Category: ILIMIN TARIHI

  • Tarihin Associate Professor Mu’azu Sa’adu Muhammad Kudan

    Tarihin Associate Professor Mu’azu Sa’adu Muhammad Kudan

    An haifi Dr. Mu’azu Sa’adu Muhammad a ranar 13/3/1964 a unguwar Tsauni garin Kudan, Ƙaramar hukumar Kudan Jihar Kaduna. Mahaifinsa Malam Adamu Muhammad (Andiyo) mahaifiyarsa Zainab (Tadabai) Bashir Kudan.Ya zauna a Kano ƙofar Nasarawa wajen wani kakansa Alhaji Aliyu Gwarzo, ya yi karatun allo daga shekara 1969 – 1972, ya dawo Kudan 1972, ya shiga firamare 1973-1979, ya wuce Sakandiren Gwamnati ta Kagoro a ranar Alhamis 24/11/1979-15/09/1981, sai Sakandaren Gwamnati ta Maƙarfi 18/09/1981-01/06/1984. (G.C.E).

    Ya wuce kwalejin zurfafa ilimi (C.A.S) Zariya 15/01/1985- 10/08/1987 (I.J.M.B), sai ya kama aiki da hukumar ba da tallafin karatu ta Jihar Kaduna (Kaduna State Scholarship Board) a sashen kuɗi (Account Section) 09/02/1988 -15/02/1995. Ya wuce ƙaro karatu digirin farko a Jami’ar Usman ɗan Fodiyo Sakkwato 30/7/1994 -31/05/1998. (B.A Hausa).

    Ya koma ma’aikatar ilimi ta Jihar Kaduna (Ministry of Education) a sashen mulki (Admin. Section)15/02/1995-2003, ya koma Jami’ar Sakkwato yin digiri na biyu (M.A Hausa) 2/09/2003 -07/09/2007. Ya koma Kwalejin Tunawa da Sardauna Kaduna 18/12/2003 a matsayin malami.

    Ya yi ritaya a 31/1/2010 yana da shekaru 22 a aikin gwamnati. Ya yi sana’ar tela shekara 30, 1977-2007. Ya koma Jami’ar Sakkwato 12/04/2011-07/11/2015 Yin digiri na uku Ph.D Hausa. Ya yi aure ranar 11/3/1990 yana da ‘ya’ya goma (10).

    Sunayen matan 5 

    1. Asma’u.

    2. Ummukhulsum

    3. Zainab

    4. Hafsat

    5. Fatima

    Sunayen mazan 5

    1.Muhammad Bashir

    2. Abubakar Sadik

    3. Umar Faruk

    4. Suleman

    5. Muhammad Irfan

    Ya yi aikace- aikacen wucin-gadi na koyarwa a:-

    Sashen remidial (KASU) Jami’ar Jihar Kaduna 2007-2008

    2. Kwalejin Adeyemo (Adeyemo College) Kaduna 2009 zuwa 2010.

    3. Kwalejin Shabab (Shabab College of Arabic and Islamic Studies) U/Dosa Kaduna 2006-2010

    4. Kwalejin Albidaya (Albidaya College) Kaduna 2013- 2014.

    5. Ya zama malami Jami’ar Sule Lamido Kafin Hausa Jihar Jigawa 2014-Zuwa yau. A yanzu haka, shi ne shugaban sashin harsunan Najeriya na jami’ar Sule Lamiɗo da ke kafin Hausa ta jihar Jigawa.

    Sunayen maƙalolin sa

    1. Muhammad M.S.(2019); Juga Nabiso. . Takardar da ya gabatar da ita a international Conference da ke jami’ar jihar Kaduna.

    2. Muhammad M.S.(2017); Tashe Majigin Bahaushe. Takardar da ya gabatar da ita a taron shekara-shekara karo na (4th Annual International Conference) a jami’ar jihar Kaduna.

    3. Muhammad M.S.(2017); Muhammadu Ashiru Sarkin Kudan. Takardar da ya gabatar da ita a taron shekara-shekara karo na uku (3rd Annual International Conference) da ke jami’ar jihar Kaduna.

    4.Muhammad M.S.(2019); Kasuwa A Kai Miki Dole: A University Research sponsored by the Sule Lamido University Kafin Hausa.

    5. Muhammad M.S; Sakin Na Hannu. Hausa Prose-Fiction Reader Project. Association of Nigerian Authors, Kano State Branch.

    6.Muhammad M.S; Dabbobi A Tunanin Bahaushe (Ph.D Thesis 2016).

    7. Muhammad M.S; Effect Of Football (P.G.D.E Project 2010).

    8. Muhammad M.S; Hauka A Idon Bahaushe (M.A Disertation 2007).

    9. Muhammad M.S; Zumuncin Bahaushe (B.A Project 1997).

    10. Muhammad M.S; Ire-Iren Abincin Hausawa (I.J.M.B Project 1987).

    11. Muhammad M.S; Kasuwa A Kai maki dole(SLU University Research 2018)

    12. Muhammad M.S; Jirwayen Maguzanci A Rayuwar Mu Ta Yau.

    13. Muhammad M.S; Bauta Da Cinikin Bayi

    14. Muhammad M.S; Kagaggen Zumunci.

    15. Muhammad M.S; Wace Ce Mace ?

    16. Riga-kafi Ya fi Magani

    17. Muhammad M.S; Jibadau Kayan Nauyi (Wanda Yace Babu Yi Masa Aka Yi)

    18. Muhammad M.S; Ballagazar Uwa

    19. Muhammad M.S; Baƙin Bature (Baƙin Mutum Da Kan Banasare)

    20. Saɓalikita Mijin Hajiya (Sunɓulallen Uba)

    21. Ƙawalliya Romon Jaɓa.

    22. Ilimi Farkonka Maɗaci ƙarshenka Zuma.

    23. Maraya da Maraici A Yau – 2014.

    24. Rowa. (Hali, Wayau, Ko Ciwo?).

    25. Kyauta. (Ɗabi’a Ko Baiwa Ko Wauta?).

    26. Ɗa, Na Kowa Ne.

    27. Me Ka Fi, Me Ya Fi Ka, Me Kuke Dai-dai ?

    28. Dokin Zuciya, Ba A Hawanka Sai An Yi Nadama.

    29. Halayen Dabbobi A Bakin Narambaɗa.

    Sunayen Litittafansa 

    1. Bahaushiyar Al’ada.

    2. Tsufa Rigar ƙaya.

    3. Maraya da Maraici.

    4. Mace Babbar Halitta.

    5. Maza Gumbar Dutse.

    6. Haƙƙoki Abin Kulawa.

    7. Ƙuruciya A Al’adar Bahaushe.

    8. Sana’a Sa’a

    9. Tarihin Garin Kudan.

    10. Ziyara A Musulunci.

    11. Zuciya Sarauniya ce.

    Lambobin yabo

    1. Ƙungiyar ɗalibai na jihar Kaduna wanda suke karatu a Jami’ar Usman ɗanfodio a 1997.

    2. Ƙungiyar ɗalibai ta Hausa na Jami’ar Usman Ɗanfodio sokoto a 1997.

    3. Darul tahfizul ƙur’anil kareem Islamiyya Unguwar Dosa Kaduna a 2006.

    4.Markazul Alh Adamu Liddarasatul Islamiyya Unguwar Dosa Kaduna a 2007.

    5. Age Mate association Kafin Hausa a 2019.

    6. Arewa Writers Association of Nigeria (AWAN).

    Sannan kuma, a yanzu halin da ake ciki yana da mataye guda biyu, wato ya ƙara aure. Sannan kuma ya zama mataimakin Farfesa (Associate Professor).

    (Mun samu waɗannan jawaban ne daga Dr. Mu`azu Sa’adu Muhammad Kudan ta hanyar rubutawa da ya yi, ya turo min ta imail ɗi na a ranar Alhamis 02/07/2020).

    Domin karanta rayuwar ‘ya mace a ƙasashen turai da kuma a musulunci danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Tarihin Garin Rigasa Da Ke Jihar Kaduna

    Tarihin Garin Rigasa Da Ke Jihar Kaduna

    Rigasa ƙauyen birni ne da ke karamar hukumar Igabi a yankin Kaduna ta tsakiya a cikin jihar Kaduna, Nigeria. Na kira yankin ne da KAUYEN BIRNI saboda wasu ƴan dalilai wanda zan bayyana su a nan gaba.

    Garin RIGASA yana ɗaya daga cikin yanki mafi girma da yawan jama’a a Najeriya, tare da ƙiyasin kimanin mutane miliyan uku ne suke rayuwa a cikin sa. Yana ɗauke da yankuna kamar su, Ɗanmani, Nariya, Maƙera, Mashi, Hayin Malam Bello, Sabon-garin Rigasa, Kwate, Mai-giginya, da sauransu.

    Yana da faɗin kusan kilomita 14 zuwa 8. Rigasa yana ɗaya daga cikin unguwanni 255 na jihar Kaduna. Garin Rigasa yana da manyan makarantun firamare da sakandare kama daga na gwamnati da masu zaman kansu masu tarin yawa, yana da makarantun islamiyyu su ma masu yawan gaske duk a cikin garin Rigasar.

    Haka kuma yanzu haka akwai tashar jirgin ƙasa daga Kaduna zuwa Abuja wanda wannan tashar tana cikin garin Rigasar ne. An yi imanin cewa Rigasa na karɓar baƙuncin manyan baƙi irin su Shugabanin siyasa, sarakuna, Air Vice Marshal Maisaka (marigayi), Shugaban Karamar Hukumar Igabi, ba tare da ambaton wasu Farfesa da Likitoci da dama da ke zaune a cikin garin ba.

    A yanzu haka Rigasa tana da mahaddata Alkur’ani masu yawan gaske, manyan likitoci, manyan ƴan siyasa, malamai, ‘yan jarida da dukkan wani nau’i na masu ilimin kimiyya da fasaha.

    Kafin rikicin addini na 2000 a jihar Kaduna, akwai ƙabilu da yaruka masu yawa a cikin Rigasar wanda a halin yanzu an yi ittifaƙin Hausawa ne mafiya yawa a cikin garin kuma al’adar Hausa ita ce al’adar wannan yanki. Kashi 90% na al’ummar wannan yanki musulmai ne.

    Danna nan don karanta dokar Najeriya

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Tarihin Marigayi Alaramma Suraj Yunus Kudan

    Tarihin Marigayi Alaramma Suraj Yunus Kudan

    An haifi  Alaramma Surajo Yunusa a ranar 07/03/1966 a garin Kudan, cikin ƙaramar Hukumar Kudan, Jihar Kaduna, Nigeria. Sunan Mahifiyarsa Maimuna, sunan mahaifinsa Liman Yunusa. Ya rasu a ranar Alhmamis 06/04/2017 dai-dai da 9/7/1438 A.H.

    Kuma ya bar mata biyu, ya bar ‘ya’ya’ guda goma sha biyu (12), Maza bakwai (7) da Mata biyar (5). Allah Ubangiji ya amince masa ilimai, musamman wajen warware sarƙaƙiya ta ɓangaren rabon gado, wanda har sai da ya yi shura tun daga ƙaramar hukumar Kudan har zuwa Zaria akan wannan fannin da sauransu.

    Karatun Addinin / Litattafai

    A ranar Litinin 06/02/1984 dai-dai 5/5/1404 ya fara rubutun Alƙur’ani. Ranar Laraba 9/09/1984 dai-dai 24/12/1404 ya kammala rubuta Alƙur’ani. Ranar 11/12/1986 ya kai Alƙur’ani gida, Kudan. Ranar Litinin 19/09/1984 dai-dai 24/12/1404 ya fara karatu wajen Malam Musa Ƙofar Nasarawa jihar Kano.

    A ranar Laraba 24/4/1991 dai-dai 11/10/1411 ya fara karatu da Malam Lawal Jinjin. Ranar 06/05/1991 dai-dai 23/10/141, ya fara karatu da Malam Mammada gidan malamai Kudan. Ranar 12/08/1991 dai-dai 2/2/1412 aka ɗauke shi aikin koyarwa a Model Primary School, Kudan. Ya tafi aikin Hajji a ranar Lahadi 15/11/2009 dai-dai 27/11/1430.

    Ya dawo ranar Alhamis 10/8/2012. Ya jagoranci sallar juma’a na riƙo na tsawon sati shida a rayuwarsa. Ya fara a ranar 10/08/2012. Sannan kuma ranar litinin aka ba shi muƙamin (S.A.S) a ƙaramar hukumar Kudan, wato Senior Arabic Supervisor (Shugaban Malaman Arabiya Na ƙaramar Hukumar Kudan).

    Karatun Zamani

    Ya halarci makarantu kamar haka;

    1. Model Primary School Kudan, Kaduna (Sep, 1973 – June, 1978).

    2. School For Arabic Studies, Kano (S.A.S) (1983 – 1989).

    3. Institute of Education, Ahmadu Bello University Zaria, Nigeria (1985 -1989).

    4. Jama’atu Institute of Arabic & Islamic Education, Zaria (2000 – 2002).

    5. Institute of Education, Ahmadu Bello University Zaria, Nigeria (2000/2002 Session). Allah Ya amshi rayuwarsa a ranar Alhamis 06/04/2017 = 9/7/1438 A.H, Allah Ya gafarta masa zunubansa, Amin.

    Don karanta al’adar Bahaushe danna nan

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Tarihin Marigayiya Hajiya Gude Mai Magani

    Tarihin Marigayiya Hajiya Gude Mai Magani

    An haifi hajiya Gude mai magani a Ƙofar Arewa gidan malam Tanko, ta yi aure a gidan malam Tanko, wanda aka yi haɗin zumunci da Yusha’u (wakili), hajiya Gude ta shahara wajen bayar da magani kowace cuta, wanda sai mutum ya tafi asibiti sun kasa sai a turo mutum wajen ta wanda da yardar Allah kuma sai ka ga an samu nasara.

    Hajiya Gude tana aiki ne da aljanu wajen warkar da mutane cutar da take damunsu, wanda hakan kuma ya faru ne  bayan an ɗaura mata aure, wata rana tana daka da rana, sai kawai aka ga ta tsaya ƙyam tana  lallauyewa,  tana yin ƙasa, tana faɗuwa ƙasa sai kawai aka ga ta kasa tafiya, to tun daga ranar ƙafar ta ba ta sake miƙewa dai-dai ba har sai da ta rasu.

    Idan an kai mace asibiti ɓangaran haihuwa, sai likitoci suka yi iya bakin ƙoƙarin su, amma kuma ba a samu nasara ba, sai a turo mace wajen ta, to da zarar ta dafa kan mace,  ta yi waɗansu addu’o’i haɗi da ba mace rubutu, sai kawai can sai a ga mace ta haihu lafiya. Haka kuma, idan mace ma tana da ciki suna zuwa wajenta domin karɓan magani.

    Don karanta tarihin ranar demokraɗiyya a Najeriya danna nan

    Bugu da ƙari kuma, akwai wani aljani wanda yake zuwa kanta wanda ake kiransa da suna “Ɗan malam”, wanda shi ne yake zuwa kanta duk ranar Laraba, wanda mutane da dama suna jin daɗin aikin ta, sannan  kuma idan mutum kayansa ya ɓace ko yana yin sata  ko dai wani abu mara kyau, to da zarar an kai mutum wajenta akan samu mafita.

    Har ila yau, idan ta gama aikin, to kuɗin da ta samu a wannan ranar takan ɗauka ta raba wa yara, haka kuma akwai wani mutum ana kiransa da suna Magaji yana ɗaya daga cikin mutanen da suke yi mata rubutun sha, wanda take ɗebowa ta ba mara sa lafiya idan ta yi musu aiki.

    Hajiya Gude mai magani ta shahara wajen bayar da magun-gunan gargajiya wajen warkar da marasa lafiya akan cututtaka daban-daban kamar su cutar Aljanu da cutar jiki (Ciwon kai, ciwon ciki, ciwon baya, ciwon ƙafa, ciwon ƙirji, rashin haihuwa da kuma maganin naƙuda), ta rasu a shekara ta 2012 ta bar ‘ya’ya guda huɗu daga ciknsu akwai Maryam (Dogara) da Abdullahi da Mustapha (muɗɗafa) da kuma Balaraba.

    Danna nan don karanta maganin damuwa

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Tarihin Hassana Abdullahi Hunƙuyi

    Tarihin Hassana Abdullahi Hunƙuyi

    An haifi Hassana Abdullahi a garin Hunƙuyi a shekarar 1980. Tana zaune da maigidanta da yaransu a garin Hunƙuyi, Ƙaramar hukumar Kudan, jihar kaduna.

    Ta yi karatun firamare, a central firamare school Hunƙuyi, daga nan sai ta wuce makarantar kwana ta ‘yammata da ke Kaduna (G.G.S.S KAWO KADUNA). Tana da takardar shaidar malanta ta (NCE). Inda take aiki da sashin ilimi na ƙaramar hukumar Kudan. Tana riƙe da muƙamin (Head mistress) shugabar malamai.

    Haka kuma ɗaliba ce a jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya. Inda take karatun digiri ɗinta a fannin library and information science. Sannan kuma, ita ce mataimakiyar Ameerah ta biyu(2) a ƙungiyar Muslims students’ society of Nigeria a Kaduna Area Unit, Maƙarfi /Kudan Area council. Haka kuma, ita ce mataimakiyar magatakardar ƙungiyar marubutan Arewa ta ƙasa Nijeriya (Arewa Writers Association of Nigeria).

    Har wa yau, ta yi aiki tare da wata ƙungiya da ke tallafawa ‘ya’ya mata, don ci gaban karatunsu, wato adolescent girls iniative Center for Girls Education. Ta taɓa cin Gasar Rubuta ƙagaggun ƙananun labarai, wanda makarantar malam banbadiya tare da haɗin gwuiwar pleasant library and book club, Katsina suka shirya, inda ta zo ta biyu a labarinta mai taken “A SASANTA”

    Ita marubuciyar littattafan Hausa ce, ta rubuta littattafai kusan ashirin, ga kaɗan daga cikin su:

    1. Makircin Zuciya.

    2. GSM Kururuwar Iblis.

    3. Kinfin Kishiya.

    4. Hangen Nesa.

    5. Komai da Lokacinsa.

    6. Mummunar ƙaddara.

    7. Illar Kwaɗayi.

    8. Tsananin Kiyayya.

    9. Rashin Jituwa.

    10. Dogon Buri.

    11. Dubu Ta Cika.

    12. Kin Yi Bajinta.

    13. Ya Fi Dare Duhu.

    14. Akwai Babbar Matsala.

    15. Mizanin Hankali.

    16. Ragayar Dutse .

    Da sauran su.

    (Mun samu waɗannan jawaban ne daga bakin Hassana Abdullahi Hunƙuyi ta hanyar rubutawa da ta yi ta turo min ta imel ɗina a ranar Lahadi 12/07/2020).

    Don karanta larabci da yanda ya shigo ƙasar Hausa  danna nan

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Tarihin Mawaƙi Salahuddeen Sani Kudan

    Tarihin Mawaƙi Salahuddeen Sani Kudan

    An haifi Salahuddin Sani a gidan limamin juma’a na garin Kudan, wanda ke ƙofar Arewa Kudan a cikin ƙaramar hukumar Kudan a ranar 01/01/1989, ya yi karatu a Model Primary school take Kudan a shekara ta 1995-2000. Ya yi karatu G.G.S.S Kudan a 2000-2006, ya yi karatu a makaranatar gaba da sakandire ta Maƙarfi wato Shehu Idris Collage of Health a 2014-2017. Ya yi aikin asibitin kuɗi da ke Kaduna Tudun Wada mai suna AITAM.

    Yanzu kuma yana aiki a asibitin Gwamnati wanda ke garin Kudan a cikin ƙaramar hukumar Kudan, jihar Kaduna. Sannan kuma ya fara karatun addininsa ne a makarantar Hayatul Islam ƙofa, wacce take bakin kasuwa Kudan, amma kuma ya yi saukarsa ne a makarantar Irshadul Aulad wacce take ƙofar Arewa Kudan, haka kuma ya fara bege ne a Irshadul Aulad a 2003 waƙar da ya fara yi ita ce “Mubar cuta”, sannan kuma ya yi karatun fiƙihu a wajen marigayi malam Suraj Yunusa Kudan, ya yi karatun allo a wajen Alaramma malam Iliya na tsawon shekara biyu kafin ya kuma zuwa islamiyyah.

    Shaharar sa

    Shi ne wanda ya assasa ƙungiyar sha’irai a garin Kudan mai suna Raudatul shu’ara’ul Islam Kudan a shekara ta 2015, wanda a yanzu tana da mutane guda ashirin. Bugu da ƙari kuma, ya iya sana’ar kafinta wanda ya koya a wajen ‘ya’yansa wato Ahmad Gaddafi, ya kuma iya sana’ar nona da kiwo, sannan kuma shi ne wanda ya buɗe makarantar Taufiƙil Islam, wanda take Furoja a garin Kudan, jihar Kaduna.

    Ya kuma rubuta ƙasidu da dama , ga kaɗan daga cikin kamar haka;

    1. Raddi.

    2.Shu’ara’u ‘yan Kudan.

    3. Raudatul Shu’ara’ul Islam.

    4. Ta’aziyyya (Rabi’u).

    5. Ƙololuwar matsayi.

    6. Ranar murna.

    7. Maulidin muke yi.

    1. (Mun samu wannan jawabin ne daga bakin Salahuddin Sani wanda ya rubuta ya turo min da shi ta waya (Message) a ranar Asabar 25/12/2020) da misalim ƙarfe 7;30 na safe).

    Domin karanta tarihin Salmanu Faris Adam danna nan

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Tarihin Salmanu Faris Adamu

    Tarihin Salmanu Faris Adamu

    An haifi Salmanu Faris A. Shu`aibu a garin Kudan a ƙofar Arewa Gidan Malam Tanko, a Ƙaramar hukumar Kudan wacce take jihar kaduna, sunan mahaifinsa shi ne Alhaji Adamu Shu`aibu Kudan ya rasu a ranar talata 05/08/2008 dai-dai da 1439 bayan hijra da misalin ƙarfe 05:30 na yamma.

    Haka kuma sunan mahaifiyarsa ita ce Fatima Mahmud Kudan ‘ya ce ga Maryam sarki Yakubu (wacce aka fi sani da ɗango), sannan kuma su goma sha ɗaya ne a cikin ɗakin su, akwai yayyan sa guda huɗu su ne Rahinatu da Murtala da Umar da Bilkisu, sai kuma ƙannan sa guda shida su ne Saratu da Hamisu da Hajara da Mahmud da Zahariyya da kuma Zulaihat, sai kuma waɗanda suka haɗa mahaifi ɗaya daga cikin su akwai Talatuwa da Labaran da Isah da kuma Lawan.

    Karatunsa Da Rayuwarsa

    Ya fara karatun allo a hannun Alaramma Malam marigayi Aliyu Labaran Kudan (Damo sarkin haƙuri) a shekara ta 1998 har zuwa Shekara ta 2008, a inda ya samu damar sauke Alƙur’ani mai girma na farko, sannan kuma ya cigaba da sauka ta biyu, ya yi karatun littattafai na addini a hannun malamai da dama kamar su Marigayi Alaramma Malam Surajo Yunusa Kudan da Malam Shitu Bashir Kudan da marigayi Malam Adamu Azare Panshekara da Alaramma Malam Misbahu Tsaure Panshekara da Malam Nura Yahaya Panshekara da kuma Sheikh Umar Sani Fagge Kano.

    Sannan kuma ya fara karatun zamani (boko) ne a makarantar Model Primary School Kudan a Shekara ta 2001-2007, sai ya wuce makarantar gaba da Firamare ƙarama ta garin Kudan wato J.S.S Kudan a Shekara ta 2007-2010, sai ya tsallaka zuwa Unity School ƙaraye, amma kuma ya kamala karatun sa ne G.S.S ƙayi Panshekara a Shekara ta 2013.

    Sai ya wuce makarantar koyar da Ilimin na’ura mai ƙwaƙwalwa (Computer), wato Troubleshooting and Information Technology (T.I.T) Kano, a inda ya samu damar karanta Data and Information Technology (Professional Diploma) da News Reporting and Photographic (Professional Diploma) da Networking and Maintenance (Higher  Professional Diploma) da Web Designing (Higher  Professional Diploma).

    Sai kuma ya tsallaka zuwa jami’ar Bayero, a inda ya samu shaidar shiga (Admission) a Shekara ta 2015 wanda ya karanci Ilimin nazarin halittu  {Bsc  (Ed)  Biology}. Bugu da ƙari kuma, ya yi karatu a ɓangaran kiwon dabbobi (Poultry farming) a  makarantar Directorate Youth Development  & Economic Empowerment Kano state  2016.

    A lokacin da yake ƙarami har zuwa tasowarsa ya ɗan yi sana’o’i daban-daban kamar su tallan attarugu da albasa da ƙosai da Tibani da Youghout a ranakun da babu makaranta ko kafin ya tafi makaranta ko kuma bayan an taso daga wata makaranta, domin samun abun sawa a baka.

    Haka kuma, a lokacin da yake J.S.S yana zuwa daji ,domin yin ƙwadugo ko kwandilo (bushashshan kashin shanu) ko Tushiya (bushashshiyar tushen dawa) ko ciyawa a lokacin da babu karatu, domin biyan kuɗin  makaranta da samun abin sa wa a baka wai  ya  fi a rataya, saboda a lokacin mahaifinsa ya rasu.

    Har ila yau, a lokacin da yake S.S.S Two (2) Yana zuwa aikin kwana masana’anta, sannan kuma da safe sai ya wuce makarantar boko da yamma kuma sai ya ɗan yi karatun allo da na Fiƙihu kafin dare ya yi, sai ya tafi wajen aikin sa, ga kaɗan daga cikin guraren da ya yi aiki kamar haka;

    1. Ya yi aikin matsen man gyaɗa a kamfanin matsan gyaɗa na Alhaji Gambo wanda yake Zuwaciki (2010-2013).

    2. Ya yi aiki a kamfanin samar da lemu na kwalba (coka-cola 2013-2014).

    3. Ya yi aiki a Wreca Staff School Challawa (2015- 2019).

    3.Ya yi aiki a Vital Academy bayan janare a Zuwaciki (2019- 2021).

    4. Ya yi aiki a Madrasatun Nuruddin Islamiyya wa tahfizul ƙur’an Panshekara a matsayin mataimakin shugaban makaranta (2015-2019).

    5. Ya yi aiki a Madrasatun Imamu Malik Bin Anas Islamiyya Panshekara a matsayin ma`ajin kuɗi (Treasure 2015-2017).

    6. Ya yi aiki a Madrasatun Darussunnah Firamare School Islamiyya Panshekara a matsayin shugaban musabaƙa (2014-2015).

    7. Ya yi aiki a Madrasatul Irshadul Aulad Islamiyya Panshekara (2013-2024).

    8. Ya yi aikin ƙwarewa(IT) na gidan rediyon Kano (Kano Radio 89.3 FM) na tsawon watanni  uku.

    9. Ya yi aikin sakai (Voluntary) a  Express Rado 90.3 FM Kano daga 2019-2022.

    10.Ya samar da ƙungiyar marubutar Arewa ta ƙasa Nijeriya (AWAN) a 2019.

    11. Ya zama shugaban ƙungiyar marubutan Arewa, wato “AREWA WRITERS ASSOCIATION of NIGERIA(AWAN)” na ƙasa daga 2019-Yau.

    13. Ya yi aiki da makarantar Cradle to Career Academy (C2C) Zuwaciki, Kano daga 2021-yau.

    14. Ya zama mataimakin shugaban tashar “Use Your talent Tv” daga 2022 – yau.

    Ya yi waɗancan karatu na na’ura mai Ƙwaƙwalwa (Computer) ya kuma shiga jami’ar Bayero Kano da ‘yan sana’o’isa na hannu.

    Fara Rubutunsa

    Ya fara rubutu ne a Shekara 1435 bayan hijira dai-dai da 2013, a lokacin yana karatu a Unity School Ƙaraye, bisa dalilin ganin irin matsalolin mace-macen aure da ya gani haɗi da gori da waɗansu mutane musulmi suke yi wa waɗanda suka musulunta ko kuma suke aikata wani abu mara kyau, sai kuma daga baya suka tuba suka koma ga Allah (Subhanahu Wata’ala). Sai ya rubuta wani littafi mai suna “KAMBUN MA’AURATA” da kuma “NASIHA GA MUSULMI AKAN SON ZUCIYA”. Daga cikin littattafan da ya rubuta su ne kamar haka:-

    1.Kambun Ma’aurata 1&5.

    2.Nasiha ga musulmi akan son Zuciya 1&4.

    3. Ramadan Mubarak.

    4. Khulasatu Siratun Nabiyyi.

    5.Ɗarikul Hudah.

    6. Ina Ma’aurata.

    7. Babban Kundi (Alƙur’ani mai girma).

    8. Righteous path to Islamic education 1.

    9. Salmanu da Salma.

    10.Kambun masoya.

    11.Mace ikon Allah.

    12.Kyauta ko Rance.

    13.Abincinka maganinka.

    14.Miskilar mace.

    15.Yar islamiyya

    16.Gwarazan Kudan (ya koma tsani).

    17. Tarkon ƙauna.

    18.Hausa ba dabo ba 1&2.

    19.Muguwar ƙaya 1.

    20.Shugabanci ko mulki ?

    21. Na duƙe tsohon ciniki (Agriculture).

    22. Mata hasken rayuwa.

    23. Duniyarka A Hannunka (Computer)

    Da Dai sauran su.

    Muƙalolin sa

    1.Influence of student’s learning difficulties in Biology on Academic achievement in Gwale local government area of Kano state (Bsc{Ed} Project 2019).

    2. Aure tushen arziki.

    3. Alƙu’ani jigon rayuwa.

    4. Sanadiyar soyayya.

    5. Matsalolin mutuwar aure.

    6. Alamomin shigar so.

    7. Magani a gonar yaro.

    8. Falalar da Allah ya yi wa mace.

    9. Amfanin shayar da jariri nono zalla.

    10. Dokin tsira.

    11. Wacece mace.

    12. Hukuncin jinin haila.

    13. Illar rubutu/karantun batsa ga marubuta da makaranta; Takardar da aka gabatar da ita a majalisar marubuta ta jahar Yobe 07/01/2021.

    14. Rayuwar Manzon Allah (S.W.A) ita ce abin koyi: Takardar da aka gabatar da ita Madrasatul Darul Haƙ Islamiyya Zawaciki Panshekara, ƙaramar hukumar Kumbotso, jihar Kano.

    15. Wacece mace ta gari.

    16. Hikimar yin zance (soyayya).

    17. Lokutan da soyayya ta fi daɗi.

    18. Illolin yin tsafi ga al’umma.

    19. Amfanin taimako.

    Lambar Yabo

    Ya samu lambobin girmamawa daga wurare daban- daban kamar su;

    1.Kainuwa Authors Kano, wanda suka koma Kainuwa Authors Forum a yanzu 2020  (2019).

    2.Darussunnah Firamare Islamiyya School Panshekara   (2016).

    3.Irshadul Aulad Islamiyya Panshekara (2016).

    4.Nuruddin Litahfizul ƙur’an Islamiyya Panshekara (2015).

    5.Imamu Malik bin Anas Islamiyya Panshekara (2015).

    6.Wreca Staff School Challawa Panshekara  (2016).

    7.Nigeria Universities Education Students Association (NUESA) Bayero University, Kano Chapter (2019).

    8.Yobe Writers Association (YOWA) a (2020).

    9. Majalisar Marubuta 2021 (akan illar rubutu da karantun batsa).

    10. Arewa Writers Association of Nigeria (AWAN).

    11. Cradle to Career Academy (C2C) Zawaciki, Kano (The most active extra-curricular activities and the effective student learning support teacher).

    12. Hadiza Ibrahim Aliyu School of Festival (HIASFEST) a matsayin wanda ya lashe gasar kimiyyar halittu (Biology) zuwa ga harshen Hausa (Hausa science book/biology) na shekara ta 2023.

    14. Hadiza Ibrahim Aliyu School of Festival (HIASFEST) a matsayin wanda ya zo na biyu a gasar kimiyyar kwamfuta (Computer) zuwa ga harshen Hausa (Hausa science book/computer) na shekara ta 2024.

    Danna nan don karanta tarihin Dakta Ado Zakari Kudan

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Haihuwarsa Da Shayar Da Annabi S.A.W

    Haihuwarsa Da Shayar Da Annabi S.A.W

    1. An haifi Mazon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) a garin Makkah ranar litinin, sha biyu ga watan rabiyul-auwal (12) Shekarar Giwaye.

    2. An ambaci shekarar haihuwarsa Giwaye, Saboda sarkin Habasha, ya aika sojoji a shekarar haihuwarsa zuwa garin Makkah, domin su rushe Ka’aba, ya kasance a cikinsa akwai Giwa mai mai girma, sai Allah (Subhanahu wata’ala) ya hallaka rundunar (sojojin), domin (saboda) girmama shekarar haihuwar annabi (Sallallahu alaihi wasallam).

    3. Suwaibatul-Assalamiyya ta shayar da shi, bayan mahaifiyarsa, wacce take yi ma babansa hidima Abu-Lahabi, sannan sai Halimatu-Sa’adiyya, har sai da ya kai shekaru huɗu (4) na daga rayuwarsa.

    Sharhi;

    An haifi manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) ne a ranar litinin sha biyu (12) ga watan rabbiyul-Auwal, ko da yake wasu ruwayoyin sun ce ranar sha bakwai ne (17) ga watan rabbiyul-Auwal, a garin Makka, a shekarar da ake kira da shekarar Giwaye . Dalilin da ya sa ake kiran wannan shekara shi ne wani gwamnan sarkin Habasha mai suna Abrahata ya shigo Makka da runduna mai yawa, bisa kan giwaye (bayan ya kame garin Yaman) da nufin rusa ɗakin Ka’aba da sauya alƙiblar mutane zuwa San’a (domin a wancan lokacin mutane sukan kawo ziyarar bauta a Ka’aba).

    Inda dama tuni ya gina wani guri don wannan ziyara. Amma daga baya lokacin da Abrahata ya iso Makka da wannan runduna tasa, sai Allah Ya aiko da wasu irin tsuntsaye ɗauke da tsakuwoyi a bakunansu, inda suka rinƙa jefo waɗannan tsakuwoyi a kan waɗannan runduna, nan take suka kashe sojojin da giwayen. Ta haka ne Allah ya yi maganin wannan azzalumi da mutanensa.

    Mahaifinsa dai shi ne Abdullah ɗan Abdul-Muɗallib ɗan Hashim; Mahaifiyarsa kuwa ita ce Amina ‘yar Wahbu, Kakansa kuwa shi ne Abdul-muɗallibi, wanda ya kasance yana da ‘ya’yaye da yawa, amma Abdullahi (mahaifin Annabi) da Abu-ɗalib (mahaifin Imam Ali) mahaifiyarsu guda ne. Don haka ya fito ne daga cikin tsatson Banu-Hashim, su kuma daga ƙabilar ƙuraishawa, waɗanda ke da dangantaka da annabi Isma’il (A.S) ɗan annabi Ibrahim (A.S).

    Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) dai ya tashi ne a matsayin maraya, saboda kasancewar mahaifinsa ya rasu yayin da ya kai ziyara Yathrib (Madina) watanni uku kafin haihuwar manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam). Tattare da baƙin cikin rasuwar Abdullah, amma haihuwarsa ta sanya iyalansa, Amina da Abdul-Muɗallib, cikin farin ciki da ba shi da iyaka.

    Sun shirya gagarumar walima ga ‘yan uwa da maƙwabta, inda aka yi yanka don murnar wannan haihuwa. A sakamakon haka duk Makka ta ɗauki murna, inda mutane suka yi ta zuwa gidan Abdul-Muɗallib don miƙa saƙon taya murna gare shi.

    A bisa al’adar mutanen makka, sukan kai ‘ya’yayensu shayarwa ƙauye, saboda samun kyawawan halaye da kuma yanayi mai kyau da dai sauransu, don haka an aika da Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) wajen da Halima ‘yar Abi-zu’aib a ƙauye, don shayar da shi. Haƙiƙa Halima ta sadu da alhairai masu yawa daga abin shayarwarta Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam).

    Har ila yau, al’adace ta Labarawa idan sun haihu, sai su nemi mace wacce za ta shayar masu da ‘ya’yansu a cikin ƙauyukan garin, saboda ‘ya’yansu su taso da hikima da dabaru iri-iri na harkar rayuwa, sannan kuma da Juriya na wahal-halun duniya daban-daban, saboda mutane da suka saba da jin daɗin rayuwar birni, za ka iya samun su  da lalaci  haɗi da rashin hikima na yau da kullum.

    Domin karanta sunayen baffanni ƙwarori da gwaggonnin Annabi SAW  danna nan

    Amma mutumin da ya saba da shan  wahala da jin daɗi na rayuwa, to za ka same shi da hikimomi haɗi da kaifin basira da jajircewa akan ayyuka na yau da kullum, sannan ba ya raina sana’a ko ɗan yaya take. Saboda haka, an san ƙabilar Banu-Sa’ad sukan fito neman yaran da za su shayar da su, sai Halimatu ‘yar Abi-zu’aibin ‘yar ƙabilar Banu-Sa’ad ta ɗauke shi za ta shayar da shi (sallallahu alaihi wasallam).

    Sannan suka yi wa Annabi (Sallallahu alaihi wasallam) laƙabi da suna ɗan kabshata, a lokacin da yake yi masu wa’azi akan su bar bautar gumaka, su dawo bautar Allah (Subhanahu wata’ala), sai suke cewa ka ji ɗan Kabasha! Yana cewa wai “yana da wanin abin bauta, ana yi masa magana daga Sama!, wato Allah yanayi masa wahayi, ba irin  Allolin da muke bautawa ba, sannan kuma Allah (Subhanahu wata’ala) Na sama ba a ganinsa” da dai sauransu.

    Halima Sadiya ta shayar da Shi tsawon shekaru huɗu (4), wanda yake a lokacin da take shayar da shi akwai abubuwa da yawa waɗanda suka faru, kaɗan daga cikin akwai: magana da zaki a lokacin da annabi da wasu mutane suka fita waje lokacin yana ƙarami sai ga wani karkeci (zaki) babba, sai sauran mutanen suka fita da gudu, sai annabi ya tsaya ya yi magana da zakin har zuwa ƙarshen labarin.

    Sannan mala’iku guda biyu (2) sun zo wajen sa da siffar tsuntsu suka tsaga ƙirjinsa shi ma har zuwa ƙarshen labarin. Sannan kuma akwai wani lokaci da annabi ya tashi cikin dare zai yi fitsari, ga shi Halimatu tana bacci a ƙofar ɗakin, sai ya ji tsoro wucewa ta gabanta, saboda kadda ta farka daga bacci, ta hana shi fita waje, saboda wancan abin da ya faru na mala’ikun can, sai annabi (Sallallahu alaihi wasallam) ya ɗauki taska ya yi fitsarin a cikinta, sannan ya koma ya kwanta bacci, can sai Halimatu ta tashi daga baccci tana jin ƙishir ruwa, sai ta ga wancan taska, ta ɗauka ruwa ne sai  ta shanye ba ki ɗaya.

    Bayan gari yawaye, sai annabi yana neman wancan taskar zai zubar da abin da yake cikinta, sai ya duba inda ya ajiye ta, amma bai ganta ba, sai ya tambayi Halimatu, tace ai na ɗauka ruwa ne har ma na shanye, sai annabi yace da ita tun da kin sha wannan, to  zai yi miki maganin cututtuka da yawa sosai a jikin ki.

    Sannan ya yi wa tsuntsaye addu’o’i a lokacin da Halimatu za ta dawo da shi gida, da dai sauransu. Lokacin da annabi ya cika shekaru shida da haihuwa sai Halima ta dawo da shi zuwa Makka, yayin da ya sami kakansa Abdul-muɗallibi a matsayin mafi alherin mai raino gare shi; domin ya kasance yana ba shi duk abin da yake buƙata na tausayi da ƙauna irin ta iyaye masu lura. Ya kasance yana ba shi matsanancin kulawa fiye da duk iyalansa.

    A shekara ta shida da haihuwarsa, sai mahaifiyarsa ta tafi da shi ziyarar danginsa na nono, wato Banu-Uɗayyu bin Najjar a Yasrib (Madina), a tare da su akwai Ummu Aiman. Sai suka saura a can har na tsawon wata ɗaya, sannan sai suka juyo suka kama hanyar dawowa Makka. A hanya ne ajali ya samu mahaifyarsa Amina, aka binne ta a Abwa’i, wanda wani gari ne da ke tsakanin Makka da Yathrib (Madina).

    Sai Ummu Aiman ta dawo da shi wajen kakansa, yayin da ita kuma ta ɗauki nauyin aikin uwa, kamar yadda kakansa Abdul-muɗallibi ya ɗauki aikin uba. Wannan kulawa dai ba ta jima sosai ba don shi ma wannan kakan nasa Allah Ya ɗauki ransa a lokacin Annabi  na ɗan shekara takwas da haihuwa. Daga nan sai kulawarsa ta koma hannun Baffansa Abu-ɗalib, wanda ya yi mu’amala da shi da ƙauna, sassauci da lura irin ta iyaye, ta yadda babu wani daga ‘ya’yansa da ya samu irin hakan.

    Ya kasance yana bacci a shimfiɗar Baffansa, yana zama gefen sa, yana cin abinci tare da shi, yana fita tare da shi duk lokacin da ya fita daga gidansa; da wasun waɗannan na daga nau’o’in lura da so waɗanda irin su ke da wuyan samu.

    Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) ya kasance yana girma a hannun Baffansa da halayensa na girma tare da shi, ta yadda har sai da ya keɓantu da wasu siffofi na nagarta a tsakaninsa da mutanensa da suka haɗa da gaskiya, riƙon amana, waɗannan siffofi dai sun keɓanta da shi ne ban da waninsa; har ma ta kai ma mutanen suna kiransa da “mai gaskiya da riƙon amana”.

    Ganin cewa dai ya fara girma kuma don kada ya zauna haka, sai annabi (Sallallahu alaihi wasallam) ya fara aiki a lokacin yana matashi. Aikin da ya fara yi shi ne kiwon tumaki/awaki (dabbobi). Sannan sai ya bi Baffansa Abu-ɗalib zuwa Sham don kasuwanci. A wannan lokaci ma dai manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) ya nuna fasaha, ƙwazo, gaskiya da kuma riƙon amana a wannan fage.

    Lamarin da ya jawo hankalin wata hamshaƙiyar attijira mai suna Khadijah ‘yar Khuwailid zuwa gare shi. Don haka sai ta neme shi da ya kula mata da wani sashi na kasuwancinta, ta ba shi wasu dukiya mai yawan gaske don gudanar da kasuwanci, wanda daga ƙarshe ta samu riba mai girman gaske da ba ta taba samu ba a baya.

    A shekarar da aka haifi Annabi Muhammad  (Sallallahu alaihi wasallam), an ga abububuwa iri-iri waɗanda suka faru. Kaɗan daga cikinsu su ne: Mutuwar wutar Kisra, wacce mutanen gari suke bautawa wadda ta ɗauki shekara da yawa ba ta mutuwa, sannan sama ta yi haske, gari ya yi tsit ba hayaniya, da dai sauransu.

    Haka kuma dalilin da yasa aka ambaci shekarar haihuwarsa da shekarr giwaye shi ne, a wannnan shekara ne sarkin Habasha ya tura giwaye da yawa sosai, domin su zo rushe ɗakin Ka’abah, wanda yake a wannan lokacin akwai gumaka guda ɗari uku da sittin (360) wanda ake bautawa, bayan gumaka na Ugunwanni da na kasuwanni haɗi da na gidaje.

    Danna nan don karanta sunayen annabi SAW

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Tarihin Abdullahi Mustaspha Mai Hoto Kudan

    Tarihin Abdullahi Mustaspha Mai Hoto Kudan

    An haifi Abdullahi Mustapha a 1985 a unguwar tsauni Kudan. Ya yi karatu Islamiyya a Madarasatul Hayatul Islam bakin kasuwa Kudan daga 1990/1997. Ya yi Firamare daga 1990/1996. Ya yi karatun gaba da Firamare daga 1997/2014.

    Ya sake komawa makaranta, wanda ya yi karatu a National Teachers Institude Kaduna (NTI), amma a ɓangaran karatun nesa (Distanca learning Studies) a reshen su da ke Hunƙuyi, wanda a nan ne ya samu shaidar malanta (NCE).

    Bayan haka, ya yi gwagwarmaya a gidan mai (Petroleum station) gidan man na mahaifinsa, tun a shekara ta 1995-1998 inda daga nan Allah ya amshi rayuwar mahaifinsa marigayi Alh. Zakari Haladu Kudan, Allah ya ji ƙansa da rahama.

    Bayan wasu shekaru ya fara tunanin ya fara aiki a studio wato shagon ɗaukan hoto, sannan ya nemi izinin babban mai ɗaukar hoto na wannan lokaci wato marigayi Hassan haske Allah ya ji ƙansa da rahama, inda a wurinsa ya samu ƙwarewa na tsawon shekaru biyar (wanda shi wancan bawan Allah yana ɗaya daga cikin mutanan da suke zuwa Kudan ɗaukar hoto a duk ranar Juma’a) kuma sun rabu da shi lafiya cikin girmamawa da ladabi.

    Bayan haka, wani lokaci Alhaji Sabi’u Ibrahim kansila a lokacin yana da studio, shi ma ya ɗauke shi aiki a shagonsa, a matsayin shugaban shagon ƙarƙashin kulawar Aliyu Wada (mai Talata) na tsawon wani lokaci. A wannan studio, ya yi aiki tare da ma’aikata uku, wato  Usman Isah (Ameer hoto) da Jamilu Zakari da Sani Umar.

    Dukkanin su ya koya musu aiki ta yanda kowannen su ya samu ƙwarewa, biyu daga cikinsu ma sun samu damar mallakar studio nasu, wato Usman Isah (Ameer hoto) da kuma Jamilu Zakari. A yanzu haka yana da babban  studio, wanda mallakarsa ne, wanda yake printing/photocopy da su. Yana yin  noma da kasuwanci, yana da  aure da ‘ya’ya, Allah ya ƙarama rayuwa albarka amin summa amin.

    Ya yi karatu a Nigerian communication commission (NCC) Zaria a reshensu da ke GSS Kudan, a inda a nan ne ya samu takardar diploma a computer,  a networking/computer engineering daga 2013/2014.

    (Mun samu wannan jawabin ne daga bakin sa, wanda ya rubuta ya turo min da WhatsApp a ranar 12/02/2021 da misalin ƙarfe 7:33 na safe).

    Danna nan karanta tarihin Hajiya Halima Jumare Kudan

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Tarihin Rt. Hon. Isa Muhammad Ashir Kudan

    Tarihin Rt. Hon. Isa Muhammad Ashir Kudan

    An haifi mai girma Isa Muhammad Ashir a garin Kudan a ranar 23rd ga watan October, 1962, a cikin ƙaramar hukumar Kudan, jihar Kaduna. Ya yi karatu a Model Primary School Kudan daga 1968-1974, ya yi karatu a makarantar Kufena wacce take a Wusasa Zaria a 1976-1980.

    Ya yi karatu a Polytecnic Katsina a 1982-1985, wanda ya samu shaidar Diploma a ɓangaren harkan kasuwanci (Business administrative), ya kuma halarci makarantar Polytechnic Kaduna, wanda ya yi karatun gaba da Diploma wato HND a 1987-1989.

    Haka kuma a 1990 ne ya halacci wajen horas da manyan ɗalibai, wato NYSC Corps a Barno (BD/KD/89/4217). Sannan kuma a 1999 ne, ya yi Post-graduate a ɓangaren  cinikayya (marketing management). Bugu da ƙari kuma ya yi Master’s degree a public policy and administration a 2000-2001 a jami’ar Bayero Kano (B.U.K).

    Har ila yau, ya tsunduma harkar siyasa a 1996 a Jam’iyyar Zero party (ZP), wanda ya tsaya takarar shugaban ƙaramar hukuma (Chairman), amma bai samu nasara ba, ya kuma sake tsayawa a jam’iyyar Social democratic party (SDP) a 1997, sannan kuma ya zama member a KSHA ƙarƙashin jam’iyyar DPW a 1999-2000. A inda  aka zaɓe shi a matsayin ɗan-majalisar jihar Kaduna (House of Assembly) mai wakiltar Kudan-Maƙarfi zuwa 2000-2003.

    Haka kuma, an sake zaɓansa a matsayin ɗan-majalisar jihar Kaduna daga 2003-2007. Sannan kuma an sake zaɓansa a 2007-2011 a matsayin ɗan-majalisa na tarayya mai wakiltar Kudan-Maƙarfi a jam’iyyar People Democratic Party (PDP). Haka kuma, ya sake zama ɗan-majalisa na Tarayya a karo na biyu daga 2011-2015.

    Haka kuma a 2014 ne ya koma jam’iyyar All progress congress (A.P.C), wanda ya yi takarar Gwamna na zaɓen cikin gida, amma bai samu nasara ba, a 2019 ne kuma ya sake tsayawa takarar Gwamna a jam’iyyar PDP bayan ya koma cikin Jam’iyyar, wanda kuma bayan an yi zaɓen gama-gari nan ma bai samu nasara ba. Haka kuma ya yi aure yana da mata guda ɗaya da kuma ‘ya’ya guda bakwai.

    Bugu da ƙari kuma, ya sake tsayawa takarar Gwamna a kakan zaɓe ta 2023, a ƙarƙashin Jam’iyyar PDP, wanda a nan ma bai samu nasara ba, tun da mutane suna ganin cewa an yi maguɗin zaɓe sosai.

    Sannan kuma, ya samu damar samun sarautar Sarkin bai Zazzau, wanda masarautar Zazzau ta naɗa shi, duba da irin tulin ayyuka na ci gaba, wanda ya samar da su a lokacin da yake kan mulkin. Haka kuma an samu ‘yan majalisun jiha da na Tarayya a ƙaramar hukumar Kudan-Maƙarfi, amma kuma ba a samu wani wanda ya kai shi aiki ba, saboda a lokacin da ya riƙe waɗannan mukamai ya samar da ayyuka kamar haka;

    1.Ya gina babban Asibiti a garin Kudan kusa da masallacin Idi na garin Kudan.

    2. Ya gina makarantar horas da ‘yan sanda a garin Kudan hanyar Sundu ko hanyar Barmo.

    3. Ya gina Masallacin Juma’a a garin Kudan, wanda yake ƙofar gidan hakimi.

    4. Ya gina makarantar koyan sana’a, wanda take kan hanyar zuwa Doka daga Kudan.

    5. Ya gina makarantar Firamare a ƙofar Arewa a garin Kudan.

    6.Ya gina ɗakin koyan sarrafa na’ura mai kwakwalwa a garin Kudan da Hunƙuyi (E-library).

    7. Ya gina wajen zaman ‘yan Sanda (Headquater) a garin Kudan kan hanyar zuwa Doka daga Kudan.

    8. Ya gina wajen koyon wasan ƙwallon ƙafa a garin Kudan wanda yake kan hanyar zuwa Garu.

    9. Ya gina ɗakin taro a garin Kudan wanda yake kan hanyar zuwa Garu.

    10. A samar da fitilloli masu samar da haske ta hanyar amfani da hasken rana (electry-Solar) a faɗin ƙaramar hukumar baki ɗaya.

    11. Ya samar da famfo wanda yake amfani da hasken rana (Water-solar) a faɗin ƙaramar hukumar baki ɗaya.

    12. Ya tura mutane ashirin zuwa ƙasar wajen domin yin karatun digiri na farko.

    13. Ya samar da tituna a cikin garurruwan da suke a faɗin ƙaramar hukumar baki ɗaya.

    14. Ya  sabunta da faɗaɗa  ginin Dam, wanda yake Kudan kan hanyar zuwa Doka ko Sundu daga Kudan.

    Guraren da ya yi aiki

    1. Ya yi aiki a ma’aikatar kuɗi (Ministry of finance) a 1980-1982.

    2. Ya yi aiki a ma’aikatar samar da kuɗin cikin gida (Internal Revenue) a 1985-1992.

    3. Ya yi aiki a ma’aikatar kasuwanci da wajen shakatawa (ministry of commercial Industry and Tourism) a 1992-1993.

    Danna nan don karanta tarihin Adamu Yero Hunƙuyi

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu