin ta ƙasashen turawa ba. A zaɓi shugaban ƙasa, da gwamna da ‘yan majalisa. In dai aka samu gwamnati mai inganci, mai adalci, mai kulawa da haƙƙin jama’a, shi kenan su wasu suna ganin cewa wannan damokuraɗiyya ce.

    Saboda haka, amana ce idan aka ɗauketa aka auna ta za a ga cewa wasu mutane ne suke damfarar jama’a su juya akalar gwamnati, duk da kana zaɓe amma ba ka da tasiri sai wasu mutane ƙayyadaddu da suke da kuɗi da ɗaurin gindi na wasu ƙungiyoyi, kamar yadda yake yanzu a Amurka take fuskantar barazanar yahudawa (Zionists) sun karɓe ƙasar sai yadda suke so, saboda suna da yadda za su yi, ba ka da damar cewa komai saboda suna da kuɗi da jaridu da abubuwa da za su iya hanaka samun wannan zaɓe, tun da ba kowa zai tsaya a zaɓe shi ya ci ba, sai ace damokuraɗiyya ce.

    Kuma akwai yawancin mutane da suke ganin cewa damokuraɗiyyar nan turawa ne suka ƙirƙireta kuma ya saɓa da tsarin musulunci. To amma shi fa tsarin musulunci nan ya danganta da wanda yake magana, misali, musulmin ƙasar India kimanin mutum miliyan ɗari biyu (200 miliyan) fiye da yawan musulmin ƙasashen Afirka, babu inda ya fi su yawan musulmi a duniya sai ƙasar Indonesia. 

      Shi wannan musulmin sai ya ce maka shi ya fi son tsarin damokuraɗiyya, saboda idan ba tsarin damokuraɗiyya ba, babu yadda zai iya gudanar da addininsa na musulunci. Saboda haka a ba wa kowa ‘yancin ya gudanar da addininsa yadda yake so shi musulmin India yake buƙata.  

    Amma kuma idan ka je ƙasar da musulmi ke da rinjaye, za su  ce mu a bar mu mu yi tsarin musulunci mu ɗabbaka shari’a, domin shi ne  zai yi mana dai-dai da yadda muke so. Don haka,  a nan an samu bambanci da damokuraɗiyya da yadda za a yi aiki da ita.

    Damokuraɗiyya kamar riga ce ko mota da za ka yi amfani da ita, ba lallai sai an bi tsarin yadda turawa suka kawo ba. Su turawan sun kawo wannan tsarin (liberal democracy) ne da a zo a yi zaɓe kuma duka abin da mutane suke so shi za ayi, kenan babu haƙƙin Allah. Tun da farko Kent ne ya zo da tsarin wayar da kai a kan babu Allah (enlightment) da suka ce kada mutum ya yarda da abin da ba ya ganinsa. 

    Tun daga nan turawa suka daina tunanin Allah cikin al’amuransu saboda waccan aƙidar ta (Enlightment philosophy). Allah da suke bauta masa shin “son zuciyarsu”, duk abin da zai tabbatar musu  da wannan son zuciyar da jin daɗi. Shi kuwa musulmi ai ba za su yarda da wannan ba. 

     Idan ka ba da zaɓi za a yi wannan, a misali ƙasar Misra, idan  ka zo ka ce za a yi damokuraɗiyya a yi zaɓe, mutanen Ikhwan su ne za su ci zaɓen, saboda haka turawa ba za su yarda a yi damokuraɗiyya a Egypt ba. Sun fi son a dinga mulki irin na soja ko sarakuna (mulukiyya) , wanda da wannan za su yi amfani su juya mutane yadda suke so. 

    Amma idan aka ce za ayi damokuraɗiyya to, tsari irin na Ikhwan ne zai tabbata. Musulmi da ‘yan ideology sun fito sun ce wai ‘yan Ikhwan ba mutanen kirki ba ne, saboda haka a nan za ka zaɓi Musulmi ‘yan Ikhwan ne ko maƙiya addinin Allah irin su Sise. Sai ka ga shugabannin larabawa suna goyon bayan Sise sun ƙi su goyi bayan Ikhwan, waɗanda za su tabbatar da adalci, su ba da dama a yi addinin gaskiya. Amma sai su goyi bayan Zionists don biyewa son zuciya, kawai.

     

    Ita damokuraɗiyya ba ya danganta da yadda ka ɗauketa, wanne tsari ka shigo da shi don ka tabbatar. Shi yasa ƙasar China da suka fi kowaɗanne mutane yawa, sun tafiyar da damokuraɗiyyarsu a kan tsari na tafiya da gwamnati mai kyau, kuma za a dauki mutane waɗanda suke da inganci su yi aiki. 

    Yanzu shi shugaban ƙasar China sai da ya yi shekara 30 yana aiki, tun daga kan matsayin Kansila ya fara, sai sun tabbatar da kai kwararre ne kafin ya zo kan shugaban ƙasa. To ka ga China da suka zo da ‘yan gurguzu (communist) ɗinsu dole ne ka ba su wannan matsayi na damokuraɗiyya, idan aka zo za a yi aiki ko na makaranta ne ko asibiti ko kwashe shara, sai sun fito da abubuwa an tambayi mutane domin a ji ra’ayinsu tare da bin diddigi a kan aiki. 

    Shi yasa masana ilimin kimiyyar siyasa suke cewa, ba za a ce China ba ta bin tsarin damokuraɗiyya ba, domin kowanne aikin gwamnati sai an tabbatar da ingancinsa, kuma sai an tambayi ra’ayin jama’a amma ba haka ba ne a ƙasar Amurka, ba ruwansu da wannan, kawai idan an yi zaɓe bayan shekara hudu an kori wannan an kawo wannan haka dai. To amma su China a tsarin damokuraɗiyyarsu da manufarsu shi ne ta yaya tattalin arziƙinsu zai juya ƙasar. Shi ya sa daga 1978 zuwa yanzu mutum sama da miliyan 500 sun fitar da su daga talauci. 

     Wane abu ne za su fito da shi da za su taimakawa mutane. Shi ya sa su a wurinsu duk wanda ya ce tsarinta ba ingantacce ba ne ya yaudari kansa. Domin sun ɗora sha’anin al’adunsu da tarihinsu. 

    Da wannan za mu fahimci cewa ita damokuraɗiyya nan da ake magana ba tsarin da za a ce don kana da gwamnati da aka yi zaɓe wai ka yi damokuraɗiyya, haka ne  ka yi demokuraɗiyya, amma akwai abubuwa da yawa da suka shafi wannan. Kamar irin abin  da yake faruwa a India, ga shi nan Indian tun 1940 suka samu ‘yancin kai ba a taɓa gwamnatin soja ba, amma yanzu india ta lalace, saboda ‘yan Hindu masu aƙidar bambancin addini, waɗanda su ne mafi yawa suke tsangwamar musulmi saboda ƙiyayya. 

    Idan zaɓe ne , to an yi zaɓe a India, kuma abin da suke so masu rinjaye (majority) su kashe mara rinjaye (minority). Wannan bai shigo cikin tsarin damokuraɗiyya ba, domin yadda aka ce, amma ana amfani da dangwalen masu rinjaye domin a cutar da marasa rinjaye (musulmi). Ya nuna cewa India duk maganar da suka yin a damokuraɗiyya ba haka ba ne. 

    Bisa wannan, idan za ka yi maganar damokuraɗiyya, sai ka yi bibiya, menene ya shafi rayuwar al’umma, an samu ci gaba ko ba a samu ci gaba ba?

    DAMAKURAƊIYYA A NAGERIYA

    Lokacin da turawa suka zo sun tarar da mutane, suna da tsarin rayuwarsu da tsarin gudanar da mulkinsu a wuraren da ake da shi, sun samu Daular Usmaniyya (Shehu Ɗan Fodio) duk suna da tsarin rayuwarsu da ƙabilu ma da ba su da tsarin shugabanci, amma suna da irin tsarinsu, na zaman lafiya da na rashin zaman lafiya da na tattalin arziƙi da zamantakewa.

    Daular Usmaniyya ta ƙasar Sokoto ta haɗa gaba ɗaya ƙasar Hausa da Nupe da Ilori da can ɓangaren Adamawa da wasu a Kamaru da Benin da Nijar da Burkina Faso. Ƙasa ce amma da sarakuna a kowanne garuruwa. Bayan jihadi aka kafa Daula mai ƙarfin tattalin arziƙi a nahiyar Afirka ta baƙar fata a ƙarni na goma sha tara (Q-19).

    Turawa da suka zo sai suka haɗe mu da yankunan Arewa da Kudu, a shekara ta 1914, domin samun dunƙulalliyar Najeriya. Bayan kowanne yanki da irin al’adunsa da addininsa daban, ta yaya za a yi wannan zamantakewar? Wannan dai bature ya haɗa ne saboda ya yi cinikayya ya samu kuɗi saboda a wannan nahiya ta savannah har zuwa kurmi akwai arziƙi ta yadda zai dinga fitar da amfanin gona, ya gyara sannan ya dawo da shi don ya samu kuɗi, wato dai saboda ƙarfafa arziƙin turawa. 

    Saboda haka suka haɗe waɗannan ɓangarori, don ya yi amfani da su wajen mulkinsa bisa samar da umarni ta ƙarƙashin sarakuna (indirect rule). Da bature ya zo zai tafi bayan shekara 60, babu wani abu da ya sani sai tsarin mulkinsa irin na nasara, wanda suka ɗora kansu a kai tun bayan da suka yi Industrial revolution a ƙasashen yammacin turai, da ƙasasahen da suka kafa.

    Wannan ya dogara da irin tsarinsu da zamantakewarsu da suka zo da su. A nan sai suka lura da cewa tun da kuɗi suka zo nema, sai su yi amfani da irin tsarin mulkinsu amma su hana waɗannan sarakuna wani iko, sai abin da suka ga dama za su yi da su, cewa haraji idan za ka biya sai da kuɗin nasara. Shi kuma kuɗin nasara ba a samunsa sai an yi aikin leburanci , ko a yi noma irin nau’in abin da za su saya. Wannan ya jefa ƙashin bayan tattali arziƙinmu cikin talauci, kuma har yanzu ana cikin wannan yanayin talauci. 

    Saboda haka aka kawo ilimin Boko wanda idan babu shi babu wani abin da za ka yi. Ya zama dole ta sa, sarakuna da mutanensu suka shiga wannan karatu, daga bisani suka ce sai an kafa jam’iyyu da tsarin siyasa. Aka yi jam’iyyu a Arewa da jam’iyyu a Kudu. Wannan shi ne ya samar da jamhuriyya ta farko kowanne larduna yana da nasa tsarin da yadda za a tafiyar da su.

    Akwai babbar matsala a wannan lokaci na wasu rukunin ƙabilu da aka rufe su ba a ma jin labarinsu, misali kamar a jihar yamma an samu matsala da tashe-tashen hankali, sai jihar Arewa suka haɗa baki da jihar Gabas suka rinjayi ‘yan majalisa na jihar Yamma domin samar da  jihar  Yamma ta Tsakiya (Mid west). 

    Abubuwa suka yi ta faruwa ana ta rikici wanda da ma tsarin ƙarfin iko daga majalisa (parliament), inda shugaban gwamnati za a zaɓo shi daga mazaɓarsa ba duk ƙasa ce take zaɓarsa ba, kuma jami’yya ce take gaba da shi, da jam’iyya za a yi amfani da jam’iyya za a yi mulki da jam’iyya ake haɗa kai da wasu aka yi wannan wake- da- shinkafar aka yi zaɓe, zaɓenma an samu maguɗi da kashe-kashe da rigingimu, har manyan kudu( waɗanda sun san abin da suke yi) suka yi ta ba da matsala a majalisa (parliament)

    Sir Abubakar Tafawa Balewa ya yi fama da ita wajen neman haɗin kan mutane. Har Antony Enahoro yake cewa; idan babu wannan mutumin ƙasar nan ba za ta zauna lafiya ba, haka Tafawa Balewa ya sha wahala. ‘Yan kudu da suka ga idan zaɓe za a yi ba za su iya kai labari ba. 

    Sai sojoji suka zo suka kifar da wannan gwamnati, suka kashe Tafawa Balewa da Sardauna da Akintola da sauransu. Domin sun ce idan ba su da yawan mutane a majalisa, to su  bi ta hanyar maguɗi a  ƙidayar jama’a (Census) wanda aka yi a shekara ta 1963 har aka sake a 1964, suka ga maguɗinsu bai ci ba. Sun fahimci zaɓe, ƙato-bayan- ƙato da ƙuri’a bayan ƙuri’a, to ɗan kudu ba zai yi mulki ba. Sai suka ce maganin wannan shi ne su zuga sojoji su yi juyin mulki.

    A wannan lokacin mafi yawan sojoji ‘yan ƙabilar igbo ne, amma ainihin jam’iyyar AG ta Awolowo ita ce ta saka su. Duk waɗannan abubuwan saboda rashin kyakkyawan nazari da ba mu da shi a ƙasar nan sai aka dinga cewa ai Inyamurai ne  suka shirya juyin mulki da wannan kisan gillar. Amma dai babbar manufar an yi shi ne don a hana mutanen Arewa mulkin Najeriya.

     Don haka akwai maganar ƙabilanci , akwai maganar bambancin addini, saboda  Sardauna mai riƙo da addininsa ne kuma yana son ƙabilarsa da addininsa su fi kowacce al’umma a Najeriya. Lallai akwai wannan amma ba shi kaɗai ba ne, abubuwa suna wuce haka. ‘Yan kudu abin da suke so a wannan lokaci shi ne, yadda zasu karɓi mulki, tun da ba su samu ta hanyar dangwale ba sai suka ƙaro rigima, inda suka kawo soja ya ƙwace mulki.

      Wannan yana da muhimmanci mu fahimce shi. Kuma Mr. SG Ikoku ya faɗa a wani taro (conference), ya ce sun yi magana da sojoji domin su fahimtar da su maganar siyasa. Shi ya ce ‘yan siyasa ne suka zuga soja aka yi juyin mulki a Najeriya.Tun bayan mutuwar Tafawa Balewa ƙasar nan ta kasa zama lafiya, kamar yadda Tony Enahoro ya faɗa cewa, idan babu Tafawa Balewa ƙasa ba za ta zauna lafiya ba.

     Haka kuwa aka yi da aka yi wannan, abin da ya biyo baya shi ne yaƙin Biafra aka zo aka kashe mutane, abubuwa da yawa  a ƙasa , aka shiga rigingimu. A daidai wannan lokaci sojojin Arewa suka hamɓarar da gwamnatin Ironsi, suka saka Gowon ya zama shugaban ƙasa. A dalilin haka da sauran abubuwa suka  ce za su yi ƙasar Biafra, wannan ya haifar da yaƙi domin tsare ƙasa daga masu ƙoƙarin ɓallewa. 

    Shi Yakubu Gowon yana tare da mutanen Arewa aka zo  yin yaƙi na Ojukwu aka shafe kusan shekaru uku ana yaƙi (1967-1970).  Gowon ya yi shekaru tara yana mulki, a lokacin manyan ‘yan siyasa, suna nan  waɗanda ba a kashe su ba, irin su Awolowo da Azikwe da malam Aminu Kano da Shagari da sauransu. Su ma waɗannan ‘yan siyasar  suka yi ta ƙoƙarin a basu mulki.

     Gowon ya yi ta yaudararsu, yau ya ce wannan gobe ya ce ya canja. Saboda ya ga irin yadda aka yi a ƙasashen Afirka, sojoji suna ta yin mulki. Kuma babu maganar yin zaɓe. Saboda haka  daga cikin sojoji Kanal  Shehu Musa ‘Yar Adua ya jagorance su , suka yi juyin mulki  suka kawo Janar Murtala Muhammad wanda dama shi ne shugabansu tun bayan da aka yi yaƙin Basasa.

     Wanda yake tsayyaye ne a kan batun rashin cin hanci da rashawa. Nan da nan suka ce za su mayar da mulki a hannun farar hula domin ƙasa ta zama ɗaya. Za a yi mulki damokuraɗiyya, wanda za a kawo tsarin shugaba mai cikakkken iko ba irin na jamhuriyya ta farko ba wato parliamentary.

    Yanzu Allah ya kawo zamani wanda mutane ba wani nazari suke yi ba da har suke kawo maganar wai a koma wancan tsari na ƙarfin iko daga majalisa (parliament). Saboda ba ma yin ƙoƙarin fuskantar abubuwa bisa nazari. 

    Shin menene matsalar Najeriya? Ta ƙarfin iko daga majalisa (parliament) ne ko kuma ta shugaba mai cikakken iko (presidential), ko ta wani abun ce daban? Sai suke ganin cewa wai a koma baya. Wannan jamhuriyar fa ita ce ta wahalar da mutane da rarrabuwar kai, wadda ta haddasa yaƙin basasa. Ita ce suke son ta dawo kawai a nan ma suna ganin idan ba haka suka yi ba, ba za su samu mulki ba daga hannun ɗan Arewa. Shi kuma ɗan Arewa gani yake, idan babu mulki ba zai cigaba ba.  Wannan matsala ce da take fuskantar ‘yan Najeriya.

    Da aka zo gwamnatin Murtala, suka kashe shi. Sannnan Obasanjo ya zo a matsayin shugaban ƙasa, gwamnatin ta yi ƙoƙari waje shirya zaɓe domin mayar da mulki a hannun farar hula, aka zaɓi Alhaji Shehu Shagari daga Jam’iyyar NPN.

    Sun zo da tsarin shugaba mai cikakken iko saɓanin tsarin jamhuriya ta farko na ƙarfi daga majalisa (parliament), wanda ba duk ƙasa ce take zaɓen shugaban ƙasa ba. Shi kuwa wannan tsari na shugaba mai cikkaken iko, duk ƙasa ce take zaɓen shugaban ƙasa da mataimakinsa. Idan za a duba magana ta hankali, ya kamata a ce wanda zai jagoranci mutane gabaki ɗaya suka zaɓe shi da hannunsu da amincewarsu ya zama shugaban ƙasa, sauran jama’a suna da ta-cewa a kansa.

     Don haka wannan fa ya fi wancan. Wancan kawai, mazaɓar shugaba ce za ta zabo shi sannan ya zo zauren majalisa, su kuma ‘yan majalisa su zaɓe shi shugaban gwamnati. Domin jam’iyyar da ta fi kowacce karɓuwa a Najeriya baki ɗaya NPC ita ce ta ci zaɓe. Tana da mutane daban-daban daga kowanne sashe na ƙasa, ba wai kawai mutanen Arewa ba ne a cikinta, da mutanen kudu da mutanen tsakiyar Najeriya.

     Wannan ce ta sa jamiyyar ta samu karɓuwa ta kafa gwamnatin tarayya. A dalilin wannan ya sa, ana tafiya har wannan gwamnati ta lalace, ana ta rigima daga baya soja ya sake dawowa ya karɓe mulki ta hanyar juyin mulki a 1983. Matsalar da gwamnatin Shagari ta fuskanta shi ne na ‘yan jaridar kudu da suka saka shi a gaba. Wannan suka da jaridun kudu suka dinga yi wa gwamnatin har mutane suka karɓa suna ganin gwamnatin babu inganci ga cin hanci da rashawa a tsakanin ministoci da sauran laifuffuka, ‘yan kudu sun sa su a gaba, saboda su suke da bakin magana. Allah dai ya kawo qarshen gwamnatin, to ita ma ba a dauki wani lokaci mai tsawo ba sojoji a tsakaninsu suka tumɓuke Muhammadu Buhari, sai Babangida ya hau.

    Daga nan ne aka fara tunanin ranar damokuraɗiyyar nan, menene ya kawo 12 ga watan Yuni? Shi Janar Babangida ya kawo sauye-sauye da yawa a cikin harkar Najeriya, kuma duk da cewa soja ne shi amma yana da ra’ayin ba wa mutane dama su yi Magana da kuma ra’ayi tattalin arziƙi da cewa ba wai lallai sai gwamnati ce zata riƙe ba, wato abubuwa za su koma hannun ‘yan ƙasa da ‘yan kasuwa.

     Wannan ya sa ya bambanta da sauran sojoji, kuma ya ba wa mutane dama su yi magana. Ya gabatar da tsare-tsare na siyasa da suka haɗa da taron makomar siyasa da cibiyar tattauna batutuwan siyasa. Da farko ya ba wa mutane damar su yi jam’iyyu suka kasa, ya zo ya yi jam’iyya guda SDP wadda ta karkata ga hagu, masu ra’ayin ci gaba da sauri da NRC wadda ta karkata dama, mai ra’ayin cigaban ‘yan mazan jiya (jari hujja). 

    Bayan da aka yi zaɓe na cikin gida a jam’iyyun sai aka ga duk ‘yan Arewa ne za su fito takara, domin Janar Shehu Musa Yar Adua shi ne ya ci a SDP sannan Malam Adamu Ciroma ya ci a NRC, wanda duk daga Arewa suka fito, aka ce wannan zaɓen fitar da gwanin yana da matsala domin an yi magudi , Babangida ya soke.

    Bayan gwamnatin Babangida ta soke zaɓen, sai ta sake ba da dama a zo a sake. Bayan sun gudanar da zaɓe, sai SDP ta fitar Chif MKO Abiola, ita kuma NRC ta fito da Alh. Bashir Othman Tofa, abokin Babangida, ɗan Arewa kuma ɗan Kano ne. Aka yi ta rigima, zaɓen ba a kammala shi ba, amma mutanen Abiola suka ce shi ya ci.

     Gwamnatin Babangida ta soke zaɓen a ranar 12 ga watan Yuni 1993. Wannan ya sa a ka cigaba da rigima daga ƙarshe dai Babangida, ya ce ya tafi (ya zakuɗa) daga shugabanci Najeriya. Ya sauka ya ba wa wata gwamnatin riƙon ƙwarya ta Chif Earnest Shoniken. 

    Sai gwagwarmayar sai an dawo damokuraɗiyya, sai an dawo da zaɓen da aka soke a Yuni tare da nuna cewa Abiola ne ya ci zaɓe aka hana shi saboda ba ɗan Arewa ba ne. Wannan rana aka mayar da ita kamar ranar sallah. Bayan da aka ba wa Shoniken shi kuma ya kasa, saboda tsangwamar mutane NADECO, sai Janar Sani Abacha ya karɓe mulkin ya shekara biyar, ya yi abin da zai yi, har Allah ya karɓi ransa yana shugaban ƙasa a 1998.

    Daga nan sai Janar Abubakar Abdussalam, ya karɓa, ana tunanin yadda za a saki Abiola bayan an tsare shi saboda ya ayyana kansa shugaban ƙasa. 

    Abdussalam ya sako shi. Ya yi ta ƙoƙari ganin an rantsar da shi ta hanyoyi daban-dabani, ya  haɗu da mutane  a wata tattaunawa da wani jami’in gwamnatin ƙasar Amurka (mataimakin minister) da wata jakadiyar majalisar ɗinkin duniya da wasu ‘yan fadarsa, Ya sha shayi a gabansu, Allah ya yi ikonsa rai ya yi halinsa. Daga nan wutar rigima ta cigaba, inda suke cewa dole mulki sai ya koma kudu. Abdussalam ya ga cewa abin da zai yi shi ne, ya miƙa mulki a hannun farar hula, inda ya shirya yin zaɓe tare gyaran kundin tsarin mulkin ƙasa. 

    Ya tuntuɓi manyan ƙasa irinsu Babangida, suka shawarta cewa, idan za a ba da mulki, sai a ƙyale mutane su yi jam’iyyu, kuma lallai a saka ‘yan kudu guda biyu su fito takara. Don haka tun da Shehu Musa ya mutu yana gidan kurkuku tun lokacin da Abacha ya tsare shi, sannan Abiola shi kuma yana raye, sai a fito da shi a ba shi tikitin takara a jam’iyyar PDP. 

    Sannan jam’iyyar APP da kuma AD wanda yarabawa ne mafi yawancinsu aka ce su haɗe wuri ɗaya, su fito da ɗan takara guda ɗaya, suka fito da Chif Olu Falaye. Aka yi zaɓe domin a ba wa ‘yan kudu damar shugabanci, ‘yan arewa suka marawa jam’iyyar PDP ta Olusegun Obasanjo baya ya zama shugaban qasa a shekara ta 1999. 

    Obasanjo ya yi mulkinsa amma kullum tunanin June 12 suke yi, a yi ta nanatawa, duk shekara sai sun yi taro na nuna goyon baya a Lagos da sauran jihohin Yarabawa a ƙarƙashin ƙungiyarsu ta NADECO, wasu kuma sun shiga jam’iyyar AD har suka ci zaɓe kamar Bola Ahmed Tinubu a jihar Lagos. Wannan shi ne asalin gwagwarmayar June 12 da ta kawo har aka mayar da ita ranar biki mulkin damokuraɗiyya a Najeriya. Shugaba Muhammadu Buhari yace ya mayar da ranar demokuradiyya ta koma sha biyu ga watan Yuni.

    RIBAR DAMOKURAƊIYYA GA ‘YAN NAJERIYA 

    Yau an samu kimanin shekaru ashirin da biyar ana bikin ranar damokuraɗiyya a Najeriya tun daga 1999-2024, amma mutanen Najeriya suna cewa su har yanzu ba su ci gaba ba. Me yasa kuma har yanzu wasu suna ganin tsarin da ake tafiya bai kamata a yi shi ba? Tsarin baya a dawo da shi, kwan-gaba-kwan baya, waɗannan abubuwa su ya kamata mu yi nazari a kansu.

    Akwai abubuwa da yawa da suka kawo rashin cin ribar damokuraɗiyya a Najeriya. Zamu kalli abu biyu zuwa uku, da farko tushe, cewa Najeriya ta samu matsaloli na siyasa, wato ko ta soja ko ta farar hula. 

    Ba ta samu dama ta kafa tattalin arziƙi a lokutan farar hula ba, haka kuma a lokutan soja, da ya zauna da gindinsa ba. Idan ba a samu kafuwar tsarin tattalin arziƙi da ya kafu da gindinsa ba, duk abin da aka ɗora masa ba zai zauna ba. Mutane kawai abin da suke hanƙoro shi ne su shiga gwamnati su samu kuɗi. 

    Idan muka duba daga 1960 tun lokacin da Najeriya ta samu ‘yanci, mutane suna ganin Najeriya zata zama wani abu a duniya, saboda duk abin da ake tunani da akwai shi a ƙasar; akwai mutane da albarkar ƙasa. Ya kamata a ce an samu cigaba.

      A jamhuriya ta farko ‘yan siyasa babu abin da ke gabansu sai yaya za a cigaba da mulki, kowanne sashi yana hanƙoro sai ya riƙe mulki, kuma sai sashin ya samu kaso mafi yawa na madafan iko a mulkin Najeriya. Wannan ne yasa a wannan jamhuriyar ba a iya assasar da wani abu ba, da ma sojojin da suka biyo baya.

    Idan ka dubi duk waɗannan ƙasashen masu hanƙoron cigaba, a wancan lokaci Najeriya ta fi su, hatta China ballantana ka yi maganar irin su Korea da Indonesia da Malaysia amma rashin shugabanci nagari ya haifar da koma baya. Shi kuma shugabanci nagari ya gagara ne saboda ‘yan siyasa ba su ɗauki za su jagoranci mutane da adalci a tsakaninsu ba.

     Kowa kallo yake yi, yaya zai samu abin da zai samu ko ƙabilarsa su samu. Duk ƙasar da ta zama tana da irin wannan ba za ta samu cigaba ba. Muddin ‘yan siyasa ba su yi hakurin cewa za su yi mulki ba tare da cin dunduniyar wani ba, to ba za a samu cigaba ba. Kamar yadda muka faɗa Sir Abubuakar Tafawa Balewa yana ta wannan ƙoƙari amma abu ya gagara.

    A lokacin da duk ƙasashen duniya suke samun cigaba, mu kuma ‘yan Najeriya muna faɗa a tsakanin mu. A shekara ta 1968 ƙasar South Korea ta fara yin masana’antar ƙarfe (steel industry), wanda a sannan suna fama da yunwa babu abinci. Amma saboda suna da jagoranci ga abin da suka sa a gaba, cewa idan ba su da ƙarfe ba za su samu cigaba a duniya ba. Suka mayar da hankali suka yi. Duk wanda ya je ƙasar aka kai shi kamfanin mulmula ƙarfensu zai ga irin abin da suka yi.

    Mutanen Malaysia suna da matsala ta ƙabilanci a cikin tsarin zamantakewarsu, amma sun yi tunani a tsakaninsu cewa ku Malay tun da ku ne kuka fi yawa zamu bar muku shugabanci a ƙasar nan amma yaya za a yi kowa ya samu ‘yanci a yi kasuwanci don kowa ya amfana. Haka suka hakura suka yi, saɓanin Najeriya sai yaƙar juna ake yi, ba a samu wannan dacewar ba.

     Idan ba a samu wannan yarjejeniyar ba, ba za a samu zaman lafiya ba. Shi ya sa duk abin da waɗannan ƙasashen suka yi mu mutanen Najeriya muka kasa yi. Yanzu Malaysia suna fitar da kaya na sama da Dala biliyan 200-300, yayin da Najeriya muna fita da kaya ne kawai na Dala biliyan 63, South Korea wajen Dala biliyan Dari biyar ($500Billion). 

    Yanzu ƙasar da take fitar kaya na dala biliyan 63 ina take da ƙarfin tattalin arziƙi da zai kai ta har a samu cigaba, har a haɗ a su da irin waɗancan ƙasashe. Saboda haka ko ance za a yi zaɓe, ko za a yi damokuraɗiyya ko mulkin soja, idan ba a lalubo hanyar tattalin arziƙi da zai riƙe ƙasar ba, ba za a samu cigaba ba.

    Duba da yanayi tattalin arziƙinmu , yanzu duniya ta canja, baka da wani siddabaru da zaka yi, idan ba za ka yi abubuwa ba a kasarka, na kamfanoni da za a yi amfani da su a cikin gidanka. Ba ka da sinadari (chemicals) ko sumunti, ko tama da ƙarafa. To yanzu a Najeriya babu ɗaya da ake da shi. 

    Sai yanzu da ance za a samar da sumunti da fetur. Maganar gaskiya ba ka da wani siddabaru idan ba ka da waɗannan kayayyaki, sannan ka ce za ka cigaba. Tattalin arziƙinmu ba zai gyaru ba saboda ‘yan siyasa abin da ke gabansu mulki, ba sa tunanin su haɗa kai don mutanen ƙasarsu. 

     Saboda rashin haɗin kai ya zama babu wata jam’iyya a Najeriya, yanzu abin da muke da shi, taron mutane kowa yana son ya yi mulki ko ya haɗa kai da wasu ya yi damfara, ya yi cuta a zaɓe ya zama shugaban ƙasa. 

    Shi yasa zaka ga wani ya yi takarar shugaban ƙasa a jam’iyyu daban- daban, ya yi PDP, ya yi ACN, ya yi a APC, ya sake dawowa PDP, wani ya yi takara a jam’iyya wani ya fito takara sosai. Duk irin wannan babu aƙida ta siyasa da manufa da tsayawa a kan kyakkyawan ƙudiri na tsari ko na shekara takwas, ko shida ko ma hudu duk babu.

    Yanzu jam’iyyar PDP ta yi mulki a Najeriya tsawon shekara goma sha shida, amma babu abin da ta aiwatar, saboda ba ta da tsari maje-gaba, na maganar tattalin arziƙi, wanda zai fitar da ‘yan Najeriya.  Tun lokacin Obasanjo daga 1999-2015 ba a yi wani abu na tattalin arziƙi mai dogaro da abincin da zamu iya ciyar da kanmu, za mu samu lantarki, za mu samu wasu abubuwan more rayuwa dasu ba. 

    Jam’iyyar PDP ba ta samar ba haka suka gama mulkinsu. APC ta zo a 2015, ita ma ta ƙare baragadarta, sai ya zamo ‘yan siyasa, wani ne zai fito ya ce zai yi takara yana son zai zama shugaban ƙasa, ya zo ya yi abin da zai yi ya ci shugaban ƙasa, ya debo mutanensa su yi abinda suka ga dama, ta yaya zaka ce zaka ci ribar damokuraɗiyya a nan. 

    Wai wannan ma ya zama labari, shi yasa za mu yi ta zama a wuri ɗaya, idan wasu ƙasashen suna yin ƙere-ƙeren nan dole a samu mota, dole a samu jirgin sama. Wane irin tunani ne za ka haɗa Najeriya da Malaysia da ba su wuce mutum miliyan talatin ba. Amma suna fitar da kaya na sama da dala biliyan dari biyu, mu kuma muna fitar da kaya na dala biliyan sittin. Ka ga daga ji ka san wannan ƙasar ba a ɗora ta a kan gaskiya ba. Idan za a shekara dubu a Najeriya ba za a samu damar ɗora tattalin arziƙi ba, ba za a samu cigaba ba. 

    An raba kan mutane, an ce wannan ƙabilarsa daban, wannan addininsa daban , wannan sashensa daban. Ana amfani da wannan don su karɓi mulki su yi abin da suka ga dama. Ya zama cewa babu inganci a yadda rayuwa take. Duk tsarin da ake bi na tabbatar da abubuwa, haka ne. 

    idan kana maganar jam’iyya haka suke, idan kana maganar ƙungiyoyi haka suke. Mutane sun kasa ganewa cewa abin da ya kamata mu yi a Najeriya, mu haɗa kanmu, mu yi maganin matsalolin da suke damunmu, ba tare da maganar ɓangaranci ba.

    Ya kamata ko mu mutanen Arewa, ɓangaranci a siyasa ba zai kaimu ko ina ba, an yi amfani da ɓangarancin nan an kawo gwamnati ta shekara takwas, me ta yi wa mutanen arewan? Kuma a arewan nan babu wasu da za su ce idan an zo siyasa ga abu kaza da abu kaza da muke so, a matsayinka da kake takara ko ɗan Arewa ne ko ɗan kudu, mu sai ka yi mana wannan zamu zaɓeka.

     

    Babu wannan, mutane ma ba su damu da hakan ba, waɗanda suke da ikon yi ba su da damar da za su iya. Saboda ga yadda jam’iyyun suke, idan kana maganar sadarwa da kafofin yaɗa labarai, duk ba mu da su. Yanzu ko kafofin sadarwa na zamani (social media) har sai sun samu labarai daga kafofin sadarwa na ainihi, sannan suke yin wani tasiri. 

    Yanzu a gidajen talabijin guda shida da su ka yi fice a Najeriya, AIT, Arise, Channels, TVC, Trust TV , a cikinsu idan ban da Trust duk na ‘yan kudu ne. Haka idan ka zo ka ɗauki jarida, ana yin jaridu guda goma sha shida kullum, guda biyu ne kawai na ‘yan Arewa kawai na Arewa. 

    Saboda haka Arewa ba su da kafafen yaɗa labarai da za su dogara da su wajen nemowa Arewan ‘yanci da neman goyon bayan da suke buƙata. Kuma ‘yan siyasa wannan ba shi ne a gabansu ba, kowa hanƙoro yake yi a ba shi takarar gwamna ko ɗan majalisa, ya je ya yi ya dawo kuma da ma mutanensa duk yunwa suke yi. 

    Tunda yanzu, gwamnati ba ta ba da ilimi kyauta, ta yaya za a yi mutane kansu ya waye, tun da babu ilimi. Sun cutar da al’umma, sun mayar da su almajirai da ‘yan ta’adda da ‘yan banga saboda rashin ilimi. Ga shi kuma babu aikin yi, haka kuma dama idan siyasa ba ta zama daidai ba, ba yadda za a yi ta tabbatar da tattalin arziƙi, ya zama daidai. 

    Ana ta zagayawa a wuri ɗaya (cycling) idan wannan zagaye ba a dakatar da shi ba babu maganar cewa za a zo a yi zaɓe, ko za a yi damokuraɗiyya dai-dai ko za a samu shugabanni nagari. Duk wannan sai dai ya zama labari, kuma duk abin da da zai faru a duniya, mu ne koma-baya, sai dai a bar mu muna suɗi.

     Idan motoci sun mutu a kawo mana daga Korea, daga Amurka, daga inane? Tun da lantarki ma mun kasa samu, balle har ace za mu yi masana’antu, ɗan Arewa ma ya riƙe ya ƙasa. 

    Saboda haka, dole mutane su ce ai damokuraɗiyya ba ta zamar mana alheri ba! Duk da cewa mutane sun samu ‘yanci da sauran abubuwa amma tun da babu tsayayyen tattalin arziƙi, damokuraɗiyya ba ta samar musu ba. kuma ba za ta samar musu ba, a dai wannan tsari da ake yi saboda ‘yan siyasar nan suna yin siyasa ne saboda biyan buƙatunsu.

     Idan za ka tsaya takara ko na jiha ko ɗan majalisa, sai kana da ubangida nasu amma yanzu har sun fara caccanza su. Sai dai kuma wani yanayi daga Allah Ya kawo juyinsa, ko wani juyi ya zo a wani zamani, a samu mutane nagari, ya zama abin ya tabbata.

     Mu daina tunanin cewa Najeriya ko tsarin gudanar da mulki ne, wato ko ƙarfin iko daga majalisa (parliament) ko na shugaba mai cikakken iko (presidential) duk ba haka ba ne, mutane ne da matsalar. Idan an samu wasu da zasu maye gurbinsu ba, wanda hakan yana da wahala.

    Mun gani a ƙasar Turkiyya zuwan Erdugon, duk wahalar da ƙasar ta sha, sai da aka samu wasu suka kutsa, amma idan ba haka aka yi ba, waɗannan mutanen ko suna PDP ko suna APC, jam’iyyu haruffa ne kawai ya banbanta su. 

    Shi ya sa za ka ji  mutum yau APC gobe kuma ka ji shi a PDP jibi ya koma Labour, haka dai za ka ga suna ta yi. Kuma abubuwan nan da suke faruwa a duniya ba wai maganar tafiya sama ba ce. 

    Ya gagara a ce gwamnatin Najeriya shekara sittin ba za ta iya ciyar da kanta ba, shekara sittin an samu ‘yancin mulki kai, amma Najeriya ba za ta iya fitar da kaya ba, kai ko da zama muke muna ciyar da kanmu da sauran abubuwa kamar yadda China take yi da yanzu mun cigaba.

    Ɗan siyasar Najeriya abin da ke gabansa, ya samu mulki amma ba yadda zai ciyar da ƙasar gaba ba. Waɗanda suke zama suke magana a kafofin yaɗa labarai ko a ina ne, sai ka yi ta shan mamaki, su kuma ‘yan siyasar sun fi son waɗanda za su fito suna zagin wane ko su ce wane ɓarawo ne, ko wanda zai zo bambaɗanci. 

     To wannan shi ne ya sa muke da matsala. Idan ba mu canja siyasar mu ‘yan arewa ba, ba za mu samu cigaba ba. Dama su ‘yan kudu tafiya suke bisa tsari, don haka za su yi ta samun cigaba. Saboda mu ba mu fahimci inda duniya ta sa gaba ba. Muna fatan Allah ya bamu zaman lafiya a ƙasa, ya magance mana fitintinun da suka addabe mu, amin, Subuhanakallahumma… 

     

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

     

                                

  • Asalin Kiɗan Fiyano

    Asalin Kiɗan Fiyano

    Encyclopedia Americana (2003), ta bayyana cewa, a shekarar 1709;

    Fiyano – Bartolommeo Cristofori ya ƙirƙiri wani abin kiɗa da ake kira gravicembalo col piona e forte. Wanda yake samar da sautin piano (soft) da forte (loud). Daga haka aka samu sunan pianoforte ko fortepiano. Daga haka aka gajerce sunan zuwa piano.

    Binta (2011:76) ta bayyana cewa “Ana jin mutumin da ya fara ƙirƙiro fiyano, shi ne Bartolemo Cristofori ɗan ƙasar Italiya. Mawaƙi kuma ƙwararre a kan sanin kayan kiɗa wanda kuma iyalan Medici suka riƙe shi.

    Amma zuwa ƙarshen 1700, kiɗa da fiyano ya zamo abin zaɓi ga masu haɗa kiɗa da kuma su kansu mawaƙan”.

    Zainab (2009:83) ta bayyana asalin fiyano daga ƙasar Italy aka ƙirƙire shi, tun a ƙarni na sha tara (19), kuma Pianoforte shi ne cikakken sunanta, kuma sunan asali. Pianoforte ita ce nau’in fiyano na farko da aka fara samu. Mawaƙi mai amfani da fiyano ana kiransa pianist. Akwai wasu abubuwa da suka haɗu, suka tayar da fiyanon kamar strings da keys da pedal da pianostool.

    Enclyclopedia Americana (2003) da Concise English Dictionary (2006), sun ƙara bayyana cewa, fiyanon na da nau’o’i biyu cikinsu akwai: Grand Piano da Upright Piano.

    Grand piano ita ce wadda take da madannai guda tamanin da takwas (88), hamsin da biyar (55) farare ne, su kuma baƙaƙe talatin da shidda (36) ne. Ana latsa madannan tsawon inci 3/8 (9.6 mm). Ita Upright piano tana da wasu ɓangarori na grand piano, sai dai akwai ‘yan bambance bambance a tsarinsu.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Wuraren da Ake Kiɗan Fiyano (Situdiyo)

  • Mulkin Soja Da Jamhuriyya Ta Uku (1983-1999)

    Mulkin Soja Da Jamhuriyya Ta Uku (1983-1999)

    Juyin mulkin soja da aka yi a 1983 ya faru ne a bikin sabuwar shekarar. Haɗin gwuiwar wasu manyan hafsoshin sojojin Nijeriya ne, suka yi haɗin gwuiwa, kuma hakan ya haifar da kifar da Jamhuriyar Nijeriya ta biyu da kuma sanya Manjo Janar Muhammadu Buhari a matsayin Shugaban Ƙasa. Juyin mulkin soja na Muhammadu Buhari jim kaɗan bayan sake zaɓen shugaban ƙasa a 1984 ana ganin sa a matsayin wani ci gaba mai kyau. Buhari ya yi alƙawarin manyan gyare-gyare, amma gwamnatinsa ba ta yi kyau sosai fiye da wanda ta gabata ba. An hamɓarar da gwamnatinsa da wani juyin mulkin soja a 1985.
    An hambarar da Janar Buhari a shekarar 1985, bayan juyin mulkin soja, a ƙarƙashin jagorancin Janar Ibrahim Babangida, wanda ya kafa Majalisar Rundunar Sojojin Ruwa kuma ya zama shugaban sojoji da kwamandan sojoji a manyan hafsoshin sojojin. A 1986, ya ƙafa Ofishin Siyasar Najeriya a 1986 wanda ya ba da shawarwari ga sauyawa zuwa Jamhuriyar Nijeriya ta Uku.
    A cikin 1989, Babangida ya fara yin shirye-shirye don sauyawa zuwa Jamhuriyar Nijeriya ta Uku. Ya ba da izinin kafa jam’iyyun siyasa, sannan ya ƙirƙiro da tsarin jam’iyyu biyu, tare da Social Democratic Party (SDP) da Babban Taro na National Republican Council(NRC) gabanin babban zaben shekarar 1992 Ya buƙaci dukkan ‘yan Nijeriya da su shiga dukkan ɓangarorin, waɗanda marigayi Cif Bola Ige ya ambata da “hannayen kuturu guda biyu.” -A sashe biyu ɗin sun kasance shawarwarin ofishin Siyasa ne.
    A watan Nuwamba 1991, bayan da aka gudanar da ƙidaya, Hukumar Zabe ta Kasa (NEC) ta sanar a ranar 24 ga Janairun 1992 cewa duka majalisun dokoki biyu na babban taron ƙasa da na shugaban ƙasa za a yi a ƙarshen shekarar. An karɓi wani tsari na jefa ƙuri’a, wanda ake kira zaɓi na A4. Wannan tsari ya ba da shawarar cewa duk wani ɗan takarar da yake buƙatar wucewa ta hanyar karɓar duk zaɓaɓɓun mukamai daga Ƙaramar Hukuma, Gwamnatin Jiha da kuma Tarayya.
    Babangida ya tsira daga yunƙurin juyin mulkin Nijeriya na 1990, sannan ya jinkirta sake komawa ga alkawarin da aka yi wa dimokiradiyya zuwa shekarar 1992. Zaɓen shugaban ƙasa na 1993 da aka yi a ranar 12 ga Yuni, na farko tun bayan juyin mulkin soja a 1983. – ya nuna ‘yan takarar Moshood Abiola da Babagana Kingiɓe na Social Democratic Party (SDP) sun kayar da Bashir Tofa da Slyvester Ugoh na babban taron Jam’iyyar National Republican (NRC) sama da miliyan biyu da dubu ɗari uku.
    Ko yaya, Babangida ya soke zaɓen? Wanda ya haifar da zanga-zangar fararen hula da suka rufe ƙasar cikin makonni. A watan Agusta na 1993, Babangida daga ƙarshe ya cika alkawarinsa na miƙa mulki ga gwamnatin farar hula, amma ba kafin naɗa Ernest Shonekan, shugaban gwamnatin rikon kwarya, An ɗauki tsarin mulkin Babangida a matsayin mafi cin hanci da rashawa, kuma yana da alhakin ƙirƙirar al’adar cin hanci da rashawa a Nijeriya.
    A ƙarshen shekarar 1993, gwamnatin wucin gadi ta Shonekan, ta taƙaice a tarihin siyasar ƙasar nan a cikin juyin mulkin soja a shekarar 1993, ƙarƙashin jagorancin Janar Sani Abacha, wanda ya yi amfani da ƙarfin soja wajen daƙile ci gaba da tashin hankalin farar hula. A 1995, gwamnati ta rataye masaniyar muhalli Ken Saro-Wiwa kan zarge-zargen kashe-kashen da ya yi wa dattawan Ogoni hudu.
    An gabatar da ƙarar ne a ƙarƙashin dokar Alien Tort Statute a kan Royal Dutch Shell da Brian Anderson, shugaban kamfanin na Shell na Nijeriya, sun yanke hukunci, ba tare da yanke hukunci ba a yayin da Shell ke ci gaba da musanta alhakin. Da yawa  miliyan dala asusun da aka gano zuwa Abacha an gano su a 1999.
    Wannan tsarin mulki ya kawo ƙarshe a shekarar 1998, lokacin da azzalumin sarki ya mutu a cikin gari. Ya saci kuɗaɗe don kashe asusu a bankunan yammacin Turai sannan ya sha alwashin shirya juyin mulki ta hanyar kamewa da karɓar janar da ‘yan siyasa. Wanda ya gaje shi,shi ne Janar ABDULSALAM ABUBAKAR, ya amince da sabon tsarin mulki a ranar 5 ga Mayu 1999 wanda ya ba da damar gudanar da zaɓuka masu yawa.

     

  • Taƙaitaccen Tarihin Kano Kashi Na Ɗaya(1)

    Taƙaitaccen Tarihin Kano Kashi Na Ɗaya(1)

    Taƙaitaccen tarihin Kano kashi na ɗaya

    Kano na ɗaya daga cikin manyan birane a ƙasar Hausa. Kano ita ce cibiyar kasuwanci ta Nijeriya gaba ɗaya, jihar Kano tana da ƙananan hukumomi guda arba’in da hudu(44).
    Kano gari ne da yake da masarauta mai ɗumbin tarihi, Masarauta ce mai kwarjini a cikin Ƙasashen Hausa da kewaye.
    Haka kuma, Kano gari ne babba wanda mazauna cikinsa suna magana da harshen Hausa. Kano shi ne gari mafi yawan jama’a a Nijeriya gaba ɗaya.
    Cikin birnin Kano akwai ƙofofi kamar haka:Kofar Gadon Kaya, Kofar Famfo, Kofar Na’isa, Kofar Nassarawa, Sabuwar Kofa, Kofar Mazugal, Kofar Dawanau, Kofar Dan Agundi, Kofar Duka wuya, Kofar Ruwa, Kofar Kansakali da kuma Kofar Mata.
    Kano gari mai tarin mutane da tasirin Sarauta
    Yawan mutanen da suke garin Kano ya haura kimanin mutane miliyan goma (10,000,000) a ƙidayar da aka yi a shekara ta alif dubu biyu da shida (2006).
    Kano tana da matukar tasiri a yawan mutane a Nijeriya, saboda ita ce ta fi kowace jiha yawan mutane a Najeriya.
    Idan ka zo Kano, za ka samu mutane daga ko’ina a fadin duniya, tun daga na Kudancin Nijeriya, zuwa ƙasashen dake makwabtaka da Nijeriya, haka kuma, za ka tarar da mutanen Sin, wato (china), da kuma na kasashen Larabawa har da Turawan Yammacin duniya. Mutanen Kano sun shahara wajen addini sosai.
    Sana’ar Rini
    Al’ummar Kano sun kasance masu son sauraren rediyo
    Kano ta yi suna wajen kasuwancin da ta bunƙasa a kai, har ya zamana ana cewa da ita Cibiyar Kasuwanci, haka kuma tarihin Kano ya nuna daman can Kano tana da suna wurin cinikayya tsakaninta da mutanen Gabas ta Tsakiya
    Domin karanta takaitaccen bayani akan jihar kano danna nan
  • Sojojin Nijeriya

    Sojojin Nijeriya

    An tuhumi sojojin na Nijeriya da kare Tarayyar Nijeriya, da tallata muradun tsaron duniya a Nijeriya, da tallafawa ƙoƙarin wanzar da zaman lafiya, musamman a Yammacin Afirka. Wannan tallafi ne ga koyarwar wani lokaci ana kiranta Pax Nigeriana.

    Sojojin Nijeriya sun ƙunshi SOJOJIN ƘASA, SOJOJIN RUWA, da SOJOJIN SAMA. Sojoji a Nijeriya sun taka rawar gani a tarihin ƙasar tun samun ‘yancin kai. Juntas daban-daban sun ƙwace ikon ƙasar kuma suka mulke ta a mafi yawan tarihinta. Zamanta na ƙarshe na mulkin soja ya ƙare ne a shekarar 1999 biyo bayan mutuwar ba-zata da tsohon mai mulkin kama-karya Sani Abacha ya yi a 1998. Magajinsa, ABDULSALAM ABUBAKAR, ya miƙa mulki ga zaɓaɓɓen shugaba wato Olusegun Obasanjo na dimokuradiyya a shekara 1999.
    A matsayinta na ƙasar da ta fi kowace ƙasa yawan jama’a a Afirka, Nijeriya ta sake tura sojojinta a matsayin rundunar wanzar da zaman lafiya a Nahiyar. Tun daga 1995, an tura sojojin Nijeriya, ta hanyar umarnin ECOMOG a matsayin sojojin kiyaye zaman lafiya a Laberiya (1997), Ivory Coast (199i- 1997), da Saliyo (1997 – 1991). A ƙarƙashin wani umarni na Tarayyar Afirka, ta girke dakaru a yankin Darfur na Sudan don ƙoƙarin samar da zaman lafiya.

    Domin sanin cikakkun bayanai a kan sojojin Nijeriya danna nan