Category: ILIMIN TARIHI

  • Dangantakar Annabi Muhammad Da Rasuwar Mahaifinsa

    Dangantakar Annabi Muhammad Da Rasuwar Mahaifinsa

    1.Mahaifinsa: Shi ne Abdullahi ɗan Hashim ɗan Abdulmanaf ɗan Ƙusayyun ɗan Kilab.

    2.Mahaifiyarsa:- Ita ce Aminatu ‘yar wahabu ‘yar Abdulmanaf ‘yar Zuhra ‘yar Kilabu.

    3.Mahaifiyarsa da Mahaifinsa;- Sun haɗu a kakansa na biyar (5), shi ne Kilabu.

    4.Haƙiƙa Baffansa ya rasu, yana ɗan shekara goma sha Takwas (18), an rufe shi a garin Madinah, bai bar masa komai ba na daga dukiya.

    Sharhi:

    A lamba ta ɗaya (1), ya ce Mahaifinsa shi ne Abdullahi (shi ne wanda ake masa inkiya da Abu-alƙamata), shi ne wanda ya auri Aminatu ‘yar Wahab, Azzuhriyyatu Baƙuraishiya, sai Abdulmuɗalib, wanda ya auri Fatimatu ‘yar Amiru Almakazumiya (Abdulmuɗalib yana ɗaya daga cikin manyan mutane Ƙuraishawa, wanda Ƙuraishawa, suke haɗuwa akan ra’ayinsa, sannan suna gabatar da shi a wajen Mu’amalarsu).

    Sai Hashimu shi ne wanda ake kira da Abu-Haris Za’im Baƙuraishe a lokacin Jahilya, sannan yana ɗaya daga  cikin manya-manya labarawa. Ya kasance yana shayar da masu aikin Hajji ruwan Zam-zam. Sannan shi ne wanda ya auri Salma ‘yar Amru Alnajariyatul Khazrajyya.

    Sai Abdulmanaf yana ɗaya daga cikin Kakannin Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam), an ce sunansa Mugira Abdulmanaf, laƙabinsa ne, shi ne wanda ya auri Aitika ‘yar Murra Assalamiyatu (ɗaya daga cikin ƙabilar Ƙaisun-ilani bin Madhar).

    Sai Ƙusayyun (Shi ne shugaban Ƙuraishawa, sannan kuma shi ne wanda aka yake kula da ɗakin Harami) shi ne wanda ya auri Hubayyu ‘yar Hulilu Alku Za’iyatu (Alkhuza’atu Bin Iliyasu Bin Madhar) sai Kilabu (ana yi masa laƙabi da Kilab ne, saboda ya kasance yana yawaita yawan farauta da Kare.

    Amma sunansa Hakimu ko Uwarta), Shi ne wanda ya auri Fatimatu yar Sa’adu, sai Murrata shi ne wanda ya auri Hindu ‘yar Sariru daga ƙabilar Banu Fahra Bin Malik (Shi ne Abu-Husaisu) Shi ne ya auri Mahaifiyar Ka’abu Mariyatu ‘yar Shaibana daga ƙabilar Fahra. Sai Lu’ayyi shi ne wanda ya Mahaifiyar Ka’abu Mariyatu ‘yar Ka’abu daga ƙabilar Kadha’ata.

    Sai Ghalib shi ne ya auri mahaifiyar Lu’ayu Salma ‘yar Amaru Alkhuza’i l, sai Fahra (shi ne wanda ƙuraishawa suke yi masa laƙabi da Ahlul Ashira), shi ne wanda ya auri mahaifiyar Ghalib, Laila ‘yar Sa’adu daga Haulin. Sai Malik shi ne wanda ya auri Jundilatu ‘yar Haris daga ƙabilar Jurhum).

    Sai Nadhir ya auri Atika ‘yar Adwana daga ƙabilar ƙaisun I’ilani, sai kinanatu shi ne wanda ya auri Burratu ‘yar Murra Addi, sai Mudrakata, amma sunansa Amru) shi ne ya auri Salma ‘yar Aslama daga Kabilar Kudha’atu,  sai Nazar shi ne wanda ya auri Saudatu ‘yar Akka sai Ma’adu.

    Danna nan don karanta jikokin annabi

    Edita; Rumasa’u Muhammad kallamu

     

  • Tarihin Adamu Yero Hunƙuyi

    Tarihin Adamu Yero Hunƙuyi

    An haifi Adamu Yero a garin Hunƙuyi a cikin ƙaramar hukumar Kudan, jihar Kaduna a ranar 12/02/1960 ya yi karatu a makarantu kamar haka;

    1. LGEA Firamare School Hunƙuyi 1972-1978

    2 UPE teacher collage Zaria 1978-1983 Grade 11

    3. Collage of Education Kafanchan 1984-1987 NCE

    4. ABU Zaria 1987-1990 BA (Hausa)

    5. KDS Poly Zaria 1997-1998 ADPA

    6. ABU Zaria 2012-2015 MA (Hausa)

    7. Rauda School Al’aƙsa center for education and vocational training Zaria June 2008

    8. KD state civic servant commission (exam)  June 2003 statement of research

    9. Teacher Registration Council(TRC)  of Nigeria April 2005 Certificate of Registration

    Ayyukansa da ƙwarewarsa

    1. Ya yi aiki a Gaskiya Firamare School Zaria  a 1982 T/ Practice .

    2. Ya yi aiki a Ƙofar Gayan Firamare School  Zaria a 1983 T/Practice .

    3. Ya yi aiki a Domoso Firamare School Hunƙuyi a 1983-1984  V/teacher .

    4. Ya yi aiki a Government Secondary School Maƙarfi a 1985- T/Practice .

    5. Ya yi aiki a Government Secondary School Maƙarfi a 1987 T/Practice .

    6. Ya yi aiki a KWSCOE Illorin a 1991-1993 Asst lecturer.

    7.Ya yi aiki a LGEA MIGA Maƙarfi a 1993-2002 HOD/PM.

    8. Ya yi aiki a Kudan Hunƙuyi a 2002-2006 HOD /PM.

    9. Ya yi aiki a LGEA GIGA Giwa a 2006-2007 HOD/PM.

    10. Ya yi aiki a LGEA Kudan Hunƙuyi 2007-2015 a matsayin shugaban ilimi na ƙaramar hukuma (E. S).

    11. Ya yi aiki a Maƙarfi zonal officer (SUBEB)  2015

    12. A yanzu kuma yana aiki a Quality Assurance and Evaluation (QAE)

    Rubuce-rubucensa

    1. Yero Adamu: Harshen Hausa da batun harshen ƙasa, wanda aka wallafa a Gaskiya ta fi kwabo a watan mayu a 1991.

    2. Yero Adamu : Matsayin rubutaccen wasan kwaikwayo a rubutaccen adabin Hausa (ABU Zaria) a watan juni a 1990.

    3. Yero Adamu : Koyo da koyar da Hausa a matsayin harshe na biyu a COE Illorin a 1993.

    4. Yero Adamu : Tashen machukule a matsayin wasan kwaikwayo na musamman a ƙasar Zazzau ( MA Thesic, ABU Zaria)Dec 2014.

    Lambobin yabo da aikin sa-kai

    1. Hunƙuyi District Development Forum a matsayin Sec. Gen a 2007/2009.

    2. National Association of Educational Secretary of Nigeria Kaduna Branch (NAESN) a matsayin Sec. Gen 2008/2015.

    3. National Association of Education Secretary of Nigeria 2012/2015.

    4. Award of excellence as the outstanding Educational Secretary in KDS. Honored by AOPSHON June 2011.

    5. Award of excellence as the outstanding Educational Secretary in Northern Kaduna. Honored by Media monitors Kaduna state may 2012.

    (Mun samu wannan jawabi  ne daga bakinsa a ranar Asabar 12/12/2020 da misalin ƙarfe 10:03 na safe wanda ya turo min da  kansa ta  WhatsApp ɗina).

    Domin karanta cinikin bayi a tarihin Afrika danna nan

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Larabci Da Yanda Ya Shigo Ƙasar Hausa

    Larabci Da Yanda Ya Shigo Ƙasar Hausa

    Da yake addinin Musulunci yana tafiya ne ɗanɗan da yaren Larabci ta yadda duk in da aka ga ɗaya to ba shakka ɗayan ma ya na nan in aka yi duba na tsanaki, duk da kuwa cewa shi Larabci bai cika neman rakiyar Musulunci ba in yai aniyar shiga wani lardi. Akwai zantuka mabambanta dangane da shigowar waɗannan tagwaye ƙasashen yammacin Afirka.

    Ustaz Sa’id Galadanci a littafinsa mai suna (حركة اللغة العربية وآدابها في نيجيريا) ya ambaci wasu hanyoyi da masana suka bayyana cewa ta su ne addinin Musulunci da yaren Larabci suka samu shigowa wannan yanki namu na ƙasar Hausan waccen lokacin. Idan muka ajiye batun shigowar Sahabin Annabi (saw) Wasil bin Aɗa(ra) wanda aka ce shi ne ya kawo Musulunci Afirka ta wannan lokacin, ko in ce aka ce da’awarsa ta dangane da wani yanki na lardin, kamar yanda wasu suka ce Libiya ce ƙasar da ya dakata, amma bayan wafatinsa da’awa ta cigaba har ta mamaye yankin gaba ɗaya.

    Duk da cewa ba maganar shigowar addinin Musulunci wannan yanki nake ba, amma babu laifi da na ɗan ci ramaniya na wuce. Ba kamar sauran yankuna da addinin Musulunci ya je musu ta ƙarfi ba, wannan kuma har yankin labarawan mu nan ba a kashe ko daki ko mutum ɗaya da sunan ya yi imani ba, waɗanda suka zo da’awa suka yi ba jahadi ba.

    Mu koma ga batun shigowar larabcin da na faro. Maganar da ta tabbata cikin littattafan tarihin zuwan Larabawa wannan yanki ta nuna cewa lalle Larabci shi ya fara zuwa ƙasar Hausa kafin addinin Musulunci ya shigo, domin kuwa a tarihi akwai waɗanda aka kira da “TUJJARU” da kuma “DU’ATU”.

    Tujjaru waɗansu mutane ne da suka shigo ƙasar Hausa domin kasuwanci, waɗanda su ne baƙuwar Al’umma ta farko da bahaushen wannan yanki ya fara mu’amala da su daga ƙabilun da ke nesa sosai da ƙasar Hausa. Lokacin da waɗannan rukuni suka shigo ƙasar Hausa sun iske al’ummar da ba ta jin yarenta haka su ma ba sa jin nata yaren.

    Manyan abubuwan da waɗannan ‘ƴan kasuwa suke siyarwa su ne dabino da kuma makamai, irinsu masu, takubba da sauransu. An ce lokacin da waɗancan Larabawa suka fara tallata dabinon da suka zo da shi sun fuskanci matsalar saɓanin harshe, wanda kuma shi ne ya ba su haske tun farko kan cewa lalle suna da buƙatar sanin harshen waɗannan al’umma da suka tarar domin sauƙaƙa harkar siye da siyarwa.

    Bahaushen wancan lokacin bai san kalar dabino irin na ƙasashen larabawa ba sai a wannan karo dan haka yana da buƙatar farko ya san menene ma tukunna sannan ya siya idan yana da buƙata. Da larabawa suka fahimci Hausawa suna yi wa wannan haja tasu kallon ko meye wannan?

    Sai suke amfani da kalmar “KUL” wacce a yarensu ta ke nufin “CI” ma’ana dai ya kai wannan da ya ke kallon wannan abu wanda kallon ke nuna kamar bai san menene ba, “CI” ka ji yanda yake, sai aka yi rashin sa’a domin kuwa kalmar “Kul” a yaren Hausa tana nufin “BARI” ko “KAUCE” ma’ana dai kalma ce da take nuni da hani, a can kuma tana nufin umarni, don haka duk mutumin da ya zo zai sayi dabino sai Balarabe ya ce masa “KUL” sai mutum ya kauce ya ba su guri abinsa, wannan shi ne abin da ya fara haɗa waɗannan yaruka mu’amala.

    Su kuma DU’ATU sun shigo ne domin yaɗa addinin Musulunci duk da kuwa an ce waɗancan ‘ƴan kasuwar sun yi abin da suka yi wajen yaɗa Musulunci su ma, musamman yanda waɗanda suka sauke su da waɗanda suka ɗauka yara a kasuwancin da suke suka karɓi Musulunci, amma dai ba kamar yanda DU’ATU suka yi ba, a nan za mu iya cewa DU’ATU su ne kamar missionaries da suka shigo don yaɗa addinin masihiyanci.

    Da yake zan yi magana ne a kan alaƙa ba tarihi ba kai tsaye, amma babu lefi idan na tsagaita haka na kuma tunkari abin da zai fisshe ni na bayyana wannan daɗaɗɗiyar alaƙa ta fuskar yare da al’adu.

    Kamar yanda yake a bayyane cewa Larabci da larabawa sun samu tagomashin girmamawa da soyayya ne kasancewarsu wasu kayan aiki ko alamomi manya da ke nuni kai tsaye ga samuwar addinin Musulunci a duk bigiren da aka ji ko aka gansu. Wannan tasa yaruka da dama kan saki al’adu wani lokacin ma da shi kansa yaren nasu su rungumi Larabci da al’adun Larabawa a tsammaninsu da ƙoƙarinsu na zama yanda Musulunci yake son su zama.

    Misali mu ɗauki yaren Hausa da al’adun Malam Bahaushe, ba na jin a tarihi an taɓa samun wata ba’ajamiyar al’umma da take ganin mutuncin Larabci da Larabawa kamar Hausawa, na san da cewa wasu ma barin yarensu suka yi suka rungumi Larabcin wanda ta kai ga yau babu ɗuriya bare labarinsa. Duk da mu ma ana cewa kaso 60 cikin ɗari na kalmominmu Larabci ne (duk da akwai waɗanda suke ganin adadin bai kai haka ba, kuma sahihin bincike ya gaskata su) wanda hakan ta faru ne sakamakon kasancewarsa harshen ƙetare na farko da Bahaushe ya fara mu’amala da shi.

    Daga cikin tagomashin da Larabci ya samu akwai karɓuwar wasu kalmominsa zuwa yaren Hausa kamar yanda na bayyana da farko wanda mai karatu zai so ya san dalilin da yasa ake ganin kalmomin ba na Hausa ba ne asalaninsu, da kuma yanda ake bi a gano.

    Ga masu karantar kimiyyar harshe akwai hanyoyi da dama da ake iya gane asalin inda kalma ta tsiro, shigowa ta yi ko ‘ƴarsalai ce, daga cikin hanyoyin da ake bi a gano asalin kalmar Larabci a yaren Hausa akwai la’akari da harufan “AL” (ma’arifa) a farkon kalma, ma’ana kusan duk kalmar Hausa da ta fara da “AL” to ana kyautata zaton balarabiyar Kalma ce asalinta, misalinsu su ne:

    1-Alkama – Al-ƙamha
    2-Alkaki – Al-ka’aka’a
    3- Allo – Al-lauhu
    4- Almakashi – Al-miƙsu
    5- Albasa -Albaslu.

    Amma kuma in muka yi duba ya zuwa irin waɗannan kalmomi za mu ga daman yawancinsu kalmomi ne da suke nufin abubuwan da larabawan ne suka fara shigo mana da shi. Don haka bahaushe yake amfani da sigar da ya ji mai su “Balarabe” yana kiransu shi ma yake kiransu da shi.

    Alhamdlilah gwara kalmomi ma daman ana yi domin shi ma larabcin ya aro da dama daga Farisanci, ga wanda yake karantar kimiyyar harshe na Larabci ya san da wannan ƙadiyar. Kuma dama aro ba kashi ba ne ga yare, bilhasli ma duk yaren da ba ya aro to akwai yiwuwar ya mutu.

    Danna nan don karanta zuwan ilimi ƙasar Hausa

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Tarihin Dakta Ado Zakari Kudan

    Tarihin Dakta Ado Zakari Kudan

    An haifi Dr. Ado Zakari a garin a Kudan a gidan Makaɗa a ranar 30 September 1962 a ƙaramar hukumar Kudan jihar Kaduna.

    Dr. Ado Zakari yana ɗaya daga cikin mutanen da suke bayar da gudunmawar su a cikin jihar Kaduna da kuma ƙasa baki ɗaya, duba da yadda harkar kula da lafiya take da matuƙar muhimmanci ga rayuwar ɗan-Adam ya sa Dr. Ado Zakari yake zuwa mahaifar sa a duk ranar Asabar, domin duba marasa lafiya kyauta tare da rubuta musu magungunan da za su yi amfani da su domin samun lafiya.

    Karatun sa

    1. Ya yi karatu a Model PrimarySchool 1971-197.

    2. Ya yi karatu a GSS Maiduguri 1977-1982.

    3. Ya yi karatu a school of basic studies ABU Zaria 1982-1983

    4. Ya yi jami’ar Ahmad Bello (ABU) 1983-1989.

    5. Ya yi karatu a ABU teaching hospital 2005-2010.

    Aikin sa

    Yana aiki da ma’aikatar lafiya ta jihar Kaduna, wanda ya riƙe muƙamai da dama a cikin jihar Kaduna kamar haka;

    1. Ya riƙe Medical Officer II 1991-1995.

    2. Ya riƙe Medical officer I 1995-1998.

    3. Ya riƙe Senior Medical Officer II 1998-2001.

    3. Ya riƙe Senior Medical Officer I 2001-2003.

    4. Ya riƙe Principal Medical Officer II 2003-2007.

    5. Ya riƙe Principal Medical Officer 1 2007-2010.

    6. Ya riƙe Chief Medical Officer 2010-yau.

    7. Ya zama Consultant Public Health Physicians 2016- yau.

    (Mun samu wannan bayanin ne daga bakinsa, wanda ya rubuta ya turo min ta WhatsApp a ranar 20/01/2021) .
    Danna nan don Karanta tarihin Malam Mammada Kudan

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Tarihin Marigayi Malam Mammada Kudan

    Tarihin Marigayi Malam Mammada Kudan

    Marigayi malam Mammada (wato Muhammad wanda aka fi sani da malam Mammada) an haife shi a garin Kudan a watan Azimi. Sunan mahaifinsa shi ne Malam Abdulhamid, mahaifiyar sa kuma Habiba (‘Yar gero), ya haifi ‘ya’ya goma sha shida a duniya, guda shida sun rasu kafin ya rasu.

    Ya auri mataye guda biyu daga cikin ‘ya’yan sa akwai Muhammad da Suleman da Ɗayyabu da Hafsat da dai sauran su. Ya yi karatun allo a garin Kudan da kuma Zaria gidan malam na Iya. Ya kuma tafi Kano ya yi karatu a wajen malamai da dama, ya kuma tafi Azare ta jihar Bauchi, ya yi karatu a can ma.

    Malam Mammada mutum ne wanda yake sana’ar siyar da garwa daga Kudan zuwa Kano, domin samun abin sa wa a baka wai ya fi a rataya in ji masu iya magana. Saboda haka malam Mammada ya samu ilimi mai zurfi a ɓangaren ilimi addinin musulunci, wanda har Alaramma malam Surajo Yunusa Kudan, wanda ya rubuta littafi akan rabon gado a wajensa ya yi  karatu.

    Haka kuma shi ne kusan babban ɗalibin sa, saboda duk inda zai tafi wajen koyar da karatu ko rabon gado, to da malam Surajo Yunusa Kudan yake tafiya. Haka kuma a lokacin da yake raye malam Mammada har sai ta kai matakin da dukkanin  littafin da mutum ya buɗe, to malam Mammada yana kishingiɗe zai biya maka littafin ba tare da ya tambaye ka sunan littafin ba.

    Haka kuma, idan mutum ya yi kuskure wajen karantowa, to sai dai ka ji kawai ya gyara ma yadda wajen yake, haka kuma Malam Shitu Bashir Kudan ya tabbatar mana da cewa idan mutum kullum zai dinga zuwa wajen malam Mammada karatu har tsawon  rayuwar sa, to ba zai iya ƙure ilimin da Allah ya ba shi ba, sannann kuma shi ne wanda yake fassara alkur’ani a masallacin juma’a na garin Kudan a lokacin da yake raye, haka kuma ya rasu a watan Azimi a ranar 16/09/1440 hijira=2018

    (Mun samu waɗannan jawaban ne ta hannun ɗan sa wato Suleman Muhammad wanda ya kira a waya ranar litinin 17/03/1442 hijira=02/11/2020 da misalin ƙarfe goma sha ɗaya na safe a lokacin ina gidan Musa Gauda shi kuma yana Kaduna).

    Domin karanta cinikin bayi a tarihin Afrika  danna nan

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Ma’anar Aure A Ƙasar Hausa 2

    Ma’anar Aure A Ƙasar Hausa 2

    Aure wani zama ne halastacce tsakanin mace da namiji bisa ga matsayin miji da mata, wanda al’adar Bahaushe da kuma addinin musulunci suka amince da shi. Babban dalilin da yasa ake yin aure shi ne, don samun yaɗuwar jinsi a doron ƙasa gami da wanzuwar al’umma. Aure ba ya inganta sai da waliyyi (mace waliyyi, namiji kuma wakili), siga, sadaki da kuma shaidu.

    Abubuwan da suke da alaƙa da aure a ƙasar Hausa

    1. Samartaka (Zance ko hira).

    2. Sallama/ nuna kai.

    3. Toshi.

    4. Baiko / sa rana.

    5. Sa lalle/ rufi.

    6. Ɗaurin aure.

    7. Wankan amarya.

    8. Biki (gidan su amarya da ango).

    9. Biɗar kai/ buɗan kai.

    10. Sayen baki.

    11. Kai Gara.

    12. Gai-da surukai.

    13. ‘Yar zaman ɗaki/ ƙanwar rana.

    Danna nan don karanta rabe-raben auren Hausawa

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Tarihin Hajiya Halima Jumare Kudan

    Tarihin Hajiya Halima Jumare Kudan

    An haifi Hajiya Halima Jumare a garin Kudan, ƙaramar hukumar Kudan, jihar Kaduna a ranar 11th Afrilu a shekara ta 1964, ta yi karatu a Girls’ Boarding Firamare School, Zaria a shekara ta 1976, ta yi karatu a Women Teachers’ College, Kaduna (GR.II) a shekara ta 1981, ta yi a karatu a College of Education, Kafanchan (NCE) a shekara ta 1985, ta yi karatu a Ahmadu Bello University, Zaria (B.ED) a shekara ta 1990, ta yi karatu a Ahmadu Bello University, Zaria (PGDM) a shekara ta 2001, ta yi karatu a Ahmadu Bello University, Zaria (MBA) a shekara ta 2005.

    Guraren Da Ta Yi Aiki

    1. 1985-1990 ta yi aiki a Government Science Secondary School, Ikara a matsayin malamar aji (Class room teacher), a ƙaramar hukumar Ikara, jihar Kaduna.

    2. 1991-1993 ta yi aiki a GGSS Maraban Kubau, a matsayin mataimakiyar shubaga (Vice Principal), ƙaramar hukumar Kubau, Jihar Kaduna.

    3. 1993-1997 ta riƙe Senior Education Officer, ƙaramar hukumar Maƙarfi, Jihar Kaduna.

    4. 1997-2007 ta riƙe Education Secretary, ƙaramar hukumar Kudan, Jihar Kaduna.

    5. 2007-2008 ta riƙe Assistant Director, School Services, SUBEB, Jihar Kaduna.

    6. 2008-2015 ta riƙe Deputy Director, School Services, SUBEB, Jihar Kaduna.

    7. 2015-2018 ta riƙe Director, School Services, SUBEB, Jihar Kaduna.

    8. 2018- Yau tana riƙe da Quality Assurance Evaluation (KAE) ta Jihar Kaduna.

    Lambobin Yabo

    Ta samu lambobin yabo a gurare da dama, sakamakon yanayin ƙwazon aikin ta, wajen hidimtawa mutane a gurare daban-daban kamar haka;

    1. 1997/1998 ta samu takardar karramawa daga ma’aikatar ilimi da kuma ci gaban matasa (Ministry of Education and Youth Development) ta Jihar Kaduna.

    2. 1997/1998 – ta samu takardar karramawa daga LGEA UNICEF Assisted Model Primary School, Kudan, ƙaramar hukumar Kudan.

    3. 1999 ta samu takardar karramawa daga Jihar Kaduna Firamare Education Board on the judicious utilization of funds, Schools Development and Improvement, effective management of staff.

    4. 1999 ta samu takardar karramawa daga ƙaramar hukumar Kudan.

    5. 1999 ta samu takardar karramawa daga Kudan Development Association, Kaduna Chapter.

    6. 2000 ta samu takardar karramawa daga Farin Wata Youth and Drama Organization T/Wada, jihar Kaduna.

    7. 2001 ta samu takardar karramawa a matsayin jajirtacciyar magatakardar ilimi ta ƙaramar hukuma ta uku (3rd Best Education Secretary) daga ma’aikatar ilimin farkon na Jihar Kaduna.

    8. 2001 ta samu takardar karramawa daga NYSC Area Inspector, Kudan Local Government.

    9. 2004 ta samu takardar karramawa daga ma’aikatar ilimi da LGEA Firamare School, Sabon Garin Hunƙuyi, ƙaramar hukumar Kudan.

    10. 2004 ta samu takardar karramawa daga LGEA Firamare School, Nasarawan Kudan, ƙaramar hukumar Kudan.

    11. 2004 ta samu takardar karramawa daga LGEA Central Firamare School, Likoro, ƙaramar hukumar Kudan.

    12. 2004 ta samu takardar karramawa daga LGEA Firamare School, Yakubu ƙaramar hukumar Kudan .

    13. 2004 ta samu takardar karramawa daga Hunƙuyi Education Development Committee, ƙaramar hukumar Kudan.

    14. 2007 ta samu takardar karramawa daga Kaduna COPHON Award for Education Secretaries.

    15. 2009 ta samu takardar karramawa daga ƙungiyar ɗalibai ta Ikara Students Association, Bayero University, Kano.

    Danna nan don karanta ƙa’idoji goma sha ɗaya na samun nasara a rayuwa.

    16. ta samu takardar karramawa daga LGEA Firamare School, Hunquyi, ƙaramar hukumar Kudan.

    17. Ta samu takardar karramawa daga Ashiru Memorial Qur’anic Recitation Competition, ƙaramar hukumar Kudan.

    18. 2018 ta samu takardar karramawa daga gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir Ahmad El-Rufa’i for our involvement in the development of the education sector in Jahar Kaduna.

    19. 2018 ta samu takardar karramawa daga Taskira Newspaper for the most outstanding service to humanity.

    20. 2018 ta samu takardar karramawa daga UK AID (Teacher Development Programme) in recognition for an outstanding performance in implementing the in-service Reforms in Jihar Kaduna.

    21. 2019 ta samu takardar karramawa daga Model Primary School Hunƙuyi in recognition of an outstanding contribution towards the development of the school.

    Tarurrukan da ta halarta

    1.Ta halarci taron ƙarawa juna sani na shekara-shekara (Annual Conference) na ƙaramar hukuma wanda Education Secretaries of Nigeria suke shiryawa a 1998 zuwa 2007.

    2. Ta halarci taron ƙarawa juna sani akan Effective Management of Firamare Schools a jihar Kaduna wanda Firamare Education Board suka shirya a 19th-20th December, 1994.

    3. Ta halarci taron ƙarawa juna sani akan ” Enhancing Productivity and School Personnel for the Success of UBE Programme” organized by Guidance and Counseling with Educational Administration and Planning Sector Department of Education, ABU, Zaria. 20th October, 2000.

    4. Ta halarci taron ƙarawa juna sani na tsakiyar shekara(Biennial Conference) na ƙungiyar National Association of local government Education Secretaries of Nigeria wanda aka yi a jami’ar Jos, jihar Plateau a 20th-25th December 2000.

    5. Ta halarci taron ƙarawa juna sani na ƙungiyar National Association of Educational Planners and Managers (NAEPM) Congress Conference on Planning and Management of Education in Nigeria; A key success to sustainable development: takardar da aka gabatar da ita akan “Management of Universal Basic Education Programme Towards Effective Goals Management” wanda aka yi a tsakanin 12th-14th October, 2004 a jami’ar ABU, Zaria.

    6. Ta halarci taron ƙarawa juna sani, wanda aka yi akan “Capacity building training on Effective School Management”, Classroom Assessment in 2011.

    7. Ta halarci taron ƙarawa juna sani, wanda aka yi akan “Due Process of Financial and Administrative Management of SUBEB and LGEA’s” wanda a Hamdala hotal da ke jihar Kaduna a tsakanin 27th-28th April, 2006.

    8. Ta halarci taron ƙarawa juna sani, wanda aka yi akan “Planning and Management of Basic Education” wanda aka yi a Jahar Kaduna ƙarƙashin ƙungiyar “State Education Sector Project (SESP)” an Intervention by the department for International Development (DFID) United Kingdom in 2000-2011.

    9. Ta halarci taron “Joint Consultative Committee on Education (JCCE)” wanda aka yi a Lokoja, jahar Kogi a 2011.

    10. Ta halarci taron ƙarawa juna sani na sati uku (three week) wanda aka yi akan “Strategic Management for Senior Managers” an yi taron ne a Cape Town, a cikin kudancin Africa, 14th March zuwa 1st April 2011. Ƙarƙashin “Ministry of Education”da kuma kulawar “State Sector Education Programme [SESP]”.

    11. Ta halarci taron ƙarawa juna sani, wanda aka yi akan “New Methods Mathematics, Nigerian Firamare English, Basic Science and Basic Social Studies” wanda ƙungiyar Learn Africa PLC ta shirya, an yi taron ne a Multi-purpose hall da ke Kaduna a ranar 12th June, 2012.

    12. Ta halarci taron ƙarawa juna sani akan ”Planning and Management of Basic Education in Kaduna”ƙarƙashin “Education State Sector Project in Nigeria (ESSPIN)” tare da ƙungiyar “United Kingdom, department for International Development (DFID)”.

    13.Ta halarci taron “Heart of Europe Schools Debate Competition” wanda aka yi a Olumouc, a cikin ƙasar Czech a June, 2016.

    14. Ta halarci taron “Management Development Services Ltd” wanda aka yi akan “Result –Driven Total Project Management, an yi taron ne a tsakanin Monday 5th to Friday, 9th December, 2016.

    15. Ta halarci taron “Executive Leadership and Management of Senior Civil Servants working in Girls Education Programming in Northern GPE” ƙarƙashin ƙungiyar “National Institute of Policy and Strategic Studies, Kuru (NIPSS)”a tsakanin 19th – 21st December, 2016.

    16. Ta halarci taron ƙarawa juna sani na ɗalibai maza da mata yara akan “Child Education Programmes”wanda aka yi a Tafawa Ɓalewa hotal a cikin ɗaki na goma sha bakwai, a jihar Kaduna a ranar 10th 11th March, 2017.

    17. Ta halarci taron ƙarawa juna sani akan “Tsangaya Education Programme” wanda aka yi a ranar 24th – 25th March, 2017 wanda aka yi a Tafawa Ɓalewa hotal a cikin ɗaki na goma sha bakwai, a jihar Kaduna .

    18. Ta halarci taron “Stakeholders Meeting on Recruitment and Deployment of Effective Teachers in the Firamare Schools”wanda aka yi a ranar 5th-6th of April, 2017 a Tahir Guest Palace, Kano.

    19. Ta halarci taron “training of the trainer (TOT) capacity building workshop on implementation of professional standards for Nigerian Teachers” na ƙungiyar “Teachers’ Registration Council of Nigeria” daga 12th-15th June, 2017 a U.l Conference Centre; a cikin U.l Hotel, lbadan, jihar Oyo.

    20. Ta halarci taron “Heart of Europe International Debating Tournament” wanda aka yi a July, 2017 a Olomouc, a ƙasar Czech, an yi taron ne a ranar 12th-19th July, 2017.

    22. Ta halarci taron ƙarawa juna sani na shekara-shekara “National Council on Education (NCE)” a July, 2017.

    23. Ta halarci taron “Training on Result-Driven Monitoring and Evaluation for optional Performance of Educational Projects” wanda aka yi a Silver Sand hotel, Katuru Road, Kaduna 7th-11thAugust, 2017.

    24.Ta halarci taron “Teaching of Literacy and Numeracy, Leadership Skills to Head teachers in Jihar Kaduna” wanda ƙungiyar ESSPIN and TDP suka shirya daga 2012-2018.

    25. Ta halarci taron “Computer Training on Human Resource Approval at Federal Polytechnic, Kaduna” ƙarƙashin kulawar gwamnatin Jihar Kaduna.

    26. Ta halarci taron “Trainings on the Teaching of Jolly Phonics to Firamare School Teachers”.

    Ayyuka na musamman 

    1. Ta zama Member – Committee on Teacher Competency Test for Kaduna State teachers;

    2. Ta zama Member – Committee on Teacher Competency Test In Kaduna L.G.A;

    3. Ta zama Member – Teacher Development Programme (ESSPIN/TDP)

    4. Ta zama Member -Teacher Registration Council (TRCN)

    5.Ta zama Component Lead -Teacher Professional Development (TPD) under the Grand Partnership in Education/Nigeria partnership in Education Programme (GPE/NIPEP). STRENGTH:Prudent management of resources, Commitment to the service for good result and respect for constituted authority.

    (Mun samu waɗannan jawabai ne daga bakin Hajiya Halima Jumare wanda ta turo min ranar bakwai ga watan yuni 2020 ta imel ɗi na).

    Domin Karanta tarihin hakimin Kudan danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

     

  • Cinikin Bayi A Tarihin Afrika Kashi Na Biyar

    Cinikin Bayi A Tarihin Afrika Kashi Na Biyar

    Cinikin Bayi a Afrika ya ɗauki salo daban-daban kamar yadda na yi bayani a baya babu abin da ya kassara Afrika kamar wannan, ta hanyoyi daban-daban har da canja wa mutane da kuma canja yanayin zamantakewa. To kowanne sashe na Afrika akwai irin nau’in bautar da ake yi ta inda mutane tsakaninsu ma ko kuma su da maƙotansu wasu su je su sato wasu.

    Duk wannan abu yana faruwa, kafin masu waɗannan su zo su waɗannan mutanen Portugal, da bayan ma sun zo waɗanda su suka kawo cinikayyar Bayi gadan-gadan da kuma su mutanen Ingila Dens da Dutch su ma suka zo suka shiga cikin wannan ciniki.

    A ɓangaren abinda ya kama daga Senegal har zuwa Port Sudan da kuma Yammacin Tsakiyar Sudan (Western Central Sudan) wanda yawancin su duk musulmai ne nan ma an yi cinikin Bayi kuma an bautar da mutane, an yi yaƙe -yaƙe a tsakanin juna, an sayar da mutane, kafin ma zuwan Turawan Portugal da bayan zuwan su.

    Saboda su waɗannan da suke wannan sashe na Afrika yawanci idan sun kama Bayin suna amfani da su a tsakanin su wasu kuma su kai su su sayar a tafi da su ta Sahara. Tunda akwai ƙasashe manya a wannan nahiya, kama tun daga kan Ghana, Mali, Songhai da Borno idan aka zo Sokoto ƙasashe ne masu ƙarfi kuma suna da dawakai suna amfani da su akan maƙwabtan su, wannan abu ya ɗauki salo iri-iri da hanyoyi daban-daban, kuma bayan zuwan su da kuma kafin jihadi da kuma bayan jihadin Shehu Ɗan Fodio.

    Tunda a cikin tarihi ma wasu daga cikin malamai sun ce ɗaya daga dalilin da yasa su Shehu Ɗan Fodio suka yi jihadi saboda ana ɗiban musulmi ana sayar da su Bayi, wannan abu ya tayarwa da malamai da sauran mutane hankali, kuma da aka yi Daular Sokoto an yi ƙoƙari a hana wannan, waɗanda kawai suka yarda a dinga siyarwa su ne waɗanda ba musulmai ba.

    Sun mayar da mutanen da suke ƙananan ƙabilu da suke a tsakiya su aka rinƙa farauta a na sayar da su, wannan abin ya jawo musu baƙin jini a wajen sauran mutane bayan zuwan Mishan, wanda Mishan sun yi amfani da wannan don su ƙarfafi ko su dasa ƙiyayya tsakanin musulmin Arewa da waɗanda ba musulmi ba, cewa dama can iyayen su, idan mutum ya karanta littattafan su zai ga duk irin waɗannan abubuwa da irin abin da suka nuna sai suka mayar da abin cewa, gaba ɗaya a wannan nahiya ba abin da aka yi sai dai kashe su da mayar da su Bayi.

    Wannan abu ya shiga zukatan waɗanda ba musulmi ba, wanda daga baya suka zo suka karɓi addinin kirista. Mun san irin waɗannan cewar wancan zamanin da yanzu ba ɗaya ba ne, to amma wannan abin ya yi tasiri gare su da mutanen su ya kuma cunkusa ƙiyayya daban-daban.

    A irin wannan yanayi na yadda ake kama Bayi a wannan nahiya ta Sudan, an yi rubuce rubuce daban-daban musamman Turawan da suka zo a da can kafin su yi mulkin mallaka, har da wanda ya ba da labarin irin abubuwan da suka faru a Borno, tunda babbar  ƙasa ce kuma suna da ƙarfi a lokacin da suke kai hari wurin irin waɗannan ƙananan ƙabilu, kuma in ba su bayar da kai ba za a ɗebo su da matan su da yaran su, manya-manyan mazan duk a karkashe su. Yara da mata a ɗebo su a sayar da su, waɗanda suke sha’awarsu su mayar da su ƙwarƙwarori ko su bayar da su duk wannann ya faru.

    Daga cikin irin waɗannan mutanen da suka ga abin da ya faru akwai Harith Barth, ya faɗi abin da ya gani da Borno ta kai hari Mandara wurin mil 300 daga ƙasar Borno (Kukawa) da irin abubuwan da suka faru aka dinga ɗebo mutanen. Duk wannan sun rubuta su kuma sun bayar da bayanai a kansu a irin wannan yanayi, mun ga shi ma kansa Luggard da sauran su abin da suke ta cewa su Turawan Ingila cewa su sun zo ne don su kawar da cinikin Bayi.

    Bayan an yi jihadin Shehu Ɗan Fodio an ci nasara waɗanda aka kama aka mayar da su Bayi, wasu a faɗace-faɗace inda wasu har ma an sayar da su an tafi da su wata ƙasa kamar irin su Nicolas wanda aka sayar da shi har ya kai Rasha, wanda Sir Nicolas ya yi Baptising ɗin sa daga nan ya tafi Spain bayan ya ‘yantar da shi, inda daga nan ya tafi America aka yi yaƙi da shi.

    Duk irin wannan ya sa a zagi Shehu Dan Fodio da cewa jihadi ne da irin wannan bautar ta sa aka kama shi ya tafi, duk mun san irin wannan idan ma ƙasashen an samu waɗanda suke son Shehun kuma suka yi amfani da wannan abin da aka yi na jihadi su ma suka tayar da rigima kamar Ab-bahiya a ƙasar Brazil. Wannan duk ya nuna mana irin yadda wannan ƙasa ta Afrika take da yanayin zamantakewa na rigingimu da faɗace-faɗace da abubuwan da suka jawo.

    A wannan nahiyar ƙasashen musulmi kenan wanda yawancin Bayin su suna sayar da su ne a Sahara wasu suna shiga Europe ɗin wasu suna shiga nan iyakar Magrib da Misra, yawancin irin waɗannan Bayin nan ake kai su, mun san cewa a irin bauta ta ƙasashen musulmi daban take da ta sauran ƙasashe tun da akwai ƙa’idoji na shari’a waɗanda aka gindaya ba za ka iya yi wa Bawanka ba da sauran su, kuma a can ƙasashen musulmi su na da tsarin cewa, mutum zai iya nemo ‘yancin sa.

    Duk da dai a nan nahiyar Sudan abin bai fiye tabbata ba, kuma da su kan su Bayi a nan waɗanda aka haife su a cikin bauta ba a sayar da su saboda sun musulunta sun zama Bayi na gida, wanda a hankali suna shiga gida har ma ya zama su mata a mayar da su ƙwarƙwarori, ko wasu da suke fara mulki suna samun ‘yanci su ma su zama wasu abu kamar yadda muke ganin Bayi a Fada. Wannan yana daga cikin abubuwan da suke faruwa a irin bautar ƙasashen musulmi da kuma nan ƙasar Sudan daban suke da sauran wurare.

    Ana ɗiban su su ma ana kai su can ƙasashen Larabawa, wasu su mutu a hanya, wasu kuma su tsira da wahala dai iri-iri. A irin ƙasashensu su ma ana samun bauta da kuma yaƙe-yaƙe a wurare irin su Upper Volta ɗin nan wanda aka ce ita ce ta zama Burkina Faso, wanda waɗannan ƙasashen ma yawanci ba ɓarin musulmi ba ne, har ma aka ga cewa a ƙididdigar da aka yi kashi 17 bisa ɗari na ƙasar gaba ɗaya an bautar da su, kafin Turawa su zo lokacin da aka hana waɗannan abubuwan.

    Kowacce nahiya da irin nata, saboda idan ka tafi can ɓangaren su Ethopia nan ma da take babbar ƙasa ce ta kirista su ma sun bautar da mutane wasu an kama su wasu kuma an sayar da su wasu an mayar da su Bayi. Akwai ƙasashen da suke na musulmi su ma suna ɗiban Bayi. Kiristocin Ethopia bayan da suke ɗiba ma suna bautar da su wasu, sun kashe wasu kuma su sayar da su tunda su ba tsarin su ɗaya da musulmi ba.

    Su ma musulmin da suke wannan nahiya ta Gabashin Afrika, Bayi ana tafiya da su can Gulf da kuma sauran ƙasashen Asia ma duk ana ɗiban ‘yan Afrika. Waɗannan abubuwa ne da suke dama kafin zuwan Portugees ɗin su fara wannan cinikayya tasu kuma har su canja yanayin yadda ma bautar da ɗiban zai kasance a wannan nahiya ta Afrika.

    Kamar yadda na faɗa su ma ƙasashen kurmi yadda suke ɗiban nasu Bayin ya sha bamban da irin namu na Savannah, saboda su ƙasashen kurmin nan yawancin su ba su da dauloli masu ƙarfi in banda irin su Benin da Oyo da France. Waɗannan manyan dauloli kuma da sauran waɗanda suke kusa da su da ‘yan Uyo su idan sun ɗiba sayar wa da Turawa suke, kuma a irin wannan wurare irin su Oyo Bayin ana yayyanka su a ba wa ababen bautar su, tunda duk sun yarda da sadaukarwa saɓanin irin  ƙasashen musulmi ko na kirista na gabashin Afrika inda ba a yanka mutum a sadaukar da shi da irin shirka da suka saba.

    Wannan yana daga cikin abubuwan da suka sha bamban da bautar musulmi da waɗanda ba musulmi ba, ta inda su musulmi idan sun ɗiba Sahara suke kaiwa su kuma waɗannan suna ɗiba ne su kai Atlantic. Duk wannan kafin zuwan Turawan Potugal waɗanda lokacin da suka zo kurmi suka yi da kuma inda yake suna da ruwa suka dinga ɗiba su da ƙabilun da suke a waɗannan wurare da mutane masu ƙarfi, amma duk kusan abin da ya faru shi ne, su waɗannan ƙasashe da na Arewacin Sudan da na Kudu na can bakin teku suna shigowa tsakiya ne suna ɗiban ƙananan ƙabilu su suke sayarwa.

    Saboda haka suka ragargaji wurin da ake cewa Middle Belt ba ma kaɗai a Nijeriya ba, inda ita kanta Middle Belt ɗin an canja mata suna kuma mun san cewa ita Nijeriya ita ta fi kowacce ƙasa yawa da yadda su waɗannan mutanen aka dinga ɗiba, waɗanda suke a bakin teku cikin ƙasa suka dinga shigowa shi yasa za ka ga yawanci su ƙabilar Igbo su aka fi yi wa wannan farmaki tunda su ne suke kusa da Ijo kuma ba su da ƙarfi ba su da tsarin gwamnati irin na waɗannan ƙasashe.

    Yawancin waɗanda aka fi kai wa farmaki ana ce musu Stateless ko kuma non-State, waɗanda ba su da tsarin hukuma irin na waɗannan ƙasashe su aka dinga ɗiba ana sayarwa a ko ina a Afrika, su suka shiga wannan tsari na ɗiban Bayi da rashin albarka na cutar da su tun ma dai kafin su Turawan Portugal ɗin su zo, tunda dama mutane suna faɗa a tsakanin su, wannan ya ɗebi wannan wancan ya ɗebi wannan, zuwan Turawa sai ya zama ya canja wannan abin gaba ɗaya yanda za mu gani su kuma wane irin tasiri abin su ya yi wa al’ummar Afrika.

    Danna nan don karanta cinkin bayi a tarihin Afrika kashi na huɗu

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Cinikin Bayi A Tarihin Afrika Kashi Na Huɗu

    Cinikin Bayi A Tarihin Afrika Kashi Na Huɗu

    Great Britain, Ingila ke nan duk da yake ita ta zama ta fi kowacce cin ribar cinikin Bayi, ba ta soke bauta ba da wuri, sai bayan an ɗauki lokaci, inda sauran ƙasashen Turai suka ce sun haramta cinikin Bayi. 

    Ƙasar da ta fara yin doka ita ce, Denmark a shekara ta 1804, Ingila ta yi a shekara ta 1807, sai Amerika ta yi a shekara ta 1808, sai Sweden a shekara ta 1817, sai Holand a shekara  ta 1814, an ba da dalilin da yasa su Turawa ba su damu da cinikin Bayi ba da azabar bautar da mutane da ake yi saboda su ma a ƙasar su ana azabtar da mutane da suka yi ɗan laifi kaɗan, sai ka ga mutum ana bin sa kuma a ƙarshe an zo an kashe shi, ko an tsire shi, ko an ɗauke shi an jefar da shi a wata ƙasa.

    Duk wannan zaluncin su ma ya dame su sai ya zamanto ma ba sa ganin zaluntar da ake yi wa Bayin, sai da abubuwa suka fara kankama tukunna, aka fara sanin cewa lallai fa Bayi suna shan wuya, wani lauya ana ce masa Grandba Shap  ne ya fara ƙoqarin maganar ‘yantar da Bayi, ya taimakawa wani Bawa da ya gudu ana ce masa Somaset.

    Wannan Bawan ya gudu aka je aka kamo shi za a dawo da shi, sa ya shigar da ƙara a gaban alƙali wato Lord…. inda aka yi wani abu da ake ce masa Read of Habees copus cewa lallai a kawo shi wannan bawa kotu, kawo shi kotu da hukuncin da shi Lord Chief Mans… ya bayar ne ya fara jawo mutane su san cewa lallai akwai azaba a harkar cinikin Bayi. Kuma abin ya samu karɓuwa, cewa a san yadda za a yi a hana wannan.

    Bayan shekara goma sha biyar ana ta wannan gwagwarmaya da mutane irin su Williams Wilberforce da wannan Grandba Shap da Thomas Clascis suka yi wata ƙungiya suka kira ta da Society for the Revolution of  Slave Trade, kuma shi Willberforce ya zama shi ne mai magana da yawun su a majalisa, har yasa dai aka yi wannann doka ta shekarar 1907.

    Amma dai sun ci gaba da yin gwagwarmaya da sauran mutane da yin wannan, inda daga baya Ingila ta ce lallai za ta hana wannan cinikin, amma dai ba wai sun hana ne don tausayi kaɗai ba,  akwai maganar tattalin arziki da maganar sun samu ci gaban masana’antu (Industrial revolution). Bayin dai buƙatar su ta ragu a ɓangaren tattalin arziki a Ingila, tunda Ingila ta ci gaba kuma suna ganin cewa, gwanda mutane a ƙyale su a Afrika su dinga yin noma don a samu wanda ake yin amfani da shi a masana’antu (Factories).

    Ingila da sojojin ta na Ruwa suka ɗauki gabaran hana wannan ciniki tunda ta fi kowa ƙarfi a ruwa, su za su yi maganin cinikin Bayin nan. Duk da haka dai abin ya ba su wahala yadda mutane suke ta ƙoƙarin su kauce mu su, sun fito da dabaru da yawa na kaucewa inda za a kama su, duk da dai an kama jirage da yawa.

    A cikin shekara 20 daga 1818-1838 an kama jirage 280 da wani abu, haka dai kullum jiragen da ake kamawa ƙaruwa suke inda a shekarar 1845 ma an kama jirage 30, amma duk da haka sun ci gaba da yin dabaru su masu ɗiban Bayin nan domin su kaucewa sojojin ruwa na Ingila, domin duk jirgin da suka kama saisu kai shi Freetown Sierra Leon a nan a ke yi masa hukunci.

    Wani lokacin ma su masu cinikin Bayin sai su ɓoye su ko su zubar da su a ruwa domin kada a kama su, sai da aka canja dokar aka ce idan an ga wasu abubuwa da suka yi kama da kayan cinikin Bayi a kama jirgin shi ma a yi masa shari’a. 

    Wasu idan an kama su an kai su Sierra Leon ɗin nan to sai a saki Bayin tun da wannan gari ana ce masa Freetown, wasu idan an sake su Mishan suna ɗaukan su su koya mu su karatu su mayar da su Kirista da sauransu. Har ma aka samu wani babban Kirista da aka taɓa yi a Najeriya ana ace masa Bishop Samuel Ajayi Crowther wanda shi ma aka sace shi aka mayar da shi Bawa a shekarar 1821. 

    Haka aka ɗauke su daga wannan hannu zuwa wannan tun da yana da rabon zai tsira aka kai shi Sierra Leon daga nan kuma dai ya samu ya kuɓuta tunda an kama jirgin da yake ɗauke su, aka mayar da shi Kirista a shekarar 1825 aka yi baptizing ɗinsa ya zama Samuel Crowther, wanda yasa aka sa masa wannan su na shi ne shugaban Cochi a nan Sierra Leon.

     Kowa ya san gwagwarmayar da ya yi wajen kawo addinin Kirista Najeriya, shi ne ɗan Afrika na farko ɗan asalin Najeriya da ya zama Bishop na Angalican kuma ya shahara, yana ɗaya daga cikin mutanen da aka kuɓutar da su daga hannun masu cinikin Bayi.

    Haka dai suka yi da aka gama cinikin Bayin nan sai ya zama cewa, Mishan sun duƙufa sosai wurin yaɗa addinin kirista, saboda su wanke laifukan su da suka yi wa mutanen Afrika su kawo mu su addinin kirista. Wannan abu ya yi tasiri da yadda su Turawan mulkin mallaka suka yi amfani da Mishan don su tabbatar da mulkin su a Afrika ta yin amfani da Mishan da cinikayya da dabaru da sauran su har suka zo suka tabbata, tun da an gama cinikin Bayi an shiga wata marhala ta danniya daban (mulkin mallaka).

    Don karanta tarihin Afrika danna nan

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Sunayen Annabi Muhammad (S.A.W)

    Sunayen Annabi Muhammad (S.A.W)

    Annabi Muhammad (S.A.W) yana da wasu sunaye har guda ɗari biyu da ɗaya (kamar yadda mai dala’ilu ya kawo su), sannan kuma wasu malamai sun ce sun kai dubu uku, saboda dalilai da halaye ne suka iya sa a kira mutum da sunaye da yawa. Ga sunayen nan kamar haka:

    1. Muhammad

    2. Ahmad

    3. Hamid

    4. Mahmud

    5. Ahid

    6. Wahid

    7. Mahi

    8. Hashirun

    9. Aƙibun

    10 Ɗaha

    11. Mansur

    12. Ɗahirun

    13. Muɗaihirun

    14. Ɗayyabun

    15. Sayyadun

    16 Rasulun

    17. Nabiyun

    18 Rasulur Rahmati

    19. Ƙayyimun

    20. Jami’un

    21 Muƙtafi

    22. Muƙaffa

    23. Rasulul malahimi

    24. Rasulur rahati

    25.  Kamilun

    26. Ikililun

    27.  Mudassirun

    28.  Muzammilun

    29.  Abdullahi

    30.  Habibullah

    31.  Safiyyullah

    32. Najiyullah

    33.  Kalimullah

    34.  Katimul Anbiya

    35. Khatimur Ruslu

    36.  Muhyi

    37.  Munji

    38. Muzakkirun

    39. Nasirun

    40. Yaasin

    41. Nabiyyur rahmati

    42. Nabiyun taubati

    43. Harisun alaikun

    44. Mu’alumun

    45. Shahidun

    4. Shahirun

    47. Shaahidun

    49. Mashhudun

    50. Bashirun

    51. Nazirun

    52. Munzirun

    53. Nurun

    54. Sirajun

    55. Misbahun

    56. Hudah

    57. Mahdiyyun

    58. Munirun

    59. Ɗa’in

    60. Mad’uwun

    61. Mujibu

    62. Mujabun

    63. Hafiyyun

    64. Afuwan

    65.Waliyyun

    66. Haƙƙun

    67. Ƙawiyyun

    68. Aminu

    69. Ma’amunun

    70.Karimun

    71.Mukarramun

    72. Makinun

    73. Matinun

    74. Mubinun

    75. Mu’ammalun

    76. Zu-ƙuwatin

    77. Zu-hurmatin

    78. Zu-izzin

    79.Zu-fadlin

    80. Muɗa’un

    81. Muɗi’un

    82. Ƙadamus-sidqin

    83. Rahmatun

    84. Bushra

    85. Gausun

    86. Gaisun

    87. Giyasun

    88. Hadiyatullah

    89. Urwatu wusƙa

    90. Siraɗallahi

    91. Siraɗun Mustaƙim

    92. Zikirullahi

    93. Saifullahi

    94. Hizbullahi

    95. Najimus saƙib

    96. Musɗafa

    97. Mujtaba

    98. Muntaƙa

    99. Ummiyun

    100. Muktarun

    101. Ajirun

    102. Jabbarun

    103. Abul-ƙasim

    104. Siraɗul mustaƙeem

    105. Kanzullah

    106. Zikirullah

    107. Mushaffa’un

    108. Shafi’un

    109. Salihun

    110. Muslihun

    111. Muhaiminun

    112. Sadiƙun

    113. Musadduƙun

    114. Sidƙun

    115. Sayyadul Mursalina

    116. Imamul Muttaƙin

    117. Ƙa’idul Gurril Muhajjalin

    118. Kalilur Rahman

    119. Barrun

    120. Mubarrun

    121. Wajihun

    123. Nasihun

    124. Na’sihun

    125. Wakilun

    126. Mutawakkilun

    127. Kafi

    128. Shafi’u

    129. Muƙimus Sunnati

    130. Muƙaddasun

    131.  Ruhul ƙudusi

    132. Ruhul Haƙƙi

    133.:Ruhul ƙisɗi

    134. Kaafi

    135. Muƙtafi

    136. Baligun

    137. Muballigun

    138. Shafi

    139. Wasilun

    140. Mausulun

    141. Sabiƙun

    142. Sa’iƙun

    143. Hadi

    144. Muhdi

    145. Muƙaddamun

    146. Azizun

    146. Fadilun

    147. Mufaddalun

    148. Fatihun

    149. Miftahun

    150. Miftahur Rahmati

    Domin Karanta Haihuwar manzon Allah SAW danna nan

    151. Miftahul Jannati

    152. Alamul Imani

    153. Dalilul Khairati

    154. Musahhihul Hasanati

    155. Muƙilul Asarati

    156. Safahu Anil-zallati

    157. Sahibus Shafa’ati

    158. Sahibul Maƙami

    159. Sahibul ƙadami

    160. Makhsusu Bil Izzu

    161. Makhsusu Bil Majdi

    162. Makhsusu Bish Sharafi

    163. Sahibul Wasilati

    164. Sahibus Saifi

    165. Sahibul Fadilati

    166. Sahibul Izari

    167. Sahibul Hujjati

    168. Sahibul Sulɗani

    169. Sahibur Rida’i

    170. Sahibud Darajati Rafi’ati

    171. Sahibut Taaji

    172. Sahibul Migfar

    173. Sahibul Liwa’i

    174. Sahibul Mi’iraji

    175. Sahibul ƙadibi

    176. Sahibul Buraƙ

    177. Sahibul Alamati

    178. Sahibul Khattimi

    179. Sahibul Burhani

    180. Sahibul Bayani

    181. Fasihul Lisani

    182. Ra’ufun

    183. Rahimun

    184. Azinul Khairi

    185. Sahibul Islami

    186. Sayyadil Kaunaini

    187. Ainun na’imi

    188. Ainul Gurri

    189. Sa’adullahi

    190Sa’adul Khalƙi

    191. Khaɗibul Umami

    192. Kashiful kurabi

    193. Rafi’ur ratbi

    194. Izzul arabi

    195. Sahibul bayan

    196. Sahibul faraji

    197. Sahibul alami

    198. Zu-mukanatin.

    199.Zu-izzin.

    200.Fadhilun.

    201.Mufaddhilun.

    Don karanta yanayin duniya kafin aiko da Manzon Allah SAW danna nan

    Edita; Rumasa’u Muhammad kallamu