Tag: yadda ake

  • Misalan Waƙafi Ababen Koyi A Tarihin Musulunci

    Misalan Waƙafi Ababen Koyi A Tarihin Musulunci

    1. Zamanin Halifofi Shiryayyu ba shakka an samiu nau’o’i daban-daban a wannan lokaci, kaɗan daga cikin misalan su sun haɗa da:

    Waƙafin da sayyidina Umar ya yi da kasonsa guda ɗari dake Khaibar, wanda ya rubuta wasiyya da kansa da cewa:- “Da sunan Allah Mai rahama Mai jinƙai, wannan takarda sheda ce ta wasiyyar da bawan Allah Umar shugaban muminai ya yi ko wani abu zai faru da shi (yana wasiyya da cewa) Samgah da Sirmata bn Al-Akwa (gonaki biyu) da dukkan bayin da suke cikinsu da kasona guda ɗari dake Khaibara da dukkan bayin da suke cikinsu”..

    Waƙafin da Sayyidina Ali Bn Abi-Ɗalib Allah Ya yarda da shi ya yi, wanda ya rubuta shi kamar haka:- “Wannan takardar sheda ce bisa abin da Ali bn Abi-Ɗalib ya yi, ya kuma hukunta da dukiyarsa cewa; na sadaukar da (amfanin gonakinsa) na Yanbu da Wadil-Kura da Azinah da Ra’ah a cikin hanyar Allah; kuma ga ‘yan uwa na kusa da na nesa, kamar yadda ba za a yi kyauta da su ba, kuma ba za a gaje su ba, a lokacin rayuwa ko bayan raina”.

    Ba shakka wannan kaɗan ne daga cikin misalai da yawa na waƙafi; a lokacin halifofi shiryayyu, Allah ya yarda da su.

    2. Zamanin Mulkin Banu Umayya

    Ba shakka akwai misalai masu ƙayatarwa matuƙa na irin nau’o’i daban-daban na waƙafi da aka yi a wancan lokaci. Ga kaɗan daga cikinsu:-

    Gina babban masallacin nan na birnin Dimashk wanda har zuwa wannan zamani namu yana nan daram, wanda kuma muka ambata a baya cewa an gina shi a zamanin Halifa Walid ɗan Abdul – Malik wanda aka ruwaito cewa; a lokacin da zai gina wannan masallaci, sai da ya sa aka kawo masa ƙwararru daga ko’ina; waɗanda yawan su da sauran ma’aikatansu ya kai kimanin mutum dubu goma sha biyu.

    Ya kuma kashe kuɗi kimanin akwati ɗari huɗu; kowane akwati yana ɗauke da kwabbunan tataccen zinare guda dubu ashirin da takwas. Sai da ya shafe tsawon shekaru ashirin yana ginin wannan masallaci.

    Gina Asibitoci Da Hanyoyi Da Rijiyoyi

    Haka nan kuma shi dai wannan bawan Allah; shi ne mutum na farko da ya gina asibitoci na musamman don amfanin mutane.

    Haka kuma ya gina waɗansu na musamman da ya keɓance su ga masu ciwon kuturta; waɗanda a lokacinsa ya killace su, ya hana su bara; ya kuma ware maƙudan kuɗaɗe don yi musu magani da ba su cikakkiyar kulawa. Haka kuma, ya bayar da umarni ga gwamnansa mai kula da Madinah a wancan lokaci Umar ɗan Abdul-Aziz cewa ya gyara unguwanninta ya kuma gina rijiyoyi, ya kuma ɗauki ma’aikatan da za su rinƙa janyo ruwa don amfanin jama’a.

    Haka nan, ya aikawa dukkan jami’ansa a ko’ina kuɗaɗena suke cewa; su ware musamman ga mabuƙata tare da shimfiɗa hanyoyi da gidaje domin saukar baƙi kyauta. Bugu da ƙari kuma, wani kyakkyawan misali na waƙafi don amfanin al’umma shi ne ; yadda halifofin Banu Umayyah na wancan zamani suka bayar da muhimmanci matuƙa wajen gina madatsan ruwa, alal misali, a lokacin halifancin Umar ɗan Abdul- Aziz haka madatsan ruwa a wurare masu ɗumbin yawa kamar su Basra, da Arnmenia, da Dimashk da sauransu.

    3. Zamanin mulkin Abbasiyyawa

    Ba shakka halifofin zamanin Abbasiyya sun bayar da muhimmanci ga waƙafi a fannin gina asibitoci; da samar da littattafai don horar da ƙananan likitoci, tare da hayar ƙwararru da za su koyar da su duk ta hanyar waƙafi. Kaɗan daga cikin misalan asibitoci da aka gina a wancan lokaci; sun haɗa da asibitocin nan da ake kira Almustashfà Al-adudiy (wanda muka ambata a baya) wanda Haifa Adudud – Daulah al-Buwaihiy ya gina a birnin Bagdad a shekara ta (366 Hijiriyyah /976 Miladiyya) ya kuma ɗauki ƙwararrun likitoci a fannoni daban-daban waɗanda kimanin yawansu ya kai 24.

    Komai na asibitin kyauta ne, ga kulawa da marasa lafiya wajen abinci; da abin sha; da ɗinka musu sababbin tufafi, baya ga tsarin bayar da guzurin komawa gida ga duk wani marasa lafiya da aka sallama. Kamar yadda kuma ya zo a littattafan tarihi cewa, waɗansu daga cikin gwamnoni na wannan daula, sukan kashe kuɗaɗe maƙudai wajen yin irin waɗannan nau’o’i na waƙafi kamar yadda aka samu cewa, Ahmad ɗan Dolon gwamnan Masar a wancan lokaci, ya gina asibiti a lokacin da ya kammala, sai ya sadaukar masa da kuɗaɗen shigar da ake samu daga dar addiwan da kasuwar bayi da waɗansu gidaje nasa.

    Haka kuma ya kafa ƙa’idar cewa; a cikin waɗanda za su amfana da wannan asibiti ban da manyan hafsoshinsa da fadawansa da ‘ya’yan sarauta; haka kuma duk wanda za a kwantar a asibitin, sai an ba shi sababbin kaya ya sa, tsofaffin kuma za a adana masa su ne har zuwa lokacin da Allah ya ba shi sauƙi sai a damƙa masa kayansa.

    Haka kuma akan yi masa sabuwar shimfiɗa a kula da cin sa da shan sa, da yi masa magani, kuma ba za a sallame shi ba, har sai ya warke sarai; ya dawo yana cin duk wani abinci da ya saba ci kafin rashin lafiyarsa.

    Haka kuma a waɗansu lokuta akan gayyato likitoci daga wurare daban-daban don bayar da kulawa ga marasa lafiya, wato kamar dai abin nan da muka sani a wannan zamani da ake kira “medical tour”; (wato likitoci ‘yan sha-ka- tafi tare da biyansu haƙƙoƙinsu da ɗaukar ɗawainiyar duk wata buƙata ta su).

    Misalai na waƙafi da aka yi wancan zamani ba wai ya tsaya ne kawai ga gina asibitoci ba; haka kuma bai tsaya ga ɓangaren hukuma kawai ba. Wani ɗan ƙaramin misali da zai tabbatar mana da hakan shi ne, wani waƙafi da wani attajiri ya yi mai suna Fakhruddaula bn Almuddalib a birnin Bagdad (ya rasu a shekara ta 578 bayan Hijira ); ya gina wata katafariyar makaranta mai suna Dar Adhdhahab, ya damƙa ta a hannun wani mashahurin malami mai suna Jamaluddin bn Fadlan Ash- Shafi’i ya kuma sadaukar mata da wata dukiya tasa da abin da take samarwa kowace shekara, ya kai kimanin dinare dubu ɗaya da ɗari biyar.

    Bugu da ƙari, su kansu mata ba a bar su a baya ba; wajen wannan ayyuka na alheri, domin kuwa ya zo a littattafan tarıhi cewa Sayyida Zubaidah bnt Ja’afar bn Mansur; matar Halifa Harun Ar-Rashid ta haƙa rijiya da ake kira da “ainul mashash a Hijaz” ta kuma sa aka yi wa ruwanta hanya a tudu da gangare; har tsawon tafiyar mil goma sha biyu zuwa garin Makkah; wanda wannan aiki ya lashe kuɗi kimanin dinare miliyan ɗaya da dubu ɗari bakwai; (wanda ƙiyasin kowanne dinare ɗaya a zamaninmu shi ne nauyin giram 4.25 na tataccen zinare).

    A ɓangare na makarantu kuwa, tarihi ba zai taɓa mantawa da jerin gwanon makarantun nan da ake yiwa laƙabi da makarantun Nizamiyya ba; waɗanda waziri Nizamul Mulk Addardusi (ya rasu shekara ta 485 Hijiriyya) ya kafa, waɗanda da yawa daga cikinsu suka zamo a sahun farko a tarihin jami’o’i a duniya baki ɗaya. Haka nan ya ci gaba da gina irin waɗannan makarantu a ko’ina a cikin daular Musulunci, kamar yadda aka sami mashahuran malamai da suka koyar a waɗannan makarantu. Alal misali, a daidai lokacin da Imam Al-Ghazali yake koyarwa a reshenta na Bagdad, shi kuwa shahararren malamin nan mai suna Imam Al-Haramain Abu Al-Ma’ali Al-Juwaini yana koyarwa a reshenta na Naisabur.

    4. Daular Musulunci Ta Andalus

    A haƙiƙanin gaskiya ana iya cewa waƙafi na ɗaya daga cikin alamomin wuraren da daulolin Musulunci; suka kafu a ko’ina a faɗin duniya; domin kuwa shi ne kamar wata alama da ta zama ruwan dare a waɗannan dauloli a tsawon tarihinsu; duk da kasancewar sun kafu ne a wurare daban-daban kuma a lokuta mabambanta. Dalilin faɗin hakan kuwa shi ne, duk da cewa daular Musulunci da ta kafu a Andalus(Spain) ta yi nisa matuƙa; daga ƙasashen Larabawa waɗanda suke gabashin duniya.

    Domin kuwa Andalus tana cikin nahiyar Turai ne, to amma duk da haka, nau’o’i daban-daban na waƙafi da aka yi a cikinta, ko kaɗan bai gaza ga waɗanda aka yi a ƙasasshen gabas ɗin ba, a Alal misali, an samu Waƙafi a fannoni da dama a zamanin sarakuna irin su sarki Alhakam ɗan Abdur-Rahman An-Nasir wanda a lokacinsa ne wannan al’amari ya kai ƙololuwar bunƙasarsa, domin kuwa a zamaninsa ne ya sa aka jawo ruwa daga wurare masu matuƙar nisa zuwa ga wuraren buƙatar jama’a, waɗanda suka haɗa da masallacin Ƙurdubah.

    Kamar yadda ya yi waƙafi a fannin bunƙasa ilmi tun daga matakin koyon karatu da rubutu; har zuwa ga matakin ƙwarewa a fannonin haddar Alƙur’ani da Hadisi da Fiƙhu da sauransu.

    Hakazalika, an sami malamai da yawa waɗanda suka yi waƙafin litattafansu ga manyan cibiyoyin ilmi mai zurfi, kaɗan daga cikinsu sun haɗa da; Al Imam Abul-Ƙasim Abdul-Khaliƙ bn Abdil- Warith as-Sayuri (ya rasu a shekara ta 462 Hijiriyya) da al-Imam Kasim bn Isa bn Naji (ya rasu a shekara ta 839 Hijiriyya).

    Wani abin al’ajabi shi ne, ganin cewa yankin Andalus yanki ne mai yawan rafuka; wanda hakan yakan daƙile walwalar mutane matuƙa, sai musulmai na wancan lokaci suka yawaita yin waƙafi wajen gina gadoji. Littattafan tarihi sun ruwaito cewa gadar da ta fi kowacce girma da shahara a wancan lokaci ita ce gadar da sarki Hisham ɗan Abdur-Rahman ɗan Mu’awiya (ya rasu a shekara ta 180 hijiriyya) ya gina wacce ya kashe kuɗi matuƙa wajen gina ta.

    Kamar yadda ya ɗauki nauyin sa ido a kan aikin gina ta shi da kansa, wanda saboda da ganin haka har sai da waɗansu mutane suka fara gunagunin cewa; ya gina ta ne don amfanin kansa, a lokacin da labari ya kai gare shi, sai ya yi rantsuwa da cewa, “Ba zai yi taɓa bi ta kan wannan katafariyar gada ba, har sai idan tafiya yaƙi ko wani dalili ne ya tilasta masa yin hakan”.

    Kamar yadda kuma waɗansu daga cikin irin waɗannan gadoji sun yi ƙarƙo matuƙa; har zuwa wannan zamani namu, misali gadar da Mansur ɗan Abi Amir ya gina a shekara ta 389 Hijiriyya; wacce ya kashe mata kimanin kuɗi dinare dubu ɗari da arba’in.

    Wani abin mamaki dangane da yawaitar nau’o’in waƙafi a daular Musulunci ta Andalus; shi ne wani waƙafi da aka yi na musamman don sayen wani irin nau’i na kifi wanda ake kawowa a wani lokaci na shekara don raba shi ga matalauta; waɗanda ‘ya’yansu ƙanana na iya shiga cikin damuwa ganin yadda ‘ya’yan attajirai suke wadata da shi.

    5. Daular Uthmaniyyah

    Daular Musulunci ta Usmaniyya wacce Turkawa suka kafa, ita ce daula ta ƙarshe da ta faɗi. Ba shakka tarihin wannan daula cike yake da nau’o’i daban-daban na waƙafi; waɗanda lokaci ba zai ba mu dama mu yi bayanin su a wannnan ɗan ƙaramin littafi ba, to amma a taƙaice duk wani nau’i na waƙafi da muka ambata a baya, to su ma Turkawa ba a bar su a baya ba.

    Sannan kuma bugu da ƙari, muhimmancin da suka ba al’amarin waƙafi kai an samu cewa; akwai nau’o’i’ da dama a waƙafi da aka yi a lokacin mulkin wannan daula, kula da dabbobi marasa lafiya.

    6. Daulolin Musulunci na Nahiyar Afirka

    A haƙiƙanin gaskiya, abu ne mai matuƙar wahala a ce za a ƙididdige irin rawar da daulolin Musulunci na nahiyar Afirka; suka taka wajen bunƙasar al’ummarsu ta hanyar waƙafi. To amma hakan ba zai hana mu ɗan bayar da misalai na kaɗan daga cikinsu ba. Daga cikin mafiya muhimmancin irin waɗannan nau’o’i daban-daban na waƙafi sun haɗa da:

    Daular Musulunci ta Songhai

    An yi wani shahararren sarki na wannan daula mai suna Mansa Musa wanda ya yi gine-gine masu yawa da suka shafi na makarantu; domin bunƙasa harkar ilmi, ya gayyato tawaga ta musamman ta manyan masana a lokacin da ya je aikin Hajji da kuma gina masallatai guda biyu; na Gao da na Tumbuktu bisa taswirar da ɗaya daga cikin ƙwararru da ya zo da su a fannin gini mai suna Ishak el-Teudjin ya zana masa. Wannan masallaci ne daga baya ya zama shahararriyar jami’ar nan ta Sankore, duk a zamanin wannan sarki, a farkon ƙarni na goma sha huɗu na Miladiyya.

    Kamar yadda kuma an samo a tarihi cewa; a shekara ta 988 Miladiyya, an sami wani malami mai suna Al-Kadi Aƙib ɗan Mahmud ɗan Umar; wanda ya lashi takobin cewa; sai wannan gari na Tumbuktu ya tafi kafaɗa da kafaɗa da sauran manyan garuruwa na duniya a fagen bunƙasar ilmi mai zurfi. Domin aiwatar da wannan aniya tasa, sai ya nemi masu hannu da shuni da su taimaka da kuɗaɗe; don katafaren aikin faɗaɗa masallacin Tumbuktu da muka ambata a baya, ta yadda zai ɗauki malamai da almajirai masu yawa.

    Wani abin mamaki da ban sha’awa shi ne, sai aka sami wata mata mai dukiya; ta ɗauki nauyin gudanar da aikin ita kaɗai, a cikin dukiyarta a matsayin waƙafi.

    Daga baya wannan jami’a ta yi matuƙar shahara; har sai da ta zamo ɗaya daga cikin manyan jami’o’i na duniya a wancan lokaci; wanda har sai da yawan ɗalibanta ya kai kimanin dubu ashirin da biyar (25,000); haka nan katafaren ɗakin karatu da wannan jami’a take da shi daga littattafan da suka kama daga; dubu ɗari huɗu zuwa dubu ɗari bakwai (400,000 – 700,000). Nagartar karatunta ya zarce da yawa daga cikin manyan jami’o’in duniya na wancan lokaci.

    Dangane da al’amarin bunƙasa rayuwar al’umma kuwa, wannan daula ta bar wannan abin alfahari da dama; domin kuwa an samo cewa a lokacin wani sarki mai suna Muhammad Askiya, ya yi abubuwa a fannoni daban-daban da suka haɗa da kulawa; da jin daɗin matafiya masu keta hanyoyin sahara da suka gifta ta waccan ƙasa.

    7. Tsohuwar Daular Ghana

    Wani abin ban sha’awa dangane da ayyukan waƙafi a wannan daula shi ne; bayan Musulunci ya shiga wannan daula ba da daɗewa ba, al’umomin wannnan yanki suka fara aiwatar da abubuwa daban-daban da suka shafi; jin daɗin al’umma ta hanyar waƙafi.

    Alal misali addinin Musulunci ya shiga wannan daula ne a kashi na farko na ƙarni na ɗaya bayan Hijira; to amma sai ga shi a cikin shekaru goma da shigarsa; wato a shekara ta 60 bayan Hijira an samu cewa; yawan masallatai dake babban birnin wannan daula; waɗanda aka gina a ɓangarorin da musulmai suke; sun kai kimanin masallatai goma sha biyu; kowannen su cike yake da manyan malamai da ɗalībai a fannonin ilmi da dama.

    8. Zamanin Da Muke Ciki

    Kamar yadda muka ambata a baya cewa waƙafi wata babbar alama ce ta samuwar al’ummar musulmai a duk inda suke; ba shakka za mu iya ganin hakan har a wannan zamani da muke ciki; domin kuwa an sami mutane masu son aikin alheri da ƙungiyoyi waɗanda suka bayar da misalai ababan koyi na waƙafi. Ƙadan daga cikin waɗannnan misalai sun haɗa da:

    Tsarin Hannun Jarin Waƙafi Na Annur

    Wannan wani tsari ne da waɗansu bayin Allah suka yi. Reshen wannan gidauniya yana ƙasar Malaysia, to amma tana aiwatar da ayyukan waƙafinta a ko’ina a faɗin duniya. Ta hanyar da wannan gidauniya kuwa take gudanar da ayyukanta shi ne, ta tsattsara ayyukan da take son aiwatarwa; sannan sai ta rarraba shi a sigar hannun jari kowanne da farashinsa; wato abin nufi, iyaka yawan hannayen jarin da mutum ya saya, su ne gudunmawar da ya bayar wajen aiwatar da waɗannan ayyuka; waɗanda ake fatan ladansu zai ɗore har bayan rayuwar wanda ya bayar da taimakon.

    Wani misali na irin waɗannan ayyuka shi ne, wani tsari na juya kuɗaɗen taimakon da aka tara a cikin gidauniyar, ta hanyoyi masu sauƙin asara; idan ƙarshen shekara ta yi, sai a buga Alƙur’anai a raba da sunan wanda ya zuba jarin don yin haka kowacce shekara.

    Gidauniyar mai Martaba Muhammad Rashid Al Makhtum.

    Wanda ya kafa wannan cibiya shi ne sarkin Dubai wanda sunansa ne take ɗauke da shi. Manufar wannan cibiya shi ne, bunƙasa fannonin ilmi na Musulunci da fannonin ilmin kimiyya da fasaha; ta hanyar bayar da tallafi ga ‘ya’yan talakawa ‘yan baiwa, don su sami ilmi da horo a waɗannan fannoni. Wani abu da zai ba mai karatu sha’awa dangane da wannan gidauniya shi ne, irin maƙudan kuɗaɗe da ake ware mata; waɗanda sun kai dubunnan miliyoyi a kowacce shekara.

    Hubusin al Rajhi ɗan ƙasar Saudıyya, a inda kafin rasuwarsa ya yi wasicin dukkan dukiyarsa, a matsayin waƙafi ga talakawa da ayyukan alheri, bayan fitar da haƙƙin magada. Ubangiji Maɗaukaki kaɗai ne Ya san adadin talakawan dake rayuwa da iyalinsu cikin wannan dukiya mai albarka.

    Waƙaful Umm:

    Wannan wani sabon tsarin waƙafi ne na zamani kamar Annur na Malaysia. Da farko akan shata wata kadara mai nauyi, sannan a kasa ƙimarta zuwa ƙananan kaso na mai ƙaramin ƙarfi; don ‘ya’ya masu albarka su saya wa mahaifansu rayayyu ko marigaya. Jimillar kuɗin ita ce za a sai waccan kadara a bayar da hayar ta ga kamfanonin kasuwanci. Ribar ita za ake aiwatar da ayyukan alheri da ita. A halin yanzu wannan tsari na gudana a wasu daga ƙasashen Larabawa; Don ƙarin haske sai a duba littafinmu Jagorar ayyukan Cigaban Al’umma Mai Ɗorewa.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Nau’o’in Masu Amfani Da Waƙafi Ko Hubusi danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Gudunmowar Waƙafi/Hubusi Da Tasirinsa Wajen Gina Tattalin Arzikin Al’umma; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Yadda Ake Turaren Sikari

    Yadda Ake Turaren Sikari

    Kayan Haɗawa

    Ruwan turare (alcohol)

    Yara-yara gwangwani 1

    Sikari kwano

    Kala

    Filabo

    Madarorin Turare 5

    Yadda Ake Haɗawa

    A juye Sikari a cikin mazubi. A juye Yara-yara, a sa madarorin turare 5. Sai a sa kala, a yi ta juyawa har sai ko’ina ya haɗe jikinsa sosai.

    Shi ma wannan turare a cikin garwashi ake sawa a turara ɗaki da shi.

    A ƙarshe dai amfani da turare ya kewaye dukkan ƙasashe. Haka kuma da sauran jihohi. Ya Kuma cancanci a ce yana ciki kasafin wata-wata na kowanne mai gida. Gidanka ƙamshi Kuma jikin matarka ƙamshi. Haka zai sa wa ma’aurata natsuwa da samu gamsuwa da juna. Duba yadda ake haɗaɗɗiyar humra.

    Littattafai da aka duba:

    Taron ƙara wa juna ilmi.

    Hikimomin Kulawa da Mai gida.

    Mu Koyi Sana’a.

    7th Nuwanba, 2015,
    Gidan Mumbayya, kano.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Turaren Ɗaki Na Musamman danna nan

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Turaren Wuta Na Musamman danna nan

  • Sharuɗɗan Mai Kula Da Waƙafi

    Sharuɗɗan Mai Kula Da Waƙafi

    An sharɗanta kasancewar mai kula da waƙafi ya kasance:

    • -Ya zamo Musulmi.

    -Baligi wanda ya halatta ya yi tasarrufi a shari’ance.

    -Ya kasance mai adalci.

    -Haka kuma ya kasance yana da ilmi ko ƙarfi da zai ba shi damar tsayuwa tsayin daka wajen
    kula da shi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Dangogin Waƙafi danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Yin Sadaka A Asirce danna nan.

    Wannan baya nin an ciro shi ne daga Littafin Gudunmawar Waƙafi/Hubusi Da Tasirinsa Wajen Gina Tattalin Arzikin Al’umma; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa; shi domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Rukunan Waƙafi

    Rukunan Waƙafi

    Waƙafi yana da rukunai guda huɗu kamar haka:

    – Mai waƙafi: sharaɗin mai yin waƙafi shi ne, ya kasance mai hankali; mai cikakken mulkin abin da zai yi waƙafi da shi na dukiya ko kadara, wacce za a iya amfana da ita, ko a bayar da ita haya, a yi amfani da kuɗin hayar.

    – Waƙafi ya zamo an yi shi ne da abin da za a iya aiwatar da shi.

    – Waƙafin ya kasance an yi shi ne da abin da yake akwai shi; don ba zai yiwu mutum ya yi waƙafi da abin da yake tunanin mallaka nan gaba ba.

    – Waƙafin ya kasance na har abada.

    – Amfanin da aka sadaukar na waƙafin ya kasance zai isa ne ga wata hanya ta neman kusanci ga Allah da biyayya a gare shi. Don ba ya halatta a sadaukar da amfanin waƙafi ga wata hanya ta saɓon Allah.

    – Yin waƙafin ya kasance ta hanyar furta wata magana da take tabbatar da niyyar mai yin waƙafi, ta yin waƙafin a bayyane.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Sharuɗɗan Mai Kula Da Waƙafi danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Nau’o’in Masu Amfani Da Waƙafi Ko Hubusi danna nan.

    Wannan baya nin an ciro shi ne daga Littafin Gudunmawar Waƙafi/Hubusi Da Tasirinsa Wajen Gina Tattalin Arzikin Al’umma; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Ma’anar Waƙafi

    Ma’anar Waƙafi

    Waƙafi kamar yadda kuma ake iya kiran sa da “hubusi” ko “tasbil” ko “tahbis”; a shari’ance na nufin sallama dukiya ko kadara, sallamawa ta har abada don neman yardar Allah Maɗaukakin Sarki; ga waɗanda mai waƙafin yake son su amfana da dukiyar ko kadarar.

    Wannan ya haɗa da gina masallatai don masu yin sallah, ko makarantu ko haƙa rijiya; don amfanar jama’a ko gina gidajen marayu ko gajiyayyu da dai sauran su.

    Domin karanta cikakken bayani akan Taƙaitaccen Tarihin Waƙafi A Musulunci danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Takaiceccen Tarihin Rayuwar Dr. Yahaya Tanko danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Gudunmawar Waƙafi/Hubusi Da Tasirinsa Wajen Gina Tattalin Arzikin Al’umma; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Taƙaitaccen Tarihin Waƙafi A Musulunci

    Taƙaitaccen Tarihin Waƙafi A Musulunci

    Ba shakka addinin Musulunci ya kwaɗaitar da mabiyansa dangane da waƙafi a matsayinsa na sadaka; wacce ladan ta yake ɗorewa har bayan rayuwar wanda ya yi ta. Kamar yadda ya zo a cikin faɗin Allah Maɗaukakin Sarki; “Kuma ku tsayar da sallah kuma ku bayar da zakka kuma abin da kuka gabatar; domin kanku daga alheri za ku same shi a wurin Allah, lalle ne Allah ga abin da kuke aikatawa mai gani ne”. (Baƙara aya ta 110).

    Haka kuma ya zo a hadisin Ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana cewa; a lokacin da ɗan Adam ya rasu dukkan ayyukansa sun tsaya in ban da abubuwa guda uku; sadaka mai gudana (waƙafi), ko wani ilmi da ake amfana da shi; ko ɗa nagari da yake yi masa addu’a.

    Haka nan fassarar abin da ake nufi da sadaka mai gudana ta zo a wani hadisi da Ibn Majah ya ruwaito; wanda a cikinsa ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yake cewa; “Lalle abin da kawai zai cigaba da iske mumuni na kyawawan ayyukansa bayan mutuwarsa. Shi ne wani ilimi da ya yaɗa ko ɗa na ƙwarai da ya bari ko wani Alƙur’ani da ya bar gadonsa; ko wani masallaci da ya gina ko kuma gida da ya gina don (amfani) matafiya.

    Ko wata ƙorama da ya tona take gudana ko kuma wata sadaka da ya fitar daga cikin dukiyarsa; a lokacin da yake da lafiya sanda yake raye wacce ladanta zai ci gaba da riskarsa har bayan rayuwarsa”.

    Haka nan kuma ya zo a cikin littattafan sirah cewa; a lokacin da Ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi Hijira daga Makka ya sauka birnin Madina. A duk faɗin birnin, babu wata hanya ta samun ruwan sha mai daɗi, sai wata rijiya da ake kira rijiyar Rumah, wacce a wancan lokaci mallakar wani marowacin mutum ce; wanda yake tsawwalawa mutane wajen sayen ruwanta.

    Ganin haka sai Ma’aiki Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kwaɗaitar da sahabbansa da cewa; “Wane ne zai sayi rijiyar Rumah (ya sadaukar da ita) Allah ya biya shi da mafiticinta a gidan Aljannah wanda nan take kuwa Sayyidina Uthman ya saye ta dirhami dubu talatin da biyar, kuma Ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce da shi “Ka sadaukar da ita ga musulmai, Allah zai ba ka lada, shi kuwa bai yi wata-wata ba ya aikata hakan.

    Haka nan Bukhari da Muslim sun ruwaito daga sayyidina Umar ɗan Khaɗɗab (Radiyallahu Anhu) cewa; ya ce da ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi na sami wata gona a Khaibara; wacce ban taɓa samun wata dukiya da ta kai darajarta a tsawon rayuwata ba”.

    Sai Ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce; “Idan ka ga dama kana iya riƙe asalinta ka sadaukar da amfaninta da Sayyidina Umar. Ya ji haka sai ya sadaukar da ita bisa sharaɗin cewa, ba za a sayar da ita kanta gonar ko a kyautar da ita ko a ci gadonta ba; tare da sadaukar da duk wani amfani nata ga talakawa, da ‘yan uwa, da bayi; da hanyoyin ɗaukaka addinin Allah, da baƙi, da kuma matafiya.

    Babu laifi ga masu kula da ita su ci ‘ya’yan itatuwanta; su kuma yi kyauta ga abokansu gwargwadon yadda aka sani a al’adance ba da sayarwa ba.

    Wannan al’amari na waƙafi ya watsu matuƙa a cikin sahabban Ma’aikin Allah; tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, bayan kwaɗaitarwar da ya yi da aikata hakan. Domin kuwa sun yi waƙafi na abubuwa daban-daban da suka haɗa da masallatai da gonaki; da rijiyoyi da kayan jihadi don ɗaukaka kalmar Allah.

    Ya tabbata cewa adadi mai yawa na sahabban Ma’aikin Allah; tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi sun yi waƙafi. Kaɗan daga cikinsu sun haɗa da Khalid ɗan Walid, da Jabir ɗan Abdullah, da Sa’ad ɗan Ubadah; da Ukbat Abdullahi ɗan Zubair, da Sa’ad ɗan Abi Waƙƙas, da uwar muminai Sayyidatina A’isha; da kuma Asma’u yar Abubakar – Allah ya yarda da su gaba ɗayansu.

    Babu wani mai hali daga cikin sahabban Ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi; wanda bai yi waƙafi ba, Haka kuma an rawaito daga Imam ash-Shafi’iya na cewa; “Labari ya ishe ni cewa mutum tamanin daga cikin sahabban ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi; ‘yan Madinah kowanne a cikin su ya yi waƙafi” .

    Domin karanta cikakken bayani a kan Manufofin Waƙafi danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Nau’o’in Masu Amfani Da Waƙafi Ko Hubusi danna nan

    Wannan baya nin an ciro shi ne daga Littafin Gudunmowar Waƙafi/Hubusi Da Tasirinsa Wajen Gina Tattalin Arzikin Al’umma. Wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Manufofin Waƙafi

    Manufofin Waƙafi

    Ana yin waƙafi saboda cimma manufofin ne guda biyu, waɗanda kuma suka yi rassa masu ɗimbin yawa, waɗannnan manufofi guda biyu su ne:

    1. Manufofi na addini

    Waƙafi babbar alama ce na ƙarfin imanin wanda ya yi shi; da kwaɗayin da yake da shi na aikata alheri da kyautatawa ‘yan uwansa.

    Ta hanyar waƙafi musulmi zai samu damar riskar abubuwan da zai iya rasawa na ladan aikata alheri, bayan ya bar duniya.

    Samun ladan bin umarnin Ma’aikin Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ta hanyar aikata abin da ya yi umarni da shi; wanda wannan ba shakka manufa ce babba.

    A cikin waƙafi da mutum ya yi wa ‘yan uwansa, akwai ladan sadar da zumunci.

    Haka kuma, a cikin waƙafi akwai ladan taimako bisa aikin alheri da kyautatawa; kamar yadda Allah maɗaukakin Sarki ya yi umarni a cikin Alƙur’ani mai girma.

    2. Manufofin Kyautata Zamantakewa A Tsakanin Mutane:

    Amfanar da al’ umma tare da magance matsalolinsu ta hanyar sadaukar da wani abin amfani a gare su.

    Magance matsalar nan ta taskace dukiya a hannun waɗansu ‘yan tsirari daga cikin al’umma da faɗaɗa amfaninta.

    Magance matsalar ajiye kadara tsawon lokaci ba tare da an amfana da ita ba.

    Haka nan waƙafi hanya ce ta samar da ayyukan yi ga mutane masu yawa; waɗanda za a ɗauka aiki don yin hidima ga ayyukan waƙafin da sauransu.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Rukunan Waƙafi danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tattalin Arziki A Nijeriya danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Gudunmowar Waƙafi/Hubusi Da Tasirinsa Wajen Gina Tattalin Arzikin Al’umma; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Dangogin Waƙafi

    Dangogin Waƙafi

    Ana iya yin waƙafi a ɓangarori da dama da suka haɗa da:

    Ɓangarorin yaɗa addini da ilmantarwa:

    1. Gina masallatai da samar da abubuwan Jin daɗin masallata:

    A cikin su waɗanda suka haɗa da rijiyoyi don samun ruwan alwala da sauransu. Ba shakka musulmai magabata sun yi ƙoƙari matuƙa ta yadda suka samar da masallatai daban-daban; tare da ƙawata su da fitilu, da cika su da Alƙur’ani da shimfiɗu, tare da ɗaukar nauyin ɗawainiyar kulawa da su, da biyan albashin masu yi musu hidima; ta hanyar karantarwa da ilmantarwa da kiran sallah da sauransu.

    Kaɗan daga cikin misalan waɗannan sun haɗa da abin da masana tarihin Musulunci suka bayyana a litattafansu cewa; yawan masallatan da suke birnin Kurɗubah ta ƙasar Andalus a ƙarni nan a uku bayan Hijira (ƙarni na goma a shekarar Miladiyya) sun kai kimanin ɗari shida. Kowannen su an samar masa duk wani abu da ake buƙata don jin daɗin masu amfani da shi.

    Kamar yadda sanannen abu ne cewa har zuwa wannan zamani namu, akwai ragowar irin masallatai daɗaɗɗu; irinsu masallacin Azhar da ke birnin Alkahira da Masjid al-Amawiy dake birnin Dimashk; da Masallacin Kairawan da a halin yanzu yake Tunisiya da sauran ire-irensu a sauran wurare daban-daban a faɗin duniya.

    2. Gina makarantu da samar musu da kayan aiki:

    Ba shakka tarihin Musulunci cike yake da labarai na waƙafi a ɓangarorin gina makarantu da samar da cikakkun kayan aiki a cikinsu; waɗanda suka haɗa da wuraren kwanan ɗalibai da wuraren hutawar su da lafiyarsu da sauran su. Kaɗan daga cikin misalan waɗannan sun haɗa da abin da aka samo a littattafan tarihi cewa yawan makarantu da aka yi waƙafin su a birnin Skilliya (ƙasar Italiya a wannan a zamani namu); a ƙarni na huɗu shekarar Hijiriyya, wanda yayi daidai da ƙarni na goma sha ɗaya na Miladiyya, sun kai kimanin makarantu ɗari uku; kowacce a cikinsu cike take da ɗalibai a fannoni daban-daban na matakan karatu daban-daban, da jin daɗin na kyautatawa.

    Wannan nau’i na makarantu za a gan shi a ko ina a manyan biranen Musulunci irinsu; Makkah da Dimashƙ da Halab da birnin Ƙudus da Bagdad da Alƙahira da Istanbul da kuma sauran garuruwa.

    3. Waƙafin ɗakunan karatu da na bincike:

    A irin wannan nau’i na waƙafi za ka iske an samar da ɗakunan karatu an kuma cika su da littattafai na fannonin ilmi daban-daban; kamar yadda akan samar musu da ma’aikata ƙwararru da za su rinƙa kulawa da su da suka haɗa da kwararru a fannin fassara da rubutu da kwamiti na amintattu da dai sauransu.

    Ɓangaren kula da jin daɗin al’umma

    1. Wannan ya haɗa da gina asibitoci da wuraren shan magani:

    Haka nan tarihin Musulunci cike yake da labarai na waƙafi a fannin kulawa da lafiya; ta hanyar gina asibitoci da kulawa da ma’aikatansu da samar da cikakkun kayan aiki da bayar da kyakkyawar kulawa ga marasa lafiya. Asibiti na farko da aka gina a tarihin Musulunci shi ne wanda aka gina a zamanin halifancin Walid ɗan Abdul-Malik wanda ya keɓance shi musamman don masu fama da larurar kuturta, aka kuma ɗauki likitoci ƙwararru, aka kuma ware musu albashi.

    Bugu da ƙari kuma, hatta su kansu marasa lafiya aka yanka musu kuɗaɗen alawus na kula da su. Waɗansu daga cikin misalai na irin wannan nau’i na waƙafi sun haɗa da asibitin Mustashfa Al ‘adudiy dake birnin Bagdad; wanda aka gina ƙarni na huɗu bayan Hijira (ƙarni na goma sha ɗaya na Miladiyya); da Almustashfa Annuriy dake birnin Dimashk wanda Sultan Nuruddin ya gina a shekara ta 549 bayan Hijira da Almustashfah Almansuriy dake birnin Alƙahirah.

    Kuma wani abin ban sha’awa a nan shi ne, tun tsawon wancan lokaci, an samu waɗanda suka yi waƙafi na waɗansu asibitoci na musammman kamar ciwon ido; da na ƙashi, da na fata da cututtukan taɓin kwakwalwa, da sauransu. Kamar yadda kuma aka gina asibitoci aka kuma yi waƙafi da su musamman ga waɗansu makarantu; don amfanin malamansu da ɗalibansu da kuma na talakawa da miskinai.

    2. Gina Wurare Na Musamman Don Kulawa Da Gajiyayyu:

    Ma’anar gajiyayyu da aka ambata a nan sun haɗa da marayu da ‘yan tsintuwa da nakasassu da makafi; kai har ma da tallakawa gidajen marasa ƙarfi wajen ɗaukar nauyin aurar da ‘ya’yansu da hidimomi masu dangantaka da waɗannan.

    3. Samar Da Ruwan Sha Da wurare Kwana Ga Dukkan Masu Buƙata:

    Ba shakka addinin Musulunci ya kwaɗaitar da mabiyansa wajen sadaukar da dukiya ta hanyar waƙafi a wannan bangare; haka nan musulmi sun yi namijin ƙoƙari matuƙa wajen aiwatar da wannan umarni; kamar yadda muka gani a baya na sayen rijiya da sayyidina Uthman ya yi, ya kuma sadaukar da ita ga ɗaukacin al ‘umma.

    4. Taimakon Talakawa Da Masu Ƙaramin Ƙarfi:

    Wannan ɓangare ya shafi sadaukar da amfanin wata dukiya ko kadara ga mabuƙata; kamar yadda sayyidina Umar Allah ya yarda da shi ya yi da gonarsa dake Khaibara, kamar yadda muka gani a baya; marasa lafiya ko talakawa ko matafiya ko ɗaliban ilmi da sauransu.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Nau’o’in Masu Amfana Da Waƙafi Ko Hubusi danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tarbiyyar Addini danna koren rubutun nan.

    Wannan baya nin an ciro shi ne daga Littafin Gudunmawar Waƙafi/Hubusi Da Tasirinsa Wajen Gina Tattalin Arzikin Al’umma; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Sadarwa A Waƙar Baka

    Sadarwa A Waƙar Baka

    Bayan makaɗan baka sun gama tunanin waƙar da za su yi; sai kuma su zo, su sadar da ita ga al’umma.

    Ana sadar da waƙar baka ga Hausawa a ɗaiɗaikun gidajensu da wani wuri da suka shirya wanda ake kira dandali; wato wurin yin wasannin jama’a da a yayin farauta ko noma, musamman a lokacin gayyar noma a fadojin sarakuna, da lokacin bukukuwan al’umma da kuma taruka na makarantu da sauransu.

    A ma’ana ta lugga ko ta ƙamus, Ƙamusun Hausa (2006:380) ya bayyana kalmar sada tana nufin (i)gama (ii) isar da (iii)sulhunta. Shi kuma littafin Ƙamus na Keɓaɓɓun Kalmomi wato Hausa Metalanguage (Muhammad, 1990 UPL Ibadan:104) cewa ya yi, kalmar Sadarwa da Ingilishi tana nufin Communication.

    Shi ma Awde (1996:135) yana ganin kalmar Sadarwa tana nuni ne Communications da Ingilishi.

    Sadarwa a ilmin waƙar baka tana yin nuni ne game da wasu dabaru; waɗanda ake amfani da su wajen isar da waƙoƙin baka ga waɗanda ake yiwa su. Ana isar da waƙoƙin baka ta hanyar rera wa mutane a wasu wurare da lokuta da yanayi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Lokaci da Yanayin Sadarwa a Waƙar Baka danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yabo A Waƙoƙin Baka danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Aiwatarwa Da Sadarwa A Waƙoƙin Baka Na Hausa wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tarihin Magabata da Haihuwar Ɗanƙwairo

    Tarihin Magabata da Haihuwar Ɗanƙwairo

    Magabatan Musa Ɗanwaƙiro Maradun su ne; kakanninsa da mahaifinsa da mahaifiyarsa da yayansa da ‘ya’yansa da kuma sauran ‘yan’uwa na jininsa.

    Musa Ɗanƙwairo da magabatansa sun fito ne daga garin Ɗankadu ta cikin Gundumar Bakura ta jihar Zamfara ta yanzu.

    2.1 Usman Ɗankwanagga: Mahaifin Ɗanƙwairo

    Usman Ɗankwanagga shi ne ɗan Kaka Maiganga, kuma shi ne ya haifi Musa Ɗanƙwairo. Usman Ɗankwanagga da zuriyyarsa mutanen Ɗankadu ne da ke cikin Gundumar Bakura, kamar yadda bayanai suka gabata.

    Usmaan Ɗankwanagga manoni ne, mai jajircewa a ayyukan gona. Haka kuma makaɗi na noma ne wanda ya shahara sosai. Sannan ya gaji kiɗan noma daga mahaifinsa, Makaɗa Kaka Maiganga. Har wa yau kuma Usman Ɗankwanagga ya gwama kiɗan fada da kiɗan noma. A kiɗan fada ya kaɗa abin kiɗa na kotso ne.

    A wani ƙauli an nun a wajejen 1914 Usman Ɗankwanagga ya bar garinsa na asali; ya fita neman wani wuri da zai yi noma shi da iyalinsa. A wannan tafiya ce ya haɗu da Sarkin Maradun, Alhaji Ibrahim I (1903-1923) a wata gonarsa ta Bazamawa. A wannan haɗuwa ce Sarkin Maradun ya amince ya ɗauki nauyin Usman Ɗankwanagga da dukkan jama’arsa; shi kuma ya zama makaɗinsa. Daga nan ne Usman Ɗankwanagga ya zaɓi ya zauna Birnin Ƙaya gari mai dausayi da ƙasar noma mai albarka. Iyalin Usman Ɗankwanagga sun zauna a ƙasar Ƙaya a wani wuri da ake kira Tunga, mai yalwar ƙasar noma7.

    Bayan da Usman Ɗankwanagga ya tsufa, sai ya yi murabus; aka naɗa babban ɗansa Abdu Kurna Sarkin Kiɗan Sarkin Maradun, mai amfani da kotso.

    2.2 ‘Yarnunu: Mahaifiyar Ɗanƙwairo

    ‘Yarnunu ita ce mahaifiyar Alhaji Musa Ɗanƙwairo. Ita kuma ‘yar asalin Goran Namaye ce, Bazamfariya ce gaba da baya.

    2.3 Makaɗa Abdu kurna

    Shi makaɗa Abdu Kurna an haife shi ne a garin Ɗankadu, a cikin Gundumar Bakura; Ƙaramar Hukumar Bakura, Jihar Zamfara a yau a daidai shekara ta 1899 bisa ƙiyasi. Tare da Abdu Kurna ne Usman Ɗankwanagga ya baro Ɗankadu zuwa Tunga ta Birnin Ƙaya, Maradun. Makaɗa Abdu Kurna ya yi kiɗan noma da na masu Sarauta . Makaɗa Abdu Kurna ne ya gaji Halifar Mahaifinsa Usman Ɗankwanagga ta Sarkin Kiɗan Sarkin Muradun. An naɗa Abdu Kurna a matsayin makaɗa na Sarkin Maradun a yayin da mahaifin nasu Usman Ɗankwanagga ya tsufa; kuma ya roƙi a maye gurbinsa na sarautar kiɗa da babban ɗansa Abdu Kurna.

    2.4 Yanayin Haihuwar Musa Ɗanƙwairo (1909)

    Yanayin haihuwar Musa Ɗanƙwairo ya riski wani hali na ɓurɓushin tasirin da zai zo wa Hausawa da al’ummar Arewa na shigowar Turawan Mulkin Mallaka a ƙarƙashin jagorancin Sarauniyar Ingila. Duk da saɓanin tarihin haihuwa; an ɗauka an haifi Musa Ɗanƙwairo a 1909, jim kaɗan da tsayar da mulkin mallaka na Turawa a 1902.

    Haihuwar Musa Ɗanƙwairo ta wakana a garin Ɗankadu na gundumar Bakura a yau ta Jihar Zamfara; kafin iyayensa su koma Tunga, Birnin Ƙaya ta gundumar Maradun. An raɗa wa Ɗanƙwairo sunan yanka na Musa.

    Shi kuwa Ɗanƙwairo wata alkunya ce ake gaya wa Musa bayan da ya kai shekaru bakwai da haihuwa; kuma ya fara sa hannu a harka ta kiɗa da waƙa a ƙarƙashin mahaifinsa Makaɗa Usman Ɗankwanagga. A cikin mataimakan kiɗa na Usman Ɗankwanagga akwai wani baransa, wani mutum mai murya wasai; mai zaƙi da shiga jiki wanda ake yi wa laƙabi da Ƙwairo. To sai Musa ya gaji irin wannan murya, shi ne mahaifinsa Usman Ɗankwanagga yake faɗin; ‘Ga Ɗanƙwairo an mayas (Gusau, 1996: sh. 104). Bishiyar Nasabar Kaka da Iyayen Musa Ɗankwairo.

    Makaɗa Kaka Maiganga

    Binta Amina Usman na Ɗankwanagga
    Sa’idu Shayi
    Mairana Naruwa Ɗantomi16
    Ali Sabon Kiɗi
    Abubakar Muh Maigayya Amadu Zuwaira Lawali Umaru17
    Lawali Shamsiyya Aliyu Musa Ibrahim Nasfatu
    (a) (b) (c)

    = Karima = Yarnunu = Ba’u (Mora)
    Abdullahi
    (Yawale) Ya Rasu a Ilorin
    Abdu Kurna Hauwa Musa Ɗanƙwairo Binta (Maryam)
    Galadima Maituwo Amina “Yardaudu Ƙauna
    (Indo A’isha)
    Ambaye Amina ‘Yaddaudu (Dosara)
    Garba Sambo Mani Ige Ibrahim
    (Ɗandarali) (Zuma) Usman (Kahiyo)
    Tamaidaji20 Umaru Karɓa Iro Abdu
    (Tsahara) ɗankutuɓe Maikano
    Tashayi (Inno) Safiya (‘Yarkwando)

    15 Makaɗa Usman Ɗankwanagga ya koma sabon mazauninsa na Tunga, Birnin Ƙaya; a Gundumar Maradun tare da dukkan wannan zuriyya ta mahaifinsa Makaɗa Kaka Maiganga.

    16 Sauran ‘ya’yan Amina su ne: Mustafa da Ibrahim da Mukhtari da Talatu da Rabi da kuma Saratu.

    17 Saruan ‘ya’yan Ali Sabon Kiɗi su ne: Abubakar da Zuwaira da Rumasa’u da Lawali.

    18 Sauran ‘ya’yan Muhammadu Maigayya su ne: Amadu da Ladidi da Hamida da Nomau Libiris (Namagarya).

    19 A dubi ‘ya’yan Musa Ɗanƙwairo a 3.3.2.

    20 ‘Ya’yan Tamaidaji (Tsahara) su ne: Ta’inna (A’isha) da Muhammadu Magaji (Sarkin Gida) da Sale da Hassi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Iyalin Musa Ɗanƙwairo danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Taƙaitaccen Tarihin Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.